Showing 123001 words to 126000 words out of 152254 words
hannunsa ɗaya yana soke makaminsa iraƙi a cikin ƙugunsa.
Ya ce "Fitar gaggawa ta kama ni, idan nayi dare ban dawo ba, ki rufe ƙofa, duk wanda ya buga kar ki buɗe, idan na dawo na hauro"
Banza tayi masa, ta cigaba da yanka albasarta.
"Ke ba magana nake yi miki ba?" Shiru ta sake yi masa.
Ƙoƙarin leƙawa yake yi, ya ga ko lafiya.
Kawai ya ga ta jefo masa murfin tukunya, a zatonsa ko ba ta san me tayi ba, kawai ya ga ta sake jefo masa rariya.
Saroro ya tsaya cikin mamaki, ta cigaba da zaro kwanuka tana jefa masa tana kuka, bai ƙara tsinkewa da lamarin ba, sai da suka haɗa ido ta jefo masa ludayin hannunta a ƙirji.
Ayshercool
08081012143
🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143
90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa
Arewabooks ayshercool7724
https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA
Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??
Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??
Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??
Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.
Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955
Tunani ya fara yi, ko tana da aljanu ne.
Ganin idan ya ƙyaleta, fashe-fashe za ta yi, ya sanya shi takawa ya riƙo hannunta, amma sai ƙoƙarin fizgewa take yi.
Kasancewar ba ta yi masa wahalar ɗauka, ya sanya ya danƙota kamar kazar cikin akurki, aikuwa ta cigaba da fizge-fizge da ƙoƙarin ƙwacewa, falo ya shiga da ita, ya tattara hannayenta ya riƙe, hakan ya sanya ta kasa cigaba da ƙoƙarin ƙwacewar.
"Meye haka ki ke yi? Kanki ɗaya kuwa?"
Kallonta yake yi, har ta fara kuka, shi bai ma san me yayi mata ta aikata hakan ba.
"Me nayi miki ki ke jifana?"
Cikin takaici ta kalleshi ta ce "Meye ma baka yi mini ba, ni bani da wani amfani a wurinka, bani da ikon roƙon alfarmarka, komai ma yi mini ka ke yi, ko yayi mini daɗi ko akasin haka, ba ka tausaya mini dama ka tsane ni, so kake yi na mutu ka huta".
"To yanzu kuma me nayi miki?"
"Wuƙa fa ka ɗauka zaka fita, idan aka yi maka wani abun ko ka yi wani laifin nikaɗai nake fama, sai su yaya walid da suke taimaka mini, amma kai gaba ɗaya baka tausayina, ba ka tausayin maraicina saboda da ma ba so na ka ke yi ba. Kodayeke ba laifinka bane, tun da sama ta ka aka aura maka ni, bayan an gama ɓata ni a wurinka. Ko hira ba ka yi da ni, in tayi maka magana kayi mini shiru, idan aka ga na mutu kai ne, sai ma na rubuta na bar wasiyya, idan na mutu kai ka ƙarasa ni da takaici"
Yayi shiru ta din ga yi, tana faɗa tana kuka, sai da ta gama tsaf, sannan ya miƙe ya ce "Ki kula da abun da na gaya miki, kar ki fita kar ki bar gida a buɗe, idan na yi dare ki kwanta zan hauro".
Ta ɗaga idanunta da suka yi ja ta ce "Sai ka fita ko?"
"Ai na ce idan ba zaki iya ba, ki koma gidanku ko ban gaya miki ba?" Tayi shiru ranta na yi mata wani irin zafi, ya fita ya kwashe kwanukan da ta watso waje ya fice.
Unguwar su ya nufa, faɗa ya haɗa ɗan unguwarsu, da ɗan unguwar su madaki, yaron ya kwaso 'yan daba yaran madaki, sun shiga unguwar su Al'amin su na ta faɗace-faɗace.
Yana zuwa chamber su, ya ɗaukko wuƙaƙensa, ya fita, sai dai da ya je, yaran suka din ga darewa, saboda wanda suka taɓa karo da shi, sun san irin ƙarfin da Allah ya yi masa.
Wani yaron madaki ne, da yake ji da tashen balaga da rashin mutunci, ya sha gaban Al'amin yayi yana zage-zage yana ƙoƙarin saran Al'amin.
Ya jefar da wuƙarsa, ya nufi yaron, wanda suka san Al'amin suka din ga ce masa ya gudu, kar ya bari ya kama shi, amma kasancewar ya yi wa wiwinsa haɗin kauri da wata ƙwaya da suke yi wa laƙabi da 'yar fara, ya sanya yake jin kansa a sama, ko barikin sojoji zai iya shiga yayi rashin mutunci.
Duk iya ƙoƙarin sa ya kasa saran Al'amin, saboda yadda yake da zafin nama, wurin kare saran, wanda idan ba professional athlete ne ba, babu lallai ya iya.
Ya shammaci yaron, ya soka masa iraƙi a cinyarsa, a take ya kurma wani uban ihu, liti ne ya karyo kwanar, riƙe da nasa makamin yana ɗigar da jini, "Mai zamani yi haƙuri, kar ka karya yaron nan" sai dai bai rufe bakinsa ba, ya ga Al'amin ya fito da dogon harshensa, ya lashi laɓɓansa na ƙasa da su, idan har yayi haka sai aiwatar da muguntar da yayi niyya, kan liti yayi wani yinƙuri ya karya ƙafar yaron ya watsar da shi yana kururuwa.
"Mai zamani, yanzu zaka sake janyo mana faɗa, madaki zai ce sai ya ɗauki fansa, da baka karya shi ba"
Ya ɗago jajayen idanunsa a slow, yayi wa liti wani irin kallo ya ce "Ya zo ya ɗauki fansar a kaina, idan ya isa" ya wulwula iraƙinsa, ya cafe ya yi gaba.
Kai tsaye gidan su ya tafi, da wannan wuƙar tana ɗigar da jinin da ya soki yaron nan.
Yana shiga ya wuce falo, sai ganinsa suka yi a tsaye a kansu da makami tsirarsa.
Salati suka fara yi da kururuwa, ya kalle su ɗaya bayan ɗaya, "Me ya kai ku gidana?" Yayi maganar yana kallon shahida.
Cikin tashin hankali ta ce "Abbu ne ya ce Mu je mu duba matarka".
"Shi ya ce ku je ku gaya mata cewar kangarewa ce ta sanya aka yi aurena da ita? Ku je ku ci zarafinta?"
Cikin tashin hankali shahida ta ce "Ba ni na faɗa ba Amira ce wallahi".
Rahila kuwa hankalinta ya dugunzuma, ta ce "Ka yi wa Allah da ma'aikinsa ka yi haƙuri, dan Allah kar ka yi musu wani abu"
Ai kamar ta tunzura shi, ya saka wuƙa a wuyan Amira, "Ya zama na farko ya zama na ƙarshe, ayi duk cin kashin da za ayi a kaina, ban da 'yar mutane da ki ka haɗa kai ku ka cutar, idan aka kuma zan yi ɓarna, wallahi sai na saka wa mutum ƙarfe"
Shahida ce ta iya cewa "In sha Allah ba za a sake ba" yayi ƙwafa ya fita.
"Amira kin ga abun da ki ka ja mana ko? Da ya illatamu, da kin cuce mu"
Amira kam kasa magana tayi, sai dafe ƙirji tana hakin tsoro.
Al'amin wuni yayi ranar, yana partrol da yaransa a unguwar, saboda kar yaran madaki su zo su afkawa wanda bai ji ba bai gani ba.
Cikin ikon Allah, har dare yaran madakin ba su sake shiga unguwar su Al'amin ba, duk da sun yi artabu sosai da wasu, dan sai da aka yi masa rauni a cikinsa, ya kama hanyar tafiya gida.
Jauhar na falo tana karatun exam, duk da sun kusa kammala jarrabawa.
Ta katangar ya diro kamar ɓarawo,s an samu cigaba, yanzu idan ya ga dama ya kan yi salama.
Sallamarsa kawai ta amsa, ba ta sake kula shi ba, ya wuce ɗakinsa, mintuna goma amma ba ta biyo shi ba, ya fito ya ce "A kawo mini ruwan zafi zan yi wanka"
Ta tashi ba ta ce komai ba, ta ɗaukki flask, aurensa da ita ta saba masa da wanka da ruwan ɗumi, saɓanin da da har a kuddudufi wankansa yake yi ya ƙara gaba.
Yanzu kuwa kusan kullum, da an kawo wuta, take dafa ruwan a heater, ta saka a flask.
Ta zo ta haɗa masa ruwan, sai dai ta ga kamar yana ɓoye wani abu.
Kawai ta leƙa ta ga me yake ɓoyewa, yanka ne a gefen cikinsa, ya saka rigarsa yana ƙara goge jinin kasancewar ba mai zurfi bane ba.
"Ka gani ko? Sai da ka je aka yanko ka ko? Abun da nake ta gudu, sai da ka zubar da jini ko, ba za kai daina zuwa wurin da za a cutar da kai ba ko master? Kodayake ma ni abun yake damu, kai ko a jikinka".
"Na ce ya dame ki ne? Ba jikina bane?" Idan ba gizo idonsa yayi masa ba, hararsa ta yi ta fice.
Shi mamaki ma take bashi, tun da ta yi rashin lafiyar nan, take rigima kuma kamar ta rage tsoron sa.
Ya shiga ya yi wanka, ya fito ya tarar da ita da ɗan ƙaramin kwanon abinci, sai kuma kayan dressing, tun na lokacin da aka yi masa wancan raunin.
Bai kulata ba, ya ja kwanon abincinsa ya cinye, awara ce da miya, ya sha ruwa.
Ita ma ba ta kula shin ba, ta saka auduga da spirit tana goge, kan ciwon, tana gogewa tsigar jikinta na tashi, kamar jikinta take gogewa, shi kuwa kamar dutse latsa wayarsa ma yake yi.
Haushi ya isheta, ta kalleshi ta ce "Wai ba zafi ne?"
"Eh babu, idan ma dirzawa ki ke da ƙarfi, dan na ji zafi, ba na ji" ta tashi ta fice fuuu, tana yi masa fatan shiriya a ranta.
Kusan awa ɗaya da rabi, ya shigo mata ɗaki, ta yi sauri ta tashi zaune, saboda ta san tsiyar da ta aikata masa.
Ya kunna fitila ya hau yi mata bincike a ɗaki.
"Me ka ke nema?"
Ya tashi ya nufo ta, ya miƙa mata hannu ya ce "Bani kayana da ki ka sace mini yanzu"
"Ni ba na sata"
Ya ce "To baki nayi ki ka ɗauka? Ko kema kin fara sha ne ban sani ba? Kodayeke biri yayi kama da mutum, da ki ka iya kallona ki ka din ga jifana nan gaba ina ga swizaland zaki saka mini ina ga"
"Ni ba na shan komai, kuma ban ɗau komai ba".
"Ba ki ɗauka ba ya aka yi ki ka san a kan me nake magana?" Tayi shiru ba ta ce komai ba.
Hankaɗata yayi, ya janyo ledar kayan shaye-shayen sa a cikin bargonta.
"Na gaya miki idan kin gaji ba zaki iya zama ba, ban ɗaure ki ba, ki ƙara gaba"
A ƙule ta ce "Ka ɗaure ni mana, zan tafi ba ka sallame ni bane, ka rubuta ka gani idan ban tafi ba. Tun da baka da tausayi idan ba mutuwa na yi ba hankalinka ba zai kwanta ba" tayi maganar tana sheshsheƙar kuka.
Ya kalleta, gaba ɗaya ko faɗan ba ta iya ba, voice ɗin ta sam ba na masu faɗa bane, shagwaɓa kawai take yi.
Ya ce "Kin yanke hukunci kenan? Ai da kin gaya mini da duk ba a zo nan ba, zan rubuta na baki, dama na gaji".
"Kuma wallahi idan ka yi shaye-shaye kai da Allah"
Bai kulata ba, ya jefo mata kwalin sabuwar waya gal, ya ce "Gashi nan, akwai layi a ciki na yi rijista, idan kuma na yi wani laifin na gudu ke za a kama".
"Bana so" ta faɗa tana kwanciya, duk da ƙasan zuciyarta tayi mamakin wayar.
Ya saka hannu ya ɗauka ya ce "To kin huta" ya fice ya bar ɗakin.
Ta kwanta ta yi shiru, sai ta fara tunanin ya aka yi ya ɗaga mata ƙafa ya ƙyaleta, sai kuma ta ga rashin kyautuwar abubuwan da ta yi masa.
Bayan sallar asuba bacci ta koma, ƙarfe takwas da rabi ta farka, tana ƙoƙarin saukkowa daga kan gadon, tayi tozali da farar takarda da biro. Gabanta ya faɗi ta ce "Na shiga uku sakin nawa ya yi?" Ba ta taɓa takardar ba, ta saukko a sukwane ta tafi ɗakinsa sai dai baya nan ya fice.
Gaba daya jikinta yayi sanyi, sai yanzu ta ƙara jinjina girman wauta da aikata.
Yau rahila har gidan su jauhar ta je, suka ƙule a ɗaka ita da Anty Zakiyya suna ta surutu da shewa.
"Zakiyya ina ga 'yar ku fa an gamu laulayi take yi"
"Kai haba dan Allah"
"Wallahi da gaske, ke 'ya mace shu'uma komai ƙanƙantarta, kin san yaron nan har gida ya zo da wuƙa ya gama ta'addancin sa tana zubar da jini, zai yi mini hauka a gida wai su Amira sun je masa gida sun yi matarsa ko me oho musu, na ga tashin hankali na ce iyee yanzu har ta samu wannan matsayin. Wallahi mamaki nake yadda ta iya zama da yaron nan"
Zakiyya ta ce "Ba ki ganta ba kamar sokuwa, kafin ki ga ta yi fushi, ko tayi zuciya da abu za a jima, ko kuma kawai tsabar ƙarfin hali ne da ƙi faɗi ba"
Rahila ta ce "Sai ta yiwu, ya ake ciki da maganar hafsa?"
"Mu na nan ana ta murginawa, ana shirin kawo kuɗin aure, na ce lallai ta ce masa a haɗo da kayan lefe, ana sallacewa ayi auren, duk da wannan matar ta nuna bakomai na san tsohuwar muguwa ce, wataƙila wani abun zata kitsa, dan haka kan tayi wani yinƙuri ayi a wuce wurin".
"Yauwwa kar ki kuskura ki sakankance ko ki yadda da ita, ni ban zaci lamarin ma zai zo da sauƙi haka ba, ku cigaba da tatsarsa kuna tarin kayan aure"
Zakiyya ta ce "Ke kin ga hidima, ai ni dai Allah ya kashe ya bani, da yanzu sai dai mu ga ana yi wa waccan yarinyar jauhar"
Rahila ta kwashe da dariya ta ce "Ga mijinta can suna fama, amma wallahi ya fara son yarinyar nan, kai amma ba ƙaramin haƙuri take yi ba bala'i Allah ya kyauta" suka cigaba da hirarrakinsu, da shirin biki.
Misalin ƙarfe ɗaya da rabi na dare, suka fito daga taron meeting, daga ofishin jam'iyya, sakamakon gabatowar manyan zaɓuka da za a gudanar a cikin Nigeria.
Yau bai san iya adadin meetings ɗin da ya yi attending ba, suka jero da shi da mataimakin firaministan jam'iyya na jiha, ya ɗan yi miƙa ya ce "Kai, yau na gaji over"
"Kai honorable, da an yi babban zaɓe an wuce wurin, haka ne, ka san ban yi sati da shigowa daga Abuja ba, can ma wasu tarurrukan ne, abun duk babu sauƙi, ina ta ƙoƙari in sha Allah sai na kawowa excellency yankina, ina nan a satin nan zan yi empowerment na matasa, kuɗina duk sun tafi a campaign ɗin nan"
"Kar ka damu honorable, hannun jari ka saya, da an wuce wurin sama zaka din ga kwashe ribarka, ka mayar da uwar da ribar ka ɓace ba zasu sake ganinka ba, sai bayan shekara huɗu" suka kwashe da dariya.
Suka yi sallama, kowa ya nufi motarsa, ko da ya je gida, matarsa tuni tayi bacci, yayi wanka ya nemi wuri ya kwanta, dama ba yunwa yake ji ba, sai dai bacci ya gagare shi, ya din ga juyi a kan gadon, ga gajiya ga baccin yana ji, amma ya kasa ya ɓuge da lissafe-lissafe abubuwan da yake son yi idan ya dace ya samu ya ci zaɓen nan.
Ji yayi kamar kansa zai fashe, saboda stress kawai ya tashi ya ɗauki mukulli, ko direba bai nema ba ya hau motarsa ya fice.
Yamma da gari yayi, ya hau kan titin gwarzo road kasancewar dare ne, titin babu ababen hawa, ya sauke glas ɗin motar kaɗan, yana tafe a hankali yana shaƙa wani abu a hancinsa. Sai d yayi nesa da cikin gari sosai, sannan ya yi parking a gefen hanya, ya rufe glasan motar, ya cigaba da shaƙa abun nan, kusan mintuna talatin, sannan ya juyo kan motar ya nufi dawowa yana tafe iskar kan titin nan na ratsowa cikin motar, sannu a hankali har ya koma gida.
Jauhar kuwa tun da tayi tozali da takardar nan ta kasa nutsuwa, ta kasa zaune ta kasa tsaye, kuma taƙi buɗe takardar, da ta leƙa ta hangota ma, sai ta yi sauri ta fito daga ɗakin, ta din ga lissafa irin halin da za ta shiga idan ta koma gida, da irin dariyar da za su yi mata.
Kuma yaƙi dawowa, har dare ba ta ganshi ba, hakan ya ƙara sanyata cikin tashin hankali, ba irin tunanin da ba ta yi ba, har ta fara tunanin ko da ya saketa, barin gidan yayi gaba ɗaya, sai dai kayansa suna nan, dan ita ta gyara ɗakin ya watso da komai ya bar mata a wurin.
Sai sha biyu saura ya dawo, idonta biyu ya dawo ba ta yi bacci ba, sai da ta tabattar ya shiga ɗakinsa, sannan ta ɗauki takardar ta bishi ɗakinsa.
Yana kwance a kan katifarsa, ya cika ɗakin da warin taba.
Yanayinsa ya nuna a buge yake, saboda fitilar ɗakinsa a kunne take, ya haye katifa ya mimmiƙe idanunsa sun yi ƙanana da ƙyar yake ɗaga su, kallo ɗaya ya yi mata ya mayar da idonsa ya lumshe.
"Master sai da ka rubuta takardar nan hankalinka ya kwanta ko?"
Bai buɗe idonsa ba ya ce "Ke ki ka ce na rubuta"
"Kuma sai ka rubuta ɗin ko? Saboda ina fargabar kar ka sake ni, bakomai maraici ne ya janyo mini, Allah ya gani na yi iya yi na, na yi biyayyar aure, amma kullum kallona ka ke yi wadda ta takura rayuwarka, ga takardarka nan, ban ma buɗe ba balle na san meye a ciki, kuma wallahi ban saku ba" ta dire masa takardar a jikinsa, ya ziro harshensa tare da naɗe shi ya mayar, ya gyara kwanciyar sa, har ta gama surutanta, bai kuma motsawa ba.
Kasa bacci tayi, ta ɗaura alwala ta tayar da salla, ta din ga addu'a Allah ya sa ya fasa sakinta, saboda ita a ganinta gara ƙalubalen gidan Al'amin a kan na gidansu.
Duk rintsi ba zai daketa ko ya ci mutuncin ta ba, ko yi mata sharri ba, sai dai miskilancinsa da gaya mata baƙar magana wasu lokutan da har daɗi take ji ya kulata, ciyar da su kuma da take yi mafi yawan lokuta baya damunta, sai ma yi wa Allah godiya da take yi da ko yaya ba ya hanata abun da zata sarrafa su ci, ko yaya ta kasa abun sayarwa za a saya dan ma ana yi mata mugunta.
Bayan sallar asuba tayi shiru tana tunani, ta ga sam ba ta kyauta ba, wasu abubuwan da ta yi masa, tun daga jifansa da kwanuka, har zuwa tsiwar da ta yi masa, ita tayi mamaki ma da ya ƙyaleta.
Yau ba ta iya komawa bacci ba, ta fito aikace-aikacen ta, tana yi tana leƙawa ko ta gani ko ya tashi.
Tana falo ta jiyo motsinsa, ta tashi ta shiga ɗakin da sallama.
Ya amsa mata, ba tare da ya kalleta ba.
Jiki a sanyaye ta durƙusa ta ce "Master ina kwana?"
"Lafiya ƙalau"
"Ka tashi lafiya, ya ciwonka?" Sai a wannan karon ya kalleta sai dai bai ce komai ba.
"Master