Showing 141001 words to 144000 words out of 185083 words

Chapter 48 - Kalbim Book 1 Complete Hausa Novel

Mamuhgee   

23 Sep 2025

5500

akan kayantaπŸ’―πŸ’―
Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune;

Atampopi
Laces
Shadda
Materials
Shoes
Bags
Veils
Trolleys
Jewellerys
Oil perfumes

Numbers
08034469681
08135142610

Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries


***********
Sai dare ya dawo gida shi kadai sbd Sayd yana jos acan zai kwana yaje karbo duk wasu takardu da records na Asibitin Zaadens daya boye bayan wanda suka tabbatarda sun karbe daga hannunsa sbd AZIZ da kansa yayi magana da Matar ismail din sbd ya bayyanar mata da kansa tareda sanar da ita komai dan haka da kanta ta kusa cikin kayan Dr ismail ta samo musu duk wani abi da zai dan taimaka musu ciki kuwa hadda date na ranar aikin da time da akai aikin da record din Ummitah na komai da sukai mata tin a asibitin dr ken tareda copies na transactions da akai musu shi da dr ken da tarin kudaden da suka ringa basu masu yawan gaske.


Koda ya iso gida kusan duka kowa ya shige dan haka kai tsaye Bedroom dinsa ya nufa yayi wanka ya sauya kaya zuwa na bacci masu dan kauri ya fito sanye da slippers a kafafunta.

A kaidar aikin Fiddausi indai yana gari to ko karfe nawa zekai bai dawoba zata jira dawowansa sbd gabatar masa da abinci kokuma tea ko wani abinda zai buqata na ci nara nauyi.

Dan haka ko yanxu ma batai bacci ba suna dakin Jannah itada falaq datai bacci a zaune sbd tsaron jannah,ita kuma tana kokarin goge mata jikinta da son sauya mata kaya taji anbude kofar dakin kai tsaye a natse.

Juyowa Fiddausi tayi a natse taga shine take ta ajiye rigar jannah din data zare tana miqewa tsaye da girmamawa tai masa sannu da zuwa.

Falaq ya kalla cikeda tausayawa yaga yanda itama ta fada kafin ya maida kallansa akan jannah wadda take qara ramewa da sauyawa sosai a kwancen.

Numfashi mara sauti yasauke kafin ya tako a hankali ya rankwafa ya dauki falaq gabaki dayanta ya juya ya fice da ita xuwa dakinta ya kwantar da ita ya rufeta da abin rufa yayi mata addua ya kashe wuta tareda daidaita mata ac ya fito ya rufeta ya koma dakin jannah din.

Koda ya isa Fiddausi ta sauya mata riga mara nauyi tana kokarin fara goge mata jikinta.

Tana ganinsa ta ajiye ahankali tareda ficewa daga dakin gabaki daya ta nufi kitchen ta hado masa lemon tea da sabon cake da aka gasa yau na chocolate sai dabino da madara me dumi ko zai saka a tea din tana ajiyewa ta juya ta fice tareda jan kofar dakin.

Zubawa jannah din idanuwansa yayi tsawon mintina kafin ya zauna ahankali tareda miqa hannunsa ya dauki towel din da baa warwareba ya warware ya saka a cikin ruwan zafin masu tsafta sosai da Fiddausin ta ajiye.

Ahankali ya rage ruwan towel din sosai kafin ya yaye rufar datake jikinta ahankali ya dora towel din da hannunsa a fuskanta yana gogewa.

Cikin nutsuwa da mamakin kansa yake goge mata fuskan harya kammala da fuskan ya gangaro wuyanta ahankali yafara gogewa a natse.

Yana kawowa kirjinta kasa wucewa gaba yayi ya tsaya cak a gurin yana saukar da idanuwansa akan aikin zuciyarta yana jin zuciyarsa na sanyi jikinsa na dumi damuwa da tausayin kansa daya rasa macen dayafi kauna
fiyeda komai a duniyarsa,
Ta tafi bazata taba dawowa ba har abada,ta tafi tabarsa da tabo da ciwon da bazai taba warkewaba na rashinta,
Kaunar Ummitah halitta ce da Allah ya halitta masa a cikin zuciya da jininsa,

Ummitah rayuwarsa ce,ruhinsa ce,jinsa da ganinsa ce,
Ummitah itace asalin ABDULAZIZ AYOUB LIMBA ayau daya rasata gabaki daya ya rasa kansa sbd gashinan ya koma tamkar me ciwon haukar juyewan kwakwalwa a boye,
Ya rasa wani bangare na rayuwarsa da har abada bazai taba dawowa ABDULAZIZ dinsa na asali ba sbd rashin Ummitah,

Kaman yanda take kallansa a matsayin uwa da ubanta da kuma hammanta a garesa shima Ummitah itace uwa da ubansa daya rasa da kuma 'ya da kanwarsa gaba daya itace familynsa datake dauke da matsayin kowa da family ke buqata ya cika.

Wasu hawaye masu tsananin zafin da baisan da su bane suka gangaro suka sauka akan fuskan jannah wadda idanuwanta suka bude tsowon seconds goma da suka wuce.

Idanuwanta da basa gani sosai sbd ciwo da dadewa a kwance ta zuba masa batareda ta iya motsa komai na jikinta,

Bata ganinsa sosai amma dai tasan shi dinne dan haka zuciyarta tai wani irin sanyi cikin damuwa da ciwo hawaye masu zafi sika gangaro da gefen Idanuwanta.

Hannunsa ya motsa ahankali ya dora akan zuciyarta dake bugawa cikin sanyi ahankali da nutsuwa tareda wani irin tsananin sonsa datake jin kaman illa ne ma gareta zuwa yanzu sbd ya gama tabbatar mata da bazai taba sonta ba har abada.

Shiru sukai kowannensu idanuwansu jajir da radadin da zuciyoyinsu suke ciki,
Bugun zuciyarta yake sauraro da tafin hannuwansa yana isa ga tasa zuciyar yana jin kaman ya ambace ta da sunan Ummitah ta amsa masa ko zai samu abinda yakeji a kirjinsa na shekaru ya dan fada masa ko zai iya dawowa cikakke lafiyayyan mutum daya rasa lafiya da cikakken hankalinsa....

Itama nata idanuwan har lokacin gangaro da hawaye masu ciwo da zafi sukeyi batareda ta motsaba dumin tafin hannunsa dake kan zuciyarta yana isa cikin zuciyarta yana qarasa mata illar da har abada tasani bazata taba iya dena sonsa ba sbd jinsa takeyi har acikin jininta ba iya zuciyarta ba,

Batasan wane iri so bane wannan wanda yake sakar mata ciwo da radadi ta kasa ciresa a ranta,
Bazata iyaba duk yanda taso hakan sbd son nasa yai mata mummunan illar da ita tata rayuwar ma ta gama mutuwa akansa, dan haka rufe idanuwanta tayi ahankali tana jin inama ta tafiyarta itama ta huta da wannan radadi da ciwon datake ji kila shima zai samu nutsuwar zuciya idan ta tafiyarta tabar masa duniyar.

Ahaka suka raba dare sosai har saida ta motsa kadan ta bude idanuwanta a wahalce sai alokacin ya dago ya kalleta yaga idanuwanta a bude sunyi jajir da hawayen dataita yi tin dazun.

Hawayen dake gangarowa daga idanuwanta yabi da kallo yana yana dauke hannunsa daga kirjinta tareda xare hannunsa daya dayake cikin nata ya juya ya fice baice komaiba ta bisa da kallo.

Nurse din dasuka dauka ne ya turo mata ita ta dauketa takaita toilet tayi fitsari ta gyaro mata jikinta daqyar sbd babu abinda yake motsi a jikin jannah din bata iya motsa komai nata.


Washe gari tinda safe dr Sameera ta iso gidan koda ta iso yana babban palo zaune tareda mama da sai Fiddausi dake kai da kawon aikin hada dining.

Falaq kuwa farin cikin ganin jannah ta farfado ya saka tinda safen ta saka Nurse tai mata wanka aka saka mata riga da wandon jeans marasa nauyi aka turota a kujera jannah dince ta turota suka fito palo jannah din batada karfi ko kadan magana ma bata iyayi bare iya motsawa sai an taimaka mata a komai.

Dr Sameera kuwa hannun AZIZ din da dr Ashir yayi dressing jiya taxo dubawa dan warwarewa ta duba ciki.

Cikin kulawa ta kallesa bayan sun gama gaisawa da mama a sake ta sake kallansa cikin kulawa tace

"Hannun zan duba naga idan zaa sauya bandage dinne"

Mama kallan hannun tayi tana cewa

"Yarsa ce bata lura da hannun ba da yanxu ta daga mana hankali ai"


Murmushi dr Sameera tayi yana miqa hannunta akan hannunsa daya dora mata akan Hannun sofan dayake zaune batareda ya kalletaba yana duba abu a waya.

Nurse ce ta kawowa Sameera akwatin first aid ta kama hannunsa a hankali zata fara warware bandage din su falaq suka shigo palon da jannah wadda idanuwanta da sukai laushi sosai sbd ciwo suka sauka akan hannunsa da dr Sameera ta riqe da sunan dubawa.

Tsayawa falaq tai tana kallan dr Sameera din zuciyarta ba dadi.

Jin shiru ya sakasa dagowa ahankali idanuwansa akan Jannah data dauke idanuwanta ahankali akan hannuwan nasu suka fara sauka ya zare hannunsa daga gyaran yana cewa ba buqatan wani bandage din abar masa hannun haka.

Falaq kuwa qarasowa tai gurinsa da sauri tana kama hannunsa da kulawa tana cewa meya samesa.

Mama kuwa jannah ta tashi ta qarasa turowa har gefenta tana mata sannu da ido kawai jannah ta iya amsawa zuciyarta ba dadi ko kadan sbd ta riga da ta rasa farin cikinta rayuwarta ta sauya daga jannah zad a yanxu batasan ita wace jannah dince ba.


Bata iya sake kallan inda kowa yakeba rufe idanuwanta tai tana sake zama weak yana lura da yanayinta dan haka da kansa ya maidata daki batareda kowannensu yayiwa kowa magana ba ita a yanzu kallansa ma batason yi sbd shine yake qara azabtar da zuciyarta dan haka ta hakura ta bawa zuciyarta salamar hakura da wanda baya kaunar komai daya shafeta.

Yana ficewa wasu hawaye masu dumi suka gangaro mata ta rufe idanuwanta tana tsananin son ganinta cikin familynta dake tsananin buqatanta a lafiya da ciwo.

Shi kansa zuciyarsa daci take masa dan haka ko abincin kirki baiciba yace Fiddausi ta hada kayan jannah din a luggage qarama.


Sayd ne ya iso shima a lokacin latif ya daukosa daga airport dan haka tin kafin ya iso gida a waya ya sanar dashi ABRAHAM da KEN sun sauka a abuja Nigeria dan haka ya saka Fiddausin hada kayan jannah.


Da kansa ya daukota tin daga cikin dakinta a hannunsa ya fito da ita xuwa mota da Sayd ya shirya musu.

Da falaq aka tafi dan haka dashi da ita jannah dinne a bayan motar sai falaq a gaba Sayd na tuqa motar suka nufa zaadens baida niyar barinta acan din amma sbd umarnin mama ne kadai zai kaita kuma a gobe zai dawo da ita limbas.

Suna isa limbas gabaki daya familyn jiran isowansu akeyi sbd sunta kira su sanar masa isowan likitocinta amma sam babu wayar wanda ya dauka sedai suka kira Sayd suka sanar masa wanda yana sane da saukar su Abraham din sbd sun saka tsaro sosai akan isowansu.

Ammar da Mimi take riqe da hannunsa sbd yanda yake kasa riqe zuciyarsa akan jannah dago jajayen idanuwansa yayi yana kallan yanda AZIZ LIMBA yake dauke da jannah a gaban idanuwansa ya wuce da ita ciki ta gabansa ita kuma idanuwanta suna kansa tana masa kallan mamaki da bankwana sbd batajin zata iya komawa gidansa ta hakura da auren sbd zuciyarta bazata iya daukan kallan qinta a cikin idanuwansa ba da kuma yanda tsananin sonsa dayake bayyane a idanuwan Fadilah da dr Sameera dan haka ta zabi dawowa hannun familynta ta qarasa mutuwarta a hannunsu idanma ciwon bame barinta bane kenan.

Har bedroom palonta dayake hade da lafiyayyan bedroom dinta yakaita ya ajiyeta ahankali ta tsaya da kafafunta tana kallansa shima ita ya kalla da idanuwansa dake bayyanar mata da wani tsananin zafin hoton da idanuwanta suka sauka akai na Ammar hakama Ammar dinne duk yanda Mimi taso hanasa isa ga jannah din ya kasa riqe kansa dan haka akan idanuwan AZIZ Ammar din ya shigo palon idanuwansa akan jannah zuciyarsa na samun sassaucin azabar dayake ciki..

Wani kallo Daya saka jannah jin idanuwanta sun ciko da hawaye yayi mata ya bude baki tsananin dayake cikin idanuwansa baya boyuwa zaiyi magana ya fasa sbd zai iya loosing control dan haka Ammar din ya juyo ya kalla ya bude baki yana controlling kansa sbd hannuwansa da suka fara wani irin rawa idanuwansa na sauyawa yace

"Ka tabbatarda wannan kallan shine na karshe akan matar da aurena yake akanta sbd nxt kallo da zakai mata irin wannan shine ganinka na karshe sbd saina tabbatarda an saka maka da dabobbi"

Dad ya kalla yace

"Idan aka take mutuncin igoyiyina wannan shine zuwanta na karshe har abada"

Tsit sukai babu wanda ya iya cewa komai sbd rasa abin fada,

Mimi gurin Ammar da hannuwansa ke rawa sosai ta nufa da sauri idanuwansa na cikowa da hawaye masu tsananin ciwo.

Jannah kuwa tinda AZIZ din ya fara magana idanuwanta suka sauka akan hannuwansa dake wata irin rawa batareda kowa ya lura da hakanba,

Wani abu taji yana danne zuciyarta me tsananin nauyi da ciwo,
A iya saninta datake dashi tasan me wane ciwo ne yake samun irin wannan yanayin sbd akan Ammar ta fara sanin hakan,

A idanuwansa ta maida nata idanuwan tana kallan yanda suka sauya hannuwansa na tsananta rawa yana kokarin controlling kansa.

Jin tayi ta kasa riqe zuciyarta daga azababbiyar soyayyarsa data rufe mata ido har ta bari ya tafi a hakan bazaiyi nisa ba zai iya loosing control na kansa kowa ya san halinda yakeji cewan yana tattare da masifaffiyar trauma shima hakama idan har wannan shine haduwarsu ta karshe data yankewa kanta tana fatar ta kasancewa abinda zata ringa tinawa da ita dashi har abada dan haka ko taku biyu baiyiba ta tattaro karfi a jikinta ta riqosa.

Su dad na ganin hakan shi yafara juyawa ya fice....

AZIZ kuwa dayake gap da rasa control da zafin gaske ya juyo idanuwansa jajir sedai ba zato ta kamo wuyan rigarsa ta ta hade bakinta d nasa cikin wata irin nutsuwa.
#MAMUH

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_*
76
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah πŸ₯°πŸ‘ŒπŸ»
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1kπŸ₯­ Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
πŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALAπŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜πŸ˜πŸ˜ da 5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜ƒπŸ™ƒKazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadΔ±πŸ˜‹800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Infection ruwan tsarki 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 5k kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki



*************
A cikin tsakiyar bakinsa bakinta ya isa direct dumin bakinsu yana haduwa da juna abinda bai taba faruwa dasu su dukanba,

Bai tinda yake bayan kumatu da goshin da hannuwan falaq dayake wa pecks lips dinsa basu taba haduwa da fatar kowaba dan haka shock din dayake ciki ya ninku sbd dumin bakinta daya shiga cikin nasa da kyau yana tayar da duk wata tsigar jikinsa hannuwansa na tsananta rawa ya daga zai janyeta daga jikinsa,
Yana dago hannun ta saka nata tafin hannun a cikin nasa ta riqe hannunsa tana kissing tsakiyar bakinsa da kyau cikin nutsuwa da sanyin daya kashe dukkanin jikinsa wutar ciwonsa na mutuwa sedai tana mutuwa ne da wani sabon masifaffen zafi da tiriri jikin daya sakasa mata wani mugun riqon daya kusan karya qugunta ta bude idanuwanta ta zuba masa ahankali shima ita din yake kalla da idanuwansa da sukai mugun ja.....

Ammar dayake tsaye kasa daukansa kafafunsa sukai wani mummunan jiri ya dibesa Mimi data kasa juyowa sbd yanda zuciyarta ke quna itama hannunsa take kokarin ja ta fice dashi amma sam kafafunsa sun mutu sai jin tayi ya zube a gurin....

Maheer ma da Anny ficewa sukai tin farkon lokacinda Jannah ta kamo LIMBAn,
Mimi ma bata tsaya ganin abinda zai faruba ta juya amma batareda ta saki hannun Ammar ba datake jansa su fice dan haka batasan meya gani ba amma zuciyarta suya take mata saida taji zubewansa ta juyo har lokacin bata kalli inda jannah da AZIZ din sukeba.

Falaq ce ta shigo kai tsaye itama da saurinta sbd ganin kowa na fitowa fuska ba dadi.

Akan Daddynta dayake riqe da jannah din datake riqe da kwalar rigarsa har lokacin idanuwanta suka sauka da sauri ta juya tana jin kaman farin ciki yana rufeta me tsanani.

Sayd ta kira da sauri tace yaje ya fiddowa da Mimi Ammar zad daga palon,

Jin hakan ya saka Maheer da Saleem nufar palon cikin tashin hankalin jin Ammar ya zube.

Shigowansu ya saka Jannah din zare bakinta daga nasa ahankali tana zare tafin hannunta dayake hade da nasa tana kallan fuskansa datai ja gabaki dayanta musamman dogon hancinsa da shima yayi jajir.

Kugunta da yayiwa mugun riqon daya kusan ballata ta dan janye tana jin kaman bazata iya tsayuwa ba tai kasa da kanta tana juyawa sbd jin bazata iya jurewa kallansa ba da idanuwansa dake neman zarar da ita....

Shi kansa jin yayi dakin yana juyawa dashi sosai hakama wani mummunan zafin dabai taba ji ba yaji yana rufesa tin daga kansa har zuwa qafafunsa dan haka bai kallo kowaba ya juya ya fice hannuwansa na dan dawowa da rawarsu sedai dumin dayake tafasa jikinsa yafi karfin rawar hannuwan.


Yana fitowa falaq taji wani irin faduwar gaban ganinsa sbd bata taba ganinsa a hakanba,

Hannunsa ta kama da sauri suna nufar kofar batareda tace komaiba,

Sayd ma yana ganin yanayinsa yayi saurin bude masa mota suka shiga yaja motar suka bar gidan da wani irin speed.

A motar wani irin kokari da karfin hali yakeyi sbd kada falaq ta gane mummunan yanayinsa wanda yau gabaki daya lamarin yafi na koyaushe yakeji sbd duk inda ruwa da jini suke yawo a jikinsa dumi yaji suna dauka tareda tayar da tsikar jikinsa yana rasa ta ina masifar ke bullowa.

Sayd kuwa gudu yake cikin kwarewa sbd su isa kan lokaci batareda kowa a motar yayi magana ba itama falaq ta gane Daddynta na cikin wani halin da baya buqatan magana shiyasa tayi shiru tana qanqame hannunsa da sigar rarrashi.

Suna isa gida Sayd na pakin Latif dake harabar gidan da gudun gaske ya iso budewa AZIZ din mota cikin girmmawa sedai kallo daya yayi masa ya sauke kai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login