Showing 75001 words to 78000 words out of 176046 words

Chapter 26 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete

za'a bin ciki mutum dashi aranan gobe hisabi idan tayi kyau abin cika sauran abubuwa idan kuma ba tayi kyauba, baza ma aje ga sauran abubuwan ba”.
Tayi ƙasa da Idanunta ganin shegen kallonda Umman take bin ta dashi bata damu ba ta cigaba da cewa.
“Ummah aduniya Allah ya Umarceki da kiyi sallah da Azumi amma Boka La'anannen yace kada kiyi, sannan ki biye masa har ki yarda sannan ki riƙa ɗaura ‘yarki akan gurɓatacciyar hanya nikam wannan al'amari yana tayar min da hankali, wannan al'amarin sam bai yi ba yanzu dama akan wannan turban kuke tafiya?”.
Ta saki Ajiyar zuciya tare da gyara zamanta kana tana ƙoƙarin maida hawayen dake ƙoƙarin zubo mata cikin dauriya ta cigaba da cewa.
“Shiyasa tun da na dawo sati biyu banga kinyi alwala ko Sallah ba?, Ni nayi zaton ma al'ada kike yi,Itama Amina naga bata sallah dana tambayeta saita kama yimin rashin kunya”.

Amina dake jifanta da mugun hararane tayi saurin katseta tare da cewa.
“Anyi miki rashin kunyar keda ba kyabin Ƙa'ida da Umarnin Bokan baga ki har yanzu baki auru ba!sai shegen iyayi da kwainane!”.

Asiya da Idanunta suka ciko da ruwan hawaye ta kalli ƙanwar nata cike da mamaki sai kuma tayi murmushi mai ciwo tace.
“Wannan Allah ne bai nufaba, idan Allah ya saƙƙo da lokaci zanyi shi domin Aure da mutuwa lokacine”.
Atsawace Hajiya Bunayya tace.
“Rufe min baki, keda ma can ba'a haɗa shiri dake ya tafi dai-dai, dama ke da magautana kike tare kina nan kamar wancan matar ce ta haifeki”.

Asiya ta danne kukan dake neman kufce mata tace.
“Ba haka bane Ummah zanso mu gudu tare mu tsira tare ne, bazan so ganin ku cikin halaka ba Umma kuyi tunani akan wannan rayuwar da kuka jefa kanku".

Hajiya Lami kuwa cikin fushi tace.
“Wannan dai akwai gantalelliyar yarinya shegiya mai shegen mugun halin jaraba, duk yanda akayi wancan gafalalliyar kishiyar Uwar taki ta baki nononta kinsha”.
Kallonsu kawai Asiya keyi cike da mamaki.

Hajiya Bunayya kuwa Afusace tace.
“Bana son gaskiyar taki ki riƙe abarki.
ki gudu ke kaɗai mu ma mu gudu mu kaɗai kiga wanda zai riga isa tsakanin mu da ke”.
Cikin tsananin tashin hankali Asiya tace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n.
Allahumma Ajirni fi musibati wa'ahlif khairan minha”.
Ta ida addu'ar tare da miƙewa ta shiga Bedroom ɗin su akan gado ta faɗa tare da dafe kanta tace wannan wani irin Masifa ce Ummah ta jefa kanta.

Acan falo kuwa Ummah suka cigaba da tattaunawa tare da tsaida matsaya akan idan sun kammala aiki zasu biya Sallolin da ake binsu.

Washe gari.
Da hantsi misalin 12:00 Khausar na kwance A Bedroom kamar daga sama tajiyo Sallamar Hajja Nana da sauri ta miƙe tare da zama Atsakiyar gadon ta kasa kunnenta dan tabbatar wa shin ita ɗin ce ko kuwa.
Aikuwa Muryan Mommyn ta taji tana cewa.
“A'a Hajjar Allah Maraba sannu da zuwa Allah raine Jaɓɓama,Jaɓɓama Yottu,yottu”.
Ita kuwa Khausar wani irin zare ido tayi sai kuma ta miƙe da sauri ta fito abakin Bedroom din ta tsaya Idanunta akan Hajja Nana da Dije dake tsaye agefenta.

Jan zuciya Khausar tayi tare da tsaida idanunta akan Hajja Nana tace.
“Kece?”.
Harara Hajja Nana ta watsa mata da faɗin.
“Toh ki koreni wato ba kyason ganina!?”.
Tura baki Khausar tayi tace.
“A'a".
Sai kuma ta juya tare da kallon Dije dake tsaye tana kallon falon da dugu ta nufi Dije tana cewa.
“Oyoyoo Dije nayi kewarki ya gida ya Goggo Nanne?,Ya Yaya Abba?,Ina Sadik?, Yasu Baffa Jauro?, Baffa Sadu?,Baffa Liman?, Baffa Garga? Ina Bishiyar Ƙare zencen ka ina Rafi?”.

Murmushi Dije tayi kana tace.
“Duk suna lafiya kuma sunce agaisheki da kyau da kyau”.
Tayi murmushi tace.
“Allah sarki nima nayi kewarsu sosai”.

Cikin sakin fuska Mommy ta fito daga kichen hannunta riƙe da Flaks da kuma kofi biyu ajiyew tayi, kana ta koma ta ɗauko fruits duk ta ajiye agaban Hajja Nana data hakimce akan kujera sannan ta zauna still fuskarta da Murmushin daya kasa ɓoyuwa tace.
“Sannu Hajja kunsha hanya ya mutanen gida?”
Ta ida maganar tana tsiyaya mata Tea a kofi.
Amsa Hajja Nana tayi ta kai bakinta.
Mommy kuwa miƙewa tayi ta shiga kichen dan haɗa mata abinci.

Hajja Nana kuwa juyawa tayi tare da kallon Khausar dake maƙale da Dije kana tace.
“Wato ba zaki gaisheni ba, Dije ce kikayi farin cikin ganinta ni bakiyi farin ciki da ganina bako!?”.

Ya mutse fuska Khausar tayi tace.
“Tun ɗazu nake ta gaisheki kina fama da ciye-ciye baki jini ba”.
Sake baki Hajja Nana tayi tare da riƙe haɓa sai kuma tace.
“Ubanki nake baciye-ciye ba”
Hannu Khausar ta buɗe da faɗin.
“Ɗanki kika zaga dama kin barsa ya kwanta cikin kabarinsa acikin salama da yafi”.
Ta ida mgnar idonta na ciko da hawaye dan Allah ya sani bata son a zagar mata mahaifi.
Hajja Nana ta ajiye Kofin shayin dake hannunta ta nuna Khausar da hannu tace.
“Ki kiyaye nifa,Ki kiyayeni fa Khausar”.
Tura baki Khausar tayi kana tace.
“To ai gaskiya na faɗa”.

Ita kuwa Hajja Nana na ɗaukar kofin shayinta tace.
“To ya miki kyau koma mene ki ƙarata can, yanzu kishirya ki haɗa kayanki tare zamu tafi zamu je muyi azumi acan”.
Kallonta Khausar tayi kana tace.
“Mu tafi ina?”.
Hajja Nana tace.
“Eh mana Khausar mu tafi Jauro Yaya”.

Da sauri Khausar ta maida kallonta gareta kana tace.
“To ai muna zuwa hadda”.
Hajja Nana tace.
“To ai wannan ba abin damuwa bane idan muka je sai Malam Liman ya riƙa ƙara miki”.

Kai Khausar ta girgiza kana tace.
“Baza ki gane bane, inada abubuwan da zanyiwa Mamana ɗin nan da kike gani ina taya ta aiki”.

Hararanta Hajja Nana tayi da faɗin.
“Dama kece mai taya ta aikin ina masu taya ta aikin?”.
Zare ido Khausar tayi kana tace.
“Tayi cikin shege ankoreta ta koma ƙauyensu.
Mai gadin muma ana canza shi saboda shi ya mata ciki”.
Da mamaki Hajja Nana tace.
“Ash'sha Subhanallahi ashe gidan naku babu tsaro kenan, ashe ku gidan bayan maita hadda rashin tsaro a'a maza-maza shirya mu tafi”.
Dai-dai lokacin da Mommy ta fito girgiza kai tayi tace.
“Kai Khausar bakyajin magana maza ki ɗauka wa Dije abinci ku wuce ɗakin ki”.

Kai Khausar ta gyaɗa tare da wucewa kichen ta daukawa Dije abincin sannan suka wuce Bedroom ɗin.
Mommy kuwa zama tayi agefen Hajja Nana tare da ajiye mata tiren abinci cikin sanyin murya tace.
“Hajja Nana kiyi haƙuri da halin Khausar zaku tafi idan hakan kike so”.
Kai Hajja Nana ta gyaɗa kana tace.
“Toh babu damuwa amma tace min baki da lafiya da gaske ne?”.

Kai Mommy ta Jinjina kana tace.
“Eh wallahi kwanakin nan duka ban cika jin daɗi ba bansan meke damuna ba!”.
Jinjina kai Hajja Nana tayi kana tace.
“Subhanallah Allah ya sawwaƙa Allah ya yaye.
Kuma da gaske ne mai aikin ku ta haihu cikin shege?".

Dai-dai lokacin Hajiya Bunayya da Amina suka shigo falon.
Ɗaga kai Mommy tayi tare da kallon Hajiya Bunayya data zauna tace.
“Hajiya ga Kakar Khausar”.
Murmushi Hajiya Bunayya tayi Idanunta akan Khausar tace.
“Ai na ganeta Hajja Nana sannu da zuwa ina yini ya gajiya kunzo lafiya?”.

Ita kuwa Amina batare data ƙarasa shiga falon ba ta ɗaga sautin Muryanta da faɗin.
“Khausar!, Khausar!! Khausar!!!,”.
Daga ciki Khausar tace.
“Me?".
Afusace Amina tace.
“Bana son rashin kunya ni zaki yiwa rashin kunya? ina kiranki kina jina ba zaki fito ba aikin san dai tunda na kira ki ina da ɓuƙatar ki!”.
Jin surutan da take yasa Khausar ta fito tare da tsayawa daga bakin ƙofa ta riƙe ƙugunta kana tace.
“To ai tunda ke kike da ɓuƙatata kinsan inda dakina yake sai ki shiga ki sameni”.

Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi dariya tana kallon Khausar tace.
“Kudai in Kun hadu bakwa rabuwa da faɗa kamar wasu ƙananun yara Allah dai ya kawo muku sauƙi kuna na kamar wuta da Auduga”.
Juyawa Hajja Nana tayi ta kalli Khausar da Amina kana ta taɓe baki tare da cewa.
“To ai kinsan haka al'amarin yake, mu zuriyarmu bama gani mu ƙyale sannan bama ji muyi shiru, sannan su kuma mayu haka suke basason mai baki shiyasa baza'ayi shiri ba”.
Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.
“Hmmm Hajiya ai tsatsonne na mayu su basu tsotsaba dan mu atsarkake muke”.
Kallon mamaki Mommy tayi mata kana tace.
“Hajiya har ke kin yarda da kalmar kenan?”.
Hajiya Bunayya ta taɓe baki kana tace.
“Ha'a abinda ake faɗa musu acikin gari mun isa mu hana ne?”.
Atake fara'ar dake fuskar Mommy ya gushe cikin rashin jin daɗin abinda Hajiya Bunayya ta faɗa tace.
“Wallahi sukam ba Mayu bane har dake ki yarda kefa komin yaya, ita Uwa ce agareki kuma kakar ’ya'yanki kuma Inde har za'ace suna ciki to mijinki ma yana ciki”.

Hajiya Bunayya kuwa cikin sauri tace.
“A'a mijina atsarkake yake.
Uwarsa kuwa ba zan musan ta mata ba yawwa a duniya idan kaji an cewa mutum maye ba zaka musanta masa ba kawai dai abinda na sani mijina ba yayi nima banayi kuma 'ya'yana na basayi.
Hajja Nana gaskiya kika faɗa taje can ta ƙarata da baƙin halinta inma tanayi can mata inma ba tayi can mata amma abinda gari dai ake faɗa tana yi, kuma mutum bashida hujjar da zaiyi musu akan hakan, gwara ma hujjar da mutum zai ɗabbaga tunda ga alamu ke yanzu ko cikin ki dake yawa zubewa bakya ta Allah ƙashi da ita!?”.

Cikin sauri tare da ɗaure fuska Mommy tace.
“A'a nikam Allah ne ya ƙaddara min zubewar ciki babu wani wanda ya zubar min da ciki”.
Murmushi Hajiya Bunayya tayi aƙasan ranta tace can miki ƙidahuma.

Khausar kuwa kallon mamaki tabi Hajiya Bunayya dashi kana aƙasan ranta tace lalle Hausawa sunyi gaskiya da suka ce iya ruwa fidda kai”.
Amina dake tsaye ta watsa Khausar Harara kana tace.
“Abbah ke kiranki kizo kakar taki tazo da wasu maza suna waje sai kije ku gaisa”.
Ta ida maganar tare da juyawa ta fice.

Ita kuwa khausar cike da farin ciki ta juya ta fice ta nufi coumpund kasa ɓoye fara'ar fuskarta tayi ganin Yaya Aliyu tsaye yaron Baffanta na Adamawa tare da Yaya Abba cikin jin dadi ta ware manyan Idanunta cike da farin ciki tace.
“Yaya Aliyu sannu da zuwa ku ƙara so”.
Ta faɗa tana yin gaba zuwa Falon Lamiɗo dake saukan baki.
Bayan sun shiga falon sun zauna ta dubi Aliyu still Fuskarta da murmushi tace.
“Yaya Aliyu yaushe kazo?".
Gyara zamansa yayi yana fuskantar ta kana fuskarsa ɗauke da murmushi yace.
“Baffanki ne ya tasoni wai sai na kawowa tsohuwar sa kayan azumi shine kuma yanzu Hajja Nana tace sai munzo”.
Khausar kuwa murmushi tayi kana tace.
“Hajja Nana rigima"
Sai kuma ta maida kallonta kan Yaya Abba dake latsa waya tace.
“Yaya Abba ya karatu?”.
Ahankali ya ɗago kansa da murmushi afuskarsa yace.
“Karatu ya ƙare yanzu wannan karon tare zamu tafi da Aliyu can Adamawa idan Allah ya nufa idan munje zan samu aiki Insha Allah tunda kinga Baffan Jimeta yana da hanya da manyan mutane Insha Allah za'a samu”.

aSaki murmushi tayi kana tace.
“Masha Allah abu yayi kyau”.
Lamiɗo ya shigo suka gaisa bayan sun gama gaisawa ya fita, Khausar kuwa Anutse ta miƙe tace.
“Ina zuwa”.
sannan ta fice.
Kai tsaye kichen ɗin su ta nufa ta ɗauko Babban Warmers da faranti ta fita.
Hajja Nana ta bita da kallo baki sake ganin Uban kula me kyau da tsari da tafita dashi.
Ba daɗewa Khausar ta dawo ta sake ɗaukan Flaks da kofuna.

Har takai ƙofa Hajja Nana data kasa haƙuri tace.
“Kede akwai Jaira mara kirki tunda nazo kike wani shan ƙamshi kamar baki so zuwa na ba, ko arzikin gaisuwa ban samu ba bare insa rai da ruwan sha, amma wa'annan saboda 'yan uwanki ne jiki na rawa kin wani kinkimi Uban kula kin fita yanzu kin dawo kin ɗauki Flaks”.
Kallonta Khausar tayi tare da taɓe baki tace.
“Kinga sai anjima Ni sauri nake”.
Tana gama fadar haka ta fice bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon.
Amsawa sukayi tare da kallonta.
Zama tayi tare da buɗe Warmers din ta ɗauki babban Plate ta zuba musu shin kafa da miyar da yaji naman kaza sai kuma haɗin coslow kana ta zuba musu shayi dake tururi.
Yaya Abba yayi Murmushi yace.
“Da'alama wannan girkin kine saboda wannan ƙamshi”.
Murmushi tayi amma batace Komai ba.

Acan ɗaki kuwa bayan ankira sallan Azahar Mommy takai Hajja Nana har toilet ɗin ta tayi alwala kana ta fito ta gabatar da Sallah bayan ta idar tayi adduo'i.
Ta juya ta kalli Mommy dake riƙe da carbi ahannunta tace.
“Aisha”.
Cike da girmamawa Mommy tayi ƙasa da kanta kana tace.
“Na'am”
Hajja Nana kuwa gyara zamanta tayi tare da tattara duk kan nutsuwarta zuwa kan Mommy tare da cewa.
“Magana ce mai muhimmanci ta kawoni”.
Cikin girmamawa Mommy da kanta ke ƙasa tace.
“Toh ina sauraronki Hajja Nana”.

Hajja Nana kuwa Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Magana ce akan Khausar da kuma ɗan Baffanta wato Aliyu”.

Jinjina kai Mommy tayi cike da ladabi tace.
“Toh Hajja Nana ina jinki”.
Hajja Nana ta gyara zamanta tare da cewa.
“Toh zuwa yanzu dai inaga Khausar ta girma, sannan inaga ta gama karatun ta yanzu idan ma bata gama ba to ta kusa”.
Jinjina kai Mommy tayi kana tace.
“Eh ta kusa Insha Allah yanzu kam Shekara ɗaya yarage bayan sallah Insha Allah zata tafi ajin ƙarshe na gama makarantar gaba da primary”.

Cikin jinjina kai Hajja Nana tace.
“Masha Allah Ubangiji ya taimaka”.
Mommy ta amsa da.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Hajja Nana kuwa duk kan nutsuwarta ta tattara tare da cewa.
“To ai yanzu dai ta samu ta kori jahilci ta yaƙesa, yanzu batun aurenta za'ayi.
Ga kuma Yayanta kuma ɗan Uwanta za'a aura Matashi magana ya ƙare sannan kuma idan karatun take so ta cigaba idan sunyi aure zata yi acan jahar Adamawa tunda suna da makarantu manya-manya acan dan haka yanzu batun aure ne ya kawo mu nazo dashi za'a haɗa bayan sallah in Allah ya yarda”.
Akuma dai-dai lokacin Khausar ta shigo ɗakin, cike ka ɗuwa Idanunta na kan Hajja Nana cikin sauri tace.
“Wai me naji kina cewa?”.
Cikin isa, gadara, Hajja Nana ta wurga mata Harara kana tace.
“Batun Aurenki nakeyi”.
Arazane Khausar ta zare ido kana tace.
“Wa.....!




*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA

By
*GARKUWAR MARUBUTA*







📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

*SAKAYYAH*
_Page 13_

_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama, ba haƙƙin kowa akanki. Littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin littafin inda zan rinƙa posting.


*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*

_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login