Showing 27001 words to 30000 words out of 176046 words

Chapter 10 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete

kidena mu ba'a rashin kunya agarin nan!”.
Ita kuwa khausar inda ya ɗan bugeta tasa hannu ta riƙe tana sosawa duk da cewa bawai zafi ya mata ba ta tura ƙaramin bakinta tace.
“To ai muma ba rashin kunya bane wannan kam”.
Dan ƙolo ya mata yace.
“Dije jata ku tafi”.
Kai Dije ta gyaɗa wacce se alokacin ta samu kuzarin miƙewa tace.
“Khausar kizo mu tafi“, Sannan taja hannunta suka fita.
Suna fita Khausar kuwa hannunta dake cikin na Dije ta janye tace.
“Yanzu ina zamuje?”.

Murmushi Dije ta sakar mata tace.
Rafi zamuje”.
Murmushi mai sanyi Khausar ta sakar mata wanda ke ƙarawa fuskarta kyau tace.
“Toh mu tafi”.
Dan sosai weather garin yake abin burgewa da sha'awa.

Cikin nutsuwa suka nufi Rafin suna hira.
Da sauri Dije ta riƙon hannun Khausar tare da nunawa mata gefen damansu, masu wasa da birine ke tafiya kana yaran rugagen dake gefe dasu na biye dashi, bisa alamun yanzu kuma rugarsu zasu shiga.
wani ƙaton Biri yake ta kolongoiso yara nata ja da baya.
Cike da nishaɗi Khausar tace.
“Muje muma mu gani”.
Kai Dije ta gyaɗa mata , kana suka nufi wajen me wasa da Biri suna ganin yanda Birin ke duk abinda aka sashi.

Cike da farin ciki Khausar ta kalli mai wasa da Birin tana ƙara kusawa cikin yara matan tace.
“Mai Biri yanzu duk abinda na sashi zai min?”.
Kai mai wasa da Birin ya jinjina yace.
“Idan kuma baki yarda ba ki gwada ki gani”.
Kusa da Birin Khausar ta matsa tana murmushi tace.
“Yauwa yaya salon mugun Malami yake idan zai daki ɗalibansa?”.
Da sauri ta ware idanunta ganin.
Birin ya wani ja baya tare da harɗe hannunsa aƙirji kana ya ɓata fuska tare da harɗe sawunsa sai kuma ya ɗauki wani sanda ya riƙe yana nuna Khausar da Dije.

Hannu Khausar tasa ta dafa kafaɗar Dije tare da tintsirewa da dariya mai cike da sautin shauƙi yayin da ɗaya hannun kuma ta ɗaura saman shafefen cikinta tana mai cigaba da dariyar.
Domin kuwa babu wanda ya faɗo mata arai lokacin da Birin ke gwadawa face Moddibo duk da kasancewarsa ba mutum ne mai Fara'a ba amma duk sanda zaisa a zaneta a makarantar Islamiyya seya sake tamke fuskarsa..
Dariya sosai takeyi wanda da yawa cikin yaran tayata sukeyi.

Ganin bata da niyyar daina dariyar ne yasa Dije jan hannunta cikin dariya tace.
“Khausar Mu tafi,Dariyar me kuma kike haka!?”.

Tsagaita Dariyar Khausar tayi sai kuma lokaci ɗaya jikinta yayi sanyi tuna wa da tayi Moddibo zai iya jira duk lokacin da tawo ya yanke mata hukunci ahankali tace.
“Kawai na tuna da wani Malamin mune”.
Murmushi Dije tayi tace.
“Allah sarki shike zaneki kena”.
Kai ta jujjuya tare da cewa.
“Wancan da shegen madarar ƙasaita sawa yake a zaneni dai yana nan jiki kamar auduga ai shi dukan ma aikine a wurinsa”.
Murmushi Dija tayi tare da cewa.
“Da Goggo Hajja zataji haka sai ta sa mishi al'barka”.
Baki ta tura ba tare da tace komai ba sukaci gaba da tafiya.

Suna shiga Rafin idanun Khausar ya sauƙa akan Bishiyoyin Piya, Caɓɓulle, Mangoro, Ayaba, Gwanda, Gwaba, Lemo, da sauran kayan itatuwa duk sun yiwa wajen ƙawanya.
Sake wara Ido Khausar tayi ganin bishiyoyin Inabi guda uku a jere,
Cikin farin ciki ta dubi Dije tace.
“Harda Inabi Laha'Ila Ha'illalhu Masha Allah zan kuwa ci”.
Ta ida maganar tare da nufar jikin Bishiyar zata hau.

Saurin riƙe hannunta Dije tayi tace.
“Kada ki hau Khausar Baffa Liman ya hanamu yace ba shida amfani 'ya'ya mata su riƙa hawa bishiya ba tarbiyya bace mai kyau”.
Ita kuwa khausar janye hannunta dake cikin na Dije tayi tace.
“Ke rabu dashi da ƙa'idojinsa hawa za muyi mu cire abinmu, ai kuma ba har can sama zamu hauba”.
Langwaɓar da kai Dije tayi kafin tayi magana suka hango wani farin saurayi kyakkyawa daga ɗaya gefen.
Hannu Dije ta ɗaga masa da faɗim.
“Yawwa Sadik dan Allah zoka cire mana Inabi wai zata ci”.

Ƙara sowa Sadik yayi idanunsa akan Khausar yace.
“Dije wannan yarinyar wa kika samo?”.
Murmushi Dije tayi tace.
“Yarinyar Marigayi Baffa Usmanu cefa yaron Goggo Hajja”.

Murmushin fuskarsa ya faɗaɗa yace.
“Allah sarki itace wacce take Birni ko?”.
Kai Dije ta gyaɗa tace.
“Eh itace”.
Ita dai Khausar ba tace komai ba.
Raɓar bishiyar yayi ya ciro musu Inabi kana ya koma bishiyar Ayaba shima ya ciro yasa musu aƙaramin kwandon dake hannunsa irin na saƙar kaba na gargajiya miƙawa Dije yayi.
Sai asannan Khausar tace.
“Mungode”.
Murmushi kawai yayi ba tare da yace komai ba,
suka fara tafiya cikin rafin akai-akai Khausar ke lumshe idanunta tana wasa da yatsun hannunta sosai weather garin ya mata daɗi.
Juyowa tayi ta kalli Dije tare da cewa.
“Garinku yayi min daɗi”.
Cikin sauri Sadik yace.
“Garinmu de kin cire kanki ne a ciki? Ko kin manta nanne tushenki kuma asalinki nanfa cibiyarki take abinne”.
Dariya tayi kafin tace.
“Hmmm Shiyasa ma naji daɗin garin inba haka bama masifar wannan tsohuwar yasa bana sha'awar zuwa garin nan”.
Zare ido Sadik yayi yace.
“Wacece masifaffiyar!?”.

Asanyaye Dije za tace.
“Wai Goggo Hajja take cewa masifaffiya”.
Sake zare ido Sadik yayi se kuma yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”,Ya dubi Dije yace.
“Meye sunanta ma kika ce?”.
“Khausar”
Dija tace.
Ya maida kallonsa kan Khausar da hankalinta yabi shuke-shuken da kallo yace.
“Khausar kiyi Istigfari”.

Khausar kuwa kallon mamaki tayi masa kafin tace.
“Saɓon Allah nayi da zanyi Istigfari?”.

Habarsa ya riƙe still Fuskarsa ɗauke da Mamaki yace.
“Goggo Hajjan kike cewa Masifaffiya”.
Baki ta taɓe tace.
“Yo ba masifaffiyar bace daga zuwa na fa kawai takama yimin bala'i”.

Kai ya jinjina kafin yace.
“Toh kar ki sake wallahi in Goggo Hajja taji abinfa baze miki daɗi ba”.
Cikin sanyin murya Dije tace.
“Allah de ya kyauta anma wannan baƙunta ai akwai kallo aciki”.
Ba wanda ya sake magana har suka fito daga cikin Rafin.
Gani tayi Sadik ya ɗauki wani babban kwando da sunyi ta fiya kaɗan sai ratsa cikin ciyawa ya buɗe ya ɗibi ƙwan Zabbi ya saka acikin kwando.

“Me kakeyi haka?”.
Khausar ta tambayesa tana kallon wajen da ciyayi masu kyau da tsari suka lulluɓe wajen.
Murmushi yayi yace.
“Ƙwan Zabbi nake tattarawa”.
Cikin lumshe ido tace.
“Ohhhh lalle kam Masha Allah abamu naci”.
Murmushi yayi tare da faɗin.
“Toh babu damuwa”.
Haka suka riƙa tafiya suna hira jefi-jefi sun kusa fita daga cikin Rafin ne Khausar ta jiyo hayaniya na tashi kamar kasuwa anata surutu da dariya jujjuya wa tashiga yi amma bata ga inda sautin surutun ke tashi ba.Ta dubi Sadik da Dije tace.
“mene nake tajin hayaniya da surutun nan kam a cikin daji?”.
Sadik ne yace.
“Mutanen Bishiyar ƙare zancen kane”.
Da sauri ta sake duban sa tare da cewa.
“Bishiyar ƙare zancen ka?,Wai mene ma'anar Bishiyar ƙare zan cenka?”.

Dije ce tace.
“Ai mu garin nan bamu da service, Service ɗinmu waje ɗaya ne inde mutum yana so yaje yayi waya seya je ya hau bishiyar ƙare zencen ka anan ne ake samun network idan kina wajen zaki iya kira sannan za'a iya kiranki kina sauƙa daga bishiyar ko kuma kina Matsawa daga wajen bishiyar toh shikenan Service ya yanke ba zaki samu kiyi magana ba kuma shima sai in layin MTN ne ko Zain”.

Cike da Mamaki Khausar tace.
“Ikon Allah wannan wani irin ruga ne?. Dama ashe har yanzu akwai irin wuraren nan daya rage aduniya?”.
Murmushi Dije tayi tace.
“Sosai ma”.
Ahankali Khausar ta ɗaga kanta nan ta hango manyan tsaunika da bishiyoyi Kallonta ta mayar kan Dije tace.
“Haba ko wannan manyan tsaunuka da bishiyoyin ai sa tare muku service da network”.

Kai Dije ta gyaɗa tace.
“Lalle kam da alama shi ya tare”.
Ta dubi Sadik dake tsintar ƙwai tace.
“Muje inga wajen”.
Kai ya gyaɗa sannan yashiga gaba ita da Dije na biye dashi ta cikin wata siririyar hanya Sadik na cigaba da tsintar ƙwo'yin suna fita asirin hanyar Khausar ta hango wani ƙaton bishiyar ɗaurawa dake ɗauke da rassan bishiya masu taren yawa saura daga sama saura kuma sun zuba yayin da ƙasansa bishiyar duwatsu ne baƙaƙe masu sheƙi ke zube wanda suke kamar kujeru.
Juyawa tayi ta maida Idanunta kan dandazon mutanen dake wajen mafi yawa Matasane sai kuma Dattijai tana ɗaga kanta sama ta hango Baffa Jauro yana waya.

Dariya ta ƙyalƙyale dashi tace.
“Baka tsoron ka faɗo ko tsohon nan?".
Dije ce ta ɗan bigi ƙeyarta tare da yi mata hararan wasa tace.
“Baban nawa ne tsoho?”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Toh baya tsoro ne kiga ya hau kan bishiya ya ɗane kamar birin can”.

Tsayuwa Dije ta gyara tare da mata hararar wasa tace.
“Ai shikam dole seya zo nan yayi waya tunda shine Jauron garin nan akwai ɓuƙatar magana da Jauro da sauran Jaurorin garirruwa”.

Khausar kuwa kai ta gyaɗa tace.
“Ikon Allah lalle de kam irin wannan gari haka”.
Tayi maganar tana kallon matasan dake sanye da kayan Fulani kowa na amsa wayar, Idanunta ne suka sauƙa akan wata tsohuwa dake waya.
Ta maida kallonta kan Dije tace.
“Wannan kuma fa?”.

Dije tace.
“Tafff!, Wannan ƙawar Hajja Nana ce”.
Kallonta Khausar ta sake yi tace.
“Ƙawar Masifa de zaki ce”.
Sadik dake gyara kwandon ƙwai yace.
“Ki bari fa”.
Ta kallesa da manyan Idanunta dake lumshe tace.
“Ai da gskene Hajja Nana in ba masifa ba meta iya!?”.

Duk mutanen wajen juyawa sukayi tare da zuba mata idanu jin tana kiran Hajja Nana Masifa,Wasu daga cikin mutanen ne suka ce Dije ina kika samu wannan yarinyar.
Dije kuwa tayi murmushi tace.
“ 'Yar Baffa Usmanu ne”.

Jin Abinda Dije tace yasa sauran mutane dake saman bishiyar kashe wayansu suka sauƙo.
Wani kyakkyawan Matashi fari ne ya nufosu kallo ɗaya zaka masa kasan akwai wayewa atare dashi yace.
“Wannan itace 'yar Baffa Usmanu itace ƙanwar Nenne ko Masha Allah?”.

Kai Dije ta gyaɗa tare da nunawa Khausar matashin tace.
“Kinga wannan?”.
Kai Khausar ta gyaɗa.
Dije tace.
“Yaron Baffa Liman ne acikin Birni yake karatun sa”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Ayyah Allah Sarki yayi kyau".
Ya dubi Khausar da murmushi afuskarsa yace.
“Hi Sister how are you?”.
Ta mayar masa da martanin Murmushin tace.
“Am fine how's everyone?”.
“Fine Long time?".
“Thank God”.
Dije ta wani ɓata fuska Idanunta akan Khausar tace.
“Kuyi magana da yaren da zanji”.

Murmushi Khausar tayi tace.
“Ba wani magana muka yiba kawai gaisawa ne fa”.
“Toh”.
Dije tace sai kuma ta maida kallonta kan Matashin saurayin tace.
“Ayyah Yaya Abba nima ka koya min turancin”.
Murmushi yayi yace.
“Ba matsala zan koya miki Kinga ga wata ma zata koya miki”.
Hira suka cigaba dayi yayin da Sadik ya cigaba da tsintar ƙwoyaye wasu ma da yawa nata tsintar ƙwoyin ko wannensu da alama akwai inda ƙwan Zabbinsa ke tsayawa akwai waya da ake sakawa atsakanin waje-jen...
Baffa Jauro daya gama waya ya sauƙo tare da zuwa inda Khausar take ya riƙe hannunta suka fara tafiya sai kuma ya fara matsa hannun, Janye hannun tayi tace.
“Wallahi tsohon nan ka iya mugunta inka riƙe hannun mutum kaita matsewa da faratu ni banaso”.
Murmushi Baffa Jauro yayi tare da sake matse hannun!.
Ashagwaɓe tace.
“Wayyo na tuba ka sake”.
Sake mata hannun yayi yana dariya yace.
“Ohhh in dai baki daina yiwa Adda Nana rashin jiba, toh fa hakan zanyi ta matse mata ke, ga jiki ba ƙwari ba'ason wahala”.

Sai kuma ya juya ya dubi Dije yace.
“Dije”.
“Na'am Baba”.
Yace.
“Kishirya Gobe idan Allah ya kaimu da sassafe zaki ɗauke ta kuje kuyi tsar Nono tare”.

Kai Dije ta gyaɗa kana tace.
“Insha Allah zan ɗauke ta muje tare”.
Kallonsa Khausar tayi still hannunta na cikin nasa tace.
“Nide inda wuya bazan yiba”.
Dije tace.
“Ba wuya ai zamu baki man shanu ki shafawa yatsunki yanda zai yi santsi.
Kai ta gyaɗa tace.
“Toh shikenan ba damuwa zanje”.

Kallon Dije Sadik yayi tare da bata kwandon Ƙwan Zabbin yace.
“Ki tafi dashi".
Sannan ya juya ya cigaba da tafiya.
“Khausar kuwa murya ta ɗan ɗaga tace.
“Kaifa baza ka bimu bane”.
Girgiza Kai yayi yace.
“A'a ban ƙarasa ɗiba ba”.

Kai ta gyaɗa tace.
“Toh inde kazo ka kawo min nawa”.
“Toh”,Yace sannan suka juya suka tafi.

Suna shiga rugar suka nufi hanyar gidan Hajja Nana kasancewar duk gidan da zaka je seka wuce ta ƙofanta,sannan duk lokacin da taji motsi seta tambaya waye.
Sallama Dija tayi cikin ladani kana suka shiga, Hajja Nana dake cikin uwar ɗaka tace.
“Waye”.
Cike da ladabi Dije tace.
“Dije ce".
Haɓa Khausar ta riƙe tare da cewa.
“Ikon Allah duk mai wucewa saita tambayesa waye sai kace wata Traffick light?”.
Ƙasa da murya Dije tayi tace.
“Aaa ki bari Khausar kiyi ahankali kar taji”.

Khausar kuwa baki ta taɓe tace.
“Ai wannan abu yayi yawa wannan mulkin mallaka haka ake yi muku agarin nan”.

Daga ciki Hajja Nana tace.
“Dije keda waye naji kamar ana magana ƙasa-ƙasa?”.

Dije tace.
“Nida Khausar ce zamuje gida kai saƙo ne ƙwoyi muka kawo”.
Ita kuwa Hajja Nana cewa tayi.
“Toh shikenan”.
Ajiyar zuciya Dije ta sauƙe sannan suka fice.
Lokacin da suka fita makiyaya sun fara dawowa daga kiwo sannan sanyin magriba na sake sauƙa sanyin ya fara yawa ahaka suka isa gidansu Dije Khausar sai lumahe ido take.
Suna isa suka ajiye Ƙwoyin.
Dije na ƙoƙarin shiga ɗaki Khausar da Idanunta suka sake lumshewa tace.
“Dije muje ki rakani ɗaukan Sweater na sanyi nake ji sosai”.

Kai Dije ta gyaɗa sannan suka fice kallon garin Khausar tayi ko ina baƙi ba alamar hasken wutar lantarki ta dubi Khausar tace.
“Wai kam garin nan baku da wuta ne?,tun da nazo banga ƙyallin wuta ko sau ɗaya ba?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tace.
“Eh babu amma ana tada Generator”.
Khausar kuwa hankalin tane ya tashi jin babu wuta garin!.
Ganin yanda tayi yasa Dije sakin murmushi tace.
“Kada ki damu kinga Yaya Abba shike tada Generator sannan yake sa kawa mutane Caji kuma aƙofar gidan Hajja Generator yake akwai ɗan haske kaɗan koda ba farin wata, bare kuma in akwai farin wata rana zakiga garin”.
Sai asannan Khausar ta ɗan saki ajiyar zuciya dan Allah ya sani tana tsoron duhu.

Bakinsu ɗauke da sallama suka shiga gidan shigarsu yayi dai-dai da kiran Sallar Magriba da akayi.
A tsakar gida suka samu Hajja Nana na alwala, kallonsu tayi tace.
“Kuzo kuyi alwala kuyi Sallah”.

Kallon ta Khausar tayi tace.
“Ni gaskiya sanyi nake ji yanzu ma rigar sanyi na nazo ɗauko kuma asamar min ruwan zafi dashi zanyi alwala”.

Harara Hajja Nana ta watsa mata kafin tace.
“Wa zai samar miki ruwan zafi?,Kina yarinya ƙarama yau har wani sanyi kirki akeyi! da har zaki nemi ruwan zafi”.

Bakinta ta tura amma ba tace komaiba.
Dije ce tace.
“Muje gidanmu akwai ruwan zafi sai kiyi acan”.

Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh shikenan”
Sannan tashiga ɗakin Hajja Nana kasancewar akwai hasken lanta da aka kunna inda trolley ta yake ta nufa ta buɗe tare da ɗaukar Sweater ta sannan ta rufe trolley juyawar da za tayi Idanunta suka sauƙa akan kuliya (Mage) dake kwance akan ɗaya daga cikin gadon Hajja Nana kasancewar gado biyu ne aɗakin sai kuma ɗan shirge-shigen ta na Tsoffin ruga.

Cikin matsananci tashin hankali da ruɗu mara misaltuwa daya bayyana afuskarta take faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n!!,Hasbunallahu!!!, wani'imal wakin Astagfirullah wa'atubu ilaik!!!”.
Aruɗe Dije ta shiga ɗakin tana cewa.
“Lafiya Khausar meye faru?”.

Aruɗe Khausar ke yarfe hannunta takamar wacce ta ƙone duk jikinta na rawa takasa furta komai numfashinta na wani irin fusga na tsananin tsoro da tashin hankali, da ƙyar ta iya furta.
“Kuliya”.
Sai asannan Dije ta lura da kuliyar da har zuwa lokacin ke kwance akan gadon Hajja Nana.

Ita kuwa Hajja Nana wani dogon numfashi taja.
Dan da kusan mutuwar zaune tayi dan jin irin karajin da Khausar ɗin tayi.

Ita kuwa Dija hannu tasa tashiga koran kuliyar.

Daga can waje Hajja Nana ke cewa.
“Kuliyar take wa wannan Ihun? zata kasheni tun kwanana bai ƙareba”.

Ina ita kam Khausar bata san sunayi ba, har zuwa yanzu tsalle takeyi a tsakiyar ɗakin tana yarfa hannunta tare da furta duk addu'ar da tazo bakin, istagfari takeyi ba ƙaƙƙautawa.

A gigice Dije ta fitar da kuliyar tana mai cewa.
“Khausar ki nitsu ya fita, na koreshi, kuliyar Goggo Hajja cefa.
Cikin tsananin tsoro da rawar jiki cike da gigita,
Ta fito cikin ɗakin Hajja Nana ta nufi gidan Baffa Jauro tana cigaba da faɗin.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n
Ya Allah na tuba ka yafe min”.
Yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ke rawa na tsananin tsoratan da tayi.

Jin shiganta Aruɗe yasa Goggo Nanne fitowa daga ɗaki wato Mahaifiyar Dije.
Matsawa kusa da Khausar tayi ta riƙe Hannunta tace.
“Lafiya”.
Asanyaye Dije tace.
“Kuliya take tsoro taga kuliyar Goggo
Hajjs ce take haka”.

Cike da tausayinta Goggo Nanne tace.
“Ayyah Subhanallah ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya kar ki damu Khausar ki kwantar da hankalinki ki nutsu kinji?”.

Kasa furta komai Khausar tayi sai Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n da take yi aƙasan ranta.
Addu'a Goggo Nanne tashiga tofa mata kafin ta samu hankalinta ya dawo jikinta.
Jauro daya fito daga banɗaki yana alwala yace.
“Yau kuliya ce haka kamar wanda taga kura haka?”.
Ya faɗa yana kallon yanda tsananin razana ya bayyana afuskarta.
Juyawa yayi yana kallon Goggo Nanne yace.
“Lalle wannan baƙunta akwai saɓani a cikinsa. Ita Addah Hajja ba zata iya rayuwa babu kuliya ba ita kuma wannan ga tsoron kuliya”.

Tana sakin ajiyar zuciya tace.
“Nide bazan sake shiga ɗakinta ba shegen ɗaki ga tarukuce ga duhu sannan ga kuliya wannan ɗakin har macizai za asamu acikinsa bazan sake shiga ɗakinta ba”.

Murmushi Goggo Nanne tayi tace.
“Ki kwantar da hankalinki kada ki damu tashi kiyi alwala ga ruwan zafi abuta”.
Batace komai ba ta miƙe ta ɗauki butar ta zaga bayi sannan ta fito tayi alwala ɗakin Goggo Nanne suka shiga da Dije cikin ɗakin duhu.
Araunane Khausar tace.
“Daƙin duhu ni gani nake ma ko ina akwai kuliya”.

Dafa kafaɗar ta Dije tayi tace.
“ki kwantar da hankalinki nan babu kuliya”.
Ta ƙare mgnar tana kunna lantansu mai ɗan karen haske,
Kai kawai ta jinjina tare da sauƙe ajiyar zuciya ganin hasken, sannan ta tada sallah suka idar da Sallah maghariba Khausar kuwa jingina bayanta da jikin bango tayi ta fara addu'a.
Dije kuwa miƙewa tayi zata fita, Kallon ta Khausar tayi tace.
“Ina kuma zaki je?”.

Juyawa Dije tayi ta fuskance ta tace.
“Zanje in dafa mana ƙwoyin da kika ce kina so ne”.
“A'a kibari ba da fawa zamuyi ba soyawa zamuyi ina akwai attaruhu da albasa da kuma maggi?”.
Kai Dije ta gyaɗa tace.
“Eh akwai”.
“Ok to kibari sai munyi Azkhar”.
“Toh”,Dije tace.Sannan ta dawo ta zauna suka cigaba da yin Azkhar ɗin Khausar nayi da ƙarfi Dije na binta wani ta iya wani kuma bata iya ba sai Khausar ta tsaya ta gyara mata suna zaune har akira Isha'i suka Idar...

GEMBILA
Anutse Momy ta gama shirin baccinta bayan tayi addu'a sai kuma ta lumshe Idanunta ahankali ta sake buɗesu ta juya kwanciyar ta daga hagu zuwa dama sai kuma ta tashi ta zauna baki ɗaya kewan Khausar ɗin ta ke damunta acikin yini ɗaya da bata kusa da ita se taji kamar wata tayi ba tare da ita ba gashi basu da network bare ta kira taji muryanta.
Jin ƙaran Knowking ɗin ƙofa yasa Momy gyara zamanta kana ta bada izinin shiga,Anutse Haiydar ya shigo bakinsa ɗauke da Sallama kana ya zauna kusa da Momy.
Murmushi Mommy tayi tace.
“Haiydar lafiya ko kana bukatar wani abu?”.
Kai ya girgiza yace.
“Momy wallahi yau gidan nan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login