Showing 138001 words to 141000 words out of 152254 words

Chapter 47 - ?arfe A Wuta Book 1 Hausa Novel Complete

15 Dec 2024

359

"Dan girman Allah ka ceto rayuwar mijina, kar a rasa ransa dan Allah"

Ya ce "Ba laifina bane ba, dole mu san meyafaru kafin mu taɓa shi".

Kan kace kwabo, sashen emergency ya cika da 'yan daba, saboda an kawo al'amin.

Babu tsammani ta ga shigowar liti tare da Walid, da wasu tawagar marsa jin suna take musu baya.

Suka ƙaraso, in da jauhar ke zaune, da Al'amin a gabanta.

Walid ya ce "Madam, ya aka yi haka ta same shi?"

Ta girgiza kai ta ce "Ban sani ba, kawai ce mini aka yi ana faɗa, na je na tarar da shi, da zai cakawa wani wuƙa amma ya fasa, kawai dai ya ce madaki ya faɗi ashe an sare shi, kuma sun ƙi duba shi wai sai ƴan sanda sun zo, dan Allah ka saka baki yaya Walid.

Ya kalli liti ya ce "Zan ɓallo ruwa, a toshe magudanan daga waje" liti ya jinjina kai, ya ja guduma suka fita.

Wasu daga cikin matasan suka shigo, suka koro wasu daga majinyata waje, suka ritsa likitoci da makamai, sai sun duba Al'amin.

Aka ce su kai shi kan gado, Walid ne ya ɗauke shi, suka kai shi kan gado, saran da aka yi masa ba ƙarami bane, yayi zurfi, hakan ya ƙara razana Jauhar.

Liti ya ce "Wannan yankan madaki ne yayi masa shi, wannan shegiyar wuƙar da aka ce ta tsafi ce, da ita yayi masa saran".

Jauhar ta ce "Na shiga uku, ba zai tashi ba kenan?"

Walid ya ce "Zai tashi ki kwantar da hankalinki"

Aka yi wa Al'amin ɗinki, kamar ƙwarya aks ɗinke bayansa, sai dai walid ba su bari an yi a gaban jauhar ba, aka ɗibi jininsa, dan dubawa idan sai an ƙara masa jini, sai dai baya buƙatar ƙarin jini, sai dai an saka masa ruwa saboda jirin da yake yi ya hana shi tashi.

Sai dai ana tsaka da duba shin, jami'an tsaro suka iso, Walid ya ce kar matasan nan su bar su su shigo, sai an gama yi masa komai.

Aka din ga artabu da 'yan sanda da dandazon, yaran da suka yi wa harbar emergency ƙawanya, da kyar 'yan sandan suka shiga.

Da ƙyar aka tarwtsa tarin matasan nan, tana zaune ta ƙurawa fuskarsa ido, ƴan sanda suka ɗauki statement ɗin abun da ya faru.

Jauhar sai addu'a take yi, tana fatan Allah ya sa ya farfaɗo.

Ta riƙe hannunsa, tana shafawa a hankali ta ce "Allah ya shirya mini kai, ya baka lafiya master, inuwarka ce kawai nake tsaye a ciki nake saka ran samun farin ciki, dan Allah ka daina zuwa ana cutar mini da kai"

Idonsa a rufe, ya ɗaga hannunsa a hankali, ya shafi fuskarta sannan ya buɗe idon a hankali ya kalleta sai dai bai yi magana ba.

"Sannu master, an yi maka ɗinki a bayanka, akwai abun da yake yi maka ciwo ne?" Ya girgiza kai almar a'a.

Ta shafi sumar kansa ta ce "Allah ya baka lafiya"

Juyi yayi a hankali, ya kwanta a kan cinyarta, muryarsa ƙasa-ƙasa ya ce "Idan kina kuka ciwon ƙara zafi yake yi" ta goge hawayenta ta ce "To na daina, amma idan aka ji maka ciwo, zuciyata ce take kuka ba na so master".
A hankali yake matsa hannunta, yana jin wata nutsuwa ta mussaman, da sassaucin zafin da zuciyar sa take yi masa.

Zuwa magariba, ya miƙe ya ce sai sun tafi gida, Jami'an tsaro suka ce za su tafi da shi, sakamakon tayar da tarzoma a unguwa.

Walid ya ce "Saboda hauka ake yi, master ku ware gida, ni ku tafi da ni mu muka je muka tayar da tarzomar"

Ana fito da Al'amin, guduma ma ya taso, da sauri, Al'amin daga shi sai dogon wando, suka tari napep suka tafi gida.

A wurin maman halimatu jauhar ta karɓi mukulli, ta buɗe musu gidan suka shiga.

Ta saka yayi wanka, yayi alwala ya rama sallolin da ake bin sa, ta kawo masa abinci ya ci.

"Master" ya kalleta "Dan Allah ka fita daga shirgin madakin nan, ba shi da imani, kar ya hallaka ka dan Allah"

"Sai dai ɗaya yayi ajalin ɗaya ko ni ko shi, shari'ata da shi, Allah ne kawai zai rabata"

Cikin rauni ta ce "Ina haɗaka da girman zatin Allah"

"Shhhh, ki daina haɗa ni da Allah, kin san nauyin abun da aya aikata mini?"

"Ban sani ba, amma ina da yaƙinin koma me zaka yi masa, ba zaka huce ba, ka yi haƙuri ka bar wa Allah mana, idan wani abun ya same ka ya zan yi ne? Yanzu kalli halin da ka sakamu a ciki, na san yanzu haka a cikin pain ka ke, ciwon a jikinka yake, amma a zuciyata nake jin raɗaɗin, haba master, haba dan Allah" tayi maganar wasu zafafan hawaye na gangarowa daga cikin idanunta.

Ya miƙa hannunsa ɗaya da ba a side ɗin ciwon yake ba, ya janyota jikinsa, ba ta musa ba ko yi masa gardama, ta kwanta sosai ta cigaba da kukan, tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa sosai, kasancewar babu riga a jikin sa.

"Ba zan ɓoye miki ba, ban taɓa tunanin zan yi wata alaƙa da wata 'ya mace ba, saboda ina yi musu kallon azzalumai, ke ki ka fara canza tunanina".

Al'amin Ibrahim shi ne cikakken sunan Al'amin, mahaifinsa haifaffen garin kano ne, gidansu gidan yawa ne, baban Al'amin shikaɗai ne a wurin mahafiyarsa, sai tarin 'yan uba da galibinsu mata ne.
Yayi karatu daga primary zuwa sakandare har yayi diploma, sai dai aikin yi ya gagara samuwa, akwai abokinsa sammani da suka yi karatu tare, tare suke yawon neman aiki, ya ja shi garin su tofa, aka samo musu gona, suka fara noma.
A can ya haɗu da Zahra'u, ya ce yayi mata, da fari tsokanarta yake yi, saboda kwalliyar da take yi ta 'yan ƙauye ce take bashi dariya, daga baya soyayya ta ƙullu a tsakaninsu.

Abu kamar wasa, har ta kai ga aure, duk da bashi da wata ƙwaƙƙwarar sana'a, sai kame-kame.

Sun sha gwagwarmayar rayuwa tare, sun yi faɗi tashi, sun yi fama da yanayin rayuwa, kafin Allah ya buɗa masa ya fara samu.
Lokacin da suke cikin wahala babu mai taimakonsa, daga shi sai ita suke wahalar su, ta samu ciki a lokacin ta haifi ɗan ta na fari, aka saka masa Abubakar Assidiƙ, sai lokacin da Allah ya fara buɗa masa, 'yan uwansa suka saka musu ido, da surutun yana zaƙewa da yawa a kanta.

Komai ya samu ita, ya tashi daga tsakiyar cikin garin kano, ya koma gwauron dutse yayi mata gida mai kyau.

'yan uwansa suka fara tsangwamar ta, da cewa ta shanye musu ɗan uwa, Ibrahim ya mayar da ita makaranta ya samo mata admission a FCE, ta ke karantar English islamic. Kasancewar ta mace kyauta, da fara'a da sakin fuska ga mutane, ya sanya take da masoya sosai. Sai dai duk da kyautarta, da son mutane dangin mijinta ba sa ƙaunarta.

A can gwauron dutsen, ta haɗu da wata mata rahila, maƙwabciyarta ce, tana yawan zuwa ta kawo mata complain a kan mijinta ba ya kula da ita da yaranta, hakan ya sanya tausayin rahila ɗarsuwa a zuciyar Zahra'au, kusan kullum cikin yi wa rahila aike take, na abun da zata kula da yaranta, kuɗi, sutura, abinci kayan masarufi, saboda Ibrahim yana sakar mata sosai baya yi mata iyaka da komai.
Tana NCE 2, Sadik ya shekara biyar, ta samu ciki, tayi ta fama ga laulayi ga karatu, rahila take barwa Abubakar ta tafi makaranta, ƙarshen wata, take biyanta da kuɗi mai kauri saboda ita ma ta samu.

Ta haifi ɗanta na biyu, aka saka masa Muhammad Al'amin, saboda haihuwar maza da take yi, dangin miji, suka ƙara yi mata caaa wai tana ta haifar maza, dan ta kwashe komai na gado idan ya mutu.


Ayshercool
08081012143






🔞₦500 ne via 0009450228
Aisha Adam jaiz bank sai shaidar biya ta 08081012143

90009343
'Yan Nijar ku turo katin airtel na 300fcfa

Arewabooks ayshercool7724

https://chat.whatsapp.com/E3bH5OKBh9jH2aYygj0ArA


Kina bukatar kaya masu kyau da inganci??

    Kina bukatar kayan kitchen wnd suke available ba order ba??

    Kina bukatar adashin gata wnd zaki dauki kaya kamar kyauta??

    Kiyi joining wnn group din namu insha Allah xakiji dadin kasancewa a ciki.

     Muna da kaya available masu kyau da rahusa💃🏾💃🏾
Ko kimin mgn ta👇🏽👇🏽
08093932955



Ya saki Sadik a ƙasa bayan ya caka masa almakashin, cikin tsananin tashin hankali, Al'amin ya yi kukan kura ya danƙi ɗan daban, amma wani daga cikin yaransa, ya lallaɓa ya sake maka masa gora a baya, ya gantsare yana wani irin ihu, suka yi gaba suka bar su.

Ya din ga dukan gate ɗin gidan, yana ƙwalawa Abbu kira, ya koma kan Sadik, ya rungumo shi, yana jijjiga shi.

Sai da garin yayi shiru, sai kururuwar Al'amin yana kiran Yaya.

Maƙwabcinsu ya fito, na kusa da shi ma ya fito, aka din ga buga gidan su Al'amin, har aka tafi nemo mota, sannan Abbu ya buɗe. Sai dai ya shiga tashin hankali, ganin Sadik a kwance kamar mara rai.

Cikin tashin hankali Abbu ya tafi kici-kicin fito da mota, Al'amin ya zuciya ya ɗauki Sadik a kafaɗarsa, kawai yayi gaba.

Da ƙyar aka riƙe shi, aka saka Sadik a mota.

Al'amin sai zubar da hawaye yake yi, ya na kiran "Yaya ka buɗe idonka ka kalleni, ka tsaya yanzu zamu je asibiti"

"A galabaice, Sadik ya motsa ya riƙa hannun Al'amin, sai kuma hannunsa ya saki. ko da suka je Asibiti, aka tabattar musu da Sadik ya koma ga Allah.

Al'amin ya durƙusa a kan gawar, ya din ga rusa kuka, kukan da ko lokacin da umminsu ta mutu bai yi shi ba, maƙwabta na ta rarrashin Al'amin.

Cikin kuka Abbu ya ce "Al'amin komai ya samu ɗa na kai ne sila, ka sa nayi rashin ɗa mai biyayya"

"A'a Alhaji Ibrahim, kar ka sake ka ɗorawa Al'amin laifi, kai ne babban mai laifi, kana sane sarai unguwar nan babu kwanciyar hankali, ka bar su a waje, da ka buɗe musu sun shiga gida, koman dare ai da haka ba ta faru ba".

A daren aka yi wa Sadik sutura, Al'amin gani yake yi kamar a mafarki, awannin da suka gabata suna tare amma a yanzu wai babu Sadik. Kodayeke Abbu yana da gaskiya shi ne sila, da bai ce zai bar gidan yayi tafiyarsa ba, da haka baya faru ba, dan kuwa Sadik ba ya yawon dare.

Har jami'an tsaro sai da suka zo suka ɗauki bayanan abun da suka faru, sai dai Al'amin ya kasa magana.

Sadik ya tara ɗimbin mutane, yara da manya matasa da dattawa wurin sallatar gawarsa, kasancewar sa mutumin kirki.

Al'amin ya ji ina ma shi aka kashe, Sadik ya rayu, yayan nasa guda ɗaya tal da yake saukewa duk wata damuwarsa ya ɗauka babu ƙosawa ko gazawa, an kashe masa shi.

Alhaji sammani, ya yi wa Ibrahim tatas, a kan yadda ya koma soko a kan gidansa, tare da ci wa Rahila mutunci tsaf, a kan abubuwan da take aikatawa.
Ƙarshe ta shiga ta fita, ta raba abotar da aka yi shekaru ana ginata, suka rabu dutse a hannun riga, suka yi uwar watsi.

Depression ya nemi ya kama Al'amin, babu wand yake ta tasa, gashi yanayin halayarsa idan ba wanda ya sanshi ya saba zama da shi ba, ba kowa zai iya masa ba, saboda miskili ne, ga nuƙufurci, ba zai taɓa cewa wani ga damuwarsa ba, shi ba abokai ba, haka ya din ga ragaita a layi, raɗaɗin mutuwar Sadik taƙi barinsa.

Ya tafi wurin 'yan sanda ya tambayi, ko sun kama wanda ya kashe yayansa, suka ce masa bincike suke yi a kai, dan har a lokacin ba su tabattar da wanda yayi kisan kan ba, kuma a ranar ba Sadik kawai aka kashe ba.

Al'amin ya koma gida, yayi ta addu'a Allah ya sa a kama wanda ya kashe masa Sadik, duk da dare ne, amma a ko ina ya ga wanda ya kashe shi zai gane, dan kuwa ƙofar gidan su akwai security light.

Duk bayan kwana biyu sai Al'amin yaje, tun suna sauararsa har suka fara korarsa.

Ga matsi ya ƙaru daga gidansu, babu in da zai samu abinci, ya yanke shawarar fara zuwa kasuwa ya duba ko dako ya fara, sai da ya je ya tarar ashe dakon ma sai ka san wani, sai an san da kai, duk sana'ar da yayi tunanin farawa sai ya ga dole sai da jari, gashi Rahila ta cigaba da ziga Abbu, ya ƙara tsanar Al'amin wai shi ne silar mutuwar Sadik.

Al'amin ya fara gajiya da yunwa da take neman tagayyara shi, ya fara zuwa gida ya ɗauki duk abincin wanda ya tarar ya cinye, idan ya tafka wannan tsiyar, sai ya gudu ya kwana a kangwaye, gashi ya koma HND tun Sadik na raye, dama shi ne yake ta fafutukar tara school fees ɗin sa kan ya rasu, yanzu kuma ga yunwa da rashin kuɗin transfort dan haka ya daina zuwa makaranta gaba ɗaya.

Gashi ko a maƙwabta aka rasa wanda zai yi wa Abbu nasiha, ko su din ga taimakonsa, saboda ana ganin babansa yana da rufin asiri.

Yana can garin yawonsa, kawai ya hango wanda ya kashe Sadik, a tsallaken titi, da tawagar matasa 'yan daba, da gudun gaske Al'amin ya tsallaka titin, sai dai kan ya ƙarasa sun ɓace masa, cikin tashin hankali ya ƙarasa wurin wani mai ice ya ce "Malam dan Allah wanda ya wuce ɗin nan ina yayi?"

Ya kalli Al'amin ya ce "Meye haɗinka da shi?"

"Yayana ya kashe da almakashi, bai yi masa komai ba, 'yan sands suna ta nemansa"

"Taɓ, ka raba kanka da wannan. Madaki kenan gawurtaccen ɗan daba ne, hukuncin kisa ma aka yanke masa a gidan yari, amma muka ga an sake shi, duk ya gallabe mu, ya hanamu sukuni mu ma, sai dai ka bar wa Allah kawai" Ai Al'amin bai tsya jin ƙarshen zancen ba, ya shiga cikin unguwar ya din ga yawo, amma bai ga madaki ba.

Washegari da sassafe, ya koma wurin 'yan sanda ya gaya musu ya ga wanda ya kashe yayansa, su tafi tare da shi a nemo shi, an gaya masa sunansa madaki.

Wani ɗan sanda ya kada baki ya ce "Ka san mutum nawa madaki ya kashe aka ƙyale shi?" al'amin ya ce "Ni ina ruwana da mutum nawa ya kashe, ku kama shi a kai shi kotu ni dai".

"Ko an kai shi ma, za a sake shi, ka je ka yi haƙuri haryanzu bamu tabattar da shi ya kashe shi ba".

Kasancewar Al'amin yana kan tashen balaga, ya sanya ya tsaya yana yi musu rashin kunya, aka saka wani sageant, ya zane shi aka kore shi. Hakan yayi matuƙar tunzura zuciyar Al'amin, ya din ga jin jinin ɗan uwansa ba zai tafi a banza ba.

Ya din ga sintiri a unguwar da madaki yake, kasancewar ba su da nisa sosai, ya samu duk bayanin da yake son samu a kan madaki, da in da yake zama da shi da yaransa.

Ya je gida ya shiga kitchen ya samo, wuƙa sabuwa gal, ya je ya ɓoye, ya saka a ransa shi ma sai ya kashe madaki, ko da kuwa za a kama shi a kashe.

Sai dai aka yi rashin sa'a, Madaki bai fiye zama a unguwar ba, sai idan zai shigo yayi rashin mutunci, Al'amin ya din ga fakonsa, har ya yi wataran sa'a ya tarar yana nan.

Gadan-gadan ya ratsa tarin matasan da suke ɗauke da makamai suna shaye-shaye, ya nufi madaki da wuƙa.

Matasan suka mimmiƙe, amma madaki ya ɗaga musu hannu, a kallo ɗaya madaki ya gane Al'amin.

Kafin ya ƙarasa gaban madaki, sani ya sanya ƙafa ya taɗiye Al'amin dan haka ya faɗi a gaban madaki, suka kwashe da wata irin dariya.

Al'amin ya yinƙura zai tashi, madaki ya saka aka take masa kafaɗun Al'amin da ƙafa, yana ƙoƙarin tashi, amma cikin ƙarfin Al'amin ya tashi, madaki ya tako gaban Al'amin ya shaƙe wuyansa.

Take Al'amin ya ji kamar an shaƙe shi da wata muguwar sarƙa mai nauyin gaske, a take ya ji numfashin sa na neman ƙwace masa. Al'amin ya saki wuƙar ya koma kokowar raba hannun madaki da wuyansa, madaki ya tsare shi da jajayen idanunsa da ya rambaɗa musu farin kwallin tsafi, yana ƙyaƙyata wata uwar dariya, daga bisani kuma ya tsuke rai tamau, ya ƙara tsananta shaƙe Al'amin, sai da ya ga ya daina motsi, sannan ya watsar da shi a wurin, ya kalli wani ya ce "Ku kai shi arear su ku watsar"

"Ba za a saita ma hanya daga duniyar ba ya ci bulus kenan?"

Madaki ya girgiza kai ya ce "Yana cikin tsananin ɗacin rashin ɗan uwansa, idan aka yage shi daga sararin nan, hutawa zai yi, sai ya gane kuskuren da ya aikata na yinƙurin da yayi"

Suka ɗauki Al'amin suka kai shi unguwar su, suka jefar da shi a sume a gaban wani mai kayan miya, suka ce wa mutanen wurin "Gashi nan, ajiyarmu ne, zamu din ga bibiyar sa ku kira tsohonsa ya ɗauke shi idan yan buƙatarsa".

'yan unguwa suka ɗauke shu, suka kai shi gida, Abbu yana nan, aka kwantar da shi a tsakar gida, ana shafa masa ruwa, mai kayan miya ya gaya wa Abbu abun da yaran madaki suka ce, aka shawarce shi a kan ya kai maganar wurin jami'an tsaro, amma Abbu ya ce babu ruwansa, tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka, shi bai aike shi wurin 'yan daba ba.

Tun daga nan madaki ya mayar da Al'amin kamar karen farautarsa, ya saka rayuwarsa a gaba, wataran har cikin unguwar su yake aikawa, a nemo masa Al'amin, a kai masa shi har dabarsa, su casa shi da zalunci kala-kala, wai sa ya saduda ya nemi afuwar abun da ya yi wa madaki, dan ba a taɓa samun wanda ya yi abun da Al'amin yayi ba, ya rasto har dabarsa ya nemi ya kashe shi, yana ƙanin ƙanin bayansa.

Al'amin ya kalli madaki ya ce "Ka yi kaɗan na nemi afuwarka, baƙin kare kuma in sha Allah sai na zubar maka da jini, kamar yadda ka zubar da jinin ɗan uwana da bai yi maka komai ba"

Ya durƙusa ya soka wa Al'amin wata kibiya a cinyarsa, cinyar sa na zubar da jini, amma saboda azabar taurin kai, ya datse haƙoransa ya ƙi ihu.

"Na fuskanci zaka yi mini amfani, na saka ka cikin yarana daga yau, zaka din ga yi mini aiki"

Al'amin ya girgiza kai ya ce "Ni fa kallon kare nake yi maka, da na bika gara na yi mutuwar wulaƙanci"

Ya ce "Shikenan zamu gani, dafin ciwon da nayi maka na fili da na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login