Showing 135001 words to 138000 words out of 185083 words
da sauri tana sake riqesa tace
"Wanka ma takeson yi tin dazu sbd ta samu karfi kadan amma ta kasa cire kayanta sbd hannunta daya nima nayi na kasa tin dazu banason taci gaba da wahala so Muje ka tayata Daddy banason ta fama hannunta"
Tsit palon sukaj hadda Sayd dayake zaune gefen mama bai dagoba yaci gaba da duba abinda yake dubawa cikin ipad din hannunsa.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
72
*UMMU_MAHNOOR LUXURIES*
(Best luxuries shop)
08034469681
08135142610
Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini?
Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka?
Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu?
Sitirar Alfarma kikeson sakawa?
Sitirar da kike ganin manyan mata da ita?
Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota?
To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida,
Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu,
Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯
Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune;
Atampopi
Laces
Shadda
Materials
Shoes
Bags
Veils
Trolleys
Jewellerys
Oil perfumes
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
***********
Mama dagowa tayi ta kalli falaq din kaman ta janyota ta bude kanta ta saka mata sanin ya kamata sbd kai tsaye take maganar komai bata tsayawa sanin me take fada ba ruwanta.
Fiddausi silalewa tayi ya koma kitchen,
Fadilah kuwa AZIZ din ta sata kallansa zuciyarta na harbawa sbd bata fatan ya ya tafi taimakawa jannah din sbd a sani da fahimtar dataiwa auren nasu da kyau da kyau bai taba kallan Jannah din a matsayin matarsa ba dan haka ba lallai sun taba samun intimacy ba.
Muskutawa ta dan yi kadan tareda kallan Falaq tana dan sake fuska tace
"Ayya ai duk bamu saniba da duka gami xamu taimaka mata,
Bara naje na taimaka mata din"
Miqewa take kokarin yi Falaq tai saurin cewa
"No,Daddy ne zai tafi ni banason kowa ya taimakawa Jannah daga ni sai Daddy se Fiddausi"
Da sauri fadilah tace
"To bari na kira Fiddausin taje ta taimaka matan"
"I said no banason kowa a yanzu,
Daddy ne zaije ai daman bai dubata ba yau da safen"
Mama da zancen yake neman sakata kunya kallan AZIZ din dayake barin palon xuwa hanyar nasa palon tace
"Kaje ka dubata mana AZIZ taji jiki fa yarinyar kuma ya kamata a sanar da iyayenta duk da zanji kunyar su ganta a yanda take yanzu"
Falaq da tini tai raurau zata fara masa kuka ya kalla yana juyawa zuwa hanyar dakin Jannah din da baida niyar sake shigansa.
Yana shiga dakin ta bude idanuwanta dake rufe ahankali ta kallo kofa tana motsawa kadan.
Ganinsa ya sanyata fara kokarin tashi zaune daga jinginen datake a tsakiyar gadon tanajin gabanta na dan faduwa da fargaba.
Kallo daya yayi mata ya dauke idanuwansa akanta yana Nufota.
Ganin ya nufota ya sakaya yaye rufanta tana ziro kafafunta kasa ta miqe hannuwanta na dan rawa sbd fargaba da shakkarsa data riga ta shigeta.
Yanda kafafunta ke rawa yasaka tsayuwar ta gagara tana neman zubewa ya sake riqota a karo na biyu yana kallan idanuwanta da itama shi ta dago tana kallo cikeda fargaban ko fada zaiyi mata.
Yanda take kallansa tsoronta na bayyana hakama yanajin yanda zuciyarta ke bugawa a kirjinsa ya sakasa dauke bude baki har saida iskan cikin bakinsa ta bugi fiskanta ahankali da wani sanyayyan qamshi mouth wash dinsa da sauti me nutsuwa ba hayaniya yace
"Kina koyawa yarinyana sakani yi miki abinda kikeso a tilas ne???
Kina amfani da ita ne??
Girgiza kai tai a hankali tana sake kallansa idanuwanta na kokarin cikowa da hawaye.
Cikin tsakiyar idanuwanta ya kalla har lokacin tana jikinsa yana karban bugun zuciyarta a nasa kirjin.
Bai sake cewa komaiba ya saketa ahankali tareda kama rigarsa datake jikinta har lokacin tai mata yawa sosai yafara dagowa ahankali yana kallan cikin idanuwanta.
Jin rigarsa datake jikinta zai cire ya sakata saurin sauke idanuwanta ahankali daga kallansa tana jin bugun zuciyarta na qaruwa.
Rigarta qarama ce ta ciki taji tabi rigar dayake kokarin cire mata da sauri ta dora tafin hannunta akan hannunsa tana rufe idanuwanta ahankali kanta a qasa.
Dumin dayake cikin tafin hannunta ya sakasa dagowa ya kalli hannun nata dayake kan nasa ta dafe kafin ya zuba mata mayun idanuwansa akan fuskanta data kasa bude ido ta kallesa.
Sake damke hannunsa tai zuciyarta na bugawa da karfi sbd jin idanuwansa akanta suna azabtar da ita.
Sake jan rigar tayi zuwa sama har lokacin hannunta yana kan nasa ta kasa daukewa sbd tana jin cinyoyinta na bayyana.
Yana dago rugar tana zuwa daidai gurin da cinyoyinta suka qare ta bude idanuwanta ahankali ta kallesa cikin tsananin sanyi da wata lallausan muryanta datai laushi can qasa ta bude baki tace
"Please"
Dakatawa yayi yana kallan bakinta da yayi maganar kaman ba ita taiba.
Ahankali yakai idanuwanta ya kalli abinda take nufi,
Kallo daya yayiwa cinyoyinta dake wani daukan idon haske da lafiyarsu ya dauke idanuwansa yana sakin rigar gaba daya tareda sakinta tai saurin zaunawa vakin gado itama tana kasa sake kallansa zuciyarta na narkew da qamshinsa daya gama shigarta tako ina.
Juyaw yayi zai fice daga dakin daidai falaq na knocking tareda budewa ta shigo tana kallansa tace
"Daddy baka taimaka mata ba?
Kama hannunsa tai suka dawo dashi da ita suka zarewa jannah din rigar batareda jannah din ta bari an zare data cikinba dan haka suna zarewa ya juya yabar dakin sbd rigar jikinta ta cikin ko bra barada ita ta lafe jikinta sosai tana bayyanarda abinda idanuwansa basu taba gane masa.
Su kuwa toilet Jannah ta tashi ta shige tana jin kaman ta samu dan karfin jikinta sbd ba qaramin so zuciyarta kewa AZIZ LIMBA ba wanda ko tsayuwa yayi a gabanta jin take kaman zuciyarta ta gama samun abinda takeso.
Shi kuwa yana fitowa palonsa ya nufa ya kira Sayd.
Tsayuwa Sayd yayi gabansa yana jera masa bayanin Dr Abraham yana inda suke jiran ya baro su kamasa haryanzu bai baroba dan haka suna buqatan qarin lokaci.
Shiru AZIZ din yayi yana sauraron bayanin Sayd wanda bayajin zai iya jiran lokacin da ake magana sbd komai zai iya lalace masa,
Zai tsani kansa tsana mafi muni idan yabari wani lamarin ya shigo ya lalata masa aikin daya kawosu,
Bazai taba yafewa kansa ba idan har ya sassautawa duk wanda yakeda hannu a kisan Ummitah dan haka bazai jira bata lokaci ba zaiyi abinda ya kawosu su tattara su koma sbd zuciyarsa bazata taba karban wani baqon yanayiba kowane irine.
Dago idanuwansa da sauka dan sauya yayi fuskansa ba sakewa kai tsaye cikin kamewa yace
"Zaadens zasusan batada lafiya sosai dan haka da kansu zasu nema zuwan likitocinta duka a cikin gaggawa wanda basu kowa bane face su ABRAHAM da 'dansa sai dayan da muke nema wato KEN,
Dukkaninsu zasu bayyane idan Zaadens hankalinsu ya tashi akan ciwon zuciyar da aka dade rufe maganar ciwonta"
Sayd ne ya dago ya kallesa cikin girmmawa yace
"Amma a yanayinta yanxu ta samu dan saukin da zai hanasu shiga tashin hankalin da ake buqata"
Batareda ya kalli Sayd dinba cikin nutsuwa yace
"Zan bata wani heart Attack din dazai kawo hakan"
Gyada kai Sayd yayi yana cewa
"Komai zai zama ready akan hakan insha Allah"
Gyada kai kawai yayi yana dan dafe goshinsa da yayi nauyi kadan.
A can dakin jannah din tai wanka ta dan samu kwari ta fito da taimakon falaq ta dan shirya cikin doguwar riga mara nauyi ko wahalan sakawa ta ranka sallolin dake kanta Fiddausi da falaq ne suka bata abincin cikeda kauna da kulawa ta koshi tasha magani bacci me dadi ya dauketa tana dan samun nutsuwar zuciya.
Har dare su Fiddausi da falaq ne ke bata kulawa sosai harma da mama da itama take nuna kaunar datake mata sosai wanda ya sakata sake samun karfi sosai tana sake warwarewa.
Dr Sameera da dr Ashir sunzo sun dubata dan haka ta sake samun saukin sosai,
Da daddare bayan ya dawo gidan babu wanda ya sani saida ya fito dinner a lokacin ne sukasan da yana gidan gashi kusan 9 tayi.
Falaq ce ta rakasa dining yanacin abinci tana masa labarin yanda jannah take samun sauki yana sauraronta batareca yace komaiba sbd duka zancen Falaq din yanxu na Jannah ne.
Yana gamawa ta jasa suka nufi dakin Jannah din wadda take zaune sanyeda riga da wandon bacci masu santsi batar qarasa rufe botiran gaban rigarta ba tana ta kasa sbd hannunta daya da baya aiki.
Qamshinsa daya shiga hancinta ya sakata qin juyowa sbd ta kalli wanda ya shigo sbd tasan shi dinne.
Ahankali ta saka hannunta daya ta dafe gaban rigarta daya bude sbd bata saka botiran ba gashi babu bra a jikinta.
Falaq kallan Daddyn nata tayi zatai magana Fiddausi tai knocking kofar a dan kiyaye cikin nutsuwa da gudun masa hayaniya tace
"Mama na kiran falaq"
Juyawa falaq tai ta nufi kofa ta fice tana cewa
"To ni me zan mata"
Tana rufe kofar numfashin jannah yayi sama tanajin bazata iya tsayawa ba a dakin itama ta miqe ahankali tareda juyowa tana jin son barin dakin itama wayarta tayi haske tana vibrating akan table din dayake gabansu.
A tare suka saukan da idanuwansu ahankali kan wayar video call ne daga Ammar Zad.
Kasa motsawa tai tana kallan wayar gabanta na dan faduwa.
A natse ya dauke idanuwansa daga kan wayar yana takowa zuwa gareta.
Tsananta shiga faduwan gaba tayi dan haka ta cire hannunta daga gaban rigarta data dafe ta miqa kan wayar da sauri ta dauka sbd tasan daukan wayar kawai zai saka AZIZ barin dakin shikuwa ba tsammani ya dora hannunsa yana hade kirjinta da nasa yana dafe rigar data sake tana mantawa sbd rikicewan datai.
Hakan ya sakata sakin wayar yannunta kan sofa data bawa Ammar daman ganinta Manne a jikin AZIZ LIMBA yana mata wani irin kallo fuskansa ba sakewa ko kadan.
Kirjinta ta kalla a hankali taga rigar ma kaman ta bude gaba daya amma komai baa gani nata sbd yanda kirjinsa ya rufeta gabaki dayanta hannunsa daya yana zagaye da ita.
Dagowa tai ta kallesa tanason janyewa yayi mata wata irin riqon daya sakata rintse idanuwanta cikin zafi.
Ahankali yakai bakinsa a kunnenta zaiyi magana dumin numfashinsa daya fara sauka a cikin kunnen ya sakata qanqamesa batareda tasan tayi hakan da wata irin murya me tafe da zafi a natse yace
"Kinada hankali kuwa?
Are really ok a cikin kanki kuwa?
Kin saba hakanne kokuwa?
Ashe rashin tarbiyan naku ya wuce hankali har haka?
A tsakanin ni dashi waye kike kokarin nunawa jikinki da zaki dauki wayarsa a wannan yanayin???
Kokuwa ke dashi din k......
Bai qarasaba zuciyarta ta kasa daukan maganganunsa sbd yanda jikinta ke rawa sosai cikin mummunan yanayin yanda kalamansa ke dukanta.
Wani mummunan bugu zuciyarta keyi hannuwan ya tsananta rawa ta zube a jikinsa hawaye na gangarowa gefen idanuwanta.
Ammar da shedan ya hanasa kashe wayar yana ganin yanda AZIZ yake fada mata magana a kunnenta har jikinta ya sake batareda yasan meya fada mataba.
Kashe wayar AZIZ ya miqa hannu yayi yana dawo da kallansa kan fuskanta kalaman daya furta mata suna tafasa cikin kwakwalwansa ya dauketa cak ya dora a gado ya ciro wayarsa ya kira Sayd yace ya kira doctors ta samu collapse.
Yana kashe wayarsa wayar Dzad ya saka kira take ya sanar masa Jan din tayi collapsing a karo na biyu tsakanin shekaran jiya zuwa yau.
Zaune Dad din yake ya miqe tsaye a hankali yana cewa
"Wat?
A cikin kwana biyu tai collapsing so biyu baa sanar mana ba?
Heart patient ce ita fa,
Innalillahi wainnna ilayhi rajiun"
Maheer da Daddy mahmoud dasuke tareda Dzad din kallansa sukai kowannesu na jiye wayar hannunsa gefe.
Ammar kuwa Daqyar zuciyarta tabar idanuwansa gani sbd tafasa da radadin da zuciyarsa ke yi ya iso palon ya tadda abinda ake fada.
Wani yawun tsananin tashin hankali da baqin ciki ya hadiye
Dad ya kallesa yana cewa
"A kira su Dr Abraham sbd kasan babu wanda zaa bari ya dubata dole zaa buqaci record na ciwonta wanda babu saka hannun familyn donor dinta a ciki so kota halin yaya bazaa bari wasu likitas din ba su dubata sai nata,
Amma kafin nan muje ka fara dubata kai kanka"
AZIZ Yana gama waya da zaadens Sayd ya kira yace
"Ka shirya komai Ken na sauka Nigeria nake buqatansa kafin ma Abraham din"
Kashe wayarsa yayi yana zaunawa bakin gadonta ya zubawa fuskanta ido yana jin zuciyarsa na nauyi.
#MAMUH
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
73
*UMMU_MAHNOOR LUXURIES*
(Best luxuries shop)
08034469681
08135142610
Aslm Alaikm ina kuke masu neman luxuries na kayan alfarmar kece raini?
Ina masu son su saka sitirar alfarma ta zamani ta manyan mata masu aji da zaa kalleki kallo daya asan sitirar alfarma e kika saka?
Shin kunsan me ake nufi sa kayan asalin yan gayu da nuna gayu?
Sitirar Alfarma kikeson sakawa?
Sitirar da kike ganin manyan mata da ita?
Sitirarda zakiyi gayun sallah dake da yaranki a dauka waje kikaje da kanki kika siyota?
To kizo ga damarki ta sameki sbd UMMU_MAHNOOR LUXURIES ta kawo miki sauki har gida,
Karkice se masu kudi ke iya siya har kema me yar dama zaki samu naki da saukin kudi kuma best quality da kalar zamani data yan gayu,
Nidai Mamuh nace duk wadda ke son a buga gayun sallan bana da ita da 'yayanta to tazo gurin UMMU_MAHNOOR LUXURIES tai siyayyar sallanta harma zuwa gaba dan nasan zakuji dadi da fahimtar abinda nake fada akan kayanta💯💯
Abubuwan da zaki samu a gurinta with the best quality na wayayyun mata masu aji yan gayu sune;
Atampopi
Laces
Shadda
Materials
Shoes
Bags
Veils
Trolleys
Jewellerys
Oil perfumes
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
**************
Maheer ne da kansa ya nutsu a cikin daren ya kira Abraham ya sanar dashi abinda yake faruwa sbd suna buqatansa duk da Ammar yana nan amma sunsan damuwa da tashin hankali zai iya hanasa nutsuwar dubata yanda yakamata.
Basu sanar da Mimi ba a cikin daren Motar Dad tareda Saleem daya jasa tabar Zaadens zuwa limbas,
Motarsa na ficewa ta Maheer tabi bayansa tareda Daddy mahmoud
Sai ta Ammar a bayan tasu suka nufi Zaadens din gabaki dayansu damuwa a cikeda kirjinsu da fargaban idan ba ciwon dasuke fatan sun rabu dashi bane kwata kwata yake kokarin dawowa ace itama wannan zuciyar datake kirjinta tanada matsala ko me??
Koda suka iso limbas Securities sun san da zuwansu wanda Sayd ya sanar masu tareda umarnin daya san ko LIMBA bai fadaba shine abinda yake daidai a mansion din nasu.,
Dan haka motar Dzad na isowa da sauri Securities suka bude masa gate ya saleem ya sako kan motar ciki,
Motar Maheer ma sako kai tayi a ciki shima da gudu yana parking gefen motarsu Dzad.
Motar Ammar na sako kai chief Security na Securities din gidan ya taso yana bada umarnin a rufe gate din yana kallan Motar ya qaraso fuskansa ba rahama ko kadan Kaman zai dauki rai a gurin yake jinsa da hannu yayiwa Ammar din alaman ya sauke glass.
Wani kallan qyama da Mamaki Ammar din ke masa tareda tsanar duk wani abin dayake cikin limbas din da dukma wanda yake gidan tin daga kan Securities har asalin masu gidan tsana me girma yake jin yana musu sbd shi kadai yasan yanda yake jin zuciyarsa daya taho sbd Jannah amma badan hakan ba zai iya zabar zuwa ga azaba akan zuwa limbas dayake jin tsananin tsanarsa da zafinsa.
Aron da bai damu da komaiba sai umarnin da aka basa dan kuwa sedai ayi ruwan albarushi a guri idan har umarni suka sauko daga LIMBA to haka zaayi kuwa koda ana mutuwa a shirye suke da mutuwa da kashewa akansa dan haka ganin Ammar din yaqi sauke glass yana jiran su bude masa gate ya saka Aron din komawa gurin zamansa yana cewa Securities din
"Mamas boy da alama bai san yana bakin limbas bane,
Idan bai sauke glass nasa ba daga nan har saiya gaji ya koma inda ya fito kada matansa ta qara ko inci daya zuwa gaba,
Idan ya qaro gaba zuwa ciki just Shoot"
Ammar dayaji abinda daya fada Dago idanuwansa da sukai jajir yayi yana kallan gate din Limbas din zuciyarsa na tafasa da narkewa ahankali sbd tinda aka haifesa ya taso cikin gata da buga lokaci tareda juya abinda yakeson ya juya yanda ransa yakeso batareda shakka ko umarnin kowaba sbd suna juya duniyarsu ne da hannunsu yanda suke sonta sbd sune ZAADENS,
ZAADENS da kowa yake shakka da tsoro,
Ayau shine a gaban gidan wani ana rufe masa gate tareda bada umarnin a harbesa idan ya qara gaba,
Duk gwagwarmayar da yayi akan jannah da ciwonta yana tashi a banza ne ko me?
Ya sadaukar da lokacinsa da kuruciyansa gurin komawa baya a karatu,
Ya sadaukar da imaninsa ya koma makashin gaske,
Ya sadaukar da rayuwarsa ya ture lokacin komai na rayuwarsa ya bayar duka akan macen da zai iya bata rayuwarsa amma a lokaci daya wani yana tsayar masa da dukkanin iyakansa akanta ta hanya mafi ciwo.
Jajir idanuwansa sukai wani irin radadi me sanyi da ciwo na cike kirjinsa ya rintse idanuwansa hannuwansa dake riqe da steering suna dan rawa cikeda radadin dayake gauraye koina a jikinsa.
Securities kuwa gabaki dayansu tsaye suke da bindigoginsu sunfi su goma babu wanda baa shirye yake da harbi ba sbd yana motsawa ruwan bullet zasuyi masa su kuma ce Shine yayi intruding dan haka sun harbesa a matsayin suspect dayayo cikinsu da mota da niyar barazana ga rayuwarsu so a taiqace sun harbesa as self defence.
Su Dad kuwa Sayd ne dayake harabar gidan ya tarbesu a natse suka isa ciki.
Dayake dare ya danyi su mama gaba daya sun shige dan haka kai tsaye dakin Jannah din suka nufa tana sanye da kayan sanyin da AZIZ din ya dora mata akan kayan dayake jikinta tana kwance babu abinda yake motsawa ajikinta hatta bugu da fitar numfashinta kaman babu ko daya.
Dukkaninsu kallo daya sukai mata suka dago cikeda matsanancin tashin hankali da mummunan yanayi suka kalli AZIZ daya kallesu hankalinsa ba alaman ya damu da yanayinsu.
Dad ne ya tsaya akanta yana kallan yanda idanuwanta sukai zurfi hancinta ya qara tsayi dosai