Showing 174001 words to 177000 words out of 196725 words

Chapter 59 - Dabiar Zuciya Book 1 Hausa Novel Complete

Mamugee   

07 Dec 2024

791

samu da namiji ita tana zaune,abinda yasa ta yanke shawarar kau da ita,ta kuma yita qoqarin ta samu haihuwa da kai koda sau daya ne.....saidai inaa,bata samu wannan rabon ba har yau........

"Wadan nan takardun na qasa sune zasu baka tabbacin maganganuna na yanzu......raihana kuwa......" Gabansa yaji yayi wani mummunar faduwa data kira sunansa

"Ya Allahu" ya furta a sarari,hakan baisa haj shuwa ta tsaya ba,don burinta kawai ta gama kwancewa mummyn zani a kasuwa

"Bayan ta gaza kau da ita daga duniya.....Gidan mahaukata jidda ta kaita.....har yau kuma tana raye......saidai ni kaina bansan wanne gida bane,kuma a ina yake......ga wadan nan,duka takardun kadarorin raihana ne data sace ta rabawa yaranta,wadan nan kuma kudaden kamfanin saraki da 'yarka tasa dana ya debo mata,ta hanyar amfani da siddabarun na'ura........


Tunda ta fita daga gidan takejin gabanta yana faduwa,abinda ya hanata dogon tsaiwa kenan cikin asibitin,ta kasa tsaiwa ma taga likitan ta juyo gida.


"Sannu da zuwa hajiya" saude mai aiki ta fada ga jidda,saidai bata amsa mata ba ta jefa mata tambayar dake cin ranta tunda ta shigo,saboda taga motar hajiya shuwa a farfajiyar gidan,batayi mamakin zuwanta ba,saboda a jiya sunyi waya,tayi mata cin mutuncin da dukka yazo bakinta,gami da kakkausan gargadin ta jawa fawwaz kunne ya maido komai dake.hannunsu,ta daukoshi zuwa daular gidanta ne saboda ya amfana shi da uwarsa darajar amintar dake tsakaninsu,hajiya shuwan batace mata ta tafas ba,wanda mummy ta dauka shakka ce tasa haka,har sai data gama sannan tace

"Ki kwantar da hankalinki,gobe zan dawo miki da komai da kaina ba saqo ba" tayi zaton zata sameta a falo a zaune,sai kuma taga falon wayam

"Su waye sukazo?"
"Hajiya shuwa ce da fawwaz,amma suna wajen alhaji" saude ta amsa mata,gabanta yayi mummunar faduwa,me ya kaita wajen daddy kuma?,me taje yi?,a iya tsahon zamansu bata taba haka ba,amma sai zuciyarta ke qoqarin gamsar da ita cewa dubashi suka shiga yi,don haka ta sauya akalarta zuwa parlor din daddyn a sukwane tun kafin hajiya shuwan ta mata wata barnar,tasan halinta sarai,bata barin kota kwana,hakanan koda zatayi asarar wani abu nata muddin zata dauki fansa zata iya aikata komai.

Najwa dauke da babban faranti data cika da fruit tabi bayan mummy,wadda batasan tana biye da ita ba,itama bata kirata ba saboda mugun haushinta takeji,saboda tana son kawowa soyayyarta dama plans dinta tarnaqi,don haka taci gaba da bin bayanta har suka shiga falon.


Kallo daya ta yiwa daddy kamar yadda shima yayi mata ta fuskanci lallai akwai gagarumar matsala,hakanan kuma komai ya qare

Dukka wanda yake cikin motar kuka yake riris,amiru ke driving kaltum na zaune daga gefansa gidan gaba,daga baya kuwa bibi ce riqe da hannun momma,sai samir daga daya side din ruqunqume da ita,zaka zaci cewa zata sake bace masa,kanta na boye cikin qirjinsa saboda haske da ya yiwa idanunta yawa,sakamakon dadewa da tayi bataga hasken rana ba.

Hadiyar wani abu kawai yake daga maqoshinsa zuwa cikinsa,idaunsa tamkar garwashin wuta,zuciyarsa na ayyana masa wanne irin hukunci ya kamata ya dauka akan duk wanda keda hannu wajen qarara da rayuwar mahajfiyarsa cikin wannan wajen?,wajen da duk wanda ka ganshi a ciki to dole ce ta kaishi bawai son rai ba?,ya dauko mahaifiyarsa ne cak ya fito da ita daga wajen,ba tare daya tsaya yabi ta ba'asin komai ba,don a yanzu ta tata yake tukunna kafin zuwan komai.

Wayarsa daya manta da ita gaba daya cikin motar ta dauki tsuwwa,tafi kusa da amiru saboda tana kusa gear

"Sabi'u yana kiranka" baiyi niyyar amsawa ba,amma jin sunan me kiran nasa yasa ya karba wayar ya kara a kunnensa.

"Najwa?,najwa kuma?" Shine abinda ya maimaita,bayan sabi'un ya bashi bayanan cewa itace waya ta qarshe da bala yayi da ita bayan ta sanya an tsinke birkinsa dana mahaifinsa,bisa taimakawar fawwaz.

"Wuce gida damu" samir ya gayawa amiru a tsawace,kamar wanda ya fara fita a hayyacinsa,yana jin cewa tabbas akwai babban tashin hankali kenan,abinda da farko ba haka ya tsara ba,ya tsara ya wuce da momma din daya daga cikin gidajensa.

Dadi ya saukarwa bibi,don dama haka takeso,tanaso taga yadda qaryar jidda zata qare,tana son taga tadda zata kalli momma raihana......


A rikice ta maida dubata ga hajiya shuwa,wadda take binta da kallo tare da murmushin mugunta a fakaice,ganin mummyn ta gaza cewa komai sai kallo da take rarrabawa a tsakaninsu tace

"Yauwa.....gwara da Allah yasa ma muka hadu,ga saqonki nan dukka na damqa hannun mijinki" take qafafun mummy jidda suka dauki rawa,wato an samu sabani kenan?.

Ta aika yara bayan fitarta su qaddamarwa hajiya shuwa su dauko mata dukkan wasu takardu nata da suka shafeta na sirrinta da take bata ta adana mata,sannan su karbo dukkan wasu kudi da takaddar kadara ta najwa dake hannun fawwaz,ashe ita nan ta nufo kenan?,ko kuma sun sameta tsallakewa tayi?,kamar tasan abinda take tunani sai tace

"Ai yaran da kika tura ya karbo miki saqon munyi sabani dasu ne,muna fita daga layin suna shiga......"

"DAGE da gaske shine mahaifin najwa?,lecturer mahaifin jawahir?" Daddy ya jefi mummy jidda da tambayar don tabbatarwa da kansa abinda hajiya shuwa ta fada.

Yadda tayi wani mugun shock daya sanyata yin taga taga zata fadi saboda girma da nauyin tambayar ya sanya duk wanda ke wajen fahimtar gaskiyar maganar,ciki kuwa harda jawahir da maganar ta sanyata kurumta na wucin gadi,basu kuma fahimci tana wajen ba sai da plate din hannunta ya fadi ya tarwatse da dukkan abinda yake ciki

"Qar.....qarya take min,so take taga bayana......qarya take" mummyn ta fada jikinta yana rawa

"Da dukka wadan nan shaidun dake hannuna?.....duk da hakan qarya take?!" Daddyn ya qarashe tambayar cikin daka tsawa mai kada hantar mutum,ya wani jirkice zuwa mayunwacin zaki dake farautar dukkan dabbar data gifta ta gabansa.

Ja da baya mummyn ta fara yi a tsorace sanda daddyn ya miqe yana tsuma yana nufota,idanunsa a birkice,tunda take bata taba ganinsa cikin siffa irin wannan mai ban tsoro ba,gaba daya ya sauya daga rashid din zuwa wani mutum da zuciyarsa da kuma fuskarsa ke cike taf da bala'i.

Cak taga ya tsaya ya tsurawa bayanta idanu ,abinda ya sakata waiwaya itama da hanzari.

Tashin hankalin da tayi arangama dashi sai taji yafi wanda ta shigo ta taras cikin dakin,tayi wata muguwar girgixa da razana kamar zuciyarta zata yanko daga qirjinta ta fado qasa.

,sai data gwammace dama bata waiwaya ba,ina ma suman qarya tayi kafin idanunta suga wannan babban bala'in da tashin hanakalin,yau din wacce irin baqar rana ce a gareta?,wanne abu ne yake shirin samunta haka?.

Tuni daddy ya miqe tsaye,labbansa suna haduwa suna rabuwa,jikinsa ko ina rawa yake,idanunsa qyam saman fuskar momma,yana son magana amma kowanne furuci ya kasa fita daga labbansa.

"Raihana.....ya akayi kika fito?" Kalaman da suka subuce kenan daga bakinta sanda momma raihana ta kafeta da idanu,a zatonta tana zanta hakanne a zuciyarta,batasan cewa maganar ya fito fili ba sai sanda taji bibi na maida mata amsa

"Ubangijin da baya barci bare gyangyadi shi yayi ikonsa ya fiddata daga kurkukun da kika jefata ba tare data aikata laifin komai ba"......

Kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai sai jin qarar mummy sukayi,dafe da gefan cikinta jini yana bin qafafunta,kafin hankali yakai ga abinda ga sameta cikin qiftawa da bismillah muryar najwa cikin wani mahaukacin sauti ta mamaye wajen

"Gwara na kasheki na kuma kashe kaina,gwara na dawwama a gidan prison,da ace wani riqaqqen dan daba talaka shine mahaifina,Allah ya isa tsakanina dake......Allah ya isa,bazan taba yafe miki ba,kin cuceni daya zama ba daddy ne ubana,gwara na kasheki....." Ta fada tana daga wuqar hannunta,wadda ta daukota ne cikin fruits din data kawowa su hajiya shuwa.

Babu wanda ya motsa saboda cetar mummy,sai zagaye da suka fara yi a parlor din,duk da jinin dake diban mummyn amma najwa yunqurin binta ta qara mata takeyi.

Hajiya qarama ce wadda basusan sanda ta iso ba ta hankade najwan ta fadi gefe

"Meye hakan?,kinyi hauka ne?ku dukanku kuna kallonta tana yunqurin kash......"maqalewa maganar tayi a maqoshinta sanda idanunta suka sauka fuskar momma,fuskar data jiqe da hawaye tana bin hafsanta da kallo.

"W.....waw.....wa nake gani kamar raihana ta?" Kusan tafi momma kuxari,saboda haka kafin ta qaraso ita ta rigata,suka rungume juna kana suka fashe da wani nannauyan kuka mai ratsa zuciya.

Hayaniyar da ta barke cikin falon yasa suka saki juna,najwa ce ta isa ga hajiya shuwa taci kwalarta da kyau,fawwaz na tsaye daga bayanta yana qoqarin rabata da wuyan mahaifiyarsa qarfi da yaji

"Munafuka algunguma,ki gaya musu gaskiya,ki gaya musu gaskiya,dama ba qaunata kuke ba?,zuwa kikayi ki rabani da ubana ki manna min wani uban?" Murmushi hajiya shuwa ta saki

"Sakeni 'yar nan,yanzu kuwa zan maimaita a gaban kowa saboda su xama shaida"

Hankali kwance hajiya shuwa ta maimaita dukkan maganar data gayawa daddy,sulalewa hajiya qarama tayi qas kamar yadda momma ta sulale itama,yayin da samir ya dafe bango jiri na shirin kada shi,kaf cikin zancan ba wanda yake hangowa.....tausayinta keson wasa da numfashinsa irin jawahir, innocent girl......son zuciya yasa mahaifiyarta ta bata mata rayuwa.....ta jirkita mata asali,ya Allah.....yanzu jawahir ba jininsa bace?,ba daddy bane ya haifeta?.

Amiru da idanunsa suka kada jazur ya dubi sashen da hajiya jidda take,jini take zubdawa sosai,kuma ci gaba da zamanta a haka dai dai yake da rasa ranta,sai ya hango fuskar jawahir.....mutuwar mummy da mummunan labarin professor rashid ba shine ainihin mahaifinta ba abun zaiyi mata yawa,abinda yasa yayi tattaki kenan ya fita ya kira driver ya taimaka suka kamata zuwa mota

"Ko kwana daya baxan iya qarawa da igiyar aurena a kanki ba.....na sakeki saki daya,na sakeki saki biyu,na sakeki saki uku jidda.....daga can idan kin rayu kada ki dawomin gidana,ki jirayi kuma sammaci daga kotu" wadan nan kalaman sune suka yiwa mummy jidda rakiya sanda su amiru suke fita da ita,abinda yasa numfashinta ya qarasa tsaiwa cak daga qirjinta......

Kansa samir ya girgiza,ya zaro wayarsa ya kira jawahir,bayan yayi qoqarin dai daita muryarsa

"Kina ina?"
"Ya saraki....ina makaranta"
"Idan kin fito ki wuce gidan hajiya qarama,gobe da safe da wuri xan turo driver ya kaiki azare wajen yadikko"

"Azare kuma yaayaa?" Ta fada a shagwabe cikin mamaki

"Eh azare, just say yes"

"Yes yaya" ta fada tana dariya,saiya maza ya katse wayar,karon farko hawaye na sulmiyo masa,yasa yatsansa ya dauke,wannan wanne irin son zuciya ne da zaiyi nasarar cusa baqinciki a rayuwar wanda baiji ba bai gani ba?.



61

Cikin kwanakin da suka biyo baya gaba daya gidan ya canza ya koma wani iri,tamkar gidan da ake zaman makoki,duk da wani ɓarayi na farinciki da ya samu cikin zukatansu,to amma mummy ta bar musu babban tabo a rayuwarsu.

Mummy tana kwance a asibiti,ta samu mummuna yanka wanda ta illata qodarta,najwa na hannun 'yan sanda,saboda asibiti da suka qi amsar mummy lokacin da aka kaita,suka dage kai da fata sai an nemo 'yan sanda,drivern gidan professor da yaga zai shiga ciki bayan bashi yayi aika aika ba yayi musu bayanin komai,take suka garzaya,suka kuma damqe najwa sukayi ram da ita,baiwar Allah jawahir na azare tana ta tambayar kanta abinda ya faru amma bataji komai ba hakanan bata ga komai ba,don haka sai tadan kwantar da hankalinta,sukaci gaba da zama da tsohuwa yadikko tana kula da ita da ciwon suger dinta daya tashi,ta ta'allaqa zuwan nata ma da ciwon nata da ya motsa.

Ta gefen dadday gaba daya tunda al'amarin ya faru yana dakinsa ya kulle kansa,babu wanda yake bari ya shiga kamar yadda shima baya fitowa,yayi kuka yayi kuka har baisan adadinsa,yayi nadamar da yace baiga amfaninta ba,yaji gaba daua siyasa ta fice masa fit a ka,ya tabbatar abinda ya sake kawo wannan matsalolin da gidansa ya fuskanta shine rashin samun wadataccen lokacin zama da iyalinsa da ya fara samu sanadin siyasa,ya tuna yadda rayuwar gidansa take a baya,ya tuna irin soyayya qauna da kulawa da yake samu daga raihana,yayi kukan da tunda mahaifiyarsa ta haifeshi bai taba irinsa ba,har sai da idanunsa suka soma rauni.

yayin da saraki ya duqufa wajen ganin an duba lafiyar mommansa an tabbatar da ingancinta.

Cikin hikima da isa irin ta ubangiji treatment kadam take da buqata,sai kuma idanunta da ya samu raunin gani saboda zama a duhu data jima tana yi,so ko yaya ta shiga haske sai yayita damunta,wannan dalilin ya sanya aka yi mata glass da zata dinga amfaji dashi sanda zafa fita ga haske har zuwa sanda ganinta zai dai daita.

Sai da yaga yadda jikinta ya fara kyau,ta fara dawowa cikin hayyacinta sannan ya karkata zuwa ga gyaran dukkan abubuwan da suka wakana.

Da farko bai sanya an kama bala ba,saboda bisa dukkan binciken da yayi ya tabbatar masa da cewa tursasashi akayi ya aikata abinda yayi din,saidai kuma ta yaya zaka yarda kaci amanar mutumin daka jima kana aiki qarqashinsa yana hidimta maka?,wannan shike nuna babu aminta ko kadan tattare dashi,wannan dalilin yasa ya sallami bala daga bakin aiki,abunda ya sanyashi cikin tashin hankali da baqinciki me yawa,haka nan ya kori fawwwaz shima,sa'an nan yana jiran samun lafiyar mummy ya hada ita da hajiya shuwa ya shigar da qara akansu,saboda lallai ba shakka akwai abinda yasa hajiya shuwa yin wannab tonon sililin,ya tabbatar ba banza ba,da ita kuma da mummy shi a wajensa dukka masu laifi ne,laifinsu daya.

Abu na gaba ya sanya an tattarewa mummy dukka wasu kaya da suka shafeta an kai Warehouse na kamfaninsa an jibge,bayan ya samu Tex daga daddyn kan ya aiwatar da hakan,saidai abu daya ya kasa tabawa ya kuma kasa magana akai shine najwa,sosai jikinsa ke sanyi idan ya tuna waye mahaifinta?,meta aikata?,don jawahir ko sama da qasa zasu hadu baya jin zai bari sunanta ko rayuwarta su baci,kuma bayajin zai bari ta kufce daga hannunsa ko a cire mata sunan 'yar uwa kuma autarsu,saidai kuma ta yaya zai binne abun?,bayan idan ta dawo zata tambayi mahaifiyarta da 'yaruwarta?,ba shakka yaqi ne babba a gabansu.

Baiyi qasa a gwiwa ba wajen sawa a cafko dukka ma'aikatan da mummy tayi amfani dasu wajen tsarewa da cutar da momma,daga nan aka miqa su kotu aka kuma fara shari'a dasu,bayan ya dora umar kan case din,cikin qaramin lokaci saiga batun ya yadu,cikin manyan shafukan jarida,labarai na gidan radio da television,kafofin sada zumunta,ko ina ka leqa zancan ake tattaunawa
"MATAR BABBAN SIYASA KUMA DAN KASUWA PROFESSOR RASHID AZARE TA BAYYANA A GIDAN MASU TABIN HANKALI,BAYAN DA ABOKIYAR ZAMANTA KUMA 'YAR AIKINTA DATA AURE MATA MIJI TAYI MATA QULUMBOTO TA BADDA ITA TSAHON SHEKARU ASHIRIN DA DORIYA SABODA KISHI KAWAI" topic ne daya dauki hankula matuqa da gaske,aka dinga tattaunashi ana yamadidi dashi.

Koda batun yakai kunnen samir sai yaji dadi da ya karbi wayar jawahir babbar ya hadata da keypad kan zai sauya mata wata,gidan yadikko kuwa ba wani kallo ta cikayi ba,yasan ba lallai labarin yakai kunneta ba,idan ba takanas wani zaiyi ya gaya mata ba.

Cikin qanqanin lokaci al'umma da dangi makusanta suka fara tururuwar zuwa yiwa momma barka da fitowa da kuma jajen abinda ya faru,abinda ya sanya samir ya bada umarnin duk wanda yazo ace momma din bata gidan,badon komai ba,sai don yana buqatar ta samu hutun daya dace,ta sake komawa hayyacinta,don har a sannan tana samun kulawar lafiya daga wajen qwararren likita da samir din yayo haya takanas aka ware daki guda ya zuba duk abinda ya kamata kamar dakin asibiti yake kula da ita.

Cikon sati na uku momma ta fara komawa nutsuwarta,da taimakon bibi da kuma kaltum da take qoqari wajen girka dukka kalar abincin da tasan zai maida ma momman lafiyarta cikin sauri,takan dafa mata dawa kamar shinkafa,tasa mata manja da gishiri,kuma momm din bata qi,tana amsa taci,hakan tasa qashinta ya fara samun qwari nan da nan,kuzarinta ya dawo,abinda zai baka mamaki,tamkar ba itace ta rayu tsahon wannan lokacin tana azabtuwa a rufe ba,saidai idan kayi duba da kasancewarta mace mai tsananun ruqo da ibada tun da can ba abun mamaki bane,to sai kuma zamanta a wancan wajen ya sake sawa ta kusanta kanta da Allah sosai,yawan ambaton Allahnta yafi na baya kafin wannan musibar ta sameta,lalllai ba shakka ambaton Allah kat ne!,dashi kadai kuma zukata suke samun nutsuwa.

Amiru shine ya ankarar da samir rashin fitowar daddy kwata kwata,sanda yaje gareshi ba yadda baiyi ya fito din ba amma daddyn yace yayi tafiyarsa,ya shiga damuwa samir,saboda yasan abinda daddyn ke dubawa da abinda ke damunsa,saidai yadda ya roqeshin ya tafin hakanan ya tafin kamar yadda ya buqata.

Wata sabuwa......sanda yake gayawa momma matakin da daddyn ya daukarwa kansa saita kauda kai

"Ka rabu dashi,qila wannan shine abinda yafi dacewa da shi,saidai a gobe inason ka hadani dashi,ina buqatar takardar sakina,don inason nan da rana ita yau na wuce gaban dangina,wadanda basu da labarin fitowa ta" kai samir ya daga,fuskarsa cike fal da damuwa gami da tarin fargaba,da gaske momma take tafiya zata sakeyi a karo na biyu ta barsu?,idan ta tafin to ya zasuyi su

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login