Showing 42001 words to 45000 words out of 180087 words

Chapter 15 - Daudar Gora Book 2 Hausa Novel Complete

yarinyar”.
           “Kona ifiritai ne wannan karon dai tasu ta ƙare. Dan haka a daren nan na yau zamu saka komai a inda ya dace kamar yanda Barbushi ya bada umarni. Dan ubansu badai sunƙi mutuwa ta sauƙi ba, to ga rayuwar yayita sai dai a cikin ƙunci da baƙin ciki da ga shi har duk wani mai iya jin zai bashi kariyar.”
    Dariya suka sheƙe da ita har da tafawa kamar wasu abokai. Kafin su miƙe cikin ɓadda kamar da suka gama shiryawa suka nufi fada yanda boka Barbushi ya basu umarni.....
 
★★... ★★....

      Kamar yanda ta saba farkawa akan lokaci domin gudanar da sallar asubahi yau ma bata makara ba. Sai dai saɓanin ko yaushe yau a firgice ta farka. Da sauri-sauri ta ke karanto addu'ar tashi da ga barci tana faman waige-waige a ɗakin mummunan mafarkin da tai a daren jiya da ya sake maimaita kansa gareta yanzu na sake dawo mata. Sosai take jin zuciyarta na tsitstsinkewa, dole taja jikinta ta maƙure kanta a fuskar gadon tana mai naɗe jikinta da son riƙe rawar da yake yi bakinta na ambaton sunan ALLAH kamar yanda kaka ya horeta da daina ihu a duk sanda tai mafarki makamantan hakan saɓanin da da take ihun. Ta ɗauka tsahon mintuna shida kafin ta ɗan samu nutsuwa. Sai ajiyar zuciya da take faman saki a jajjere. Da alama ita ɗaya ta kwana a ɗakin batare da tasan sanda ya fice ba. Hanunta ta kai saman goshinta da zuwa yanzu Alhamdullah babu matsanancin ciwon kan nan data kwanta da shi. Sai ma ɗan sanyi-sanyi da damshin zufar data haɗa ya haddasa mata. Janyewa ta sake yi tana mai lumshe idanunta, haka kawai take jinta wata daban a yau kamar ba Iffahn Babiy da Ummu ba. Ko miye dalilin jin hakan bata sani ba. Kabbara salla da aka farayi ya sata miƙewa zumbur tana ture komai gefe. Gaba ɗaya jikinta babu ƙarfi, ga mafarkin da tai ya sake nunar mata da gaɓɓan jikin baki ɗaya. Haka dai ta ɗan watsa ruwa mai ɗumi ko zai saki sannan tayo alwala ta fito. Bayan ta gabatar da salla maimakon ta koma ta kwanta sai tai zaman karatun Alkur'ani ko zata samu nauyin da zuciyarta ta mata na kwana biyu ya ɗan rage...

       ★ Saɓanin ita shi ko rintsawar ma baiyi ba gaba ɗaya. Dan tun bayan barowarsa ɗakin da take yana zaune ne gaban laptop yana aikin da shi ya barma kansa sani. Har kusan uku yana zaune kafin ya tattara ya ajiye ya ɗauro alwala. Bai tashi a sallayar ba sai lokacin asubahi da zai wuce masallaci. A maimakon Gym da ya saba shiga ko yin wasan takobi a wasu ranakun sai ya nufi sashen Malikat Bushirat ta sirrintacciyar ƙofar dake kaisa sashen batare da kowa ya gansa ba idan yaso hakan. Jin nutsatstsiyar muryarsa nayin sallama a can ƙasan maƙoshi Jasrah da Malikat Bushirat suka dubi juna a yanayin mamaki. Cikin rashin aminta da abinda suka jin Malikat Bushirat ta bada umarnin shigowa. A maimakonsa shi ɗinne kuwa. Shi kam baiyi wani mamakin ganinsu taren ba duk da a yanzu aka idar da salla, dan yasan ɗunbin shaƙuwar dake tsakaninsu ta dabance. Maimakon zama a cikin kujera a hankali ya kai zaune kusa da Malikat Bushirat dake zaune kan sallaya har yanzun. Dan tana idar da salla Jasrah ta shigo mata. Gab-gab da ita yake zaune yana mai tanƙwashe ƙafafunsa tare da ɗaura kansa a kafaɗarta. Ajiyar zuciya ya sauke a hankali yana lumshe idanunsa.
       Malikat Bushirat da ke kallonsa cike da tausayawa sanin in har ta gansa a yanayin nan yana cikin damuwa ta kai hanunta kan tattausar sumarsa yalwatacciya ta shafa a hankali. Nan ma ajiyar zuciyar ya ɗan ƙara saukewa. Kafin ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta “Barka da asuba ya Ammie-na”.
       “Ka tashi lafiya Saiful-malik”.
  Ta amsashi da kulawa tana sake tura yatsunta cikin sumar kansa a hankali. Kai kawai ya ɗan gyaɗa mata, sai kuma batare da ya dubi Jasrah da ke kallonsa ba ya ce, “Aunt good morning”. Murmushi ta saki jin yau kuma ita ake gaidawa. Itama ta amsashi da kulawa tana tasowa da ga inda take ta dawo ta ɗayan gefen Malikat Bushirat suka sakata tsakkiya ita da shi. Idanunsa ya ɗan buɗe kaɗan ya mata hararar wasa, a zahiri kam babu alamar ko murmushi a fuskarsa. Cikin fisgo maganar tasa da kamar an masa tilas yace, “Ammie kice ta tafi ta barni, ita kullum tana nane da ke tai auren ma baki huta ba”. Wani sassanyan murmushi Malikat Bushirat ta saki, dan yanda yay ɗin sai ya tuna mata da ƙuruciyarsa lokacin idan sunje dubashi harda Jasrah. Yata mita kenan Jasrah ta tafi tunda ita tana ganinta kullum har sai mahaifinsa ya shiga lallashinsa yake haƙura. Ita kanta Jasrah sai komai yake dawo mata, fuska ɗauke da murmushi tace, “Nikam babu inda zanje, sai dai kai ka koma inda ka fito ka barni da mamata”. Fuska ya ɗan kauda gefe yana sake tsuketa, amma baice komai ba. Ita kuma Jasrah ta cigaba da ɗan tsokanarsa kamar yanda takeyi a baya Malikat Bushirat na karesa tana musu dariya. Shi dai da ya fara takalo wasan bai sake ce musu ko kanzil ba.
        Bayan wasu ƴan mintuna Malikat Bushirat taci serious tana maida dukkan hankalinta kansa. Murya cike da kulawa ta ce, “Baka da lafiya ne?”. Kai ya juya mata alamar a'a. Sai kuma ya motsa lips ɗinsa kaɗan ya furta “Ina missing ɗinki ne my first luv”. Ji tai wani daɗi na ratsata, kanta na sake kumbura da alfaharin kasancewarta mahaifiya ga wannan ƙasaitaccen bajimin ƙyaƙyƙyawan sarkin. Ta sake shafa fuskarsa da kulawa matuƙa. “ALLAH yay maka albarka, ya cigaba da kulamin da kai da baka kariya”.
       “Amin”.
    Ya furta a saman lips, Jasrah kam a zahiri tana murmushi. Idanunsa ya maida kan Jasrah, fuskarsa babu alamar wasa ya furta “Mi kikeyi anan da safen nan kika bar mijinki?”.
      Murmushi ta masa ganin a serious yay maganar babu wasa a ciki. Tana ɗan wasa da yatsunta dan bazata iya kallonsa ba tai maganar dake bakinta duk da a shekaru itace sama da shi, sai dai ALLAH ya kwace girman ya bashi matsayinsa na namiji kuma sarkinta, a hankali ta ce, “Maganace mai muhimmanci ta kawoni”. Ta ƙare maganar tana ɗan ɗagowa ta dubi Malikat Bushirat. Shima kallonsa ya maida ga Ammien tasa. Malikat Bushirat ta sauke sassanyar ajiyar zuciya tana ɗan shafa kansa, “Magana ce muhimmiya Jasrah tazo da ita a kanka Saiful-malik”.
       Kaifafan idanunsa ya ɗan tsura ma Jasrahn ganin yaƙi yarda ta kallesa ya janye su ya sake maidawa ga Ammien sa. “Wani abu ya faru ne?”.
          Kai Malikat Bushirat ta girgiza masa, “Komai bai faruba, na baya ne dai da suka faru musamman akan abinda yarinyar nan ta aikata. Ba kowa ne zai fahimci irin abin da naji ba a lokacin da na fahimci zan iya rasa tilon ɗan dana mallaka a duniya. Amma sai na danne zuciyata wajen maida hankali na maka addu'ar samun lafiya fiye da ɗaukar mataki. Bani da jayayya akan hukuncinka, sai dai ƴar uwata tazo da shawarar dana gamsu da ita nima”........✍️



   
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*

𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (23)



.......Kansa dake a kafaɗarta ya ɗago a hankali jin yanda take maganar a serious, sai dai baice komai ba. Itama batare data kallesa ba ta cigaba da faɗin, “A nawa ra'ayin ka rabu da yarinyar nan, sai dai bazan tirsasaka kan hakan ba zan jira har lokacin da za'a yanke mata hukunci bisa abinda ta aikata. Amma kamar yanda Jasrah ta faɗa ya kamata ka ƙara aure. Ina son ka samu farin ciki kaima kamar kowane namiji mai irin shekarunka. Ina son naga zuri'arka Eshaan. Na kuma shirya fito-na-fito da duk mai son daƙile waɗan nan zaren farin cikin namu ta hanyar kashe yaran da basu ji ba basu gani ba dan kawai kasancewarsu matanka. Nima a wannan karon na shirya, na shirya tarar kowa Eshaan...”
    Kuka mai tsuma zuciya ya sarƙe ta. Har cikin ransa yake jin kukan nata, sai dai babu alamar zaice wani abu. Jasrah da itama ke hawayen ta miƙe a hankali zuwa gabansa, zama tai ta kamo hanunsa cikin nata cike da kulawa ta kira sunansa. Ɗagowa yay a hankali ya zuba mata idanunsa da baka isa gane yanayin da yake ciki ba koda a cikinsu. Hawayen da ke cigaba da zubo mata ta share tana ɗan kauda idanunta zuwa ƙasa, dan kaifin nasa sun mata yawa. “Kayi haƙuri ka fahimcemu Abni, muna tsananin jin zafin abubuwan da ke faruwa da gaba ɗaya sun ta'allaka da kai ne matsayinka na shugaba sama da kowa na ƙasar nan. Lokaci yayi da zamu tashi yin fito na fito da kowa a wannan gaɓar. Ba zai yiwu mu cigaba da zuba ido ba kuma. Kafin yau mun tattara hope ɗin mu gaba ɗaya kan yarinyar nan, amma daga ƙarshe itama tai shirin halaka ka ma. Shiyyasa nai tunanin ya kamata a nema maka wata matar dan nasan kai dai baka da wannan lokacin, mu kuma Insha ALLAHU zamuyi duk shirin da ya dace don ganin mun kamo bakin zaren. Fatanmu mu dai kawai amincewar ka, dan wannan al'amarin baya buƙatar cigaba da zuba idanu kuma”.
        Uffan bashi da alamar cewa, bai kuma canja da ga kallon da yake musu ba a zahiri. Suma sai duk sukai shiru, dan sun san halinsa sarai....

      ★★....

Bayan barowarsa daga sashen Malikat Bushirat ƙayataccen Gym ɗinsa mai ɗauke da nau'ikan machines na zamani ya nufa. Tuni hadimai masu tsaron wajen suka zube kan gwiyawunsu suna miƙa gaisuwa. Idanunsa kawai ya lumshe yay shigewarsa batare da yako kallesu ba. Da alama dai yau ƴan mulki ne bisa kai da miskilancin, ko kuwa maganar da yay da su Ammien tasa ne ke tsikarar masa rai oho dai. Sosai Gym ɗin ya ƙayatu ga mai kallo, dan hatta kaya motsa jikin an musu wadrube ne na musamman gasu nan iri-iri. Tattausar jallabiyar jikinsa ya cire ya ajiye, sannan ya fiddo set ɗaya na kayan ya ɗauka dogon wandon kawai ya saka. Sosai mutum ne buɗaɗɗe da baka gane hakan kai tsaye idan baya cikin riga. Cikin zafi-zafin da ke nuna kamar yana cikin fushi ya fara sarrafa machine ɗin gudun idanunsa a rufe ruf. Ya kwashe tsawon lokaci yanayi dan sai da yay sharkaf da zufa kafin ya kashe ya koma wajen ɗaga ƙananan ƙarfe irin na riƙewa a hannun nan ko kana daga zaune zaka ɗaga, duk da dai a zahiri kallon kitse akema rogo suna da matuƙar nauyi. Nan ma kusan mintuna goma sha biyar ya ajiye ya koma ɗaga ainahin ƙarfe daga kwance rigingine. Haka ya dinga caccanjawa har ya shafe tsahon awa biyu da wasu mintuna a ciki. Kafin yaja rigar wandon ya saka tare da ɗaukar goran ruwa ya kwankwaɗa yana sauke numfashi, dan shi ɗaya ke zuwa nan kawai bayan hadiman dake tsaren wajen. Ko amintaccen hadiminsa baya zuwa da shi.
        Kamar yanda aka saba ya samu shayinsa na ƙa'ida a ɗakin da ya kwana, dan masu aikin girka abincinsa sun cigaba da aikinsu tare da amintacen hadiminsa. Zaman shan shayin yay yana mai shaƙar daddaɗan kamshin da ɗakin keyi na gyaran da ya sha harya kammala. Da ga haka ya nufi bayi tsaftace jikinsa. Ya kwashe lokaci mai tsayi anan ma kafin ya fito ya shige inda kayansa suke domin shiryawa.

       Masha ALLAH na ambata lokacin da yake fitowa cikin wata irin shiga ta alfarma. Ga wani ni'imtaccen ƙamshi na musamman da ya sake gauraye ɗakin cikin ƙanƙanin lokaci. Dubansa ya kai ga agogon ɗakin yana ɗan ɓata fuska. Yana da buƙatar zuwa ya duba yaya ta kwana. Ga shi kuma ya makara, dan yanada shari'ar da zai gudanar a fada yau. Batare da ya yanke hukuncin abinda ya dace yay ba ya fito cike da takun nan nasa na izza da ƙasaita tamkar mai tafiya a saman iska tsabar yanda yake wani ɗaga ƙafafun da sauke su a nutse. Fuskar nan tsam babu alamar yama san minene yaran murmushi. Har ya nufi hanyar da zata sada shi kai tsaye da falo ya ɗan dakata, gajeren tsaki ya ja da juyowa sannu a hankali ya doshi ɗakin da Iffah ta kwana.
        Ƙamshinsa da sautin takun sawayensa da ke alamta isowarsa waje ya sata ɗan ɗago idanunta ta zubama ƙofar, sai kuma ta kauda da sauri ta cigaba da tsamar dabinon da aka zuba cikin zuma a wani ɗan farin bowl da ke a cinyarta. Kamar yanda yay sallamarsa ciki-ciki haka itama ta amsa masa can ƙasan maƙoshi batare da ta motsa da ga yanda take ba har ya iso tsakkiyar ɗakin.
    “Barka da safiya”.
Ta faɗa kanta tsaye batare da ta ɗago ta kallesa ba, duk da kuwa tana matuƙar buƙatar hakan amma ta kwaɓi kanta. Maimakon amsa gaisuwar da tai masa sai ya jeho mata tambaya a bazata yana wani shanye idanunsa da ke binta da kallon ƙurilla.
          “Kina jin wani ciwon ne a yanzu?”.
     Idanunta ta ɗago sannu a hankali ta zubasu a kansa karo na farko. Gabanta yay wata irin mummunar faɗuwa ganin exactly kayan da tai mafarki da shi dai sune a jikinsa daren jiya da asubahin yau ne dai abin kamar wani almara. Sai dai kwarjinsa da wata barazanar cikar haiba ta cika mata idanun. Babu shiri ta maida nata ta rissinar zuciyarta na wani irin bugawa da sauri-sauri. Amma a zahiri ta wani sake tsuke fuskar ne kamar yanda tashi ke'a tsuke. Kanta ta girgiza masa maimakon amsa masa da baki.
     Sosai fitinar yarinyar nan ke bashi mamaki, a fuska bazaka taɓa tunanin halayyarta ba, dan tanada suffar mutane masu sanyin hali da rashin son yawan magana ma, sai dai inta buɗe baki ko kanari albarka ya kada ita. Rigimarta ta musamman ce sama da duk ta wani rigimamme da ya sani a tsayin rayuwarsa. Lips ɗinsa ya ɗan laɓe cike da sake tsuke fuska magana can ƙasan maƙoshi a fisge ya furta, “Akwai phone a side drawer, zaki iya magana da Mammy game da abubuwan buƙatarki, idan kuma zaki online shopping ne da kanki fine. Da akwai card tare da ita” ya ƙare maganar yana ɗan matsawa ga table ɗin dake ɗauke da takardun da bata san na minene ba ya ɗauka pen. Ɗan rubutu yay a takarda ya tako har gabanta ya ajiye batare da ya sake cewa komai ba ya juya zai bar ɗakin.
      “Jazakallahu khairan”.
Ta faɗa a hankali, lumshe idanu yay batare da yace komai ba ya cigaba da tafiyarsa. Kamar wadda aka tsikara ta miƙe zumbur. Kaɗan ya rage tai tuntuɓe da lallausan carpet ɗin gaban gadon ALLAH dai ya bata sa'ar tsallakewa ta cimmasa. Yana ƙoƙarin ɗaura hannunsa kan handle ɗin ƙofar sai ganinta yay a gabansa kamar wata aljana. Mar-mar ta ɗan yi da idanunta tana motsa pink lips ɗinta a marairaice. “Indai fita ta wuce iya nan sashenka ka haƙura kar kayi Pleaseee”.
       Idanunsa ya tsura mata da wani irin kallo da ta kasa bama fassara, dole ta risinar da nata tana ɗan wasa da bazar veil ɗin abayar jikinta da tai mata matuƙar ƙyau kasancewar blue black. Itama dai tashi tai kawai ta ganta bata san daga ina ba, amma tasan dai shine ya ajiye kamar yanda ya ajiye mata jiya. Idanun ya sauke a hankali kan hanun nata fari tas da babu wani datti a ƙunbunan suma. Kamar bazai ce komai ba sai kuma ya sake maida idanunsa kan fuskarta a fisge ya furta, “Akan wane dalili?”.
      Baki ta ɗan turo kaɗan, ta ce, “Kawai”.
          “Kawai?”.
      Ya maimaita a sigar tambaya da wata irin muryar jinjina wautar ta. Kallonta ya cigaba da yi cike da nazari.. Tsintar kanta tai da jin ƙafafunta na rawa, dan idanunsa kaifafa da ya tsareta da su ji take suna sagar da ɗan sauran ƙwarin gwiwar tata. A hankali ta motsa da nufin barin wajen ya tareta da hannunsa. A marairaice ta ɗago tana dubansa kamar zata fasa kuka, sai kuma ta sake maida idanun ta risinar tana ɗan ƙara tura baki dan yaƙi daina kallon nata..
Idanun ya ɗan lumshe da sake buɗewa a kanta, a wata irin ƙaramar muryar da inba kusa da su kake bazaka taɓa sanin yana magana ba ya ce, “Kin san a gaban wa kike

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login