Showing 21001 words to 24000 words out of 152254 words
ace mun mayar da hankali a kai, ba bawa ɗan daba kariya ba"
Ya ajiye jaridar hannunsa ya ce "Kalle ni da kyau, ba na abun da babu manufa a kansa, dan haka kawai ka saka ido"
Waya ce ta fara ringing, ya ɗaga sannan ya miƙo masa.
Ya karɓi wayar tare da yin sallama.
"Wa'alaikum Salam, barka dai ya ƙoƙari?"
"Alhamdilillah sir, an yi clearing matsalar jiya, duk da an kusa samun akasi, yaron ba ya ji ko kaɗan, idan aka cigaba da tafiya a haka, kar asirinmu ya tonu fa, dan hakan tamkar yi wa doka karan tsaye ne, mu na saɓa ƙa'idar aiki"
Yayi murmushi ya ce "Kar ka damu, doka ce ta fara yi wa yaron karan tsaye, shiyasa nake amfani da dokar, wurin bi da komai"
"Haka ne sir, amma fa police suna neman shi ne ruwa a jallo, mu kuma muna kare shi, muna taka doka da yawa"
"ASC, ko sun kama Al'amin, ba zasu bari doka ta yi aiki a kansa yadda yakamata ba, za su bar shi da masu son zuciya ne, su yi abun da suka ga dama da shi, ba wai hukumar ce kawai take nemansa ba, akwai lauje cikin naɗi ne a neman da ake yi masa"
ASC ya numfasa ya ce "Shikenan, amma laifukansa sun yi yawa, duk wani ta'addanci da za'ayi a garin nan sai ka ji yaransa ne, slide mistake za'a iya kama shi, duk da wani abun kuma idan muka bincika, sai mu tarar ba shi ɗin ba ne ba"
"Haka ne, amma idan an kama shi ma, sunana na ko naka, babu wanda zai fito, haryanzu bai san ko ni waye ba, kuma ba zan bari ya sani ba, kuma yana aikata wasu laifuka ne dan ya tilasta na ƙyale shi, ko kuma na bayyana kai na a gare shi, amma ka rabu da shi, komai cikin tsari nake yin sa, ka bar police su cigaba da neman sa, hukumarka kuma ta cigaba da aikinta, kamar yadda na ce maka"
Ya amsa da "Shikenan sir, am always loyal to you, na gode"
"Yauwwa ASC, duk halin da ake ciki dai, ina buƙatar ka sanar da ni"
"No problem, sai an jima" bayan sun yi sallama, yayi wata irin dariya, da shikaɗai ya san ma'anarta ya ce "Wannan shi ne jifan tsuntsu biyu da dutse ɗaya" yayi maganar yana kallon yaronsa da yake tsaye yana kallon sa.
Ya ce "Lallai, amma zan so in ji wani irin shiri ne haka ka ke yi sir"
"Za ka gani a aikace, kai dai ka cigaba da biyayya ga abun da duk na umarce ka, nima zan yi amfani da ƙarfin iko da kujerata, na yi abun da ya dace".
"Ok sir, in sha Allah".
***
Misalin ƙarfe takwas na dare, wasu daga cikin manya na ƙungiyar ƙato da gora na unguwar suka tattaru suka zauna meeting a cikin ɗan madaidaicin office ɗin su. Duba da abun da ya faru, na faɗan daba da aka yi da yaran Aminu da na Madaki a waccan unguwa, sanin ya na shigowa unguwar lokaci zuwa lokaci, sannan kuma akwai yaransa a unguwar, ya sanya su zaman yin meeting, dan ƙara ƙarfafa tsaro a cikin unguwar su, kar su gama da can su dawo nan.
Suna tsaka da tattaunawar, wasu zaratan matasa suka yi sallama, suka amsa suna bin su da kallo.
Suka shiga cikin office ɗin, suka kewaye su, duk suka tsaya suna kallon su.
A hankali ya sauke face mask ɗin fuskarsa, a take suka shaida shi.
Kafin su yi magana ya ce "Awa ɗaya rak nake buƙata, zan gama abun da ya kawo ni na fita, muddin na kuma shigowa unguwar nan, ku ka sako ni a gaba, kamar kare za ku kama ni, wallahi sai na yi muku abun da na yi wa malam lawan".
Shugaban ƴan sintirin ya ce "Dan meyasa zaka din ga shigo mana unguwa? Kai da hukuma take nema ruwa a jallo, ka san kai tauraruwa mai wutsiya ne, duk in da ka je sai ka yi fitina, tun da yaranka suka yi ɓarna jiya, na san cewa nan ma zaka shigo. Duk ka lalata mana yara ka tafi ka barmu da masifa, kuma yanzu ka dawo kana cigaba da bibiyarmu"
Cikin tsawa Walid ya ce "Kai, ka iya bakinka, wallahi ko na ɓare maka shi har ƙeyarka".
Cikin tamkakiyar fuskarsa Viper ya ciro zungureriyar wuƙar da take ƙugunsa, ya karta ta a ƙasa tayi wata irin ƙara, sannan ya ɗora ta a gefen wuyan mutumin ya ce "Ƴaƴanku za su cigaba da yi mini biyayya, sai na mayar da unguwar nan mafi munin sansanin ta'adancci da zubar jini, komai ya faru ai ku kuka so, yanzu dan Allah kai ba ka ji kunyar faɗar abun da ka faɗa ba? Duk in da zan je zuciyata na tsakiyar unguwar nan, kuma zan cigaba da shiga da fita yadda nake so, har sai na yi maganin azababbiyar ƙishirwar da ta addabi ruhina. Duk abun da na aikata muku na ɓarna, ku kuka so, mutanen banza masu butulci, kun taki sa'a da nake dakon alƙawari mai nauyi a kaina, ban da haka tun a fitowa ta, ɗaya bayan ɗaya zan yi muku kisan gilla. Idan na sake shigowa unguwar nan, kai da wannan mutanen, ku ka yi yinƙurin yi mini wani abu, duk wanda na kama, zai zama mutum na farko da zan yi wa yankan rago!" Gaba ɗaya suka zuba masa ido, suka kasa ko motsin kirki, saboda yadda suka zagaye su da miyagun makamai.
"Ku karɓe wayoyinsu, ku rufe mini su, ku saurari order da zan bayar. Duk wanda yayi muku gardama ku karya mini ƙafarsa, ko ku tsarge masa cinya".
"Angama boss"
Yana fita daga office ɗin, suka mayar suka rufe, suka ƙwace musu wayoyi, sannan suka tsaya a kansu da wasu irin zabga-zabgan wuƙaƙe, kamar a abba tuwa.
Babu wanda ya iya wani ƙwaƙwƙwaran motsi, dan a yadda matasan suke muzurai, kuma shaye-shaye ya huda su, duk umarnin da ya ba su za su bi.
Sannu a hankali yake tafiya, har ya kawo cikin layin, ya tsaya a ƙofar wani gida, ya shafe tsawon lokaci kawai ya zubawa gidan ido, yana zancen zuci, daga bisani ya ƙarasa ya ƙwanƙwasa na kusa da shi, ya ja mask ɗin sa, ya rufe fuskar shi.
Yaro ne ya fito ya ce "Waye?", ya cewa yaron "Ka je ka cewa babanka an zo duba shi"
Mintuna kaɗan yaron ya dawo, ya ce ya shiga.
Bai yi sallama ba, haka ya kunna kai cikin gidan, har tsakiyar falon maigidan, ba tare da an yi masa iznin hakan ba.
Daga maigidan har matar gidan, da ƴan matan yaran, tsuma suka hau yi, ganin wanda ya shigo har cikin gidansu.
Ya zaro wuƙarsa ya ajiye a gaban malam lawan, sannan ya ɗaga wani mukulli ya ce "Na rufe gidan nan da kwaɗo ta ciki, kuma duk wanda ya yi wani ƙwaƙwƙwaran motsi, zan zaunar da shi kamar yadda na zaunar da kai" yayi maganar yana kallon malam lawan.
Ya durƙusa kama ƙafar malam lawan, da aka naɗe da bandeji, ya dudduba sannan ya ce "Ɗori yayi kyau, sai dai na yi mamakin yadda aka dawo da kai gida, maimakon ka yi jinya a asibiti"
ya saita tsinin wuƙarsa a cinyar malam lawan ya ce "Waye ya ɗauko ka daga asibiti?"
Cikin tashin hankali matarsa ta fara kuka ta ce "Dan girman Allah Aminu kar ka yi masa wan....
"Wallahi ki ka sake magana, sai na karya ɗaya ƙafar, ka gaya mini kafin na huda cinyarka" yayi maganar cikin razananiyar muryarsa.
Cikin matsanancin tashin hankali ya ce "Wallahi wasu mutane ne, ban san su ba, su ne suka sauya mini asibiti, lokaci zuwa lokaci, suke zuwa da likitansu ya duba ƙafata, kuma sun gargaɗeni a kan muddin wani ya ji kaine ka yi mini haka, sai sun kashe ni"
"Waye ya kai ka asibiti ranar da abun ya faru?"
Cikin kyarma da rawar murya malam lawan ya ce "Wallahi kana barin wurin, ina wannan kakarin, wani ya zo yayi mini kashedin muddin na ce kai ne zai kashe ni, ya watsa mini wani abu, ban sake sanin in da kaina yake ba, sai da safe maƙwabta suka tsince ni, na ce masu masu ƙwacen waya ne suka yi mini"
Aminu ya ware masa jajayen idanunsa sosai ya ce "Idan na samu labari akasin abun da ka gaya mini, kar ka manta take na, maciji nake mai mugun dafi, sai na maka karayar da ba zaka sake taka ƙafarka ba a doron duniya. Zan cigaba da zagayowa zan kuma cigaba da sanya maka ido. Kar ka manta ka yi mini ganganci daban-daban, na kawar da kai, na riƙe biyu a raina idan ka yi na uku kasheka zan yi har lahira".
Malam lawan ya jinjina kai, yana jin yadda mararsa ta cika fam da fitsarin tsoro.
Viper ya a miƙe ya juya ya bi hanyar fita.
Sai da suka tabattar da tafiyarsa, sannan matar malam lawan ta ce "Na shiga uku, baban su Amir dan Allah meya aike ka sake shiga sabgar mutumin nan? Daga ƴan sandan har ƴan ƙato da goran kar wanda ya ƙara tambayarka abu a kansa ka ce ka sani, kalli bala'in da ka jefa mu a ciki?"
"Ke dalla rufe mini baki, tun da yanzu na tsira da raina shikenan, ina ga sayar da gidan nan zan yi na bar unguwar, idan ba haka ba wataran kasheni zai yi "
"Ai koma menene Allah ya ƙara wallahi, abun da ka yi wa bawan Allah nan ka yi butulci da yawa"
"Au so ki ke na rufawa mutumin banza asiri Haule? Ni ki ke gaya wa haka?"
"Oho ai gaskiya ce" haka suka cigaba da faɗa, tana mita da ɗora masa alhakin janyowa kansa ko ma menene.
Aminu kuwa, ta waya ya ce wa su ɗan mama, su baro ƴan vigilante ɗin, su bi shi gida.
A gidan suka tarar da shi, ya dubi Walid ya ce "Ka yawaita survey a cikin unguwar nan, mutumin nan ya tabattar mini da cewa, wanda suka canza masa asibiti, suna zuwa da likta har gida yana duba shi".
"To shikenan Oga, in sha Allah za ayi yadda ka ce"
"Kuma na san mutanen nan ne, da mutumin yake kirana a waya, ya zama dole na san waye, da kuma manufarsa a kaina, da yake bibiyata har haka".
Walid ya ce "An gama maigida"
Nabila kuwa tun da ta shiga aiki tana office ɗin ta, suna communicating da Yaya Nasir.
Wayar sumayya ce ta shigo ƙaramar wayarta, dan haka ta ajiye ta hannunta ta ɗaga da sauri ta ce "Sunayya yaya ake ciki?"
"Kamar dai yadda na yi tsammani" ta bata amsa.
"Me ki ka yi tsammanin? Yi mini gwari-gwari"
"Ba irin labarin da suke buƙata ba kenan, hakan ka iya kawo musu naƙasu ga cigaba da kuma tasirin gidan radiyon su, kuma wai ba ni da cikakkiyar shaidar abun da na faɗa"
"Haba Sumayya, ni ina da shaida fa, ga kuma yaya Nasir ma, kuma ya zaki tsaya a wurin wannan shashashar matar da ba ta son cigabanki? Ki yi wa Manager magana mana direct, nima ina da lambarsa, sai na yi masa magana".
Sumayya ta ce "Nabila kenan, duk kanwar ja ce, shi ne ya jaddada mini hakan da kansa".
"Allah wadaran naka ya lalace, Yanzu sumayya shikenan zuba ido zamu yi? Babu wani abun yi?"
Sumayya ta ce"Idan na matsa zan iya rasa aikina, abun da ya nuna mini kenan, wai ba za su iya jayayya da hukuma ba, kuma na kawar da kaina a kan abun da ba zan iya jurewa ba, da ina da wata hanyar samun kuɗin, da ajiye aikin nan zan yi Arfa"
"Shikenan, zamu yi magana anjima, see you later" ta ajiye wayar ta zauna ta yi shiru.
Wani irin tsaki ta ja, tana mamakin yadda galibin private organizations suke buɗe wurare, for their personal interest kawai, kodayeke na gwamnatin ma menene, duk ɗaya.
Ganin ɓacin ran ba zai amfanata komai ba, tana da abubuwan da yakamata ta yi, ya sanya ta fita ta tafi office ɗin Barrister Habib.
Yana ta aiki a system, ya ɗago ya amasa mata sallamarta, ya cigaba da aikinsa.
"Barka da aiki barrister".
"Yauwwa" ya amsa a taƙaice.
"Barrister wai haryanzu fushin ka ke yi, na shiryu fa na daina duk wani abu da nake yi, sonake na zama cikakkiyar lawyer abar koyi ga wasu, kamar gwanata Barrister Naja'atu Bunkure" da ɗan sauri ya ɗago ido ya kalleta ya girgiza kai ya ce "No wonder, shiyasa ba zaki cigaba ba"
"Subhanallah, meyasa?" Tayi maganar tana ware ido.
Maimakon yayi magana, sai yayi mata shiru.
Wani irin kallo tayi masa, a zuciyarta ta ce 'Sai fa ka yi magana barrister'
A zahiri kuwa ta ce "Ni dai haka kurum nake sonta, ayyukan ta na jin ƙai suna burgeni, ina son zama kamar ita. Amma tun da haka ne ma, na canza kamar kai nake son zama, daga yau kai ne mudubina" tayi maganar tana murmushi.
"Ke da ba zaki iya zalunci ba, mu ne azzalumai ai"
Nabila ta ce "Innalillahi wa Innalillahi raji'un, waye ya faɗi haka? Wallahi ba haka bane ba, ni ban ce ba"
"Idan har kina son zama shahararriya, dole ki yi iya yinki, a kan duk abun da ya zo hannunki, ko da kuwa babu tabbacin zaki yi nasara, idan ba zaki iya ba kuma, you can leave"
"No, zan iya, ai na shiryu yanzu"
Ya buɗe drower gabansa, ya ɗaukko wani file ya ajiye mata sannan ya ce "Wannan client ɗi na ce, a nan ƙofar na'isa gidanta yake, zan turo miki cikakken adress ɗin ta, ki je ku yi magana, sannan ki yi tunani a kan case ɗin nata" Cikin girmamawa ta ce "Na gode sosai, zan yi in sha Allah "
Tana fita daga office ɗin nasa, ta gyatsine baki, ta ce "Kamar ni za a aika, gidan wata ƙatuwa, ba ma ta zo office ta same mu ba, hamshaƙiya saboda ga ƴar Nabila ƴar wahala. Amma bakomai da na zama abun da nake so, na fi ƙarfin kowane irin wulaƙanci" ta koma nata ofishin tana cigaba da ƙunƙuni.
Da ta koma gida ma, ba ta bi ta kan aiken da barrister yayi mata ba, ta kwanta ta sha baccinta, bayan ta tashi ta shirya ta yi wanka, ta tafi gidansu sumayya.
Sun jima suna tattaunawa da sumayya, a kan harkar aiki, har sumayya ta din ga ja mata kunne, a kan kasadar da take yi, tare da nuna mata illar hakan a matsayin ta na ƴa mace, ta kunnen hagu maganganun sumayya suka din ga shiga kunnenta suna fita, dan ba ta ji sun shigeta ba.
Ta bawa Sumayya labarin aiken da barrister Habib ya yi mata.
Sumayya ta ce "Kuma zaki ɗin?"
"To ya zan yi?"
Sumayya ta yi dariya ta ce "Ai na zata taurin kan yana nan?"
Nabila ta yi murmushi ta ce "Na ajiye taurin kai, zan kama aikina yadda yakamata, ai sai burina ya cika sai na binciko wacece Bunkure kuma in sha Allah, sai sunana ya shafe nata a tarihin duniyar ma'abota shari'a".
"Allah wadaran naka ya lalace, Nabila, wai ke wani irin taurin kai ne da ke ne? Ke abu ba ya wucewa a wurinki ne? Ki bar ta kawai, idan Allah ya so, tana raye zata ga nasarar da zaki yi a rayuwa"
"Ina kwance nasarar za ta zo ta same ni kenan? Ke ƙyaleni, ina ga sai Allah ya kaimu friday da yamma, zan je waccan unguwar gidan matar, na ga bai turo mini contact ɗin matar ba tukuna, zaki rakani?"
Sumayya ta ce "A'a gaskiya, wannan unguwar, ana ta fama, kamar ba kya jin radiyo, yadda suke fama da faɗace-faɗacen daba. Ki gayawa barrister ya ce kawai matar ta je office ɗin ku, ko kuma ki bari komai ya lafa, dan kullum cikin faɗan daba suke"
Nabila ta ce "So ki ke in kasa samun information ɗin da nake so daga bakinsa kenan? Ai lallaɓa shi zan tayi, sai na san wacece matar nan. Kodayake ma na saka Yaya Nasir ya rakani" sai kuma ta yi shiru, ta sake maimaita zancen Sumayya a zuciyarta.
*Wannan unguwar ana ta fama da faɗan daba*
Ta sake kallon sumayya ta ce "A unguwar ne aka ce yaran Aminu Viper sun yi sare-sare?"
Sumayya ta yi shiru tana kallon idon Nabila.
Nabila ta yi murmushi ta ce "Kar fa ki kawo komai a ranki, ba wani abun zan aikata ba, bari na tafi kan Abba ya dawo ya nemi ina nake" ta ɗau jakarta ta fita, tana jin kamar matsalarta ta zo ƙarshe.
*Masu nema daga farko, ku yi joining link channel ɗina na saman page, idan kun shiga zaku samu daga farko*
Arewabooks ayshercool7724
Watpad
ayshercool7724
Ayshercool
08081012143
[7/21, 2:16 PM] null: *ƘARFE A WUTA*
AISHA ADAM (AYSHERCOOL)
MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION
BRIGHT PENS SECOND BATCH
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
7
Katafaren falo ne, wanda girmansa ya ishi wani talakan gina gidan da zai rayu a ciki, talabijin ɗin da ke falon kawai ta fi rabon bango.
Kujera set biyu ce a falon, kuma tsakanin kowane set da wani akwai tazara.
Tinkis-tinkis haka ya fito cikin wata irin dakakkiyar shadda maroon, sai ƙyalli take yi, ba sai an faɗa ba ka san akwai tazara mai nisan gaske tsakanin sa da talauci.
Ba wata ƙiba ce da shi ba, amma cikinsa yayi kurtsitsi a riga, har wani nishi yake yi.
Ya nemi wuri ya zauna a ɗaya daga kujerun falon, ya kalli matasan da suke zaune a ƙasa a kan carfet. Dukkansu babu mai suturar kirki a cikinsu, kansu duk askin banza, yanayin shigarsu da fuskarsu kawai za ta tabattar riƙaƙƙun masu laifi ne.
"Allah ya taimaki maigida" cewar ɗaya daga cikin su.
"Ya aka yi madaki?"
"Akwai ƙura ne, ƙurar kuma na neman zama gagarumar guguwa"
"Ina jin ka"
"Aminu Viper, haryanzu jami'an tsaro ba su kama shi ba, ya sa an kaiwa yarana mummunan hari, an yi musu miyagun raunuka, jami'an tsaro sun kama yarana sun saki nasa, wanda aka kai asibiti ma, an kwashe su daga asibiti babu wanda ya san in da aka kai su"
Mutumin yayi tsaki ya ce "Ina mamakin yadda mutum ɗaya ya gagari kamun hukuma, ni anya ba raina mini hankali ma suke yi ba a kansa? Yanzu menene abun yi?"
"Ka saka a sakar mini yarana, dan sai da su ayyukanka suke yiwuwa, kuma dole mu yi shiri sosai, idan da hali mu mu nemi in da yake mu kashe shi kowa ya huta"
Mutumin yayi shiru yana kallonsa sannan ya ce "Aikuwa da na yi maka tukucin da baka taɓa tunani ba, zan saka a saki yaran nan anjima kaɗan, sai dai duk yadda zaka yi ka yi, a samo