Showing 177001 words to 180000 words out of 180087 words

Chapter 60 - Daudar Gora Book 2 Hausa Novel Complete

Ammarah) sun zo suka kwana itama da cikinta ɗan watanni biyar da wasu kwanaki. Da alama dai zancen Babiy ya tabbata. Ita da Ummu idan ka gansu abin sha'awa kamar yaya da ƙanwa. Sai ma shirye-shiryen bikin Hanash da sukeyi dan shikam ya koma ɗan ɗakin Mamy, Iffah dai na nan ƴar gaban goshin Ummun ta kuma autarta. Dan duk ƙurarta idan ta yaya Ummu dai, itace abokiyar shawararta itace abokiyar sirrinta. Sai an gama Mammy kanji da Babiy. Iyakarsu dariya idan na dariyane. Idan na fatan alkaicine kuma suyi addu'a. Iyyani da kaka kuwa ai dama tuni sun dawo cikin masarautar. Ko yaushe zaka sami Iyyani tare da Malikat Haseenat ne da ƙanwarta Yamma. Tsaffin sun matuƙar haɗe kansu sun zama iyayen kowa. Hakama Kaka da su Sayeed Fayzul-haq sun zama aminan juna dattijan ƙwarai kuma a masarautar kuma iyayen kowa har shi kansa Shahan-shan ɗin....

        *_BAYAN WATTANI UKU DA HAIHUWAR IFFAH DA MUTUWAR MALIKAT BUSHIRAT (BIKIN AL'ADA)_*

          Kamar kowacce shekara a wannan karon ma tarin al'ummar ƙasar ruman da kewaye sun cika birnin Dahab da akafi sani da DAULAR RUMAN tako ina domin gudanar da bikin wasan al'ada. Kowa ka kalla a wannan karon yasan wasan na musamman ne sannan ana gudanar da shine cikin tsafta da nutsuwa. Duk wani wasan ganganci da za'a iya rasa rayuka an kafa masa doka, hakama matakan tsaro tako ina an baza domin kare kowa da kowa. Duk wani boka ko ɗan bori ko malamin tsubbun an hanasu yin kowane motsi a yanzu. Dama yanzu kam dokane, in har aka kamaka to hukuncin kisa kawai ake yanke maka.
     A yau kam Iffah taga mutane da yawa da suka kawoma Shahan-shan gaisuwa. Ciki harda Sir Fawzan da tuni yay aurensa. Tare da yaran Shahan-shan su Azaan da a yau kam sukaita faman sinne kai na kunyar abinda ya faru tsakaninsu da ita a shekarun baya. Ita dai murmushi ma ta dingayi, shi kansa uban gayyar Shahan-shan murmushin yaƙe yi dan kawai ba'a ganin fuskarsa ne. Su Ajwaa da Ajwaad sunsha addu'oi yau a wajen mutane. Duk da ma bawai kowa ake bamasu ba. Yaran sunyi ɓul-ɓul abinsu gwanin sha'awa. To mi yafi ransu suna samun kulawa da tattali da soyayyar iyayensu. Dan zuwa yanzu ma dai kam Iffah ta tattara inata-inata ta koma sashen Shahan-shan ɗin gaba ɗaya ita da yaranta. Dan yace shikam babu wani sashen matarsa da ban nasa daban. Idan ka ganta a sashenta sai in tayi baƙine ko yin wani abun dai tunda babu mai hurumin zuwa sashen Shahan-shan ɗin sai ita. Hatta da amintaccensa ma zuwa yanzu iyakarsa hawa na na uku ne kawai, idan ka gansa a hawan ƙarshen sai ƙwaƙwƙwaran dalili.....

          ★Alƙawarin ALLAH ya cika akan zartar da hukuncin su Miran Jasim da Miran Arshaan a yau. Dan kuwa wanda ya kashe dole ne a kasheshi. Hatta da malikat Bushirat Tajwar Eshaan ya gama yanke hukunci a yau ɗin zai zartar da hukunci a kanta irin hakan sai ALLAH kuma ya ɗauki ranta kafin zuwan yau ɗin. Sosai al'amarin ya girgiza kowa matuƙa, musamman ganin iyalan Miran Jasim ƙalilan ne a cikinsu suka koka saboda wahalar daya basu a rayuwa. Shi dama Arshaan ba'a ajiye kowa ba. Amma duk da haka Jasrah mai karyayyar zuciya sai da tai kuka. Al'ummar ƙasa sun taru wajen nema musu afuwar ƙarƙashin cigaba da zama a cikin kurkuku tsahon rayuwa. Hakan yasa duk sai jikin Tajwar Eshaan ɗin yay sanyi, dan shima yanajin ɗaci fiye da irin ɗacin da kowa ke ji kasancewar su kaɗai ne Uncle's nasa makusanta da mahaifinsa da suka rage a duniya sai mata. Ganin dai jama'a sun dage ɗin kuma harda iyalan Sayeed Khairul-Bashar da kansu dana Sayeed Hifzur-rahaman ɗin suma yasa aka maidasu cikin kurkukun a bisa sassaucin ɗaurin rai da rai. To saima dai ta ALLAH dan shi Miran Jasim ma bawani cikakkiyar lafiya ce da shi ba. Hatta Miran Arshaan ɗin kansa kawai dai a rufe rufau ne.
         Uwa kam da aka fiddo cikin sarƙa cike da ƙarfin iko kowa ke shelanta a kasheta!! A kasheta!!! A kasheta!!!. Kallonsu kawai take tana kuka da dariya da kiran sunayen gumakansu duk a lokaci ɗaya. A haka aka ɗaureta jikin ƙarfen. Mutane zasu fara jifanta da dutsina aka dakatar da su. Dan wannan aikin ba nasu bane na mai gayya da aikine da kansa tare da matarsa. Bayan lafawar kowa fiye da yanda ake buƙata Shahan-shan ya fito hannunsa na dama riƙe da na Iffah, na haggun rungume da Ajwaa da aka canjama gayu ita da Ajwaad. Da shi kuma ke a hannun Iffah. Masha ALLAH aka shiga ambata, dan a zahirinsa ya fito ga mutanensa babu wani shamaki yana son su gansa ya gansu. Haka itama Iffah duk jikinta a rufe amma fuskarta a bayyane ga al'ummar ƙasarta. Bayan sunyi gaisuwa ga al'ummar ƙasar su da fatan alkairi aka kawo kwari da baka na tsire Uwa da zasuyi. Iyyanni da Malikat Haseenat ne da ke tare da su suka amshi twins, yayinda Tajwar Eshaan ya kamo hanun Iffah a hankali cikin nasa yana kallonta ƙasa-ƙasan nan nashi ya tsayar da ita gabansa. Matsawa yay ya jingina jikinsa a nata tare da kamo duka hannayen nata biyu cikin nashi ya saka mata kwarin tare da ɗaga hannayen nasu a tare ya daidaita su sannan ya daidai mashin da zasuyi amfani da shi cikin bakar saitin manya-manyan idanun nan na uwa da ke kwasar dariya da kuka kamar sabon kamu...........✍️


   
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN

MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171

SAI A TURA SHAIDAR BIYAN

09033181070

IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA

09166221261

*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*

+227 96 09 67 63

Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA

KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.

MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.



*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*


𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲


✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)



𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻



𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (95 END)



______________



*_MAAB LUXURY HOME._* _Duniyar kayan Kitchen da decoration din gida na keta raini. Ina uwar gida da Amarya, Ku ziyarci shagon mu dake No 22 Ahmadu Bello Way, Kano state. Ko kuyi order daga shafin mu na Instagram @maabluxuryhome. Ko Facebook @maabluxuryhome. Ko Ku nememu a lambar waya *08034631010*_.

__________________


..........Wata irin mahaukaciyar razananniyar ƙara ta saki lokacin da kibiyar mashin ke sauka a cikin idonta ɗaya. Kafin ta gama dawowa cikin hayyacin azabar data shigeta suka sake soke ɗayan ma. Tuni jikinta ya shiga matsanancin karkarwa ta cigaba da ihun ambaton gumakansu. Na uku kama sai da suka saita maƙogwaronta sannan suka sakeshi. Kakari ta shigayi irin na mai fitar rai. Yayinda al'umma ke ta faman kabbara. Gaba ɗaya Iffah ta juya ta rungume Shahan-shan tsam-tsam ta fashe da kuka. Hannu biyu ya amshi abarsa ya rungume ko tuna ɗunbin mutanen dake a zagaye da su ma bayayi. Ai tuni jami'an tsaro da Ghazi dake zagaye dasu suka musu zobe, yayinda ƙatuwar umbrella ta musu runfa daga sama. Ganin wannan damar ta samu Shahan-shan ya ɗago fuskar sohaa ɗinsa ya manne lips ɗin sa a kan nata cike da ɗunbin so da ƙauna. Murmushi mai sanyi da ƙayatarwa kawai Malikat Haseenat tayi ita da Iyyani....

        Shike nan kuma an shafe da babin Uwar mushirikai itama. Wanda mutuwarta itama kuma yay dai-dai da haihuwar Daneen Ammarah ta samɓalo ƙyaƙyƙyawar ƴarta mace mai kama da babiy. Ai sai bikin al'ada ya cigaba dana murnar haihuwa, yarinya taci suna Arfah. Zo kaga farin ciki wajen Iffah Nina Arfa ɗin ta ta sake dawowa. Daneen Ammarah kuma ta cika alkawari, dan a ranar a gaban kowa ta damƙa Arfa ga Ummu. Ummu tasha kuka matuƙa Mamy na tayata. Daga ƙarshe ta dawo mata da Arfa akan ta bata shawayarwata har yaye. Babiy da Kaka dai nasu murmushi ne hakama Hanash da shima matarsa ɗauke take da ƙaramin cikin itama dan tanata fama ma da laulayi.....


        *_BAYAN WASU SHEKARU_*
        

Abubuwa da yawa sun faru, wasu masu daɗi wasu marasa daɗi. Wasu a tuna wasu baza'a ma iya tunawar ba. Haka rayuwa ta gada dama. Zuwa yanzu kam zamu iya cewa hankalin Iffah da Tajwar Eshaan ɗinta ya kwanta sosai, dan manyan matsaloli dai sun ɗan ragu musu musamman wanda suka shafi tsafe-tsafe da sauransu. Amma na maƙiya kam har goben-gobe a kwaisu. Dan duk inda bawa yake, komai ƙyautatawarsa ya sani akwai wanda su burinsu kawai cin dunduniyarsa. Ƴar uwa karki damu, kamar yanda Bily bata damuwa. Dammu masoyanmu sun wadatar damu😘. Haka dama rayuwar take dole ka kasance a zagayen abu biyu, (Masoya da maƙiya) idan ka kwantar da hankalinka duka sai su amfanar da kai. Idan har MANZON ALLAH da yafi kowa a halitta, ɗan gatan ALLAH zai fuskanci ƙalubale na maƙiya, masu hassada da kushen abinda yazo da shi daga umarnin UBANGIJI kai waye da bazaka samu kanka da irin waɗan nan mutanen zagaye da kai ba. Kai dai kawai yi abinda zaka iya, kuma ƙyautatama duk wanda ke tare da kai maƙiyi ko masoyi duk zakai alfahari da hakan wataran. Wannan shine abinda su Iffah da Tajwar Eshaan suka haƙƙaƙewa rayuwarsu da zukatansu suka zauna lafiya. Sun ajiye komai, basa ganin komai sai kansu da masoyansu. Sun fi kallon masoyansu fiye da tuna maƙiyansu, suna shimfiɗa mulki a tare cikin gaskiya da riƙon amana, randa suka sami saɓani kuma sukan binne a tsakaninsu suyi haƙuri dan yau da gobe sai ALLAH. Duk inda zo mu zauna take sai ka samu zomu saɓa.
Iffah ta ƙara haihuwar ƴarta mace taci suna *_Bilqeesa_* (Dan bazanyi a banza ba sai na ma kaina takwara a ƙasar ruman ehe🥱😂). Ajwaa da Ajwaad sun girma abinsu masha ALLAH. Yara ƙyawawa da ke samun soyayya ga mutane, wasu ko basu da wanda suka tsana kamar su a yanzu musamman ma Miran Ajwaad da kowa kema kallon magajin mahaifinsa. Sai dai kuma babu abinda suka isa yi dan tun ran gini tun ran zane.
Burin Iffah ya cika akan karatu, inda a yanzu haka ta zama cikakkiyar ƴar jarida koma muce shugabar gidan jaridar nan na *African eye* da mijinta ya kafa. A zahirance dai kamar yanda yake ɓoye kansa a baya itama haka take ɓoye kanta a yanzu. Sai dai rubuce-rubucenta da zaƙule-zaƙulen sirrikan munafukai na matuƙar tada hankalin wasu. Dan a duk lokacin da tai wani rubutu game da wata ɓarnar da akeyi koma ta fitar da muryar wasu da abin ya shafa kusan duniya ɗauka take aita cecekuce musamman da ya kasance bayan kafofin yaɗa labarai a yanzu social media ma na taka rawar gani akan yaɗa abu cikin sauri. Sai ta gama zaƙulowa da tallace mutum mijinta kuma gwarzonta ya zama gaba-gaba wajen hukunta mai laifin idan a ƙasar sa ne. Idan ba ƙasarsa bane zai yi duk yanda zai yi ga shugaban da ke shugabanta ƙasar da mai laifin ya fito dan ganin an hukuntashi, cikin ƙananan lokaci sunan da take amfani da shi yay wata irin amsa kuwa, mutane har zalamar jiran fitar wani abu da ga African eye sukeyi, dan sun san mai amfani ne kuma na gaskiya ne. Takanyi ayyukanta a gida, idan kuma fitar sirri ta kama sukanyi ita da Mijinta harma subar ƙasar batare da wani ya sani ba koda a masarautar ne kuwa.


★★...

Ƙoƙarin kamota yake tana zillewa, ya kwaɓe fuska da ɓata rai kamar gaske. Gwalo ta masa da ga inda take tana cigaba da dariyarta mai narkar da shi.
A hankali ya furta, “ALLAH Sohaa karki bari na kamaki, kizo nan na yarda zamu raba 50-50”.
Kafaɗa ta maƙe masa tana mar-mar da idanu da tura baki gaba. Fuskarta a shagwaɓe ta ce, “Naƙi wayon sai dai na baka 30 na ɗauka 70”.
“Tunda na fara jin tsoronki ko?”.
Ya faɗa cikin ɗage gira sama. Baki ta ɗan murguɗa masa itama. “To dama ai tun tuni tsorona kake ji”. Murmushi ne ya suɓuce masa, shi baima san yanda zaiyi da tsiwar yarinyar nan ba. Fitinanniyar yarinya ce ta bugawa a jarida, yara uku har yanzu bata san ta girma ba. Hannayensa ya tura cikin aljihunsa wandonsa har yanzu fuskar tasa da murmushi ya nufeta. “Okay shikenan na yarda 30-70 ɗin, sai dai yanzu yarana najin yunwa zo muje a fara cin abinci amma da sharaɗi”.
“Nami?”.
Ta tambaya tana matsawa da baya-baya. Tana ganin ya kusa isa inda take tai yunƙurin sake zurawa da gudu. Wani ɗan tsalle yayi ya cafkota, bai saurari ɗan ihun da take masa na taɓara ba ya murɗe hannun ya amshe ɗan box ɗin dake cikin hannun nata. Cak ya ɗagata ta shiga watsal-watsal da ƙafa. Dariya ya shigayi ganin yanda take kukan taɓara da faɗin ita sai ya bata abunta. Sai da ya zauna akan kujera ya ɗaurata a kan cinyarsa sannan ya dungure mata kai da faɗin, “K yarinyar nan rigimarki tayi yawa, wai nida abuna”.
Da sauri tace, “Nawa dai, dan 30 ne naka a ciki”.
“Tun kan kiji sharaɗin nawa ma kin yanke hukunci”.
“Ka faɗi sharaɗin mana banga wanda bazan iya ba”.
“Okay haka kika ce?”.
“Eh”.
Ta faɗa cike da ƙarfin gwiwa. Murmushi yayi ya ce, “Okay muje a fara cin abinci mu dawo zamu gani ai”.

★Kamar ko yanda ya faɗa yaransu na zaune a falo zaman jiran fitowarsu. Balqeesa dake tsalle-tsallenta ita kaɗai da gudu ta nufesu, a hankali ya kai duƙe fuskarsa da ƙayataccen murmushi dan a rayuwarsa yana matuƙar ƙaunar yaransa, bai haɗa su da komai ba. Hakan kuma bai hanashi tsayawa akan tarbiyyarsu ba. Mulkin al'umma kuma bai hanashi shaƙuwa da su ba, rungumeta yayi tare da miƙewa da ita a hannunsa duk da kuwa takai shekaru shida a duniya. Cikin ƴar muryarta ta ce, “Abbie ina sonka kai da Ammie”.
Idanunsa ya lumshe fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce, “Muma muna sonku mai gadon zinari na”.
Sosai yarinyar ta ƙanƙamesa tana dariyar jin daɗi. Kallon juna sukai shi da Iffah suna murmushi. Dai-dai nan Ajwaa da Ajwaad suka iso garesu suma. Yara masu nutsuwa da shiru-shiru kamar mahaifinsu. Suma hannu ya miƙa musu alamar suzo garesa. Fuskokinsu ɗauke da murmushi suka rungumesa. Baki Iffah ta zumɓira ita a dole taji haushi. Murmushi yayi itama ya mata alamar tazo. A hankali ta matso jikinsu tana murmushi ya haɗesu gaba ɗaya ya rungume........✍️



*_🥱To nima dai na haɗaku gaba ɗaya na rungume masoyan albarka ababen alfahari. Alkairin ALLAH da rahamarsa da ni'imarsa sukai gareku ku da zuri'armu baki ɗaya._*


*ALHAMDULILLAHI🙏*


_Ya rabba na gode daka kawoni wannan rana badan iyawata ba ko dabaruna. Ina roƙonka ka yafemin kurakuraina, abinda ya kasance dai-dai a cikin wannan ɗan littafi ya rabbi ka haɗamu a ladan. ALLAH ka amfanar damu amfanin cikinsa, wanda ya kasance mai cutarwa ALLAH ka hanashi tasiri a zukatanmu.🙏_


Bazan gaji da faɗa ba. Rubutun nan nishaɗine. Fadakarwa ce. Wani lokacin ma harda ban haushi. Wasu abubuwan akan saka ne kawai domin ayi nishaɗi. Ina roƙonku yin watsi da duk abinda bamai amfani ba a ciki.

_Mungode! Mungode!! Mungode masoyan Zafafa. Alkairin ALLAH ya kai gareku, yanda kuka kasance damu kuma ALLAH ya kasance daku cikin rahama da amincinsa. Yanda kuka somu domin ALLAH kuma ALLAH ya soku haka❤️❤️🙏_


*_Yanda muka fara lafiya muka kammala lafiya ALLAH ya haɗamu ana gaba cikin lafiya da nutsuwar zukata. Wanda duk naima kuskure ko ba daidai ba dan ALLAH ya yafemin a yayin wannan rubutun ajizanci ne banda burin ƙuntata kowa koda da magana ne🙏. Ngd Ngd sosai masoya ƴan DAUƊAR GORA CONVERSATION, ku ɗin na dabanne a cikin daban gareni. Alkairin ALLAH ya kasance daku a duk inda kuke. Ku na dabanne a zuciyar Bilyn Abdull 😘😘Nikam kune Sohaas ɗina TAURARINA⭐._*



*Bilyn Abdull ce 😘😘🙏*


*_ƙaunarku nake irin trillions ɗin nan🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰😘😍😘😘_*

_🙈🙈Yau sunan magena har yanzu banga kun fara kawo kayan Barka ba 😂😂 fa. Bye bye idan na mutu da ga nan kowa ya yafe min🙋🏻‍♀️🙋🏻‍♀️🙋🏻‍♀️😭🙏🏻_




   
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*

*DAUDAR GORA Billyn abdul*

*KI KULANI hafsat xoxo*

*A RUBUCE TAKE Huguma*

*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*

*IDON NERA Mamuh ghee*


_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_

_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_

_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_

_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_

_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_

_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_

_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_

ZAKU

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login