Showing 129001 words to 132000 words out of 185083 words
da suka ciko idanuwanta ta miqe ta zagaya gefensa tafara serving dinsa hannuwanta na dan rawa zuciyarta cikeda damuwan datakejin kuka da kewan gidansu na zuwar mata.
Dauke kallansa yayi daga hannuwanta dake rawa yana cewa abincin ya ishesa.
Ruwa da juice din da Fiddausi ta shigo dashine taga yanda jannah din hannuwanta ke rawa ta qaraso ta ajiye ta juya.
Ajiye masa komai gabansa jannah din tai ta koma ta zauna sedai ta kasa cigaba da cin abincinta daci zuciyarta ke mata dan haka miqewa tayi ahankali tabar gurin jikinta a mace.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
69
*UMMU_MAHNOOR LUXURIES*
(Best luxuries shop)
08034469681
08135142610
Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini?
Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka?
Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu?
Sitirar Alfarma kikeson sakawa?
Sitirar da kike ganin manyan mata da ita?
Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota?
To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida,
Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu,
Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯
Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune;
Atampopi
Laces
Shadda
Materials
Shoes
Bags
Veils
Trolleys
Jewellerys
Oil perfumes
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
***********
Shima ruwa ya dauka yasha a natse ya miqe yabar gurin batareda ya qarasa cin abincin ba.
Fiddausi dataga yanayin da jannah ta wuce a cikinsa dakinta ta bita ta zauna tana tayata fira tana sake gyara mata dakin tin tana kasa cewa komai har ta biyewa Fiddausi din suna fira tana bata labarin kuruciyan falaq da yanda suke fama da ita a lokacin idan daddynta yayi tafiya ta gane bayanan.
Dadin firar jannah takeji sosai zuciyarta na sanyi da jin yanda falaq ta taso wanda a cikin firar ta fahimci kila a gurin haihuwan falaq mamanta ta rasa ranta sbd a kaf labarin babu inda aka fadi asalin mamanta,Fiddausin ce kenan ta reneta tin tana jaririyarta itada mama dan haka kauna da jin falaq din a zuciyarta ya qaru taji zata iya daure komai sbd bawa falaq din kauna irin ta uwa data rasa duk da tariga tasan har abada babu me iya hawa matsayin da mahaifinta ya riga ya cike na uba dana uwa dan kuwa koda uwartata zata dawo duniya to bazata iya cike gurbin daya riga yacikeba sedai kwatantawa sbd ita kanta falaq din babu wani dan adam dayake duniya da zata iya bawa matsayin data bawa mahaifinta ba sbd ba qaramin tsananin kauna take masa ba dan duk da tana yarinya babu abinda takejin bazata iyaba sbd daddynta shiyasa taiwa Ammar tsanar gaske duk da bata gama sanin tsanar me take masa dinba.
Har magrib Fiddausi na dakinta tana tayata fira da kalle kallen da suke a ipad ga kuma qatuwar flat screen tv datake dakin nata dayakeda girma sosai.
Falaq na dawowa kai tsaye dakin ta nufa tana ganinsu ko uniform na islamiyya din bata cireba ta xauna cikinsu jannah na tayata cire hijab din jikinta dayake qamshi me dadi duk da anyo yawon makaranta amma sbd tsadan turarenta da ake siya mata yasaka komai na jikinta qamshin yakeyi me sanyi.
Hularta ta jannah ta zame mata sbd tasha iska tana cewa
"Falaq kodai zaki cire uniform din kiji dadi?"
Girgiza kai tayi tana shan ruwan da Fiddausi ta miqa mata cikeda kulawa.
Mama data jisu shiru ta dauka basa nan sai bayan magrib suka fito dukansu kowannensu da walwala akan fuskansa.
Kallan falaq tai da uniform a jikinta tace
"Me kikeyi da uniform a jikinki har yanzu falaq?
Oh ni Sakina wannan yarinya anyi shiryayya"
Murmushi jannah tai tana cewa
"Ko data dawo mama ta gaji ne shine ta huta sai yanzu zata sauya"
Kallan jannah mama tai tana cewa
"Allah na gode maka,kema yanzu jannah sahun AZIZ zaki bi kuna biye mata komai tayi bata laifi daidai ne ko??
Murmushi jannah din ta sake yi tana kallan falaq tace
"Je ki kicire uniform din kilama sunata damunki"
Dariya mama tayi tana kallan Fiddausi kaunar jannah na sake cikata tace
"To ai shikenan saiku bada himmar qarasa lalatata kunyiwa mijinta bayani daga baya"
Falaq na jin hakan ta dawo da sauri tana cewa
"Mama Jan tace na dena shiga dakin Daddy tinda safe ba kyau sai nayi aure dakin mijina kawai zan ringa shiga karna sake shiga na kowane namiji sai nasa"
Mama cikeda mamakin falaq din tace
"To wannan nasihar datai miki wayace miki ana fada?baa fadawa kowa gaskia ta fada miki"
Basusan da isowansa ba sai zancensa sukaji wanda ya sakasu yin tsit Fiddausi na hadiye hadiyarta da sauri tana kama kanta.
"Wane mara hankalin ne ya sakata fadawa yarinya hakan?
Fuskansa a daure take sosai bacin ransa na bayyana a cikin sautinsa dayake fita a natse ya kalli jannah din wadda ta kasa dagowa
Yace
"Wane kalan tarbiya ne kikazo dashi?
So nawa zan fada miki tarbiyanku dana mutane ba daya bane,
Kinsan inda maganganunki zasu kai tinaninta?
Meya hadata da maganar zuwa dakin miji a wannan shekarun?
Ke tin kina yarinya qarama aka nuna miki xuwa dakin mijin ne or wat??
Like seriously??
Mama ce ta katsesa da cewa
"AZIZ me kake fada haka?
Tana bata tinani me kyau ne ai sbd tintini ya kamata ta dena shiga dakinka anyhow,
Ta girma ya kamata tafara sanin ta girma hakama tin a yanzu ne ya kamata tasan baa shiga dakin kowane namiji saina mijinta idan akai mata aure shima"
Hawayen da jannah ta kasa barin su saukone ta hadiye su ta maqoshinta suka wuce mata da wani irin daci ta kasa dagowa.
Shi kuwa maman ya kalla yace
"Mama duka wannan zancen ba yanxu ne lokacin yinsu ba,
Tana buqatan kiyaye kalan namu tarbiyan da dabiun dasu basuda shi banason zance kowane iri yana shiga kunnen Falaq din"
Falaq jannah din ta zubawa ido itama nata idanuwan na cikowa da hawaye ta miqe ta koma gurinta tana rungumeta ta dago ta kalli daddyn nata tana bata fuska.
Mama ma tausayin Jannah din taji duk ya rufeta amma bata ji zafin AZIZ din sosaiba sbd ganin take bai saba da kowa na saka masa hannu ko baki bane a tarbiyan yarsa bayan ita da sayd dasu kadai ne suke masa discipline nata.
Fiddausi silalewa tai tabar palon jiki a mace Sayd ma dayake tare dashi shiru yayi sbd ba hurumin shigar kowa bane bayan maman sai kuma falaq da itama take iya sakasa da hanasa.
Cikin karfin hali jannah ta dago tana hadiye damuwa da radadin zuciyanta tana nunawa mama ba komai bayan barinsa gurin.
Falaq zuwa tai ta cire uniform dinta taqi sake fitowa dakinta har lokacin cin abinci yayi taqi fitowa karshema rufe dakinta tayi.
Tin Fiddausi na daukan abin wasa har taga dai da gaske take take hadda su kuka sosai dan haka ta fito ta sanarwa su jannah da mama.
Jannah ce ta nufi dakin ta ringa Knocking tana kiran sunanta cikin kulawa da rarrashi.
Qin budewa tai wanda hankalinsu ya fara tashi sbd kuka takeyi sosai taqi magana.
Jannah hankalinta mugun tashi yayi sbd tana gudun AZIZ din yaji ta sake wani laifin dan haka ta ringa rokon falaq din akan ta bude amma sam taqi.
Mama tasan zaayi hakan daman Falaq din na wannan sakarcin har sai Daddyn yamata abinda takeso idan ba hakan ba haka zata qi fitowa ta dagawa kowa hankali.
Basu san abinda yake faruwa ba sai da ya dawo kusan 10 na dare ya tararda Fiddausi da jannah din tsuru cikin damuwa.
Ko kallan inda suke baiyiba ya wuce hanyarsa yana duba time.
Sayd ne ya kalli Fiddausi yace
"Lafiya dai?akwai abinda yake faruwa ne?
Hanyar da AY yabi Fiddausi ta saci kalla tace
"Falaq ce tin bayan magrib tana daki ta rufe tanata kuka sosai kuma tin dazu ma munji shir..........
Cak din da AZIZ din ya tsaya cak sbd maganarta tsaf a kunnensa ta saka ya saka Fiddausi kasa qarasawa tana sauke kanta qasa.
Shi kansa Sayd din da sauri ya juya ya kalla ko AZIZ din ya shige ya gansa yana sauya hanya zuwa bedroom din Falaq wanda jannah ke can tsaye tin dazu idanuwanta duk sunyi ciki ita kanta tana cikin tsananin buqatan me kulawan da ita tai kalan tausayi jikin yayi tsananin sanyi sbd tasan itace zata hadiyi baqin cikin akan wannan lamarin.
Jin qamshinsa da taku a bayanta ya sakata janyewa gefe tana juyowa taga shi dinne kuwa fuskansa babu sauki ko kadan.
Tsayuwa yayi a bakin kofar ya ambaci sunan falaq da muryansa kai tsaye.
Kafin ya sake kiran falaq din juyowa yayi cikin zafi ya kalli jannah din ransa na quna yace
"Babu abinda kika daidai ne a rayuwanki ke??
Idan ta rufe kanta kusan awa biyar me amfaninki da bazaku nema mutane ku fada musuba?
Cikin tsananin sanyi da mutuwan jikinta datake jin zazzabi sbd wahalar tsayuwa da buga kofa ta bude baki a sanyaye tace
"I'm sorry"
Kaman tafasashen ruwa haka yaji muryanta datake bayyanarda itama ciwone a jikinta na sauka a zuciyarsa,
Da karfin gaske ya buga kofan yai wa falaq din kira daya daya saka falaq din mugun firgita sbd bata taba jinsa hakan ba.
Ita kanta Jannah sarawa kanta yayi sbd faduwan gaba ta dafa bango.
Acan ciki kuwa falaq ciwonta ne ma ya tashi jin tai kaman numfashi na gagara shiga cikinta,
Bugun zuciyarta tsananta yayi sosai har tana jin azabarsa ta dafe kirjinta tana jin abinda bata taba jiba.
Saukowa tai daga gadonta bata gani sosai jiri na dibanta tana son isa kofar sedai ko taku uku bataiba ta zube a tsakiyar dakin.
Jin faduwanta a qasa ya sakasa juyawa da sauri yace Sayd ya kawo keys.
Da gaggawa aka kawo keys ya bude dakin
Ganinta zube qasa ya sakasa jin kansa gabaki daya ya dauki zafi da saurin gaske ya isa gareta ya dauketa cak yana sayd yayi sauri ya kira likita.
Jannah ma tashi hankalinta yayi taji gaba daya ta rasa kuzarin jikinta ta rabe gefe tana kallan yanda falaq komai nata baya motsi.
Sayd da sauri ya fidda wayarsa yana ficewa daga dakin ya saka kiran sabuwan dr din da suka samu anan din mace da namiji ta bangaren ciwon falaq kawai.
Ganin ya rasa taimakon da zai bawa falaq din ya saka jannah zuwa bakin gadon tafara taimaka mata ganin numfashinta bai tsaya gaba dayaba sbd tayi karatun bada taimakon gaggawa a Greece sbd yanayin ciwonta hakama Ammar ya koyar da ita abubuwa da dama sbd koda wani abin zai sameta ba kowa dan basa wasa da lafiyanta sam.
Yanda takeyiwa falaq dinne cikin taka tsantsan da kulawa ya sakasa kallanta yana jiran jin wani abu daga gareta sbd ganin falaq din tana dan kokarin daidaituwa a yanda kirjinta ke wani irin ja.
Baa dauki lokaci irin sosai dinnanba dr Sameera ta iso tareda wata nurce.
A lokacin mama data shige tini ta fito duk suna palo cikin damuwa Fiddausi idanuwanta sunyi jajir sbd Kauna ce me karfi da shakuwa kamar uwa da 'ya itama a tsakaninta da falaq sbd shayar da ita ne kadai bataiba amma duk wata dawainiyar falaq itace meyi tin falaq na zanin jariranta.
Jannah ma a zaune take sanyaye zazzabi me karfi ne itama yake cinta na walaha.
A gidan dr Sameera ta kwana Sai Falaq ta farka.
Dr Sameera kwararriya akan aikinga kuma mace ce Kyakkyawa mai kyan jiki da tsari tareda ilimi sosai kuma tin ganin farko Allah itama ya jarabceta da kaunar AZIZ LIMBA wanda bai taba mata kallo biyu xuwa uku ba ko yau din datake cikin gidansa sbd 'yarsa.
A dakin Falaq dr Sameera ta kwana ya hana jannah kusantarta kwata kwata wadda ta kwana cikin damuwa da zazzabin da batada maganinsa.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
70
*UMMU_MAHNOOR LUXURIES*
(Best luxuries shop)
08034469681
08135142610
Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini?
Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka?
Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu?
Sitirar Alfarma kikeson sakawa?
Sitirar da kike ganin manyan mata da ita?
Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota?
To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida,
Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu,
Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯
Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune;
Atampopi
Laces
Shadda
Materials
Shoes
Bags
Veils
Trolleys
Jewellerys
Oil perfumes
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
*****************
Washe gari tinda safe Jannah ta nufi dakin Falaq kafin ya fito ta dubata bayan sun gaisa da dr Sameera wadda ke bin jannah din da kallo sbd sanin itace matar AZIZ LIMBA din.
Ta jima a dakin bayan ta dan tambayi dr Sameera din yanayin jikin falaq din ta bata tabbacin zata iya farkawa kowane lokaci.
Kasa komawa dakinta tai ta nufi dakin mama tai mata ina kwana mama ta sakata tai zamanta anan tai baccin safenta wanda bata samu tayiba da dare sbd cikin tsananin zazzabi da yunwa ta kwana.
Karfe goma da mintina ta farka ta sake zuwa dakin Falaq ta dubata kafin ta wuce dakinta tai wanka ta shirya ta fito tana waya da Maheer kafin ta kashe tana isa dakin falaq ta tarar da tana farkawa dan haka da sauri ta qarasa gareta tana zaunawa gefenta shima a daidai lokacin ya shigo a karo na babu adadi.
Falaq na ganinsa idanuwanta suka ciko da hawaye suna gangarowa..
Jannah ta zari tissue tana share mata hawayenta cikesa kulawa da kauna.
Dr Sameera ficewa tai a dakin aka barsu su kadai.
Miqewa jannah tai ta basa guri zata bar dakin Falaq ta kalleta tanason kiran sunanta amma bata iya bude bakinta sbd she's very weak.
Sake yunqurawa takeyi na son dawowan jannah din amma batada karfin hakan...
Ba tsammani jannah taji ankama hannunta cikin nutsuwa batareda ance komaiba.
Cak ta tsaya batareda ta juyoba sbd sanin shi dinne tinda basa tareda kowa a dakin hakama girman hannun da yanayin yanda dumin tafin hannunsa ya shigeta ya tabbatar mata da ba Falaq bace.
Shiru sukai dukansu kafin ta juyo ahankali tareda dagowa ta kallesa shi kuma bai juyo ya kalletaba falaq dake zubarda hawaye har lokacin yake kalla zuciyarsa na susa da kukan datake faman yi.
Sake mata hannu yayi Ahankali ganin ta fahimci abinda yake nufi ta koma dayan gefen Falaq din ta zauna tana cigaba da share mata hawayenta.
Zaunawa yayi Ahankali a sofa yana kallansu su duka biyun kallan nutsuwa kafin ya bude baki kai tsaye yace
"Falaq meyake damunki?
Meye kikewa wannan kukan?
Akwai abinda yake miki ciwo ne?
Girgiza kai tayi ahankali tana kallansa a marairaice.
Tea da abinci tareda ruwa me dumi Fiddausi ta shigo dashi ta ajiye a table wanda jannah ta zaunar da ita ta fara bata tanasha ahankali sbd akwai yunwa sosai a tareda ita.
Shiru yayi yana kallansu harta gama bata abincin tana goge mata baki kafin ta kamata suka shiga toilet shikuma ya dan fita sbd amsa waya a natse bayason hayaniya komai kankantarta a dakin falaq din sbd tattalin samun lafiyanta.
Ko tsayuwa Falaq din bata iyayi sbd idan aka samu collapse irin haka a ciwonsu dukkanin karfi da kuzarinka tafiya yake gaba dayansa sai bayan dan lokaci yake dawowa.
Wanka ta taimaka mata tayi wanda ya sakata jiqewa gabaki dayanta kayan jikinta suka jiqe sosai dan haka dole daga can itama rigar wankan falaq ta sako wadda tai mata kadan sosai duk da tayi mata amma tai mata guntuwa sosai dan kadan ta sauko a cinyoyinta hakama daga saman bata wani rufeta sosaiba amma bata damuba suka fito sbd ba kowa sai su kadai.
Falaq ta samu dan karfin jikinta sbd wankan ya dan sake mata jikinta dan haka itama rigar bathrobe din ce a jikinta amma ita sbd tata ce daidai tai mata ta rife mata yanda ya kamata.
Suna fitowa daga toilet taji sanyin Ac ya kado musu sosai har saida tsikar jikinta ta tashi ta kalli inda remote din yake tana dan sakin falaq ta nufesa dan rage sanyinsa sosai kodan falaq din da babu lafiya duk da itama bata wani son sanyin sosai.
Vibrating na waya taji daga bayanta wanda ya sakata juyawa da sauri tagansa a zaune yana kallan rigar dake jikinta a natse.
Kanta taji yayi mugun sarawa ta saki falaq gabaki daya tana kokarin juyawa daga ita har falaq din suka zame sbd da sakinta da yanda taja kafarta da sauri zata juya lokaci daya ta ja da kafar falaq din wadda batada karfi ko kadan dan haka baida zabin daya wuce taresu su biyun sedai ita yana tareda kofar toilet din ya koma da ita gabaki dayanta yana barin falaq wadda ya tsayar jikin bango sbd Sayd daya sako kai dakin tareda dr Sameera.
Falaq dake kusa kofar toilet din ta janyo tana kallan Sayd da Dr Sameera dake kallanta.
A cikin toilet din cikin zafi ya dago xai mata magana idaniwansa suka sauka akan gaban rigar data bube kadan Tabon aikinta seti da zuciyarta ya bayyana baro baro wanda ya saka zuciyarsa Skipping bugawa idanuwansa na kasa daukewa daga gurin har lokacin suna hade da junansu.
Yanda zuciyarta ke bugawa kirjinta na sama yana kasa ya xubawa dinkin setin zuciyarta tasa zuciyar na bugawa idanuwansa sunyi jajir.
Jin tai bugun zuciyar nata itama yana tsananta ta dago idanuwanta ahankali ta kallesa a lokacinda ba zato taji saukan tafin hannunsa akan zuciyarta wanda ya saka kirjinta bugawa da karfin gaske..
Bugun farko na zuciyar Ummitah dayaji a tafin hannunsa baisan lokacinda ya rintse idanuwansa ba yana sake matseta jikinsa hannunsa dake kan kirjinta yana wata irin rawa me sanyin data sakata kasa tsayuwa kafafunta na sanyi tana