Showing 108001 words to 111000 words out of 185083 words
wani yunkuri Ammar din ya fara haukace musu da sauri Maheer ya rungumesa yana kokarin calming dinsa amma ina dan haka dole Anny tai masa allurar da baisan da itaba kuma batareda sanin kowa ba high dose ta basa dan haka bedroom dinsa Maheer yakaisa y kwantR tareda rufesa ya daidaita masa ac bayan ya sauya masa kayansa zuwa na bacci marasa nauyi dan haka baccin kwanciyar hankali suka sakasa.
Anny jin tai hankalinta ya kwanta dan daga Mimi har Ammar din insha Allah sai gama daurin aure zasu tashi dan haka itace ta karbi ragamar hidiman bikin cikeda farin ciki.
Dad da wuri ya shige zuciyarsa na shiga wani irin rashin nutsuwa haka kawai ga jininsa daya dan hau dan haka yasha magani ya shige.
Kiran Alh saad ne ya shigo wayarsa suka gaisa ya bayyanar masa da matsayinsa na wakilin AZIZ suka dan tattauna akan goben kafin sukai sallama.
Maheer ma damuwar yakejin ya shiga haka kawai sbd jin kaman abind yake faruwa bai kamata ba amma Anny ta dage ta sakasa dawowa da mood dinsa daidai.
********Washe gari tinda safe Su Baba alhassan da Alh Ahmed da Alh saad suka taho gidan suka sake gabatar da kansu sukai neman aure yanda ya kamata tareda kudin neman Aure ten mil suka baro sai kuma sun hade gurin daurin auren karfe goma sha biyu na ranar.
Saleem daya kasa yadda da cewan Jannah AZIZ takeso saida yayi magana da ita ya tabbatarda da hakan dan haka shima bai wani daga hankalinsa ba duk da su dad basu bude masa zancen sosaiba dan haka koda akace damuwa ta saka su Mimi fitowa sai bai takura Mimin ba tinda ya shiga ya sameta tana bacci hankali kwance hakama Ammar din dan haka kai tsaye cikin farin ciki yahau shirin daurin auren mutane biyu dayake tsananin kauna.
Jannah kasa Fitowa tayi duk da gidan akwai mutane rufe kanta tayi a daki tana kasa fitowa duk da batasan meyake faruwaba dan taqi barin kowa ya shigo mata hakama ta kashe wayarta hakama jamaar bikin basusan shaanin da ake cikinsaba hidima kawai Ake Anny kaman zata tashi sama sbd farin ciki.
Yau ranar aurenta da Ammar amma ayau din zata rasa farin cikin zuciyarta har abada dan haka zuciyarta take cikin wani irin yanayi na sanyi da rashin kuzari ko kadan dan hakanne ta kasa barin kowa ya ganta har lokacin daurin auren yayi.
Cikin shegun motocin dake Zaaden masu tsadar gaske da tarin securities su Dad suka fito zuwa daurin auren harda Daddy Mahmoud wanda yake cikin wasu shegun kaya masu tsadar gaske da sandarsa dayake takawa ahankali dan ya fara takawa.
Kowannensu asalin dukiyace a jikinsu tin daga manyan kayan dake jikinsu zuwa agogayensu da shoes
Luxuries tako ina kawai.
Koda suka isa masallacin da zaa dauka gabaki daya anguwar koina securities da jamian tsaro an cika.
Su Alh saad already sun iso suma dan haka AZIZ din ake jira wanda very late ya iso.
A cikin wata black RR ya iso gurin wadda ta saka aka san da shine din ya iso.
Sayd ne ya fara fitowa da fahad wanda ya baifi mintina arbain da sauka Nigeria dinba.
#MAMUH
#TWO PSYCHOS
#CRAZY Lovers
#limbas
#zaadens
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
58
Dad da Maheer dake jin matsuwar a daura auren suna jin sanarwan isowansa ajiyar zuciya suka sauke a tare cikin sirri sunajin nauyin kirjinsu na raguwa sbd maganace kadai basuyi da junansu ba amma babu wanda babu shakkar Zuwan AZIZ LIMBA a zuciyarsa sbd a yanda yake baa gane alkiblansa zai iya qin zuwa ko cewa bai karba aurenba wanda a daidai wannan lokacin idan yayi hakan ayau sun gama saukowa daga zaadens a idon mutane sun koma dezaans kila dan haka duk murmushi da farin cikin dayake bayyane a fuskokinsu fargaba da rashin nutsuwa ne a fuskokinsu saida sukaji isowansa suka saukin abinda ya toshe kirjinsu.
Fitowa yayi mota sanye da wani black tsadaddiyar luxury cashmere datai masa wani irin kyau da hula a kansa qamshinsa kadai me kirari ya shaqa take ya sauya kirarinsa yana qarawa da me qamshin alkhairi da babu irinsa.
Securities ne suke sake bawa gurin tsaro yana wucewa kai tsaye ciki Sayd na gefensa da Securities a bayansu sai fahad dayake gabansu ya basa kariya ta gaban.
Suna shiga masallacin take aka fara kokarim daura auren sbd ana kokarin gota lokacin da akace.
Dakatar daurin auren AZIZ din yayi lokacin da yake kokarin qarasowa har gurinsu Baba alhassan dake kokarin gabatar da komai.
Wani irin kallo Maheer ya dago da sauri yanawa AZIZ din zuciyarsa na bugawa da karfi da kuma mamakin menene.
Dad kuwa numfashi ya sauke ahankali yana dan lumshe idanuwansa yana jiran jin abinda AZIZ zai fada wanda zai iya sakasa samun Mummunan shock a gurin komaima zai iya faruwa dan haka kasa dagowa tayi yana jiran jin wani abin.
Maheer kuwa kafe AZIZ din yayi da ido yana jiran abinda zai fada sedai idanuwansa na bayyanarda sanyinsa da tsinkewansa sosai tareda qasqantar da akai akan kada komai ya samu auren farin cikin Jannah.
AZIZ saukar da idanuwansa yayi akan Dad da sadakarwansa take a bayyane cikin jiran abinda zai biyo baya,
Maheer kuwa tamkar magiya ce a tsakiyar idanuwansa dake kokarin sauyawa ammma yana hana hakan bayyana.
Sauke nutsatsiyar numfashi AZIZ din yayi yana samun nutsuwa daga tashin hankalin daya gansu a cikinsa batareda sun fada ko nunawaba shi ya hango sarewa da magiyar koma me zaiyi kada ya fasa auren a wannan lokacin.
Bazai fara aurenba sbd shima yanada reputation dayake son karewa kawai tashin hankalinsu da tsoronsu yakeson gani shiyasa dan haka kallansu baba alhassan yayi tareda sake wani Kyakkyawar murmushi daya saka kwarjinsa cike gurin sosai yace
"Bismillah Baba daman zaunawa nakeson nayi sbd na karbi igiyoyin aurena da kyau"
Dariya aka sake cikeda mamakin rahar tasa sbd abace da bayayi.
Daurin auren aka fara su Dad na sauke ajiyar zuciya zufa na dan tsinko masa yana tinanin babu wanda ya isa yayi musu hakan a rayuwa sai wannan me isar da zafin kan amma zasu daidaitasa ne idan suka gama samun abinda sukeso.
An daura Auren na AZIZ AY LIMBA da JANNAH ZAADEN akan sadaki dubu dari uku laqadan ba ajalan ba, a bisa koyarwan maaiki,
AZIZ LIMBA a yanzu shine me cikakkiyar iko kowace iri ce ta rayuwar jannah Zad..
Ajiyan zuciya da numfashi me dumi suka sauke dukkaninsu take aka fara adduar Allah ya sanya alkhairi ana tayasu murna ta koina sbd aure dai y dauru an daurasa.
Baba alhassan da Alh saad har cikin ransu suke jin wani irin farin ciki da nutsuwar AZIZ din yayi Aure sbd ya dauki lokaci sosai kafin yayi auren a lokacin da basu saka rai ba dan haka kudi sosai suke fitarwa suna rabawa.
DZad ma farin cikin ne me yawan gaske a ransa da kan fuskansa dan haka ya saki fuska sosai cikeda farin ciki yana amsa addua tareda godia ga manyan baqinsu manya da suka samu halartar daurin auren.
LIMBA dinma mutane yake gaisawa dasu sosai sedai ba wani sakewa da zallan bayyanarda farin ciki kaman familyn zaadens da nasa.
Sayd kuwa bakin Aljihu ya bude kaman bai taba sanin zafin kudi ba yace aje a rabawa maroqan dake can waje sbd karfin securities dake gurin bai basu damar shigowa ba kusa ko kadan sbd manyan mutanen da suke riqe da qasar kusan duk suna gurin shiyasa tsananin tsaron yai mugun yawa.
Dayake Saturday ce daga can bayan manyan baqinsu sun rage sosai duk sun wuce suma motocinsu suka fada tareda securities nasu suka baro zuwa gida zuwa lokacin Time na sallah yayi dan haka Masallaci suka fara tsayawa dukkaninsu da tarin securities sukai Sallan Azahar kafin Dzad ya roki su baba Alhassan din sosai suka nufa Zaadens.
Motocin AZIZ da securities dinsa dauke hanya sukai sukam zuwa gida.
Maheer ne ya lura da hakan ya sanarwa dad.
Dad baba alhassan yayiwa magana sai gashi ya kira AZIZ din yace ya dawo.
Sbd kaunar da Baba Alhassan yayiwa Ummitah da kasancewansa mahaifi ga Sayd ya saka baya taba tsallake umarninsa da maganarsa sbd shine wanda ya zama Uba nagari mai kare mutunci da gatan Ummitah a lokacinda baya nan shiyasa matsayinsa a ransa yakeda mahimmanci.
Ajiyan zuciya ya sauke tareda dago idanuwansa da sukai wani irin laushi suna bada sexy vibe ya kalli Sayd da ido yai masa alaman su juya.
Juya motar sukai securities ma juyowa sukai aka nufi zaadens din.
*******Tinda Maheer ya kira ya sanarwa Anny an daura auren wata farin cikin data sake rufeta dakin Jannah din ta nufa ta bude kai tsaye ta shiga fuskanta cikeda farin ciki da murna.
Zaune jannah din take bakin gado daga ita sai towel zata shiga wanka sbd ta samu karfin jikinta ya dawo sosai wayarta take kalla tanason kunnawa sbd tasan Ammar yana can yana kiranta coz by now ta riga ta zama matarsa burinsu ya cika dagashi din har ita amma kuma batajin farin ciki na shigarta kaman yanda tai tsammani.
Kallanta Anny tayi tana cewa
"Jan,
Yaya haka?
Baki shirya ba haryanzu yau daurin aurenki?
Pls yauri kiyi wanka ki fito kina buqatan shiryawa kafin angonki ya iso"
Dago idanuwanta tai ta kalli Anny din wanda farin cikinta yake a bayyane
Jin tayi inama farin cikin Fuska da zuciyar Anny ya dawo kanta ta nunawa duniya tana cikin tsananin farin cikin wannan ranar da burin Ammar da nata dana Mimi ya cika.
Numfashi me sanyi ta sauke ahankali tareda miqewa ta nufi toilet ta shige tana sakawa ranta dole daga lokacinda ta fito toilet din da farin ciki zata fito sbd tabbas ranar farin cikinta ce koba komai zatai farin ciki da rayuwar tattali a hannun Ammar dan haka bai cancanta wannan Yanayin daga gareta ba ya cancanta ya dawo ya taddata cikin Adon farin ciki.
Wanka tayi cikin nutsuwa ta fito tana fidda wani irin qamshin daya gauraye dakin me sanyi.
Har lokacin Anny na dakin ta fiddo mata kayan sawa na wani black Applique Lace mai Adon dark purple a jikinsa me tsadan da baida hayaniya ko kadan.
Dinkin half boubou ne da straight skirt,
Zaunawa tayi tafara shirywa fuskanta ba kaman farko ba daidai gwargwado ta sake ta dawo jannah dinta duk da zuciyarta sam ba walwala.
Shiryawa tayi batareda makeup ba sai eyeliner kawai da lip gloss kadan shima da baama ganinsa Amma kuma tayi wani nutsatsiyar kyau sbd skin dinta dake glowing sosai sbd gyara da hutun da aka taso cikinsa.
Simple English gold sarka da earrings ta saka da zobe daman akwai English gold zoben dayake hannunta koyaushe sai ha qara daya suka zama biyu.
Bata iya daura dankwali ba dan haka Anny ce ta tayata daurawan cikin sauki mara hayaniya.
Qamshinta kadai sake saka Anny farin ciki yake idan ta tina Daga karshe dai ta zama family da AZIZ LIMBA wanda hakan shine burinta shiyasa take jin kaman tafi kowa farin ciki da wannan auren sbd bata hangowa kanta talauci tafe ba ko kadan jin dadi da hutu kawai.
Hannu jannah ta miqa zata dauki wayarta Anny tace
"Karki damu ki kunna wayarki anriga an daura auren tin kusan mintina 50 da suka wuce ko awa daya ma
Kin tashi daga Jannah Zad kin koma Jannah Limba..."
Dago idanuwanta tayi cikin sanyi ta kalli Anny din wadda batasan meta fada ba gurin sauri.
Wayarta data kunna ce kira ya shigo wanda kaman ana jiran ta kunna wayar.
Sweety Falaq Aziz" shine sunan data gani akan wayar dan haka ta sauke ajiyar zuciya me sanyi tana kokarin dauka Maheer ya shigo dakin yana kallanta cikeda farin cikin ganinta tayi kyau sosai ta fito a amaryanta me cikakken gata.
Hannu ya miqa mata yana qarasowa gurinta yace
"Congrats my darling,
Kin zama mace ayau aure igiya 3 ne akanki,
Congrats my baby"
Rungumesa tayi idanuwanta na cikowa da hawaye sedai kafin su sauko Saleem shima ya shigo dakin ya ware mata hannu yana cewa
"My love ta zama matan aure,
Allah ya sakawa aurenki albarka ya baki farin ciki me dorewa,
Zakiyi rayuwan kwanciyar hankali da farin ciki sosai a hannun LIMBA yana cikin best mutane dana sani"
Gangarowa hawayenta sukai tana qanqamesa shida Maheer lokaci daya sbd har lokacin jin take kunnuwanta na ji mata sunan AZIZ a matsayin wanda suke ambata mijinta kuma kunyar tambaya take sbd kada ya zama tana tambayar wani da auren wani akanta dan haka ta zabi yin shiru tana barwa kunnuwanta abinda suke jiwa kansu.
Kamo hannunta Maheer yayi suka fice Saleem kuwa gurin Mimi data qi fitowa ya nufa har lokacin bacci takeyi ya tabata ya duba yaga lafiyanta kalau baccin dai takeyi sai kawai ya kyaleta sbd ya fahimci dole an bata wani maganin ne sbd ta samu nutsuwa daga shock din data shiga jiyan na tension da akace anshiga na faduwan jannah da baya nan.
Anny kuwa itama cikin nata adon na alfarma ta fito tabi bayan Saleem zuwa gurin baqi daketa tambayar Mimi tana ce musu batajin dadi sosai an samu ta kwanta tana dan bacci ne.
Mommy matar Daddy mahmoud ce ta tsaya akan baqin sunata kaida kawo cikesa farin cikin ana harkan girma da kwanciyar hankali sbd bawai bikin hayaniya bane.
Palon Dad Maheer ya nufa da ita
Suna kokarin shiga palon hancinta ya shaqo mata kamshin daya sakata dago kanta da idanuwanta ahankali ta kalli kofar gabanta na faduwa.
Jin tayi kafafunta na neman sanyi dan haka ta dan dakata tana kallan Maheer.
Juyowa yayi ya kalleta duk saiyaji ta basa tausayi me tsanani dan soyayya batai musu adalcin dataiwa Jan dinsu mummunan kamun data koma kalar tausayi sbd ganin kaman wanda take tsananin son baya mata irin wannan son.
#MAMUH
#BEST LOVE
#CRAZYLOVE
#BESTREVENGE
#BROTHERsLOVE
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
59
*TALK WITH SIDDEEQAH*
Operation Ciniki Dole
08149588205
Ni Olayyah na shiga uku na kwashe kudi na saro kaya domin in fara kasuwanci online, na gaji da zaman sai Yallaɓai ya bani kudin kashewa, kullum ni ce koma baya cikin danginsu, dukda yana kokarin sa, amma dai gwara in nemi na kaina kodan yan uwa da iyaye.
Amma bari in kira Besty nah Huriyyah nasan zata samu maganin wannan damuwar tawa.
Tunda na kira Huriyya na faɗa mata abunda ke hanani Bacci ta faɗa mun wani sirri da ya girgizani.
Wato ashe itama da ta fara business online kuma bata ciniki amms tunda aka bata number din Coach Saddiqah komai ya fara tafiya daidai a kasuwancin ta ( Talk with Saddeeqah).
Tunda ta shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP komai ya warware mata ciniki babu kama hannun yaro. https://wa.link/8al2f0
Ai ba shiri na nemi Coach Saddiqatu nima domin in shiga tsarinta na Saddeeqah Biz Growth Academy.
Kuma Alhamdullilah ina shiga nafara ganin canji a business dina, har ma sabon online business na buɗe daga cikin abunda na koya a Operation Ciniki Dole Online Boothcamp.
https://wa.link/8al2f0
Gaskiya wanda ya koya a wurin ƙwararriya ya huta domin ko dubu 100,000 akace in biya in shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE zan biya domin amfanin da na samu cikin Boothcamp bazan iya faɗaba, gashi yanzu na samu na sayi machine din delivery na maida daki guda shago cikin gida na.
Hurayyah ta taimaka da ta haɗa ni da Coach Saddiqah. OPERATION CINIKI DOLE ONLINE ya bani damar yin ciniki yadda ya kamata ba tare da wana damuwa ba.
Indai kina business ko kina son ki fara Operation Ciniki Dole Online Boothcamp shine ajin farko da Coach Saddiqah zata rike hannun ki ta nuna miki duk wani sirri da dabaru na kasuwancin online.
Daga rashin ciniki zaki koma sold out domin kuwa zaki dinga yin 6 figures monthly, in kin shiga OPERATION CINIKI DOLE ONLINE BOOTHCAMP baki ga sauyi mai kyau a business dinki ba za'a maida miki kudinki bayan 90days.
Da Naira Dubu Goma kacal Pre-lunching Price zaki samu damar shiga OCD.( Kina biya zaki fara kwasar ilimi)
Zakuma ki iya jira sai 20th January ki biya Naira Dubu Ashirin.
*********
Janyota kusa dashi sosai Maheer yayi yana kama hannunta daya ya riqe cikin kulawa da tsananin kaunarsa datake bayyane suka shiga palon..
Kanta a qasa yake amma a hankali ta dan rife idanuwanta sbd qamshinsa daya gauraya palon duk da akwai nasu Maheer da dad harma dana su Alh saad dika masu tsadar ne amma qamshin nasa ya fita daban tana jinsa a cikin numfashin datake shaqa yana isa zuciyarta yana karya dukkanin kuzarinta.
Kasa dagowa tayi sbd sanin tabbacin yana palon dan haka Mimi kawai taji tana buqata a wannan lokacin sbd ta rungumeta ta samu nutsuwa daga uwa da karfin gwiwa.
Bata qarasa isowa tsakiyar palonba Ammar daya farka cikin wani irin tsananin nauyi da ciwon kai yana saukowa daga gadonsa daqyar ya iya duba time baisan lokacinda jiri na dibansaba ya fito zuciyarsa na neman faso kirjinsa ta fito sbd tsananin harbawan datake ba daidaiba yana jin kaman zai rasa numfashinsa.
Dakin Mimi yai niyar nufa ya fasa ganin akwai baki a gidan dan haka kai tsaye ya nufi palon Dad yana isa Jannah da maheer na shigewa da sauri ya qaraso idanuwansa akan Jannah baya ganin komai da kowa sai ita.
Maheer ganin yanda Dad ke kallan bayansu ya sakasa juyawa a hankali cikin basarwa ya kalli bayan idanuwansa suka sauka akan Ammar dayake sako kai palon a mummunan yanayi.
Sayd dayake kusa da kofar shigowan Kallo daya yayiwa Ammar ya juya ahankali ya kalli uban gidansa wanda yake zaune a kujera hankalinsa kwance yana fidda wani irin kwarji kamewa daga jannah din data shigo har Ammar din dake shigowa ko inda suke bai kallaba duk da babu wanda baisan da zuwansa a gurinba cikinsu sbd ita yasan ta shigowanta a gurin,Ammar dinma kallo daya yayiwa Dzad da Maheer ya faminci Ammar suke kalla a kofa sbd yanda yanayinsu ya nuna.
Sayd akwai abinda ko AZIZ bai kallaba bare magana yana gane umarninsa ko abinda yake nufi kokuma abinda ya kamata yayi dan haka miqewa yayi.
Gadan gadan Ammar ya nufo Jannah wadda batasan dashiba tana kokarin bude baki ta gaidasu Baba Alhassan..
Kafafunsa da hannuwansa har wani rawa sukeyi ganin manyan rigunan shaddodi masu shegiyar tsada da huluna masu tsadar suma suna daukan ido a jikin kowa
Jin yayi ma suna kashe masa ido sbd masifar dayakeji tana kunnuwa a kirjinsa da cikin kansa
Jannah din yake kokarin kamowa jikinsa tukuna yayi magana sbd yafisan duk abinda zai fada ko tambaya ya zama tana hannunsa already sbd kada a a rabasa da ita dan ayau yakeson a daura musu