Showing 117001 words to 120000 words out of 180087 words
Chapter 40 - Daudar Gora Book 2 Hausa Novel Complete
fatan alkairi."
Malikat Haseenat tai shiru tana jan ajiyar zuciya, yayinda Iffah kejin kaguwa matuka da
son jin cigaba, sai dai batayi magana ba har sai da Mammah ta cigaba dan kanta bayan tasha
ruwan zam-zam dake gabanta.
"'Tafiyarmu itace mafarin kaddarar Ammarah,sannan itace mafarin yakice uwa da ga wannan zuri' ar, sannan itace mafarin yin kuka garemu
dama duk al'ummar kasar ruman, sannan itace mafarin hawan Haysam karagar mulki matsayin
madadi ga mahaifinsa. Bayan wucewarmu umarah, bisa yarjewar Jasim UWA ta sakasu yin yankan nan dai dana sa Tajwar Abdul-majeed bijire mata akansa, ta kuma basu umarnin daura auren daya daga cikin kannensu da wani bawa
ko cikin talakawan gari. Son zuciya da sanin makomar dan da ake so a samar ko ya ta
wannan hanyar suka aurar da Ammarah ga dan mai dinka kayan dokin masarautar, domin a
ranar sunzo kawo kayan kwalliyar dokuna na bikin al'ada dake tunkarowa. Babu waya a
lokacin balle ta sanar mana ko wani ya sanar mana,hasalima sunyi auren ne a sirrance sai ita
da suka dauka suka kai wa yaron bisa tirsasashi Ya kusanceta in ba hakaba zasu kashe dukkan
ahalinsa da shi kansa. Dolene ya tsorata ya aikata abinda suke bukata yana kuka itama
tanayi. Shi UBANG|JI mai hikima ne, sun taya ya kuma isar musu bisa ikonsa, badan baya son
Ammarah da wannan bawan ALLAH bane, ba kuma dan yana son nuna Uwa a saman kokarin
mu bane. A'a wannan itace kaddararsu. Kuma ALLAH ya rubuta sai an samar da wannan abun haihuwar ta wannan hanyar. Sai dai alhmallh, ina godema ALLAH da sake gode masa, dan kuwa koba komai ta hanyar biyan sadaki da sheda aure abinda ya farun ya faru. Mun dawo muka
tadda Ammarah a wani irin yanayi, dan kuwa ta birkice musu matuka, a lokacin kowa ya sake
tabbatar da iska a tare da ita. Muni kuka ni da Mahaifinsu da dan uwanta sosai, mahaifinsu
kuma ya fusata a wannan karon har ya kulle Jasim a kurkuku tare da duk wanda suka goya
masa baya akan aikata aikin, yayi kiranyen uwa amma taki zuwa, an sa malamai domin mata
kiranye nanma taki zuwa. Har takai an hada da bokaye irinta amma amsa daya suke bamu tafi
karfinsu. Hankalinmu ya tashi matuka, musamman bayan wasu watanni da ciki ya bayyana ga Ammarah, gashi lafiya taki samuwa gareta, tama koma wata iri kamar mai ciwon
hauka, ta daina magana da kowa, sai kuka,abinci ma sai an tsaya kanta take ci.ALLAH ne kawai
ya zama kariya ga wannan ciki har zuwa ranar haihuwarsa. Tajwar Abdul-majeed ya sakka
a nemo masa mijin da suka aura matan, sai dai anje ba'a dace da samunsu ba, wai sun bar asalin kauyensu a wani dare. Iya nema da bincike kuma ba'a dace ba dole aka hakura. A daren wata juma'a ALLAH ya sauki Ammarah
lafiya, sai dai tasha matukar wahala kafin ALLAH ya kawo haihuwar. Ta haifo yarinyarta mace kyakykyawa, sai dai babu ta inda take kama da ita sai tambarin tabon tawadar ALLAH da zuri'ar wannan gida ke da ita, bamu san mahaifinta ba kuma balle musan ko da shi take kamar. Mun amsheta hannu biyu, sai dai zagaye take da addu'ar neman kariyar UBANGIJI da ga sharrin uwa. A randa aka haifi yarinyar a ranar ALLAH ya
kawo wani mai magani.
Malikat Haseenat ta saki murmushi mai ciwo.Tare da fadin "kin san wani abu?" kai Iffah da ke sharar hawaye ta girgiza mata. Malikat Haseenat ta sake sakin murmushi. "Mai maganin nan hatsabilin kansa ne, dan kira daya yayma uwa a randa ya cika kwana uku a masarautar nan a take ta bayyana gabansa
gaban kowa wujiga-wujiga. Ya tabbatar mata shi ba azzalumi bane, da sai ya wahal da rayuwarta ta yanda bata isa sake numfashi a duniya ba, amma ko'a yanzu bazai kyaleta ba sai ya nakasa rayuwarta ta yanda bazata kara tunanin cutar da
Wani ba. Ya sakata ta warware duka wani tsafi data aikata zagaye damu batare da mun sani ba, sannan ya bude dukkan surukanta a gabanmu yay mata korar wulakanci da gargadi
mai tsaurin gaske. Sosai ta dinga kuka da neman gafara da tabbatar masa ta zubda
makaman yakinta bazata sake ba a barta taci gaba da rayuwa damu amma yaki saurarenta.
Majiya karfin hadimai aka saka suka kwasheta zuwa can tsakkiyar dokar jeji mai tsananin rintsi da hadari suka jefar da ita. Wannan shine mafarin barin uwa tare damu, sai dai kuma a
wannan dare ALLAH yay ma jaririyar da Ammarah ta haifa rasuwa, washe gari shima
Shahan-shan Abdul-majeed yabar duniya sakamakon bugawar zuciya da saran macijin da aka rasa tushensa, sai kuma ya kwana da tashin hankalin abubuwan da Uwa ta dinga sakasu sunayi na shirka da yanda bayan ya tsawatar wasu suka zagaye sunayi ciki harda dansa
Jasim. Abdul-majeed ya rasu, uwa ta shude,jinjirar Ammarah ta koma. Haysam ya zama
Shahan-shan. Bayan duk faruwar wadan nan abubuwa da shudewarsu zukata suka hakura
abubuwa suka fara komawa dai-dai. Saurayin nan da Ammarah ta shirya gabatar mana matsayin miji ya dawo da burin aurenta duk da ba'a boye masa komai da take ciki ba. Yace yaji
ya gani, dan ko a baya da ya janye jikinsaJasim
a samesa da gargadin karya sake zuwa an mata aure. Bayan kuma yaji an saketa dan auren kwata-kwata na sati biyu ne ya sake dawowa amma aka hana mishi ganinta ma kwata-kwata.
Ammarah taso bijirewa, dan har lokacin bata dawo dai-dai ba, amma naita lallabata da mata
nasiha ni da yar uwarta hatta hakura aka daura aure. Sai dai sam auren bai wani je ko'inaba ta
fito, sakamakon wata sabuwar kaddarar data afka mata, a duk sanda mijinta zaije gareta sai a
sauya halittar matancinta ta koma ta namiji.Dole babu yanda zaiyi ya rabu da ita ta dawo
gida, daga nan bata sake aure ba, daga nan bamu sake jin labarin uwa ba, daga nan bamu
sake jin labarin bawan ALLAHn nan da ya taimake mu ba akan Uwa ba, daga nan Jasim ya
nuna mana ya tuba, sha'anin mulkin Haysam ya cigaba da tafiya a tsaftace dan a masa
gargadin nisantar duk wan mushiriki akan al'amurin mulkinsa..
Hawaye sosai Iffah takeyi na tausayin Daneen Ammarah, da tausayin su Malikat Haseenat dan labarin nan ya matukar girgizata, al'amari haka
kamar a wasan kwaikwayo, wannan wace irin duniya ce mai cike da son zuciya. Kowa burinsa
ya kasance a sama, mai nasara bisa nasarar dan uwansa, kai kai rayuwar gidan sarauta dabance,
dabance a cikin duk wani rikicin gidaje da zuri'arsu. YaYanda Iffah ke kuka sai Malikat Haseenat ce ta koma lallashinta. Sai da ta
tabbatar ta samu nutsuwa sannan ta mikar da ita. "Hafida-ti, kinga tashi ki tafi dare yayi maybe ma mijinki nacan na jiranki".
Cikin share hawaye Iffah tace, "Ai bai san ma na taho nan ba".
Idanu sosai Mammah ta waro da fadin "Ya ALLAH, aiko kinyi laifi, maza wanko fuskarki muje na miki rakkiya to".
Bata musa ba taje ta wanko fuskar, Malikat Haseenat ta mika mata wata yar kyakykyawar
jaka tana murmushi. "Kije da wannan, duk abinda ke ciki kiyi kokarin dinga amfani da shi
kamar yanda na rubuta, ki yawaita shiga ruwan zafi har ki saba da daina jin ciwon".
Kai Iffah ta sunkuyar cike da jin kunya, sambatai tunanin Mammah din zata gane ba yau,
musamman yanda take dauriyar dai-daita tafiyarta duk da zafin da take ji……..✍️
Hummmm babu abin cewa kam yau 🥱🚴
DAUDAR GORA…..I
Book 2
Chapter: 61
Tunda suka shigo idanunsa kyam a kansu, yana zaune a falo zama na kasaita da izza da jiran ta inda zata bullo. Tun bayan dawowarsa sallar isha'i ya duba bai ganta ba. Shegen miskilanci ya hanashi tambaya har sai bayan kusan awa daya sannan ya bincika ta cctv camaras. Anan yaga fitarta harma da nufar sashen Malikat Haseenat ita kadai ko tsoro babu tattare da ita duk da darene. Yayi tsammanin zuwan bamai jimawa bane, amma sai gashi har yay wanka yaci abincin dare yay yan ayyukansa babu labarinta, harya kwanta da tunanin zai iya shareta sai hakan ya gagara, gangar jikinsa da zuciyarsa suka tabbatar masa bafa zai iya rayuwa babu mahadinsa ba. Shine ya dawo falo yay zaman jiran ganin ta inda zata bullo kusan awa daya kenan.
Gaba daya sai Iffah taji ta tsure da kallon nasa, dan haka ta koma da baya-baya ta labe a bayan Malikat Haseenat. Idanunsa ya dauke daga kanta ya maida ga Malikat Haseenat din shima. Cikin dan motsa lips dinsa ka dan ya furta, "Barka da dare Jaddah".
Amsa masa tai cike da kulawa, tare da juyawa ta kamo hanun Iffah da ke labe a bayanta ta maidota gabanta. "Ga matarka nan tane tare dani tun dazun, ALLAH ya tashemu lafiya". Daga haka ta saki hannun Iffah ta gara kekenta ta nufi Elevator.
'"ALLAH ya huta gajiya". Ya fada a hankali yana dan lumshe ido da risinar da kansa alamar girmamawa a gareta. Shiru falon bayan tafiyarta babu wanda ya sake kwakwkwaran motsi. Shi ya
zuba mata idanun nan nasa masu kaifi, ita kuwa tana tsaye a inda Malikat Haseenat ta barta kanta a kasa tana wasa da yatsun hanunta, tsigar jikinta sai yamutsawa take dan har cikin jininta takejin tasirin kallonsa a kanta. Sun kwashi mintuna masu dan tsaho a haka kafin ya mike, gabanta yaje ya tsaya, ta rumtse idanu da karfi a tunaninta saukar mari ko wani abu dai mara kyau zata ji daga garesa. A mamakinta sai jin tattausan tafin hannunsa tai a saman nata ya zare jakkar hanunta, cikin takun nan nasa daddaya cike da izza ya rabata ya wuce.Numfashin da ta rike a kirji da makoshinta ta saki da karfi, sai kuma ta bude idanunta tabi bayansa da kallo har ya bace ma ganinta. Dan tarin dake neman rike makoshinta ta fara, dole ta nufi dining room ta samu ruwa ta sha. Daga haka takai zaune tana sauke numfashi. Sai da ta dan samu nutsuwa sannan ta tashi tabi bayansa tana addu'a a ranta.
Bata da tabbacin a inda yake, dan haka kawai ta nufi inda zuciyarta ke raya mata da fatan ALLAH yasa ba'a nan din yake ba. Sai dai kuma da alama ta taki rashin sa'ar. Dan tana shiga taci karo da shi zaune a kan gado da lap-top kan cinyarsa. Dakin babu haske mai karfi, sai hasken screen din laptop dinne ya haske kyakykyawar fuskarsa ma'abociyar kamewa da
kwarjini. Sum-sum ta wuce hanyar bathroom tana dan turo baki. Sai da ta gama tsaftace kanta ta fito cikin bathrobe, yana a yanda ta barsa, hakan sai ya bata damar tsayawa ta bayansa ta shirya cikin kayan barci masu dan kauri da turarruka. A take kamshin dakin ya sake karfi. Fahimtar kamar fushi yake ya sata takowa inda yake cikin sanda, zaune takai gefensa amma ya share abinsa bai ko nuna ya san da zamanta ba. Cikin dan bata fuska da jin haushi sharetan da yay ta zame ta kwanta tare da dan ture lap-top din tasa kadan ta daura kanta a cinyarsa ta kwanta. Da kyar ya iya cigaba da rike kansa yaki kulata. Ganin ya cigaba da aikin dai ya sata kurama fuskarsa idanu, sai kuma ta kai hanunta kan kwantaccen gashin kumatunsa ta fara masa tafiyar tsutsa. (@) Yarinyar nan da tsokale-tsokalan masifa kike * ). Yayi kokarin ganin ya danne ya cije amma aikin na neman gagararsa, baima san sanda ya cije lips dinsa da rumtse idanunsa da dan karfi ba.
" ALLAH kayi hakuri bazan sake ba.ALLAH banyi zaton zan dade ba na samu Mammy batajin dadi ne fa".
(Yarinyar nan sai ta kasheni zata huta) ya fada a zuciyarsa dake faman bugawa da sauri-sauri cikin kaikawo. A hankali ya janye hannayensa dake sarrafa lap-top din ya daura na damar kan nata dake cigaba da shafa fuskarsa. Rikesa yay yana kokarin son gain ya janye amma sai tai wani irin juyi ta maida fuskarta saitin cikinsa ta sakalo dayan hanun nata a bayansa ta kankamesa.
'"Kasheni kawai ki huta" ya fada cikin subutar harshe jikinsa na saki gaba daya.
Iffah da bata fahimci ita mima yake nufin ba ta kyalkyale da siririyar dariya har yana jin dumin numfashinta a kan Fatar cikinsa. Ita a nata shirmen kankamesan da tai ne yaji zafi. "dan na kasheka dawa zan zauna?". Ta fada cikin dariyar tana kara cusa kanta jikinsa. Dole ya ajiye lap- top din ya kai kwance tare da dagota gaba dayanta ta hau saman jikinsa. Fuskarsa take kallo cike da dakewa kamar yanda shima yake kallon tata idanunsa a shanye. "Miyasa baki son a zauna lafiya?". Ya fada a hankali yana sake kankance idanunsa cikin nata. Idanun ta juya tana shagwabe fuska da dan cuna masa lips dinta. "Toni mi nayi? In dai zuwa wajen Jaddah ne ai nace kayi hakuri".
Dariya maganar ta bashi amma sai ya gimtse baiyi ba, ya dan tabe baki da tsatstsareta kaifafan idanunsa. Cikin dan dage gira
"Har na kai ki?".
"Hu'um, ni a suwa kuma, kana kallon kanka a mirror kuwa da kyau?. Badan kar ace nayi karya ba sai nace kafi kowa kyau a kasar ruman". Harga ALLAH ta bashi matukar dariya yanda ta fadi maganar cike da yarinta, yayinda zuciyar sa tai wani irin shiga farin ciki, domin kuwa bawai yafi kowa kyau din bane kamar yanda ta fada a zahirance, ya fahimci ta fara caukar karatunsa son sa ya fara shiga zuciyarta. Domin abinda kake so ne kawai kake ma kallon kasancewarsa a sama dana kowa. Shi kansa duk da yasan akwai kyawawan da suka fita ganinta yake samada kowa saboda kawai ita kadai yake so,kyawuntane kawai ke kayatar da shi. Bai fahimci murmushi yake ba sai da yaga yanda ta kura masa ido. Ya dan waro idanun waje alamar miye kuma, ita kuma sai ta girgiza masa kai tana murmushi da dan kauda idonta dake cikin nashi."Murmushi na maka kyau, gashi kuma baka son yi".
Hannayensa duk biyu ya doro a saman bayanta ya sake matso da ita ta kwanto jikinsa sosai, fuskarsu ta koma gab-gab har hancinsu na gogar na juna. "A komai k ta dabbance my sohaa".
"Kaima haka ai".
Ta fada tana dan sumbatar lips dinsa, sai tai saurin jan jikinta zata sauka dan sai da tai babban kokari wajen masa kiss din, amma kunya take ji. A hankali ya rikota bayan ya fisgo numfashinsa da ya nema kufcewa da kyar.Mirginasu yay suka koma saman hannayensu suna fuskantar juna, batare da jiran wani abu ba ya manne lips dinsu waje guda..
🥱🏃♀️Anfi karfin alkalamina anan.
Babu alamar wasa tattare da shi, da ga tsayen da yake a kofa yana dubanta a yatsine ya ce,"Kifadi abinda zaki fada ina jinki, dan bazan wuce minti ashirin ba anan".
Rai bace Ameera Haifah ke duba Miran Arshaan mai maganar, tai karamar kwafa da tabe baki," Arshaan kenan, idan kana ganin Kanada mafitar da zata iya kwabemin ne ma,dan har da kai sai dai ka shirya mu duka zata kwabe Dar harda kai, idan har ban tsira ba da ga yarda ka maida Jasim kaima zan bude maka aiki ne. Zan kuma tabbatar maka na fika iya makirci dan mace sunana idan ka manta".
"hhhhahh! Ni kike tunanin zaki iya budema aiki Haifah? to ina baki shawarar fita a hanyata da ga yau, in ba hakaba why zan kasheki na binne gawarki a cikin masarautar nan kuma na kashe banza".
"Oh really? To Dan ALLAH ko zaka gwada ne? Nace ko zaka gwada kashenin muga!!!".
Tai maganar cikin tsananin hargowa tana wani hahhankada kirji a gabansa. Wani irin tafarfasa yaji zuciyarsa nayi, dama a wuya yake, a fusace ya kaima wuyanta wani irin shegen shaka na tashin hankali. Cikin kankanin lokaci manyan idanunta suka sake yowa waje ruku-ruku, ga kakarin mutuwa da ta fara da mutsu-mutsun ganin ta fisge hannunsa da ga kan wuyanta. Sai dai kuma hakan ya gagara, dan karfinsu ba daya ba. Tafiya ya dingayi da ita cikin rufewar ido har jikin bango, ya kara matse wuyan da karfi tare da wajigata ya buga kanta jikin bango. Wata irin wahalalliyar kara ta fasa da ta jawo hankalin Jasrah dake daki kwance ta farka tana nemansa, dan su suna'a falon baki ne kasancewar cikin shigar badda kama Ameera Haifah tazo a nufin bako tasa amintaccensa imata iso saboda baya daga mata waya yanzun. Sai da yazo yaga itace. Gaba daya idon Miran Arshaan da alama ya rufe, dan tuni ya sake jijigata ya buga a bango, jini ko ya samu hanya ya balle.
lya karfi da budewar murya Jasrah ta daddage ta kwalla wata irin kara na firgita, dan ganin jini ya wanke fuskar Ameera Haifah ga Mijinta shake da wuyarta sai ta dauka ta mutu.Wani irin wancakalar da Haifah Miran Arshaan yayi yana duban Jasrah data yanke jiki ta fadi. Har rige-rigen shigowa hadiman masu tsaron sashin keyi, ganinfa abinda ke faruwa tuni wani ya firgita ya kyalla a guje ya sanarma jami' an tsaron gidan dan wannan faninsu ne...✍️
DAUDAR GORA
Book 2
Chapter: 62
...…….Tofa dan-dan-dan, da alama dama irin wannan damar Iffah ke jiran samu, dan cikin
kankanin lokaci duk da darene masarautar ta dauki dumi, yayinda aka kwashi Ameera Haifah da Jasrah zuwa asibiti, Miran Arshaan kuwa da jikinsa ke tsumar toro gaba daya ya gama
gigicewa, dan sai zuwa yanzu ya dawo a hayyacinsa. Tuni kuwa ya tsure da ganin abinda ya aikata, sai kawai ya bige da borin kunya.
Sudai jami'an babu wanda yace da shi komai,sun tattara komai akan sai zuwa da safe za'a kai
maganar ga Shahan-shan. Abu dai mafi daure kai shine miye tsakaninsa da Ameera Haifah din
har haka a irin wannan tsohon daren, dan a kala fa karfe biyu na dare kenan.
大大
A lokacin da duk ake waccan dambarwar anan ta-kurya ce ke ganawa da manomin ganyayyakin shayin Shahan-shan. A cikin badda kamarta take, dan haka shi bai san wacece ba.Hasalima magana da Jazaa sukeyinta ita dai tana hakimce komai batace ba. Da farko yaso ya, amma ganin wata lukutiyar jakkal da zinare ga barazanar halaka zuri'arsa kunne tuni ya mika wuya akan an gama. Malikat Bushirat tai murmushin basawa ta dauke kanta.Kwalayen ganyen shayin da uwa ta kawo kan ya fara kaiwa sashen Shahan-shan din kafin wanda zasu noma ya tsiro nan ma Jazaa duk ta ajiye masa su har uku..
Hummm🥱🚴
**
Zaune take bayan idar da sallar asuba, yanda ta kurama waje daya ido zai baka tabbacin tunani take. Sai lokaci zuwa lokaci da takan saki murmushi, harda cusa kanta cikin kafafunta kamar mai jin kunyar wani da