Showing 21001 words to 24000 words out of 180087 words
Ruƙuƙi ya disashe sa. Amma ta jure ta danne domin samun cikar burinta ya shafe kowanne ƙalubale da zai iya shafarta.
Boka Ruƙuƙi ya gimtse fuska bayan ya gama kwasar dariyar tamkar bashi ba. Ya ƙara juya jajayen idanunsa da ke sake fidda munin fuskarsa yana mai girgiza ƙaton kansa. “Duk ƙasar ruman babu wani boka mai ƙarasa miki aikin da uwa ta fara. Ki ɓace, ki ɓace gareni butulu inba hakaba zan ruguza duk wanda tai jajircewar gina miki. Uwa uwar kowa ce mai share kukan masu kuka, butulu ki ɓace gareni, maza ki ɓace!!!!”.
Ba ƙaramar gigitata tsawar tayi ba, tuni ta manta da matsayinta ta fito a matuƙar kiɗime har tana gware da dutsi ALLAH dai ya taimaketa kan bai fashe ba. Tana gama fitowa ta fara kwara amai, amai matuƙa tamkar zata amaryar da ƴan hanjinta. Kasancewar daji ne ga kuma dare ya tsala daga inda amintacen hadiminta ke jiranta ya dinga jiyo kakarin amanta. So yake yazo ya taimaka mata sai dai yana matuƙar jin tsoro, jin dai ta cigaba dayi yay ƙundunbalar nufarta cikin matuƙar sassarfa hannunsa ɗauke da gorar ruwa. Ƙasa ya zube duk da duhuwar da wajen ke da shi, cikin rawar jiki yake jera mata sannu da miƙa mata gorar ruwan. Amsa tai dan tana matuƙar buƙata, ta ɓalle murfin ta shiga sheƙama fuskarta batare da ta damu da yanda yake jiƙa har jikinta da tsadaddun kayanta ba. Sai da ta kusa juyesa tas kafin ta kuskure baki da sauran ta tsillar da robar tana sakin numfashi da ɗaɗɗaya. Batare da tace da hadimin ko ci kanka ba ta nufi motar da suka zo bayan ta maida norse mask ɗin fuskarta batare data bar hadimin ya ga ainahinta ba. Da gudu ya miƙe ya rigata isa, shi ya buɗe mata murfin har sai da ta shiga sannan ya nufi mazaunin driver...
Daga nesa da masarautar ya tsaya a inda suka ɗauka motar, Ta-ƙurya dake a bayan motar ta jawo dukkan kayan ɓadda kamarta ta maida a jikinta, haka shima hadimin nata sannan suka fita a motar. Kamar yanda suka fita ta ɓarauniyar hanya da taimakon hadimintan haka suka koma cikin masarautar. Ta sauke bahaguwar ajiyar zuciya lokacin da take zubewa a saman ƙawataccen gadonta. Har yanzu kanta juya mata yake, har yanzu warin da ta shaƙo ya gagara barin hancinta. Ga matsanancin tashin hankali, taya ita kam zata lallashi uwa, bayan ɓacin rai ya rufe idanunta ta faffaɗa mata maganganu marasa da ɗi. Ta ina zata fara? Matsaloli sake yawa suke a rayuwarta....
★★.... ★....
Samun lafiyar Tajwar Eshaan Ibn Haysam Abdul-majeed ta saka razanin a zukatan wasu a cikin masarautar matuƙa. Dan da gasken gaske ba haka suka so ba. Ga soyayyar mutanen ƙasa tako ina bisa ɓoyayyun alkairansa da suka gano sanadin ganin fuskar a zahirin Shahan-shan ɗin su yanzu. A yanzu kam babu inda zakaje kaji ana zaginsa sai abinda ba'a rasa ba kasancewar duniya duk masoyanka sai ka samu maƙiya, hakama duk maƙiyanka sai ka samu masoya.
Shari'ar farko da yay shirin fara gabatarwa itace kawo dai-daito tsakanin iyayensa. Sai dai kuma sam hakan yaƙi yiwuwa saboda Malikat Bushirat ta matuƙar ɗaukar zafi. Dan gaba ɗaya tana kallon Malikat Haseenat ne a mai son kanta da fifita bare sama da gudan jininta. Harzuƙar tata na hauhawa ne bisa jagorancin rura wutar da su Miran Jasim keyi ta bayan fage. Yayinda ita kuma Malikat Haseenat tai biris kamar ma bata san mike faruwa ba. Ta kuma tsaya tsayin daka wajen bama Iffah kariya da ƙara tsaurara tsaro na hana bama kowa hanyar iya cutar da ita. Al'amarin na ƙara rikitar da kowa dan an kasa gane bakin zaren takun saƙar tasu akan Iffah balle manufar kowanne.
A randa doctor ya sallami Iffah dole aka maidata kurkuku, dan rikici neman tashi yayi a zaman fada tunanin wasu haka shine take-taken Tajwar Eshaan ɗin. Shi dai komai baice musu ba har suka gama cece kucensu. Sai a washe gari ya bada umarnin tsaida ranar da za'ai zaman shari'a. Dan a zahiri ba su Miran Arshaan bane kawai ke tada jijiyar wuya kan ganin anyi shari'ar, har Malikat Bushirat zungurarsa take yi matuƙa akan al'amarin. Acewarta in har bai gurfanar da Iffah ba ita zata ɗauka duk matakin da ya dace a kanta...
★....
*21/4/2022* Rana ce data kasance na zaman shari'a tsakanin Iffah da ahalin Tajwar Eshaan akan yunƙurin halaka ɗan su. Ƴan jarida sun so halartar wannan shari'a ƙwarai da gaske, hakama jama'ar gari. Sai dai hakan bata faru ba sakamakon cewar Shahan-shan wannan shari'a ce ta cikin gida. Ba haka su Miran Jasim suka so ba, sai dai basu ce komai ba dan kar nuna zaƙewarsu yay yawa ya harbosu dan sun san hatsabibi ne. A yanzun ma suna cikin taka tsantsan ne a duk wani motsinsu.
Kasancewar shari'ar cikin gida ce kamar yanda Shahan-shan ya faɗa da kansa anyi zaman gudanar da ita ne a falonsa na biyu. Zaman ya kasance a iyakar waɗanda ya shafa, sai manyan masu faɗa aji a ɓangaren shari'a. Falon yay tsit kowa ya nutsu kawunansu a rissine duk da kasancewar duk iyayensa ne a wajen da kuma yayunsa, sai dai girman da ALLAH ya ɗaura masa na shugabancin da har suma suka kasance a ƙarƙashin sa ya tilasta musu biyayyar da girmama wannan girman koda basa so. A sannu ya ke binsu da ido ɗaya bayan ɗaya har idanunsa ya sauka a kanta ƙyam. (Miyasa kika fi yarda da zaɓa mana haka a lokacin da zaɓin ya fi rinjayen kasancewa a zaɓin wasu?) Ya ayyana a zuciyarsa cikin ɗan jansu idanunsa luuu, lumshesu yay tare da ɗan matsesu, sai kuma ya buɗe yana mai kauda kansa. Kusan tsahon mintuna biyu yaja isaka ya fesar yana mai ɗanyin gyaran murya da sake saita kansa.
A nutse Sayeed Hanifud-Din ya fara da, “Alhmdullih kamar yanda na sani kuka sani yau ranar 21/4/2022 zamu fara sauraren wannan ƙara. Muna roƙon UBANGIJI ya bada ikon kamanta zartar da hukuncin adalci wajen bama mai hakki hakkinsa batare da san zuciya ba”.
A tare aka amsa da amin har lokacin kawunansu dai a ƙasa. Ƙoƙarin hana idanunsa da ke fusga gareta yay. Sayeed Hanifud-Din ya cigaba da faɗin, Muna buƙatar sake ji da ga bakin masu ƙara. Muna fatan abinda ke a zukatansu ne zai fita a harsunansu, kuskuren hakan na nufin ɗaukar mataki takowace fuska da shari'a a ta koyar damu”.
Kawuna suka shiga gyaɗawa da ambaton (Insha ALLAHU) alamar tabbatar da abinda ya bukata ne zai tabbatan. Miran Arshaan ya sake rissinar da kansa da gyara zama na tsantsar nutsuwa da duba ladabi. “Ni sunana Miran Arshaan ibn Abdul-majeed Aliy. Zan kasance mai wakiltar ahalina dangane da guba da Zawjata-almilk ta zuba ga ɗanmu a yunƙurinta na kasheshi ranar 21/2/2022. Muna roƙon adalin shugabanmu mai albarka daya yanke mata hukunci dai-dai da laifinta dan ya zama izina ga ƴan baya. Ngd.”
Babu wanda ya motsa a falon, tsahon mintuna biyu Shahan-shan ya nisa yana mai ɗauke dubansa ga Miran Arshaan ya maida ga sauran ahalinsa. A karon farko ya motsa lips ɗinsa a hankali, “Ko masu ƙara nada sauran wani ƙarin bayanin bayan wannan?”.
Kawunansu suka shiga girgiza wa alamar a'a. Komai baice ba ya ɗauke kansa ya maida ga Iffah da tun da aka shigo da su a falon bata ɗago ta kalla kowa ba. “Ko wadda ake tuhuma tana da ja akan abinda ake tuhumarta da shi? Ko abin cewa?”.........✍️
Miran Jasim Miran Arshaan kuyi takanku aradu ba ruwana😂🏃🏻♀️🏃🏻♀️
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*
*DAUDAR GORA Billyn abdul*
*KI KULANI hafsat xoxo*
*A RUBUCE TAKE Huguma*
*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*
*IDON NERA Mamuh ghee*
_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_
_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_
_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_
_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_
_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_
_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN
MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171
SAI A TURA SHAIDAR BIYAN
09033181070
IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA
09166221261
*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63
Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.
MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (12)
.......Iffah da ke ƙoƙarin danne kukanta ta girgiza kanta alamar a'a. Idanunsa dake mata kallon ƙasa-ƙasa ya ɗauke ya maida ga Sayeed Hanifud-Din dake riƙe da takardar tuhume-tuhumen da akema Iffah. Miƙewa Sayeed.. yayi yana mai risinawar girmamawa ga Shahan-shan. Kafin ya sake gyara tsaiwarsa ya maida kan Iffah. “Ranki ya daɗe wannan kotu mai adalci na son ji daga bakinki dangane da waɗan nan laifuka da ake zargin kin aikata su. Shin kin aikata da gaske? Ko kuwa dai abin ba haka bane......”
“Ba haka bane? Kenan ma ƙazafi mukai mata bayan da bakinta ta furt.....” Jasrah ce mai maganar rai ɓace. Sai dai muƙut ta haɗiye batare da ta ƙarasa faɗar ba sakamakon kallon da Tajwar Eshaan yay mata, dan a yanzu sarkinta ne shi ba ɗan yayarta ba. Idanun nasa ya juya kan Sayeed.. alamar ya cigaba. Sayeed ya sake rissinar da kansa da ɗan rankwafawa sannan ya sake maida hankalinsa ga Iffah.
Tayi matuƙar jarumta da ƙoƙarin danne hawayen domin hanasu cigaba da zuba. Sai dai tanajin raɗaɗinsu a ƙarƙashin zuciyarta, har hucinsu na rige-rigen fita da numfashinta. Ta sani basai Jasrah tace komai ba, su dukansu zafinta sukeji, dan dukansu taga hakan a fuskokinsu, Daneen Ammarah ce mai ɗan sassauci, bakuma tada abinda za tace a kanta itakam.....
“Kotu na sauraren Zawjata-almilk”.
Sayeed Hanifud-Din ya faɗa a girmame duk da kuwa ya haifeta. Murmushin da ya bama kowa mamaki Iffah ta saki, tare da ɗago fuskarta a karo na farko yanda zata iya duban kowa. Sai dai bata aminta ta haɗa idonta da kowan ba. Tsaiwarta ta gyara idonta na kallon sashen su Miran Jasim ƙasa-ƙasa, murmushi ta sake saki a karo na biyu dan ganin yanda duk suka shiga yanayin firgici sai mazurai suke, duk da suna ƙoƙarin dannewa kuma. (Ku kwantar da hankalinku ai ba'a zo wajen ba) ta faɗa a zuciyarta tana ɗauke kanta. A zahiri kam natsuwarta ta sake tabbatarwa tana fuskantar kotu da ƙyau. “Ni Fareedah bint Zayyan zan fara da bada haƙuri kafin cewar da kowa ke buƙata da ga baki na. Nasan ko ba'a kawoni nan an gurfanar ba na can-can-ci acema bana numfashi a dalilin taɓa rayuwar mutum mai girman iko kamar Shahan-shan. Basai na wahal da Shari'a ba tabbas nice da kaina na bashi madarar da ya sha mai ɗauke da dafin macizai....”
Babu wanda bai zaro idanu ba a mutanen falon dan mamakin ƙarfin halinta. Shiko uban gayyar da furucin nata yazo masa a bazata kafeta kawai yay da idanu zuciyarsa na matuƙar mamakin ƙarfin halin takife ɗin yarinyar...
Cikin ɗan taɓe baki Iffah ta ɗage kafaɗu tamkar bataga yanayin da duk suka shigaba ta cigaba da faɗin. “Sai dai ba bashi madarar bace ya kamata ya zama abin mamaki ga wannan kotu mai adalci, sannan kuma ba itace ya dace ta zama abin tuhuma ba ko burin ganin an hukunta nin da kowa ke faman haƙilo da kai kawo sai kace kunajin tsoron numfashina barazanace gareku. Ni inda nice ku, tushen samuwar madarar zan maida hankali sani. Amma duk da haka ina so mai girma Shugabana da ku ahalinsa ku duƙufa wajen bincikowa, ba kuma dan inajin tsoro ko shakkar hukuncin da za'a min bane. Ba kuma dan zan kasa kama sunan wani bane wajen bayyana yanda akai madarar tazo hannuna ba. Ku da kanku nake son ku gano kafin ku sami dukkan amsoshin da kuke buƙata daga gareni dan ko numfashina zai tsaya sai na fesar da su ne tun daga tushe, ku kanku masu kisan Zawjata-almilk na baya sai ku shirya ranar tonon silili na tunkaro ku in har numfashina na harbawa daga gangar jikinna. Da ga ƙarshe ina roƙon wannan kotu mai adalci data sallami amintaccen hadimin shugabana tare da masu dafa masa abinci dan basu da laifin komai, su kuma masu ganin sun binne Iffah ne su shirya akwai sauran wasan dan ko filin ba'a share ba. Dan sai sun biya fansar jinin ƴan uwana uku da na iyayena koda zasu sami nasarar shafe nawa babin a doron wannan ƙasar”.
(Fitinanniyar yarinyar nan zata sa su binne ni a tsakkiyar ƙasata) ya faɗa a zuciyarsa yana mai lumshe idanunsa da ke bin lips ɗinta da kallon ƙasa-ƙasa, murmushi da ke neman suɓuce masa ya haɗiye a zahiri acan ƙasan zuciyarsa kuwa yinsa yake. Wanda bai sani ba sai ya ɗauka idanun nasa a lumshe suke, ga fuskarsa cike da barazana mai saka ruɗani ga duk wanda zai iya dubansa saboda yanda ya ɗaureta tamau.....
Kusan kowa sai da ya ɗauke numfashi a falon. Zukatansu kam na wata irin duka kamar ganguna, kalaman Iffah basu da banbanci da saukar nakiya a tsakkiyar kasuwar da bazaka iya banbance akan kanka ta fashe ba ko makwafcinka dan tsabar ruɗani. Cikin rashin yarda da kai aka shiga kallon kallo, kowa tsoron fara tankawa yake ko yin ƙwaƙwƙwaran motsin da zargi zai iya sauka a kansa. (Kun san mai kaza a aljihu fa baya jimirin asss). Malikat Ashwaq ta ɗan juya idanunta cikin ɓacin rai zatai magana da sauri Ameera Danish-Ara ta danne mata yatsun hannu tana mai haɗiyar yawu da ƙarfi. Shiru tai ta haɗiye abinda yake shirin suɓuce mata. Hakama Malikat Bushirat duk da kalaman Iffah sun daketa da ƙayatar da ita sai take jin kamar wani makircine yarinyar ke son ƙullawa domin kufcewa hukunci. Itama yunƙurawar tai zatai magana Daneen Ammarah ta girgiza mata kai da sauri.
Sayeed Hanifud-Din da gaba ɗaya shima yay mutuwar tsaye da waɗan nan kalamai na Zawjata-almilk da babu ɗar ko shakku na tsoro a idanunta duk da raunin dake tattare da yanayinta, jiki a sanyaye ya maida dubansa ga Shahan-shan. Babu alamar zaice wani abu har tsawon wasu mintuna da tashin hankalin duk wani wanda ke a falon ke sake bayyana. Sai da ya mula dan kansa yay gyaran murya. Cike da nutsuwa da ƙasaitar data zama ado ga sanyinsa ya ɗan sake dubanta da kallon da ke tada mata tsigar jiki a duk sanda ya yinsa. (Kinfa kife fuska tunda kin ɓallo min ruwa) a zahiri kam sai ya sake gyara gilashin fuskarsa kaɗan. “A bisa baƙon al'amarin da ya shigo a wannan shari'a bisa furucin wadda ake tuhuma, zamu ɗage wannan zama har zuwa nan da kwanaki uku. Za'a sake tsaurara tsaro ga wadda ake tuhuma fiye da da. Roƙon sakin wasu bai karɓu ba. Idan kuma da mai buƙatar cewa wani abu kotu na saurarensa”.
Shiru kowa ya kasa cewa komai, da alama wasu sun tsargu da tunanin cewar tasu zata iya zama talala musamman a sanin kaifin basira da sukaima Shahan-shan ɗin nasu. Hannun da yaga an ɗaga ya bi da kallo har ya sauke idanunsa kan kakar tasa, hakama duk wanda ke'a falon kallon nata yake. Malikat Haseenat ta jinjina kanta cike da dattako bayan kotu ta bata izinin maganar data nuna bukatar yi. A ladabce tai ƙasa da idanunta. “Muna godiya da wannan adalci na adalin shugabanmu, muna kuma roƙo a bisa adalcin wannan kotu ta bamu belin wadda ake tuhuma kodan kare lafiyarta da ranta da za'a iya nema a koda yaushe a dalilin furucin ta, babu yanda za'ai masu waɗan nan laifukan da ta ankarar su koma gefe su naɗe hannun zaman jiran a bankaɗosu batare da yunƙurin cuta mata ba”.
Nanma shiru kamar bazai amsa ba, bayan shuɗewar wasu mintuna kuma sai ya motsa. “Kotu ta gamsu da roƙon, sai dai bazata iya bada belin wadda ake tuhuma ba har sai an samo wani haske koda ƙanƙani ne da ga abinda ta faɗa ɗin. Za'a iya sake nema a zama na gaba”.
Daga haka ya miƙe abinsa cike da ƙasaita yana takun nan nasa na izza da bajinta. Dole kowa yay ƙasa da kansa har sai da ya fice sannan kowa ya ɗago. Iffah da ke jin ana kallonta ta ɗan ɗago kanta, ilai kuwa idanun Miran Arshaan da Miran Jasim ta gani na kallonta kamar zasu faɗo. Wani irin shegen makirin murmushi da ya nema wantsalo zukatansu waje ta saki tana mai kanne musu ido ɗaya da musu wani irin salo da yatsunta uku ta ɗauke kanta. Dan jam'ian dake tsare da ita sun zo tafiya da ita za'a maidata kurkuku.
(Wannan ƴa ta Babiy dai to sai ta sa anyi farfesunta a daular ruman 🥲🚶)
★★★......
Har karo suke da juna yayin tafiya tsabar fita a hayyaci. Da ƙyar suka iya ƙarasa kai kansu falon Miran Jasim da ya zamar musu mahaɗar tattauna matsalolin su.
“Tabbas kasheta zanyi, da hannuna kuma zan kashe matsiyaciyar yarinyar nan a yau”.
“Da hakan mizai hana kaje kace masa kai ne kawai ka bada madarar”. Miran Jasim ya faɗa cikin tsananin ɓacin rai yana wurgama Miran Arshaan da yay maganar farko harara. Shima a harzuƙe ya dubesa. “To mi kake