Showing 27001 words to 30000 words out of 180087 words
Chapter 10 - Daudar Gora Book 2 Hausa Novel Complete
sanya ido kan wanda duk suke zagaye da kai shine mai muhimmanci. Idan ni banci nasara a yau ba, su zasu iya ci watarana, duk da nima ba haƙura nai ba zan sake gwada sa'a ta a karo na biyu”. Ta ƙare maganar a salon juya manyan idanunta da yamutse fuskarta dake tsuke tana laɓe baki idanunta dake cike da hawaye a kansa. Sai kuma ta janye su ganin yanda ya tsareta da nasa.
Bai iya ya motsa ba, kallonta kawai yake da ƙoƙarin danne abinda ke taso masa a kanta tun daga yatsan ƙafarsa har zuwa cikin tsakkiyar kansa. (Yarinyar nan ko) ya faɗa a zuciyarsa. A zahiri kam tsaf ya shanye komai daga kan fuskarsa ya haɗiyema ransa yana mai furzar da iska kaɗan tare da sake yin gyaran muryar da ta sakata sake ɗagowa dole, sai dai bata jure kallon nasa ba ta maida kanta ta rissinar. Shima ɗauke nasa yay daga kanta tare da miƙewa, ta ƙasan ido tabi takun sawayensa mai cike da izza da nutsuwa da kallo, sai da ya kai ƙofar fita gab ya dakata sai dai bai juyo ba, “Na baki dama ta biyu, in har kikaci nasarar kaudani a karo na biyu daga nan zuwa shekara ɗaya tukuycinki zama sarauniyar daular ruman bisa karagar mulkin Shahan-shan. Idan kika gaza hukuncinki zama uwar yarana biyar a ƙarƙashin ƙarfin iko ba soyayya ba....”
“Bana yarda aci riba kaina bisa ƙarfin mulkin mallaka koda anfi ƙarfi na. Taya zakaci riba biyu a shekara ɗaya duk a kaina, Iffah ba tsuntsuwar da ake ajiyewa a gida domin ado bace”.
Wani ɗan murmushin gefen baki yaso suɓuce masa amma sai bai bar hakan ba. A ransa ya furta (Ƴar barazana ce yarinyar nan) a zahiri kam sai yay ƙoƙarin ficewarsa maimakon bata amsa. Dan kansa har ya fara ciwo. In ba da iyayensa da Malikat Haseenat ba bayaji ya taɓa magana mai tsaho da wani a rayuwarsa kamar ta yau, shi kansa mamakin ma hakan yake, a rayuwarsa babu abu mafi bashi wahala kamar yin magana mai tsawo, shiyyasa yafi yarda da yaren kurma koda a fada ne...
“Banfa yarda ba.... Soyayya kuwa ni bama ta taɓa zama abinda nake kallo da muhimmanci ba da har zanyi kwaɗayin yima wani bayan ta ahalina”
Ya tsinkayi furucin nata yana ƙoƙarin ficewa. Yanzu kam sai da yay murmushin a zuciyarsa da sake jinjina ƙarfin halinta. Bai kuma juya ɗin ba yay tafiyarsa. Ta ɓarauniyar hanyar da ya fito ya koma sashensa, dan dama fita ce ta ɓadda kama. Turus ya ɗanyi da ganin Malikat Haseenat da bai zaton gani a irin wannan lokacin ba, kuma a falonsa da bazai iya tuna sanda ta shigo shi na ƙarshe ba. Basar da yanda take binsa da kallon tuhumar da ya gani a idanunta yay ya ƙarasa takowa gareta. Sai da ya kai zaune ya riƙo hanunta ya sumbata. Sannan ya furta “Idan amintacciya na buƙatar ganin gudan jininta shin ba umarni kawai zata bada ba ya isa gareta”.
Murmushi ta saki a karo na farko, itama cikin nata salon girmamawar garesa duk da matsayinta kanta ta ɗan rausayar. “Idan uwa ta girmama ɗanta da ke amsa sunan shugabanta laifi ne Hafidi?”.
Kansa ya girgiza yana ɗan murmushi a karo na farko. Ta san iya amsar kenan daga garesa. Dan haka cikin rashin nuna damuwa ta cigaba da faɗin, “Fita ce ta sirri, dan idanuna sun kasa rintsawa a wannan daren a dalilin furucin Zawjata-almilk”.
Idanunsa ya ɗan motsa, kamar bazaice komai ba sai kuma ya nisa, “Jadda-ti miye abin hana barci a ciki? Faɗin akwai wanda ta ambata bayan mun san da su? ko kuwa furtawarta kasancewar bamu taɓa ji da ga bakin wani ba?. Shirmenta da son kare kanta da ga laifinta ne kawai ya sata furtawa itama, nasan tana da hujja kan wani ba.....”
“Ina bazai yiwu ba Eshaan. Na jima da fahimtar wannan yarinyar nada wasu ɓoyayyun al'amura tattare da ita, sannan tana da ɗabi'ar zama kaifi.....”
(Mai hatsarin gaske ma kuwa, dan tafi duk yanda kike tunaninta Jaddah) ya ayyana a zuciyarsa. A zahiri kam sai ya ɗan yamutsa fuska kaɗan, dan kansa ke ciwo. Can ƙasan maƙoshi ya ce, “Yanzu mi kike son ayi?”.
“Karmu matsa mata da son sanin da wa sukai wannan aikin. Kamar yanda tace mu bincika da kammu muyi ƙoƙarin hakan, dan akwai wata hikima a zancen ta na bamu damar mu bincika ɗin”.
“Yanda kikace haka za'ayi Jadda-ti. Sai dai kuma idan bamuyi bincike ba taya za'a yanke mata hukunci? Ni fa ƙara aka kawo min, dolene na hukunta mai laifi ko na wankesa akan gaskiyarsa”.
Murmushi tayi mai ma'anoni da yawa da ita tasan dalilin kayanta. Taja numfashi ta fesar da ƙara damƙe hannunsa cikin nata. “Wannan sune siffofin adalin shugaba. Sai dai inaji a jikina a kwanaki ukun nan daka bada wani abu zai iya faruwa, dan duk masu hannu a ciki a yanzu hankalinsu ba'a kwance yake ba sam. Suna can neman hanyar ɗaukar mataki a kanta kafin cikar kwanaki uku harma da mu kammu”.
Idanu ya tsira mata da mamakin jin kalamanta. Amma sai bai iya cewa komai ba. Itama bata sake cewar ba ta sumbaci hannunsa tana mai lumshe idanun da buɗewa alamar sallamar kenan. Shima nasan ya lumshe tare da rissinar da kansa ya buɗe a hankali fuskarsa da ɗan yanayin murmushi sai dai bayin yake ba. Sai dai ta kurema ganinsa sannan ya janye idanunsa da ke binta da kallo. Ya maida bayansa jikin kujera ya maida idanun ya lumshe...
Duk yanda yake son hana tasirin kaikawonta a zuciya hakan ya gagara. Ƙarfin halinta, tsaurin ido da kauɗin zance na matuƙar zaburar da shi. Koda a tsoracan take sak take a zahirinta. Ba mata ba mazan ƙasar ruman gaba ɗaya shakkar masa magana suke kansu tsaye, amma ita tar idonta da muryarta ke fita garesa. Itace ta farko dake iya kallon cikin idonsa ta faɗi magana bayan mahaifinsa, amma ko Malikat Bushirat da Malikat Haseenat bejin tunda ya mallaki hankalin kansa sun taɓa hakan musamman a yanzu da yake matsayin Shahan-shan, suna masa magana da taushin harshe da kuma kimantawa, duk da kasancewar sa ɗa garesu. Amma ita duk da akwai girmamawar tattare da fitar sautinta garesa kai tsaye take babu alamar shakku, bata kuma iya ɓoye abinda ke ranta koda a inda tasan anfi ƙarfi ta ne.
“Fitinanniya”.
Ya furta a hankali kan tausasan lips ɗinsa yana mai miƙewa da wani irin makirin murmushi a kan ƙyaƙyƙyawar fuskarsa..........✍️
_🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️wanga Shahan-shan ya fara bani olo_
*LITATTAFAN DAI SUNE KAMAR HAKA*
*DAUDAR GORA Billyn abdul*
*KI KULANI hafsat xoxo*
*A RUBUCE TAKE Huguma*
*RUMBUN K'AYA Hafsat rano*
*IDON NERA Mamuh ghee*
_LITTAFI DAYA: 400_
_LITTAFI BIYU: 600_
_LITTAFI UKU: 800_
_LITTAFI HUDU :1000_
_LITTAFI BIYAR: 1200_
_KUDIN TALLATA MAKU HAJOJIN KU KUWA SUN KASHI KASO 4:_
_TALLA A DUKKANIN SHAFUKAN MU DA KE MANHAJAR YOUTUBE, FACEBOOK, TELEGRAM, WATTPAD, INSTAGRAM, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES. YA KAMA :25,000(DUBU ASHIRIN DA BIYAR)_
_TALLA NA IYA SAMAN SHAFI DAYA NA BOOK DAYA: 1000 1K_
_TALLAN TSAKIYAR SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA: YA KAMA 800_
_TALLAN KARSHEN SHAFI NA BOOK DAYA RANA DAYA. YA KAMA NERA 500_
_ZAFAFA BIYAR 2023!! ZAFAFA PAID BOOKS!! LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR_
ZAKU TURA KUDIN A WANNAN ACCOUNT DIN ME DAUKE DA SUNAN
MARYAM SANI
ACCESS BANK
0022419171
SAI A TURA SHAIDAR BIYAN
09033181070
IDAN KUMA KATI NE KU TURA TA WANNAN NUMBER HADE DA SHAIDA
09166221261
*ƳAN ƘASAR NIGER🇮🇳. ZAKU TURA KATIN AIRTEL TA WANNAN NUMBER WAYAR KAI TSAYE KUMA*
+227 96 09 67 63
Books biyar 1250CFA
Books hudu 1050CFA
Books uku 850CFA
Books biyu 650CFA
Bookk daya 450CFA
KARKU BARI AYI BABU KU, KU GARZAYO MU DAMA A CIKIN WADANNAN GWALA-GWALAN LABARAN MASU MATUKAR SANYA NISHADI.
MUNGODE DA ZABIN ZAFAFA BIYAR A KOWANNE LOKACI.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏽_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
✨𝕯𝕬𝖀Ɗ𝕬𝕽 𝕲𝕺𝕽𝕬✨
(𝕮𝖎𝖐𝖎 𝖐𝖆 𝖘𝖍𝖆𝖙𝖆)
𝓑𝓲𝓵𝔂𝓷 𝓐𝓫𝓭𝓾𝓵𝓵 𝓬𝓮🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔 (15)
........“Wlhy gaba ɗaya kaina ya kulle Akia, shin yarinyar nan wani ƙulli ne take son yi dan ta kuɓutar da kanta saboda tasan babban burin kowa sanin mai kashe matan Abni ne? ko kuwa gaskiya take faɗa? Idan gaskiya take faɗa taya akai tasani mu a tsahon shekaru muka gagara ganowa? Anya kuwa shigowar yarinyar nan cikin masarautar nan tun farko bada wata ƙullalliya ba?”.
Shiru babu alamar Malikat Bushirat zatace wani abu, hakan bai damu Jasrah ba ta cigaba da faɗin, “Al'amarin Mammah ya cigaba da bani tsoro a wannan gaɓar. Anya ba akwai abinda take ɓoye mana ba daya kamata mu sani?”.
A karo na farko Malikat Bushirat ta ɗago ta dubi Jasrah. Sai kuma ta miƙe cikin yanayin ƴar zabira. “Kamar mi kike tunani?”.
“Abubuwa da yawa Akia. Ciki harda halayyarta ta yanzu dake bayyanar da ita a mara gaskiya. Zuciyata na rayamun abubuwa da yawa fiye da yanda kike zato. Abin tambayar anan miyasa take goyawa yarinyar nan baya? Miyasa take son bata kariya? Bayan gudan jininta ta shirya halakawa? Ki duba kiga yanda taƙi bamu goyon baya akan shari'ar nan ita da Ammarah. Yarinyar nan ita aka fara kaiwa sashen Abni, kuma ita ta kaita, batai ko ciwon kai ba aka kai wata daga baya ta rasa ranta. Mi hakan ke nufi? Kaɗan daga cikin zarge-zargena kenan”.
Kai kawai Malikat Bushirat ke jinjinawa alamar gamsuwa da bayanin Jasrah, dan itama wannan tunanin ya jima yana mata kaikawo a zuciya. Taƙi fiddashi ne saboda tuna halayen Malikat Haseenat ɗin masu yawa kafin yau, amma yanzu kam zuciyarta na mata rawa akan a bubuwa da yawan gaske......
★★.... ★.....
Barbushi dake kwasar dariya bayan gama sauraren Miran Jasim da Miran Arshaan ya tsagaita dan kansa ya tamke fuskar tamau kamar bashi ne yayi ba. “Ƙwarai kuna a tsaka mai wuya, tsakar da in har bakinta ya buɗe ta furta ƙarshenku yazo. Abu ɗaya zamuyi akanta, idan mun taki sa'a kun tsira. Idan akasin hakan ya kasance ku zargi kanku....”
Komai basu iya sunce ba, dan zuciyarsu ta fara saka musu shakku akan gazawar Barbushi. Inba gazawa ba taya ƴar yarinya ƙarama zai dinga nuna kamar ta gagaresa. Bayan a da ya musu ayyuka manya da har a yanzu suke taka rawa da bazarsa. Ransu ɓace suka baro wajen nasa, zukatansu na matsanancin ƙuna, kowa kuma da abinda yake tattaunawa da ransa akan matakin ɗauka. Dan ko ana ha maza ha mata bazasu bar Iffah ta cigaba da numfashi ba a wannan gaɓar. Kai hatta da uban gayyar za'ai ƙurun-ƙus a wuce wajen dan sun gaji da gafara sa basuga ƙaho ba. In ba hakaba yarinyar nan zata ɓallo musu aiki....
★★... TA-ƘURYA ★★...
Tun zaman shari'ar nan ta kasa zaune ta kasa tsaye. Ta rasa makamar kamawa. A lissafi bayan boka Ruƙuƙi ta ziyarci manyan bokaye a ƙalla huɗu amma amsa guda suke bata bazasu iya mata aiki ba ta koma ga UWA. Tsabar takaici har kuka tayi, kuka irin wanda ake kira kuka data ɗauka tsahon shekarun da bazata iya tuna sanda tayi makamancin sa ba ma. Jin tsanar Iffah take fiye da komai yanzu a duniya. A kwanaki biyun nan da suka gabata bayan zaman shari'a ta yanke shawarar gwada kasheta amma duk hanyar da tabi sai ta sameta a toshe. Wannan ne ya sake ƙona mata rai da sake jin raɗaɗi mafi girma.
(Ki ajiye komai ki sake komawa ga uwa, karki bari wahalarki ta wuce a banza) shawarar aminiyarta ta sake dawo mata a karo na babu adadi. Jagwab takai zaune, cikin don danne hawayen dake ƙoƙarin zubo mata tace, “Mike shirin faruwa da ni ne haka? Shirin dana ɗauka shekaru kusan arba'in inayi ne wata mitsitsiyar halitta zata zama sanadin rushemin, micece ita? Mi take takama da shi?” hawayen da take dannewar suka zubo saboda radaɗin da take ji. Bata da sauran zaɓi a yanzu face sake nemo UWA. Zumbur ta miƙe tamkar wadda aka tsikara. Ta lalubo kayan surkullen da take kiranyen uwa da su, da ƙyar ta gano robar da hayaƙi ke ciki ta bulbula a burner, take ɗakin ya harmutse har baka iya ganin komai, ita kanta numfashinta har wani fisgar yake tsabar ƙarfin hayaƙin. Idanunta ta rumtse tare da zubewa bisa gwiwunta ta fara hurwa na kiranye cikin yaren surkulle. Amma tsahon lokaci babu alamar uwa, har hayaƙin ya Kore, bata gajiya ba ta cigaba tana mai sake ninka rauninta (Wa'iyazubillah).
Ta share tsahon awa guda tana abu ɗaya babu uwa babu alamar ta. Sai ranta ya ƙara sosuwa, ta dunƙule kanta waje ɗaya tana mai jin hawaye nason zubo mata. Amma ta hana hakan saboda taurin zuciya. Har karfe biyu na dare da masarautar ta nitsa bakajin motsin komai alamar anyi barci, in ma da wanda bai barcinba ya kasance a killace ƙarƙashin inuwar karamin motsi. Waya ta ɗauka tai danne-danne ta kai kunne, a bugu ɗaya aka amsa mata. Kafin ace komai da ga can cikin bada umarni ta furta, “Ki sashi ya jirani a garden”. Daga haka ta yanke kiran. A gurguje tai shiri cikin ɓadda kama ta fice, bazaka taɓa ɗauka mace bace, ta canja kammani cikin kayan jami'an dake aiki bada tsaro a masarautar. Dan haka babu wanda ya maida hankali kanta harta isa babban garden ɗin masarautar dake a ɓangaren kudanci. Wajen nada ƙarancin haske, sai kukan tsuntsaye da ake kiwo jefi-jefi. Da sauri ya fito da ga maboyarsa, ya zube a gabanta yana miƙa gaisuwa. Nuni tai masa ya miƙe batare da ta amsa masa ba. Mikewar yay, kansa a rissine, dan haramunne a garesa kallonta.
Sai da ta gama ƙare masa kallo sama da ƙasa ta mika masa anvelope ɗin hannunta. “Daga daren yau zuwa safiyar gobe ina buƙatar jin kuka, ina buƙatar naji kukan mutuwar Zawjata-almilk. Idan aka samu kuskure kuwa kukan mutuwarka ahalinka zasuyi. A jefata a babban ruwan swimming pool na garden ɗin gabashi”.
“Umarninki shine abin jirana da cikawa”. Ya faɗa da sauri cikin matuƙar girmamawa. Bata sake tankawa ba ta juya tabar wajen. Sai da ta ɓacema ganinsa ya iya ɗago kansa dake a risine yana sakin nannauyar ajiyar zuciya. Ba yau ya fara mata aiki ba, sai dai a shi kansa har yanzu bazai iya sanin ainahin wacece ba. Dan a koda yaushe cikin ɓadda kama take bashi umarni ko ta saka amintacciyar ta ta bashi, sai dai a duk lokacin da ita ta bashi da kanta ya san ba aiki bane ƙarami. Anvelope ɗin ya buɗe, ya wani zaro idanu da ganin makudan kuɗin da ke ciki miƙaƙƙu sababbi ƙal sai ƙamshin sabunta suke. Fuskarsa washe da murmushi ya sumbaci kuɗin, ransa fes da samunsu. Duk da dai yasan bazai cisu a banza ba, dan wannan aikin bazai taɓa zama mai sauƙi ba a garesa kasancewar matsanancin tsaron da kurkukun da Zawjata-almilk ke ciki, amma kodan waɗan nan taurarin dolene ya cika umarni.......
★★......
Ya kai mintuna goma yana kallon yanda masu tsaron kurkukun ke kaiwa da komowa, kowanne kuma da makami tare da shi. Ga haske ƙal tamkar rana dan ko allura ka yar ka duka ka ɗauka abinka batare da ka nema ba. Bugawar ƙaton agogon masarautar da ake iya gani tako wace kusurwar daular ta ruman ya sashi jan numfashi a sarƙe. Karfe uku dai-dai kenan, awa ɗaya garesa kacal na kammala wannan aikin. Dan huɗu nayi zaka fara jin motsin hadimai na tashi domin fara ayyukansu, musamman masu share-share da goge-goge. Zaman ɗammarar ƙugunsa ya gyara da ƙyau, hakama hular kansa kalar kayan jikinsa na ainahin amintattun jami'an dake cikin sashen Tajwar Eshaan. Ya ƙara saita kansa da ƙyau cikin dakewa ya tunkaresu hannunsa ɗauke da babbar jaka. Duk da sanin matsayin masu waɗan nan kayan a gidan gaba ɗaya sukai masa ca. Bai nuna razana ba duk da zuciyarsa na faman dukan dari-ɗari ne. Cikin sake matse kansa ya sara musu alamar girmamawa yana mai miƙa musu I'd card ɗinsa.
“Umarnine da ga shugaba, zan sada kayan nan ga Zawjata-almilk domin sakasu a gobe idan zata fita, na kwashe na dattin dake tare da ita”.
Kallonsa suke kawai suna sake kallon katin domin tantance shi ɗinne a hoton kokuwa. Sai dai hoton ya ɗanyi duhu, duk da kuma hasken wajen dai rana bazata taɓa zama ɗaya da hasken lantarki ba. A dake ya sake faɗin, “Ba tantancewar kaɗai ake buƙata ba. Ya kamata ku kira sashen shugaba domin tabbatarwa, wannan shine cikar aikin masu tsaro”.
Kalamansa sun ɗanyi tasiri garesu, sai dai duk da haka wani ya tubure akan sai ya fara zuwa ya tabbatar bawai kiran waya ba. Dan ko ƙuda an tabbatar musu su kasance masu himma wajen hanashi gittawa zuwa inda Iffah take sai da ƙwaƙwƙwaran dalili. Tsabar ƙarfin hali na hadimin nan, babu ko nuna gezau ya bada goyon baya. Hakan ya ƙara saka sauran jin sun yarda da shi, sai dai wancan ɗin babu alamar hakan. Sai ma tabbatar musu da yay su cigaba da tsaresa zaije ya dawo”.
Tsahon mintuna goma da tafiyarsa sai gashi ya dawo, batare da yace komai ba yay masa nuni da ya shiga. Wata irin wawuyar ajiyar zuciya ya saki da ɗan kashe ido wa jami'in da a yanzu yake ta faman sinne kai kamar wani munafuki. Sauran basu damuba dan su dama sun aminta tun dazun, dan haka ya wuce hankali kwance.
Tana tsaka da ɓarawon barcin da ya sace ta bayan ta idar da sallar da take tsaiwar yi duk dare domin miƙa kukanta ga UBANGIJI taji kamar numfashinta na fita a fisge, firgigit ta farka da ƙoƙarin kai hannunta saman hancinta, sai dai aikin gama ya gama dan ya riga ya shaƙa mata abinda ke cikin handkherciff ɗin. Duk yanda taso sake yunƙurawa hakan ya gagara sai ma jikinta dake saki baki ɗaya. Daga haka bata sake sanin inda kanta yake ba.