Showing 132001 words to 135000 words out of 180087 words
Chapter 45 - Daudar Gora Book 2 Hausa Novel Complete
kasaitar nan tasa da magana a fisge yake sanar masa. "Ayi musu komai da ya dace, nan da kwanaki biyar bayan anyi salla sai ku biyo bayanmu, dan ina son ku iso ne randa zamu koma zaman shari'ar".
"Umarninka da cikawa shine abin jiranmu Insha ALLAHU"
Iya abinda Iffah kenan ta iya ji ta shige. Lokacin da ya shigo dakin zai shirya tata fatan ya shigo da file din amma sai ya shigo babu komai. Kuma bai mata maganar ba. Amma koda suka kammala shirinsu suka fito Sultan da kansa yau ma da yayansa maza biyu da uwargidansa sukai musu rakkiya har airport Iffah harda kwallarta hakama Uwargidan Sultan abinka da sabon mata bayan shigarsu jirgi sun zauna tana a jikinsa yana lallashinta sai ga file din nan ajiye a gefensa. Ta danyi mamaki amma sai ta basar, sai dai zuciyarta na sake tabbatar mata da koma akan wa file din ya kunsa yanada matukar muhimmanci ga mijin nata. Jirginsu na dagawa babu dadewa barci ya kwasheta…...
* KASAR RUMAN
Duk da saukar dare sukai tako ina a airport din zagaye yake da matakan tsaro. Kai da gani kasan mai kasar ruman dinne da kansa zai sauka. Ta bangaren masu tarbarsu kuwa manyan masarautar ne masu fada aji. Ga wasu lafiyayyun motoci ababen birgewa ga mai kallo. Sosa barcine a idon Iffah dan yanzu kam bata da aikin da yafi wannan. Hakan yasa ta kasance a kusan rabin jikinsa lokacin da suke fitowa, Dole duk wanda ke wajen yay kasa da kansa cikin jin nauyi. Shika gogan nasu ko'a kwallar rigarsa rungume yake da ita hankali kwance yana daga musu hannu daya alamar amsa gaisuwarsu har zuwa motar da aka ajiye domin su kawai. Sai da suka shiga har aka rufe sannan hadiman da sukal masu rakkiya ke fitowa a jirgi suma. A wannan tawaga musamman ta matan Diwa ce kawai zuciyarta ke a tsarkakake game da nado labari, amma sauran duk yan daukar rahoto ne. Sai dai kuma basu samo yanda suke so ba sam kasancewar su/Iffah'r sun musu wahalar ma gani ba kamar yanda su Uwa sukai tunani ba.
Tun daga airport har cikin masarauta jami'an tsaro ne, a cikin masarautar ma tarba suka samu da taima Iffah dadi, dan harda Malikat Haseenat da Daneen Ammarah da kanta. Sal wata da Iffahr bata sani ba amma suna kama da Daneen Ammarah sosai kuma tana kama da Jaddah. Haka kawai taji a ranta itace Daneen Waheeda da aketa fada. Lokacin da take dagowa da ga rungumar da taima Malikat Haseenat zata rungume Daneen Ammarah idanunta suka sauka kan wata kyakykyawar farar budurwa sol tana balla mata harara. Bata santa ba, dan haka ta dauke idanunta ta maida hankali ya Daneen Ammarah din cikin rashin damuwa. A hankali ta saketa ta nufi Daneen Waheeda da ke tsaye tana kallonsu kusa da Malikat Ashwaq fuskarta babu yabo babu fallasa. Gabanta ta rissina ta gaisheta tare da Malikat Ashwag din. Amsa mata tai da dan murmushin yake sakamakon kallon da Malikat Haseenat ta watso mata. Sai kuma ta nufi Malikat Bushirat ta rungume, itama dai gain kallon da ake musu ne yasata shafa kanta tana yake, Jasrah kam saita boye bayan Malikat Bushirat din dan da gaske kunyar Iffah take ji. Murmushi Iffah tai itama ta rungumeta, dan koba komai kafin faruwar hakan al ta nuna mata soyayya ta gaskiya..
Tuni shi Tajwar Eshaan ya shige ciki, dan haka itama Malikat Haseenat ta kama hanunta tana facin,"Kinga zomuje kema ki huta kunyi buda baki a jirgi babu nutsuwa". Da ga haka ta nufi ainahin sashenta da ita dan an sake masa gyara na musamman. Bayan wucewarsu abubuwa da yawa sun faru a cikin masarautar, ciki hard jajircewar Malikat Bushirat akan komawar Iffah sashenta. A zahirance dai babu wanda ya kawo komai a ransa game da hakan, sai Malikat Haseenat ce ma take gain Malikat Bushirat din na son hakanne da tunanin Iffah ta kanainaye mata Eshaan, ta kuma san sai dai Bushirat din tayi ta gama Iffah da Tajwar Eshaan sun riga sun gama zama abu daya. Ga tabbaci nan ma a yau ta sake gani, dan duk mai hankali da zai kalli Iffah'r a yau yasan tana tare da juna biyu. Komai nata ya canja, ga kyau data kara da budewa. Yanzun ma Malikat Bushirat na gain sun nufi can ta saki wani lafiyayyen murmushi tana fadin, (yes) a zuciyarta alamar akwai abinda suka kulla a sashen kenan.
Ko dar Iffah bataji da komawarta sashenta ba. Sai ma farin ciki data tsinta kanta a ciki. Ga hadimanta duk an dawo mata da abinta, a ganinta ma ita wannan wata dama ce da zatai yakinta da kyau a yanzun. Wanka ta farayi bakinta dauke da addu'a, kasancewar duk tayi sallolinta tun a jirgi shirin kwanciya kawai tai ta haye gado abinta sai ko barci.
Cikin barci take jin kamshinsa na sake shige mata hanci, a zatonta mafarki take, sai tai kokarin yin juyi abunta. Jinta jikin mutum a gaske ya sata bude idanunta da kyar. Akan kyakykyawar fuskarsa ta sauke idanun nata. Tashi tai a dan zabure ya rikota, maidata yay ya kwantar yana mai tura yatsunsa cikin gashin kanta, sai kuma ya matso da fuskarsa saitin tata ya daura goshinsa kan nata hancinsu na gogar juna.
"Yaushe kazo?"
Ta fada cikin muryar barci. Shiru kamar bazaice komai ba, sai da ya mula dan kansa sannan. "Dama zaki iya barci babu ni a tare da ke?". Kankamesa ta sakeyi tana sakin ajiyar zuciya, itama a hankalin ta furta, "Kawai dan banda yanda zanyi ne".
"Toni gani nayi yanda zanyi ai".
Ya bata amsa yana sake matseta cikin jikinsa kai kace amshe masa ita za'ai. Luf ta kwanta kuwa suna sauke ajiyar zuciya a tare. Sai kuma ya hade bakinsu a hankali. Da ga haka labarin ya sauya salo...
Karfe uku nayi ya gudu, sai farkawa tai taga babu shi a dakin. Murmushi kawai tayi ta tashi zuwa bayi tai brush da tsaftace jininta ta fito. Madara mai dumi kawal tasha matsayin sahur. Duk da barcin dake cin idanun nata sai bata kwanta ba tayo alwala ta danyi nafilfili da karatun Alkur'ani. Bata tashi a wajen ba sai da tai sallar asuba, Tana idarwa kwanciyar ta sake yi, bata tashl ba sal azhar. Tayi mamakin barcin da tayi, amma kuma sanin yanayin da take ciki da rashin isasshen barcin da bata samu a Saudiya ba yasa ta fahirci akwai ramuwa dole dama.
Tsaf tai shirinta cikin kyakykyawar abaya kamar ka sace ta ka gudu. Dama ga ko'ina ya sake fita da fitar kwarjini da kyawun haiba na ciki. Cike da girmamawa a gareta hadimanta ke zubewa Rasa gaisheta lokacin data fito. Nuni tai musu da su tashi, cikin sanyin da ciki ya haifar mata yanzu ta basu izinin mata rakkiya zuwa sashen Malikat Haseenat da ga nan su wuce na Malikat Bushirat. Da girmamawa suka arsa mata tai gaba suna take mata baya. Duk da akwal tazara a tsakaninsu bata shiga motar da aka ajiye domin ta ba tunda ta fito, A kafa ta taka hadimanta na take mata baya. Dolene ta birgeka, dan yanda ta fito da kafan ma sal ta kara kima a idanun hadiman. Ta ko'ina kuwa ta gitta hadiman ne ke zubewa mika gaisuwa, hannu kawal take daga musu fuskarta da dan murmushi dan sam bata daureta ba. Yayinda Amintacciyar hadimarta ke amsa musu da baki ita kuma.
Tun kan shigowarta aka sanar da Malikat Haseenat da ke zaune Daneen Ammarah da Daneen Waheeda tare da ita. Sai Iftihal diyar Daneen Waheeda dake zaune a can gefe tana latse-latse a laptop. A nutse ta shigo bakinta dauke da sallama. Dan haka suka dago a tare. Sai dai kuma a hankali Iftihal taja sirrin tsaki da maida kanta ta cigaba da abinda take yi. Babu wanda ya jita, sai dai Iffah kam taga kallon da tai mata sarai. Amma tai kamar ma ita bata ganta ba ta nufi Malikat Haseenat da ta bude mata hannu fuska duke da murmushi alamar tazo gareta. Ita din ta nufa cike da kunya, ta durkusa a gabanta tana murmushi da gaisheta. Cikin murmushi Malikat Haseenat ta ce, "A'a kinga Hafidah tashi ki zauna keda ke fama da kanki, ALLAH dai ya raba lafiya".
Sosai kirjin Daneen Waheeda ya buga, yayinda Daneen Ammarah ke murmushi kawai tana bin Iffah'r da kalion kasan ido, Bayan ta gaishe da su duk cikin girmamawa Daneen Ammarah ta nuna mata Daneen Waheeda. "Ga wata maman taki nan tazo kuna Saudiyya, nasan kin san dai sunanta da labarinta tun kafin yau". Fuskar Iffah cike da murmushi ta jinjina mata kai. Kafin ta kara gaishe da Daneen Waheeda din da zancen cikin nan va sata sumar zaune, cikin murmushin yake ta kai hanunta kan Iffah'r ta shafa. Daneen Ammarah ta sake waiwayawa ta nuna mata Iftihal da tai kamar ma bata san mi ake ba "Wannan yar uwarki ce ita kuma, sunanta Iftihal, itace first born a wajen mamanki. Tanada kanne maza har uku".
Murmushi kawai Iffah tai sai dai batace komai ba kamar anda itama Iftihal din ko dagowa batai ba. Yanda tai din kuma sai ya zafi Daneen Ammarah. Ita kanta malikat Haseenat dai tayi shiru ne amma fuskarta ta nuna jin zafin abinda Iftihal din tayi. Ita kam Iffah ko'a kwalar rigarta, hankalinta kwance suka cigaba da hirarsu da Daneen Ammarah da Jaddah...✍️
DAUDAR GORA
Book 2
70
....Sai da tai sallar la'asar a sashen Malikat Haseenat sannan ta baro, fuskarta dauke da murmushin abinda take kullama Iftihal. Dan ta dau alwashin sai tayi dana sanin zamanta a masarautar nan duk da gidan kakanninta ne. Da ga nan sashen Malikat Bushirat ta nufa, sai dai ta samu wai bata nan tana a sashen Shahan-shan. Hakan bai bata mamaki ba, ba kuma ta nuna ya dameta ba ta koma sashenta ita da tawagarta. Sai kusan karfe biyar ta nufi sashen Tajwar Eshaan..
***
A lokacin da Iffah ke nufar sashensa a lokacin shi kuma yake fita ta kofar sirrinsa zuwa sashen Malikat Haseenat. Cikin sa'a kuwa ya sameta ita daya a dakin. Kyawawan idanunta na tsufa ta zuba masa har ya kammala sakama kofar key ya cigaba da takowa gareta a nutse. A hankali ya kai zaune gabanta ya tankwashe kafafunsa.
"Barka da yamma Jaddah".
Ya tada a kan lips a dan fisge kamar baya so.Murmushin ta sakar masa cikin yar tsokana ta amsa da "Barkan ka dai Abbien unborn". Idanunsa ya dan waro mata na alamar mamaki, sai dai kuma bai iya cewa komai ba dan yama rasa bin fadar. Dariya Malikat Haseenat tayi mai kayatarwa, tace, "Ni dai bana fata ko mace ko namiji da za'a haifa su gado min wanna miskilancin naka Hafidi. Ace magana a bakin mutum amma furta ta ta zama aiki", Kasa ya dan yi da kansa kawai yana murmushi. Kafin cikin son kauda maganar ya ce, "Amm Jaddah! Kamar yanda kika bada shawara nayi amfani da ita. Ani musu gwaji ta wasu abubuwan hallitar jikinsu kamar gashi da yawu jini batare ma da sun san duk muni hakan ba. Ita na bada nata, Sayeed Tasadduq-Husain kuma ya samomin na iyayen nata dan kamar yanda na fada miki dama tunda na saka a kaudasu a kasar shine yay aikin kuma shi kadai suka sani ya kuma san inda suke a yanzu haka ma".
Cike da zumudi Mammah tace, "Ya ake ciki? Mi result din ya nuna kuma?"
Sai da ya dan ja iska kusan minti daya kafin ya nisa. "Al'amarin gaskiya yazo da rudani zance ne koba haka ba oho. Result din sun nuna shi Mahaifinta ne,amma macen ba itace ta haifeta ba".
"What! Kamar yaya kenan?".
"Shine na kasa fahimta why Jaddah. Tun a Saudiyya a rikice lissafina yake. A daidaiton kwanakin watan haihuwarta da na yarinyar Mamy dake rubuce kwana uku ne, sannan tambarin da ke nan a ajiye iri dayane da na jikinta, ita waccan ta mutu a randa aka haifi ita Fhareedahn. Sai nake ji kamar akwai abinda ya kamata mu sani, amma idan na auna yiwuwarsa ni a karan kaina sai naji abin yazo ba daidai ba".
"Kai mi kake tunani akan hakan?".
Nan ma sai da yay jima kafin ya bata amsa. "Itama Mammy a mata gwajin halitta tare da ita. Kinga muma sai mu samu nutsuwar yarda ba ita bace, ko itance. To amma ya akai ta samu tambarin zuri'armu bayan mahaifinta bashi da alaka da wanna masarautar? Sosai nakejin kaina a rikice a duka abinda nake tunani da fatan ya tabbata".
"Tabbas al'amarin akwai rudanin, rudanin kuma suna da yawa, dan inhar babu alaka tsakanin wannan yarinya da Arnmarah to tabbas tana da alaka da wani a wannan masarautar kuma dole ne mu sani. Sai dai dabi'un yarinyar na rikita mun lissafi Eshaan. Dan babu abinda ya banbanta da na Ammarah tana a irin shekarunta. Sai dai ni nasan diyar Ammarah ta rasu tunda da hannuna na mata wanka da hadata aka kuma kai ta aka bizne".
"Kamar yanda na fada miki Jaddah akwai abinda ke boye. Dan da gaske yarinyar nan akwai aljanu a kanta wilhy. Naga alamominsu da yawa tattare da ita, dan a wan lokacin ita kanta aljanar ma nake kallonta".
Dan murmushin karfin hali Malikat Haseenat tayi, amma a ranta fal yake da rudani... Sun cigaba da tattaunawa har zuwa gabanin magriba sannan ya baro sashen domin zuwa yay shirin massalaci…..
A bangaren Iffah kam data nufi sashensa kai tsaye kitchen ta nufa, inda masu kula da abincinsa ke ta kaikawon lissafin abinda zasu shirya masa na buda baki. Tana shigowa duk suka zube kasa suna kwasar gaisuwa. Hannu kawai ta daga musu, kafin tai zaran bibiyar duk abinda suke shirin yin da kallo. Duk lissafinsu sal da ta wargaza ta shimfida nata, karshe ma ita ta koma shirya abincin da taimakonsu. Wannan al'amari ya matukar basu mamaki kam, dan ko'a tarihin masarautar basu taba jin a inda wata Zawjata- almilk ta shiga kitchen girka abinci ba koda na Shahan-shan ne kuwa. Sai gashi a yau Itfah ta ajye tarihin,
A matukar gajiye suka kammala aikin, tayi tibis da ita saboda a yanayin da take, duk da dama cikin nata nada saukin laulayi da tsurfan abinci. Sannan ita dai bazatace ga wani waje na mata ciwo ba mai jigatarwa. A dining room din ma tana tsaye suka shirya komai, aka kara turaren wuta ko ina ya dauka harami. Bayan duk wucewarsu bedroom nashi ta nufa, ta dinga binsu daya bayan daya tana lekawa har sai da ta shiga a inda ya kwana. Kamar ko yanda tai hasashe ba'a gyarashi ba, tunda ita da kanta ta hutar da amintaccensa tun kan su wuce. Duk da yanda take jin kanta haka tai dauriyar gyarawa, sannan ta shiga toilet din tayo wanka shima bayan ta tsaftacesa Bata da matsalar kaya anan kam tunda tasan tabarsu tunkan su tafi ba, tako shirya cikin wandon jeans 3quater blue da karama roga mara nauyi fara tas, sai hoton heart da akayi babba a gaban rigar. Kayan sun mata kyau. Tana barbaza gashinta da haushi na rashin son a taba mata shi ya shigo dakin da sallama. Dan turus yayi yana kallonta irin na rashin tsammani. Dan a yanzu haka da yake shigowarnan da ita a ransa ya shigo, kewarta yake ji sosai, dan duk yau bai ganta ba, rabonsa da ita tun daren jiya da ya kai mata ziyarar sirri sashenta.
A hankali ya cigaba da takawa cikin dakin yaje gabanta ya tsaya. Jitai kawai an tura mata yatsu cikin gashi. A firgice ta dago dan ko kadan bayaji motsin shigowar tasa ba. Cikin juna idanunsu suka shige, kowanne cike da kewar dan uwansa kamar sun hada watanni basu hadu ba. Itace ta fara janye nata a slowlv. kamar mai in kunvarsa ta maida kanta kasa ta dukar. Numfashi ya dan furzar kadan, tare da dukowa
ya zare ribbon din hanunta ya saka cikin tsintsiyar nasa hannun kamar maisa bangles, sai kuma ya maida duk hannayen biyu saman kanta ya tattaro gashin a tsakkiya ya dare mata.
"Thanks you".
Ta fada cikin siririyar muryarta da ke ratsa masa jiki, yasan tsaiwarsa a wajen bazata hafar masa da da mai ido ba. Dan haka ya rabata ya wuce cikin tafiyar tasan nan daddaya dan azuminsa ya isa lafiya. Da kallo ta bisa har ya shige bayi, sai kuma ta saki sassanyar ajiyar zuciya ta mike. Closet dinsa ta nufa kasancewar akwai finger print dinta yanzu akai itama. Lallausar jallabiya kalar maroon ta zaba masa, tare da alkyabba irin ta sarakan saudiyya. Fitowarta dal-dai da tashi. Kallo daya ta masa ta dauke kai dan har yanzu ta kasa sakewa da kalion wanna jikin nasa. Kanta a kasa ta karaso gabansa, karamin towel da ke hannunsa ta amsa, babu musu ya sakar mata, sai da ta lumshe idanunta sannan ta fara tsane masa jikin. Dan garetan murmushi ya saki idanunsa kan kyakykyawar fuskarta harta kammala. Man da yake amfani da shi ta ajiye zata gudu ya rikota a slowly yaNmaidota baya. Sai da ya gama kare mata kallo da gaNsama har kasa sannan ya dire kan fuskarta da idanun ke lumshe. A can kasan makoshi ya furta, "Shi man wazai shafa?". Batare data bude idon ba ta ce, "Ka tayani".
"Naki wayon".
Ya bata amsa yana maidota gabansa da kyau. Dan murmushi tai zatai magana ya ce mata, "Shilli!!!" Shiru tai ta hadiye abunta. Shi kuma ya daura mata man a kan hannu. "Oya zan makara sallar magrib". Babu yanda ta iya dole ta shafa masa. Kirjinta sai bugawa yake da sauri-sauri dan da gaske jikin nan nasa toro yake bata. Ta rasa mike birge maza suke maida kansu haka ita kam. Rashin mafita ya sa dole har shiryawa sai da ta taimaka masa wajen yi. Tana kammala saka masa turare ya kamo fuskarta cikin tafukan hannunsa ya sumbaci goshinta da idanunta da karan hancinta, sai kan habarta. Sassanyar ajiyar