Showing 165001 words to 168000 words out of 171805 words
Chapter 56 - Inso Cuta Ne Book One Complete Hausa Novel
sumamme, n na fashe da kukan bakin cikiina shasheqa na nufosa ina ihu, nurse's sukayo knmu gadan gadan aka daukeshi aka nufa wani daki dashi ni kuma akace in tsaya a waje....
[10/30, 3:52 PM] +234 803 727 9133: INSO CUTA NE..82
Book din na kudine Ga masu bktr cigbn su nemi 08033368013.
*Sabon book Dina me suna AUREN YIMA KAI..fans karku bari a baku labari, labarine me cikeda nishadantarwa da fadakarwa,and ilmantarwar.*
Nan na tsaya inata kuka kmr raina ze fita, na daura hannu bisa kai nurse's sukazo suka koreni sukace na damesu, harda zagina suketayi na fito waje ina cigaba da kukana hannu na bisa kaina,Ina fadar nashiga ukuna ni hibbarh shikenan komi nawa ya ruguje...wata baiwar allah babbar mace me cikar kamala dagni yar Nigeria ce tazo shiga asibitin ta ganni, inata kuka,hartayi gaba ta dawo bya tna tmbayata mike faruwa,,,na kara fashewa da kuka kwata kwata bna hayyacina...haka kawai taji tausayina ya dirar mata a zuciyarta, yarinya meke damunki,,,, na fada jikinta ina kuka, batare danasan nayi hknba,,,,seda ta jima dani a jikinta, danta yazo yajata suka shige cikin asibitin...Nan natsaya naci gaba da kukana, zuwa wasu lokuta, wata nurse tazo tajani muka shiga inda mahaifina yake, Nan nagnshi kwance bisa gado, an lullube masa fuska, Nan nurse din tacemin sede haquri Allah yayi masa rasuwa,sanadiyar bugun zuciya....nan na fadi kasa sumammiya, sede farkawa nayi naganni kwance bisa gadon asibiti, har mutane sunyiwa mahaifina wanka sunka kaishi makwancinsa na gaskia....ina farkawa abinda ya faru ya dawo sabo ga zuciyatarh kuka na fashe dashi, Nan jikina ya rikice, seda nyi kwanaki biyu bnsan inda kaina yakeba...kudin asibitinma ya gagareni,Nan likitocin suka riqeni, har tsawon sati daya, Allah ya kawo matarnan ta biya kudin komi kna suka barni na tafi, Ina tafe ina kuka harna isa gidanmu, tin daga farkon layi, aka fara gulmata, ana zagina ana nunani cewar gatacan ita ta kashe ubanta, byn yy mata cikin shege, hkna shiga cikin mummunan rayuwa, gashi babu kou abinda zansawa bakina,...yunwa tacini ta cinye, gashi kullum da bakin cikin duniya nake kwana dashi nake tashi,...Abu kmr wasa harya zamana da kyar nake iya tashi,...dangin uwata dana ubana duk suka gujeni dukda bamu da nisa dasu, sunsan halin danake ciki amma basu kula daniba,.. a hk me restaurant dinmu yazo yimin gaisuwa yatarar dani ina cikin mayuwacin hali, shi yasemin abinci ya bani jikina na rawa na amaa nafaraci seda na qoshi duk yna zaune yna kallona nasha ruwa. Ya kalleni cikeda tausayawa, yace "hibbarh ya haquri..."
daga masa kai kawai nyi saboda bnda bakin mgna.
Cikeda tausayawa yake kallona, yace "hibbarh da gaskene abinda aketa fada a gari cewar kinada ciki..."
Nan na fashe da kuka,..ya kara tmbyata sannan yace kada in boye masa komi,Nan na kwashe labarin komi na gaya masa ina kuka...jinjina kai yy cikeda mamaki, Domin beyi tsammanin hakan daga ibrhim ba. Hk ya tafi ya barni byn ya bani wasu yan silallah, na amsa nyi masa godiya,...ga azabar whlr duniya ga azabar laulayi se abun ya hadarmin biyu,,,wata rna Yan anguwarmu suka hadu zasuyimin duka, harsun tinkaro kofar gidanmu, se naga sun juya da gudu a tsorace, bnsande me suka ganiba....wata rna ina kwance nga wani mutum fari me gemu, da kaya blue, a fari naji tsoro, Amma se nji tsoron ya fita a zuciyarta.
Hamza yasamu ibrhim da mgnr nan yy fir gudun kunyar duniya yace shi bashi yymin cikiba, Nan ya runtse ido yahau matsifa, cewar hibbarh tayi masa sharrine...Dole hamza ya bashi haquri Domin beda shaidarh yaje yasanr da hibbarh komi, Nan takara shiga tashin hnkli, harda rantsuwa tarinkayi masa tabbas hamza ya yarda da cewar cikin na Iburahm ne, Domin yasan hibbarh ba mutuniyar bnza bace, Amma beda yadda zeyi da rayuwarshi.
Watannin cikina hudu, aka koreni a gidan da muke saboda bnda yadda zanyi in biya kudin haya, Kuma kudin hayanmu ya kare. Nafito da kullum kyana narasa ina zan nufa, sena nufa restaurant dinmu, gun hamza, ya bani abinci naci ya tmbayeni lafia nabashi labarin komi, ya tasani a gaba, muka nufa, bngaren Iburahm, muka sameshi a falo, Ina dora idona a knshi naji na qara tsanarshi. Shi knshi kallo daya yymin yaji tausayina fal rnshi. Hamza yace in fadi cewar shine yymin ciki....tin kafin inyi mgna ibrhm ya fara borin kunya, Nan yayi mna korar kare, yace inhar bamu fitaba, se ya kira mna police,...dole muka fice nida hamza, yakaini gidanshi gun matarshi nanma zaman yaki yuwwa, matar ta kwashe kynta tabar gidan, taje gidan mahaifiyar Hamza , aikou tazo ta fara zaginsa race zata tsine masa inhar be koreniba, hamza yaso temakona amma abun yaci tura, dole na tattara kyana nabar gidan, Hamza na kukan tausayina. Hk rayuwa ta kasance, nakoma bin bola bola, inacin abincin da aka zubar, duk inda naje, se an tsangwameni, duk anbi an tsaneni.wata rna ina cikin bola wannan mtr data taba temakona a asibitin, ta biyamin kudi a lokacin da mahaifina ya rasu. tazo wucewa a mota ta ganni ta tsaya ta daukeni, cikeda tausayina, ta kaini gidanta dake nan indian, mtr babbar macece don zata haurawa 48yrs zata kai 50yrs, ta tmbayeni labarina nasanar da ita, seda tayi kuka tsabar tausayina, tasanr da mijinta komi ya aminta da zamana tare da ita, Nan mukayi wata daya kna muka dawo nijeria dmn aduba lafiartane yakaita indian, matar bata taba haihuwaba, Allah be bata haihuwaba shiyasa ta doramin son duniya. Damuka dawo nijeria a jahar katsina daman suke ita haifaffiyar nance, da mijintama, mawadatane sunada arziki sosai, sede tana riqon wani yaro yama girma dan zekai 25yrs yaron kanwartane, Sam yaron bayaji rnr daya ganni yarinka kallona, daki na musamman aka waremin. A kullum in nayi sallarh sena roqi Allah ya sakamin bisa tsakanina da Iburahm saboda yabarni da mummunan tabo mara kisaltuwa...Wata rna nasamu hajiya rukayyarh na tambayeta kou ana zubar da ciki...tacemin eh ana zubarwa inasone,,, nace mata A Nan tayita tsoratr dani haka na haqura da cikin jikina,.... Saleem yaron da hajiya rukayyarh take riqo, duk yabi yasamin ido, dabadan hajiyar tana taka masa burkiba, da har fyade se yymin....
A hk cikina yy 8month ciki yy nauyi, sosai,,,,hajiya rukayyarh tana bani kulawa kwarai, danginta suka gane ina gidan, suma Nan sukahau tsegumi da gulma, Amma duk rukayyarh taki kulasu.....(zuwa wannan labarin hibbarh ce ke bayarwa da bakinta Domin Iburahm ya jima dayin shiru, inno tace, hibbarh taci gaba da bada labarin.)
Saboda naki yadda nabawa, Saleem hadin kai yasa bama shiri nidashi sam ya tsaneni kouson ganina bayayi,...
Ina watan haihuwata ciwon hajiya rukayya ya tashi, dmn tnada ciwon sugar, Nan aka kaita asibiti, batayi minti talatinba ta mutu,,,,nayi kuka kmr raina ze fita, saboda hajiyar tayimin halacci tabbas ita yar halaq ce sannan ta kasance, cikakkiyar bakatsiniya duk inda bakatsine yake akwai kara da karamci da haquri da kawaici.
Tin kafin a kaita makwancinta, Saleem ya koreni a gidan yymin korar kare, dagani se kyn jikina hk na fito, ina kuka ga uban katon cikina, dayaketa murdamin ynamin ciwo, marata kuwa kmr zata fashe, a hk nayi tafiya me nisa, nashiga wata anguwar talakawa, ina shigowa kasuwarsu na zube a sume,Nan mata suka temakamin, aka kaini gidan wata dake kusa da kasuwan, ba jikawa, aka shiga dani se haihuwa, na haifa Yan biyu duk mata, Amma dayar babu Rai, byn nasha wata uwar whla bnmasan inda kaina yakeba matan suka tsaftacemin jikina, sukayima diyata wanka, nima suka samin ruwan wankan nayi, nan naji karfi, a jikina, suka bani abinci tuwon dawa da miyar kuka naci na koshi, suka bani diyar na bata nono ta kama kuwa tahau tsotsa, haushin yarinyar nakeji, Domin duk itace silar rushewar komi nawa....kwana na daya a gidan matar tace Ina ne gidana, nace bkm zan tafi, hk na dauki diyata nayi musu godiya nabar gidan na nufo hnya batare danasan inda zanjeba,,,rnr Nan kn titi muka kwana nida yar da bata da suna,,,,
Duk inda nabi se an kalleni kawai na yanke shawarar ajiye jaririyar inyi tafiyatarh hk kuwa nayi na ajiyeta a inda za a gnta, nayi tafiyata ina tafe ina wauwayonta, uwa da ya sannan nasha whla a knta, Amma dukda hkn bna sonta sede tausayi na uwa, juyowar dazanyi na qarshe naga bngntaba sede nga ban wani mutum ya wuce da ita a hannunshi....harda kuka nyi ina ihu ina fadin ya dawomin da yata, Amma be saurareniba yy tafiyarshi,... Hk naci gaba da rayuwar whla da kalu bale, a hk na hadu da wata mata, me samarwa mutane aiki, tasamar min aiki, nanma bb ddh saboda danta beda tarbiya hk nabar gidan aikin, na samu wani a gun saida abinci ina wanke wanke ana bani abinci inaci kullum tunanin yata na zuciyatarh, seda nyi shekaru hudu ina wanke wanken kna aka samar min aiki abuja matar me mutumci sede aikin dayawa, sannan tnada yara maza dayawa, a cikinsu dayane muhseen shikadai muke shiri, shima ina dardar, Domin na tsorata da maza,....Allah ya jarabci muhseen da soyayyatarh Amma mahaifiyarsu taki yarda da hakan dole ya haqura,...nan naci gaba da rayuwa da dadih da babu ddh kullum da tunanin diyata da tunanin iyayena, da kuma tunanin cutar dani da Iburahm yy bazan taba dena masa Allah ya isaba, har gaba da abadan... muhseen ya gaza haquri kouda yy aure still yna sona, ganin hkn yasa da yy tafiya mahaifiyarsu ta koreni, shine na nufo kasuna, nanma nasamu wanu aikin basa biyana amma ina musu bauta suna bani abinci, tinda na fara rayuwatar a wahalce, har zuwa ynzu a wahalce nake....a kullum cikin mafarkin yata nakeyi, a ynzu hk bani da kowa bani da komi sama da ita, duk byn kwana biyu, senaje katsina, inda na ajiyeta, Nan nake zuwa kou Zan gnta inyita kuka, dukda ba yar halaq bace na tabbatr da ina ganinta zan rage jin wani radadin a zuciyar, kouda Iburahm ya bugeni na fitone soyayyar kayan miya, shine, nga wata kmr diyata, inata binta harna hau titi bnsani ba...Iburahm bazan taba yafe makaba..... hibbarh ta fadi hkn hadi da fashewa da kuka tana nuna iburahm da hannu....
Duk iyahirin wanda yake falon, seda yayi kuka musammanma hammad tsabar kukan da yy har knshi ya fara ciwo, hatta mommah seda tayi hawaye, iyalin alhaji iburahm ma ta tausayawa lamarin ... duk munafukaima sun tausayawa hibbarh...innoma tayi kuka matuka harta gaji ta dago idanuwanta masu dauke da fararen glass ta saukesu a kn iburahm, murya na rawa tace, "tabbas Allah baze barkaba iburahm ka cutar da yarinyar mutane, Kuma ga sakayyanan Allah yy mata, kou rashin haihuwa Allah ya barka dashi, aiya jarabceka babban jarabawama, ga rashin kwanciyar hnkli, da an kalleka ansan baka cikin hayyacinka,...bka ga komiba...." Tna fadar hkn ta miqe jiki a sanyaye, ta kalli daddyn hammad tace, "a maidata asibiti, a ajiye mata Komi na bukatar inaso a kula da ita kmr wani da na wannan family din, kafin zuwa rnr daza a sallameta, a nemo gida sabo dal me dauke da kayan more rayuwa asata a ciki sannan asa mata ma"aikata insha allahu tagama whla a duniya,,,,Allah ya saka miki hibbarh..." Inno na fadar hkn tna hawaye ta dogara sandarta tabar falon, tna tafe tna kuka.
Tabbas ibrahim ya dauki duk wani hukunci daga mahaifiyar tasa amma kalamanta sun girgizashi....
Daddyn hammad yayi abinda aka umarceshi, ya mayar da hibbarh daketa kuka har lokacin asibiti,.... ibrahm ma aka dawo dashi asibitin,....
Kowa ya watse a falon, kowa zuciya bb ddh. Hammad Kam asibitin ya dawo, yna zuwa ya snr da jannarht komi,bkrmin tausayawa tayiba, itama seda tayi kuka me yawa, a zuciyarta taji dmn iyayentane, ita inhar zataga iyayenta ba damuwarta sun haifeta ta hanyar zinaba sam hkn baze dametaba,Domin tasan kaddara, sannan bawa baya kaucewa kaddararshi, babu wanda zece ynajin dadih 100% kou annabawa seda Allah ya jarancesu ballan tana mu yan adam. Allah ka bamu ikon cin jarabawarka me kyau da akasin hakan.
Byn kwana biyu, mnyan family suka hadu ciki harda daddyn hammad da Daddyn anwar, sukaje gun inno Dan nenawa ibrhm gafara,Nan suka cikata da natsihohi, batasan sanda imani ya shigetaba tace ta yafe masa duniya da lahira.
Suka samu hajiya nafeesat matar daddyn abuja itama tace bb komi ai kaddarace kuma duk musulmin kwarai dole ya yarda da kaddara khairihi wa sharrihi.
Sosai ake bawa, hibbarh kulawa ta musamman Kan kace meye ta murmure kyaunta ya Kara bayyana, jiki yy kyau, inno tazo gaidata yafi sau biyar don kullum setazo. Byn sati biyu, aka sallameta, Amma bata iya tafiya, aka nufa gidan da inno tasa a sata gidane katafare na gani a fada gidan ya tsaru, Nan aka kaita da maaikata sunkai goma. Inno da knta take zuwa gidan kullum tna gaidata, danta maidata tmkr diyarta ta cikinta.
Jannarht Kam tin rnr dataji lbrin nan taji tnada bukatar sa masu labarin a idonta, tace hammad ya kaita, yaki yarda yace seta samu sauki.
Ibrhim tini yabar asibitin, ya dawo gida, ya kara neman yafiyar inno tace ta yafe masa sede ya nemi yafiyar hibbarh....hk yaje gidan da hibbarh take don neman yafiyarta, tace bazata taba yafe masaba harse rnr dataga yarda yayi mata cikinta ta haifa, Dan tna tunanin itace, yarta tal a duniya, Dan bazata taba aureba harta koma ga ubangijinta,.... Jiki na rawa a rnr daddyn abuja ya nufa katsina yafara binciken inda zega yarshi, Dan tin kafin ya gnta Allah ya jarabceshi da soyayyarta fatanshi Allah yasa yaganta tabbas lokacin zataga gata iya gata, Domin koudanda aka haifa ta hanyar aure seta fishi gata, Dan duk dukiyarshi yy alqawari,seya mallaka mata komi nashi. Seda yy sati a katsina yna bincike, Amma babu labari, Domin ynada tabbacin inya gnta seyaji a jikinshi....hk ya haqura ya koma kano nanma bb lbri, hk yyta zagaye gari gari, dashi da yaranshi, amma ina, harya gaji ya dawo kaduna cikeda damuwa, nafeesat tanata tausarsa,dukda tnajin kishi Amma ta danne, dan farin cikin mijinta shine nata ....
Yau tinda ta tashi, ta tubure tace, dole se hammad ya kaita taga wannan matar da daddynshi daya bata lbri, Dan kou baccin kirki batayi, zuwa lokacin cikinta yakusan wata hudu, hk hammad yy mata wanka, yasa mata doguwar riga da hijjb dinta cikinta harya turo kmr cikin wata shida, hammad yna mamakin girman cikin, dukdama ya shige cikin hips dintane, ni'ima na kallonsu tna murmushi. Sunkutum ya dauketa be direta a kou inaba, se a car , niima tazo ta shiga shima ya shiga dreva seat yaja motar yabar gidan. Daddynshi ya kira ya tura masa address din gidan. Kafin su isa gidan, jannarht duk abubuwan data gani se hammad ya tsaya yase mata taci, wanima bata iya ci. Hammad Kam se biye mata yakeyi, a hk suka isa gidan
[10/30, 3:52 PM] +234 803 727 9133: INSO CUTA NE..83
Book din na kudine Ga masu bktr cigbn su nemi 08033368013.
*Fans inaso ku fahimci wani abu guda daya, dukda nasan kunsan hkn, duk duniya babu macen daza tace tasamu komi 100% kou ince made babu mahalukin dazece, yasamu komi yadda yakeso, inhar dan adamne, Allah yace ya haliccemune danya jarabcemu,....Nan novel dina akwai batsa, Amma nasan kou yayane an qaru, sannan bb yadda za ayi jannarht tasamu komi yadda takeso itafa yar adamcee, tasamu miji komi 100% aiko be yuwwa ace a rayuwarta babu qalu bale, dolene setasha whla sannan a wani fannin tasamu dadih, hk rayuwar take, babu macen daza tace tasamu miji 100% sannan tasamu dangin miji 100% sannan iyaye 100% ita kenan bata da wata jarabawa...gaskia ban taba ganin hknba ga rayuwata dolene seka tawaya a rayuwarka, hknne ya faru da jannarht karkuga lefina pls, nagode fans Allah yabar kaunarh.*
SA'ADATU BINTU ABDULLAHI✍🏽
Packing yy a packing space, kna ya fito yaga car din daddyn abuja da securitys dinsa. Budewa jannarht yy ya daukkota, ni'ima ta fito tace, "Irin wannan aise ka kara narkata..."
Murmushi hammad yy yace "ai Ni dama zata narken dana fison hkn..."
Niima ta kwash da dariya cikeda shaawar take kallonsu tna fatan Allah, ya bata miji kmr hammad.
Suna tafe tana binsu a tana har suka Isa falon Gidan. Falon ya kayatu matuka iya kayatuwa harya gaji da kayatuwa. Ajiyeta yy bisa kujera, babu kowa a falon se ma'aikatan gidan keta kai kawo sunata hidindimu, da aikace aikace a falon. Gaishesu suka shigayi, duk suka amsa Hammad ya tambaya kou Ina me gidan,, Yar dattijuwar tace "tana dayan falon tanada bakone.." Hammad yasan waye bakon daddyn abujane danyaga motarshi a harabar gidan, da motar securitys dinsa. Zazzaunawa sukayi jannarht na jikinsa, niima,na zaune bisa 1sttr ta zubawa katon tvn Dake manne a falon ido, shikam Hammad rankatakaf hnklinshi na bisa jannarht dinshi.
A dayan falon kuwa daddyne durqushe a gaban hibbarh tin safe yake Gidan TNA rokonta kan ta yafesa.. Kullum seyazo Gidan, amma Sam bata kulashi dukda zuwa lokacin, tafara jin tausayinsa, amma dukda hakan batajin zata yafe masa. "Dan Allah hubbarh ki yafeni wallahi ba laifina bane lefin zuciyatarne, dakuma kaddara kinsan kaddara tariga fata pls ki yafemin hibbarh nasan ni me lefine gareki..."daddy yy mgnr kmr zeyi kuka..
Hibbbarh kam hawayene kawai ke zirya a kuncinta... HK yaci gaba da rokonta, yna tsugunne bisa guiwowinsa, a gaban kujerar datake zaune...
A falon kuwa masu aikin suka cika masu table da kayan motsa baki jannarht ta tashi tahauci acici kenan Hammad Kuma yna danna mata, niima de tanaci tana kallonsu tana mamakin wannan ci da jannarht takeyi, mace kmr rumbu,kullum ci babu koshi. Data tasa peper meat a gaba seda tacinyeshi Tass duk uban yawan dayake dashi, Hammad kowa shike kara tura mata. "Wai wannan bby nada ci gaskia..."
Hammad yace "ai inajin yan biyune ...kode yan ukune my love." Ya karashe mgnr idonshi na kn jannarht. Jannarht ta zaro mnyan idanuwanta tace, "what...." Tyi mgnr tana dafe kirji, dmn tin zuwansu Gidan takejin bugun zuciya sosai a ynzu setaji ya tsannanta.
Hammad kam seyasha kou mgnr daya fadane, yasa ganin firgici bisa fuskarta. "Yeah.. Kou bakisone..." Murmushi Kawai tayi tace"koude zamu tafine naga har yanzu basu fitoba.."
Hammad yace "no bari inje inyi musu mgna ..." Yy mgnr yna miqewa ya nufa falon da aka Nuna masa dazu. Da sallamah yashiga, falon yaga daddy tsugunne a Zuciya yace "wato da