Showing 81001 words to 84000 words out of 185083 words
dayake dauke da tea set da dabino dayake cikin bowl me kyau tana qarasawa cikin office da mugun gudu taga jini a tissue koina....
Ihu ta kurma wanda ya saka mama fitowa da sauri Falaq data mugun firgita ma bayan maman ta biyo tana roqe rigar maman sbd tsoro suka nufo office din.
Da gudu Fiddausi ta kwaso tissues din da hannunta a rikice ta nufo su maman tana nuna mata jinin dayake jiki sosai bakinta na rawa tace
"Sir LIMBA ne Sayd ya fita dashi jini yana fita jikinsa sosai baya numfashi kaman ba rai a jikins......
Bata qarasa ba Falaq dake bayan mama cikin tsoro ta fito tana kallan hannun Fiddausin muryanta na rawa sa sauri tace
"Daddyna??
Meya samesa?
Meya faru dashi??
Kikace ya mutu....??????
Bata qarasa ba ta kirjinta yayi mummunan bugawan data yanke musu jiki a gurin tai collapsing.
Sabon tashin hankali suka shiga wanda ya saka mama duk rudewa tana cewa
"Uban waye yace ki kafa a gabanta ne Fiddausi"
Daukanta Fiddausi tayi da duka karfinta tana nufar cikin gida da ita mama na bin bayansu tana kwalawa Nena kiran ta kawo musu ruwa da sauri.
A palo suka kwantar da ita nena ta kawo ruwa da sauri suka zuba mata amma sam ba alamar zata tashi hankali tashe suka dauketa zuwa asibiti mama nata kiran Sayd sedai sam baya dagawa sbd baima san tana kiranba sbd koda ya isa asibiti AZIZ ya zubarda jini sosai dan haka take aka karbesa da gaggawa akai ciki dashi sbd shock ne da attack daci uban wanda ya shiga ko lokacin da ya samu labarin rasuwarta.
Sosai hankalinsu dr Raheem ya tashi sbd kokarin ceto Ransa da suke sedai baya alamar yana karban treatment din dan haka suka sauya method cikin gaggawa kwarewa.
Sayd kuwa ana shigewa da AZIZ din zubewa yayi gurin a qasa yana cusa kansa cikin kafafunsa tareda fashewa da wani irin kuka me karfin gaske yana dukan kirjinsa dake wani irin azababben radadi da ciwon kwatanta azabar da Ummitah ta shiga kafin rasuwarta,
Da ranta aka zare mata zuciyar datake bugawa a kirjinta batareda wata nakasa ba,
Da karfi da yaji aka zare mata zuciyar da Allah ya halicceta da ita,
Kasheta akai kisa mai ciwa da radadi batareda taga ko abinda ta haifa da kanta ba....
Wani gawurtaccen kukan ya sake sakewa radadin da zuciyarsa da kirjinsa ke masa suna tsanantar da shima ya kasa riqewa ya fara dafawa zai miqe sedai gangar jikinsa kasawa tai ya zube a gurin yana fasa kukan dayake fitowa tin daga tsakiyar zuciyarsa dayakejin inama tasa zuciyar aka cire aka bar Ummitah da tata.
Gaggawan zuwa akai shima aka kwashesa zuwa emergency sbd ganin irin yanda namiji babba kuma kakkarfa kamarsa da bai rasa komai na jin dadin duniyaba yana kuka sosai yana shidewa ga gangar jikinsa tana kasa daukansa.
Ana shigewa dashi su mama na isowa asibitin da falaq wanda itama aka karbeta sbd patient dinsu ce dan haka baa shiga emergency da ita ba ita dakinda zaa kwantar da ita aka nufa da ita da sauri acan suka fara bata taimakon gaggawa duk da sunsan abune me wuya ta farfado yanzu din.
Su mama da basusan nan asibitin su AZIZ suke ba zaman jira suka fara cikin tashin hankali da damuwa kala kala kuma har lokacin bata dena kiran wayar Sayd ba.
Rin suna zaune har suka kasa zaman sai kaida kawo suke, shima suka gaji suka fita suka dawo babu zancen komai hakama ba bayanin komai akan AZIZ.
A asibitin suka kwana cikin masifaffen tashin hankalin daya gama rikice musu..
Guraren 6 na safe Sayd ya farfado cikin hayyacinsa ya tashi zaune yana rintse idanuwansa sa sukai tsananin nauyi da kansa.
Ya jima a zaune nurses na sake dubasa kafin dr Raheem yazo ya sake dubasa ya sanar dashi Falaq na asibitin tin daren jiyan itama aka kawota.
Yanajin hakan ya dago da sauri sbd take yasan ansake triggering ciwonta kenan..
Saukowa gadon yayi ya nufi toilet din dakin cikin karfin hali da jarumta yayo alwala ya fito a dakin yayi sallah.
Yana gama addua ya dauki wayarsa dake gefen gadon yaga kiran mama sunfi guda hamsin.
Miqewa yayi yana sallamar kansa ya fice daga dakin ya nufi gurinsu mama wainda suna ganinsa Fiddausi ta miqe tsaye tana zuba masa duka idanuwanta jiran abinda zai fada.
Mama kuwa da tini itama ciwon zuciyarta yaketa kokarin tashi sbd tashin hankali da damuwa kasa tashi tayi daga zaunen ta zuba masa idanuwanta da sukai ciki sbd damuwa da rashin baccin da sukai a daren.
Muryansa datai tsananin nauyi sbd yanayinsa ya bude baki yace
"Mama yaya falaq?
Meya sameta?badai collapsing tai ba??
Mama data rasa wace tambayar zata amsa tace
"Daddynta dataji ba lafiya ta zube,ina AZIZ din?yaya yake,meya samesa??
Shima a qataice ya amsa tambayarta da cewa kawai attack ne ya samu amma insha Allah zuwa yanzu ma ya samu dawowa daidai.
Juyawa yayi ya nufi dakin da falaq take yaga tana kwance sanyeda wasu abubuwa da aka daura mata.
Rintse idanuwansa yayi yanajin wani irin nauyi da qunci na danne kirjinsa na tinawa da suna tsaye a kofar dakin da ake ciki ana cirewa Ummitah zuciyarta suna gadin banza batareda sun saniba a wancan lokacin...
Juyawa yayi da sauri yabar dakin ya nufi waje gaba daya ya isa mota ya bude ya fada tareda rufewa yana dora kansa a steering yana dafe kirjinsa da hannuwansa duka biyu sbd ciwon dayake masa sosai..
A wannan lokacin da ake cirewa Ummitah zuciyarta da abu ne da Allah zai nuna musu zai fasa kofar dakin ya shiga ya cinnawa gabaki daya likitacin dake ciki wuta batareda ya bar hakan ba dan zai iya tada asibitin gaba daya daya bari a taba ko kirjin Ummitansa bare rabata da ranta karfi da yaji.
Dukan kirjinsa yake da karfi idanuwansa na cika da hawayen da suka qafe sunma kasa gangarowa sbd radadin dayake cikinsa.
****Acan ciki kuwa Karfe goma AZIZ ya bude idanuwansa ahankali da suke jajir kamar wanda yayi shekara a cikin matsanancin hali...
Akan fuskan Mama datake zaune a dakin ya sauke idanuwansa batareda ya kyafta ba,
Tasowa mama tayi ahankali tana kallansa cikeda fargaban ganin jan idanuwansa.
Bakinta ta bude cikeda tsananin kulawa da kauna zatai magana ya rigata a hankali da wani irin sauti me tsananin sanyi da rashin hayaniya yace
"Mama wani irin kewana Ummitah tayi a lokacin da bana nan kafin kafin rasuwarta,
Wane irin yanayi ta shiga a lokacinda ciwon ajali ya taso mata???
Cak mama ta tsaya cikeda matsanancin mamaki da tsoro sbd tinda akai rasuwar a tsawon shekarun bai taba ambatar kalma daya data danganci rasuwarta ba bare yanda ta rasun suma sunyi shiru sbd bai taba tambaya ba ko maganar sai yanzu kwatsam taji tambayar kamar saukan aradu..
Dago idanuwanta tayi ta kallesa shima ita yake kalla har lokacin batareda komai ya motsaba a jikinsa wanda ya saka gaban mama mugun faduwa tana nufosa da sauri sbd tsoron idan ba paralys dinne ya kuma samu ba.
Hannunsa ya daga ahankali ya dakatar da ita yana rintse idanuwansa sbd bayason motsawa ko kadan sbd wutar datake cin jini da gangar jikinsa tareda zuciyarsa.
Dakatawa tayi tareda zaunawa ahankali kan kujera idanuwanta na dan sauyawa sbd itama harga Allah batason tina rashin Ummitan da sukai.
"Kafin tasowan nakudarta tinda kabar qasar Ummitah bata taba samun lafiya ko sauki ko kadanba,
Ciwone yake cinta wanda muka rasa gane kona mene,
Rama takeyi jininta na tsotsewa tana komawa ba kyan gani,
Bata iya ci bata iya sha,bata iya yiwa kanta komai sai yanda akai da ita,
Duka wannan ciwon a jikinta yake amma a zuciyarta kaine kadai abinda zuciyarta ke tsananin buqatan gani da kasancewa sedai mun hanata barin kasan halinda take ciki sbd kada hankalinka ya tashi amm.........
Wasu hawayen da babu wanda ya taba ganinsa dasu ne duk duniya suka gangaro masa ya rintse idanuwansa yana damqar bargon dayake rufe da jikinsa wata irin wuta me tsananin zafin gaske tana cin zuciya da gangar jikinsa....
Cigaba mama tai itama idanuwanta na gangarowa da hawaye sbd yaune ranar data samu damar fadar ciwonta da radadinta na rashin Ummitah tareda shi hawayenta na saukowa bayan shekaru itama tace
"Ummitah ta rasu da tsananin ciwon rashin ganinka ko jinka,
Ta tafi batareda ta saka abinda ta haifa tabari ba,
Ta tafi da tsananin tausayinka bana kanta ba,
Kaine damuwarta,kaine a ranta,kaine a tinaninta kaman tasan tafiya zatai tabarka....
Kasa cigaba da magana maman tayi ganin yanda yake kuka sosai abinda bata taba gani ba a rayuwarta,
Tin yana yaronsa Allah yabasa wani irin karfin halin da baya kuka hakama duk gwagwarmayar daya shiga ta rayuwa baya kuka amma ayau kuka yakeyi sosai dukkanin jikinsa na jijjiga.
Kukan takeyi itama sosai na tsananin tausayinsa sbd tana kwatanta irin radadi da azababben ciwon dayake ji..
Sayd da Fiddausi da fahad daya iso tareda dr Raheem da suke kofar dakin dukkaninsu tsayawa sukai jigum jigum babu me motsawa zuciyoyinsu na sanyi da shiga wani irin damuwa da tsananin tausayinsa sbd suna jin kukansa daya saka gabaki dayansu tsikar jikinsu tashi sbd yau ne Allah ya basa ikon fasa kukan rashin Ummitansa wadda sun san tsawon shekarun nan ciwo da gyambon hakan na nan a tsakiyar zuciyarsa sai yau Allah ya basa ikon fashewa tinda ya samu ya fasa kuka.
Fiddausi ma kasa riqe kanta tayi kukan takeyi sosai mara sauti sbd tsananin tausayi da yanda su kansu rashin ya dawo musu sabo.
Fahad ma hawayen ne suka cika idanuwansa sedai basu saukoba,
Sayd jajir idanuwansa sukai ya sunkuyar da kai kukan AZIZ din na ratsa zuciyarsa yana yankawa..
Dr Raheem kuwa sanyi jikinsa yayi sbd jin kukan wanda yake ganin yafi duk wanda ya sani taurin zuciya da kamewa a rayuwarsa dan haka shima ya kasa shiga sbd wannan moment din babu wanda ya kamata ya kasancesa idan ba mahaifiyar tasa ba wadda ita kadaice a ciki kuma ita kadaice ya kamata taga kukansa.
#MAMUH
#BEST REVENGE
#VILLAINS ARE MADE NOT BORN
#AZIZ AY LIMBA
#ZAADENS
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
mamuhgee
A DUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo
Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi
Shedan biya
09033181070
Or mtn vtu at
09032345899*_Arewabooks@Mamuhgee_*
43
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC (kayan mata)
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa niβima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah π₯°ππ»
Bononza Bononza Tsimin mangoro 1kπ₯ Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 4200
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
π£οΈπ£οΈπ£οΈπ£οΈπ£οΈπ£οΈ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALAππ½ππ½ππ½πππ da 6k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata ππ½ππ½ππ½ππKazar gadali ta mallara Rabi 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadΔ±π800 Garin 7in1 1k Gumba 3 balai 500 Gumba kwakwa da dabino 500 Na Infection 1k Garin zunzurutun dadi 1200 Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 12k All at 6k https://wa.link/l1gcz8 kedai dannan link dinnan don samun naki ki maza kiyi bucking koda kudinki saida Rabonki
****************
Sun dauki lokaci sosai ahakan babu wanda ya iya doguwar motsi zuciyoyinsu a jagule da damuwa da mutuwar jiki,
Dr Raheem ne yabar gurin yabarsu suji da damuwan dayake damunsu gavaki dayansu sbd ya lura matsalar ta taba zuciyoyin kowa a familyn dan duka kallan family daya yake musu wanda kaf dinsu basu hada alaqar jini ba kawai kaunace data hadu ta zama kamar jini daya da babu sirki.
Sayd yafisu zama abin tausayi sedai yafisu karfin halin riqewa a zuciyarsa kansa na sunkuye har aka dauki lokaci sosai kafin sukaji tsit a dakin babu sauti komai bayan mama tagama fayyace masa labarin yanda sukaita fama da yanda dr ken ya turasu zaadens hospital ta qarasa fayyace masa cikin radadin tinaw da ranar har saida takao ta kasa cigaba da magana ta bude kofar dakin ta fito idanuwanta jajir tana share fuskanta da tissue ta janyo kofar dakin ta rufe tana bude baki a sanyaye tace abarsa shi kadai tukuna.
Wucewa tayi zuwa dakin Falaq ta zauna tana sauke ajiyan zuciya wani abu daya danne kirjinta da dadewa taji ya yafa mata sbd daga karshe yau dai tayi maganar Ummitah da AZIZ wanda takejin sassaucin ya zai samu sassaucin shima tinda ya samu ya furta kuma ya saurara.
Fiddausi ma datasha kuka sosai a sanyaye ta shigo dakin ta nufi toilet ta wanko fuskanta ta fito ta zauna tana duba wayarta da akaita kira batama saniba.
Acan ma fahad barin asibitin yayi ya koma office Sayd kawai aka bari kofar dakin zaune shiru.
Wutace ta gama cinye zuciyarsa tas yakeji ta tsananin qi da zafin Zaadens da baida tabbacin a cikinsu wayene zuciyar Ummitah take bugawa a kirjinsa duk da suna zargin JANNAH ZAD ce sedai kuma ba lallai ita din bace da kuma son sanin waye Dr zad din da ake fada amma dai koma waye aka kashe Ummitah dan a rayasa tabbas bazai taba farin cikiba a rayuwarsa.
Wuni guda babu me shiga dakin da AZIZ din yake har Sayd kuwa sbd ya hana kowa ya shigowa garesa bayan dr Raheem wanda ya sallamesa dan haka babu wanda ya gansa saida ya bude kofar dakin ya fito da kansa sanye da kayan sanyi tareda fcap da facemask daya rufe fuskansa.
Ahankali yake takawa cikin nutsuwa Sayd ya taso yana masa sannu tareda fahad wanda shima ya sake dawowa.
Mama ma da Fiddausi sannun sukai masa babu wanda ya amsawa da baki sai kansa daya dagawa kowa a hankali cikin nutsuwa suka nufi mota batarea da ansanar dashi falaq na asibitin ba sbd kada abin yayi masa yawa.
Sayd ne ya bude masa mota ya shiga ya rufe tareda zagayawa ya shiga gaba fahad kuma ya shiga mazaunin driver ya tada motar suka fice daga asibitin motar tsit ma sauti komai saina ac dayake ratsa kowannensu.
Suna isa gida da daddare ne dan haka parking kawai fahad yayi ya fito ya bude masa motar ya fito ahankali ya wuce ciki batareda ya iya cewa komaiba..
Daidai yana gap da shiga palo wayarsa dake hannun sayd tayi ringing,
Sunan Dr Nico sayd din ya ambata wanda ya saka AZIZ din tsayawa cak batareda ya juyoba yana dan rufe idanuwansa da babu abinda yake cikinsu sai azabar zafin da tiririn wutar dake ci a zuciyarsa da jininsa.
Qarasowa Sayd yayi tareda daukan wayar ya saka handsfree batareda AZIZ din ya karba ba.
Cikin sanyi dr Nico yace
"Jikin Ismail ya rikice gabaki daya bayajin lallai ismail din zai tashi sai wani ikon Allah,
Amma kafin ya rikice din a jiya bayan kun kashe waya ya bada wasu bayanai ta hanyar motsawa da hannuwansa...."
Dan Shiru yayi sbd tinanin yanda AZIZ zai karbi zancen tinda shine likitansa yasan halinda suka shiga gurin treating nasa wancan karan daya samu paralys daqyar sukaga Allah ya nuna ikonsa akan AZIZ din ya tashi dan haka yake kiyaye abinda zai fada masa akan Kanwar tasa.
Ahankali ba zato sukaji muryan AZIZ din ya furta
"Babu abinda zuciyana bazata iya daukaba a duniya yanzu,just go ahead and say it"
Numfashi Nico ya sauke yana cigaba da cewa
"Ya bada tabbacin Cire zuciyarta akai bayan ta haihu da kanta kuma lafiya kalau sedai already koda aka kawota asibitin kusan brain dinta yagama mutuwa sbd ba aranar aka fara shirin cire zuciyartaba ahankali sun kashe brain nata,
Zuciyar na zaadens tana bugawa a kirjin wani daga cikinsu wanda bai samu nuna waye ba a cikin hotinan zaadens din dana nuna masa jikinsa ya rikice sbd brain dinsa da zuciyarsa bazata iya daukan pressure din zancen ba dan haka idan akwai abinda kuke buqata dashi kuzo kafin time dinsa ya cika"
Wani boyayyan numfashi AZIZ din ya sauke mara sauti numfashinsa na cunkushewa yayi gaba batareda yace komaiba.
Sayd ma wayar ya kashe yana bin bayan AZIZ din wanda yana shiga palonsa ya rufo kofar yana jingina bayansa jikinta ya rintse idanuwansa dake radadi yana dora hannunsa setin zuciyarsa dake tsananin ciwo da radadi ya gurfane gurin yana cusa kansa cikin qafafunsa kamar qaramin yaro yana jin tsananin sanyin rayuwarsu ta baya da suke rayuwa a cikin mataccen gidansu yana dawo masa tareda mahaifiyarsa da Ummitah tana qarama.
Rawar sanyi jikinsa keyi yana kakkarwa sosai yana tinano dumi na jikin Ummitan idan tana jikinsa a lokacin sbd bata kariya daga sanyi rungumeta yakeyi sanyin yana shigewa shi a jikinsa......
Wasu zafafan hawaye masu radadi ne suka fara biyo gefen Idanuwansa yana jin kewanta na kashe kowane lungu da sakon tasa zuciyar.
Sayd dayake bakin kofar jin yayi karar fasa kayayyakin palon taka tashi da karfin gaske tareda kukansa dayake yaga tasa zuciyar.
Gwiwowinsa Sayd yakai kasa a kofar palon yana sunkuyar da kansa idanuwansa na sake sauyawa zuwa jajir yana jin kaman ya bude ya rungume AZIZ din ko zai samu kashe masa wutar datake ci a zuciyarsa amma ba damar hakan sbd yasan a wannan lokacin ko kusantarsa wani yayi zai iya rabasa da ransa fit dan haka yakejin radadin AZIZ din har tasa zuciyar.
Duk abinda yake palon babu abinda ya bari da sauran amfani sbd ya fasa komai hannuwansa jini sukeyi sosai sbd glasses da suka yankesa koina amma sam bai damu ba a hakan ya zube qasa ya kwanta yana rufe idanuwansa yana jin buqatar bugawan zuciyarta a hannunsa,baa kirjin koma waye takeba a hannunsa yakeson karbota ya rabata da kirjinda aka kashe Ummitansa akai,
Bazai taba jin abinda yake tokare da kirjinsa ba ya fada sai ranar da zuciyar Ummitah ta sauka a hannunsa yakai kabarinta ya rufe mata ita dik da babu abinda ya rage a gangar jikinta amma zai kai mata zuciyar kabarinta ya rufe mata ita.
Koma waye aka raya bayan kashe tasa yar uwar zai tabbatarda da hannunsa zai ciro ya basa abarsa a hannunsa,
Duk wanda ya taba hada ko hulda d zaadens saiya tabbatarda duniya ta dena masa dadi kwata