Showing 15001 words to 18000 words out of 176046 words
su dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk jihar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida. Set ɗina akwai manya akwai ƙananan set akwai kuma na tsakiya, ƙananan set ɗin daga 40k 35k 30k 25k 20k 15k 10k shine ƙara ɗan cukulan haɗiba bana haɗin kasa da 10k sai kuma haɗin kwanon ƙasaitacciyar mace shi 8k set ɗin tsakiyan su da 50k 60k 70k 80k 90k ne manyan kuma daga 100k ne zuwa yadda zaki iya Hajia ta*
GARKUWAR MA'AURATA
Cikin sanyin jiki Khausar ta miƙe tsaye tare da juyawa a hankali ta bar falon Mommy ta wuce ɗakinsu.
Ɗakin mai girmane wanda ke ɗauke da matsakaici gado ƙiran Italian bed sai durowarsa dake gefe wanda ke ɗauke da ƙofa shida, daga kusurwan gabas babban TV plasma ne da DStv sai tattausan canis carpet pinch color dake shimfiɗe Atsakiyar ɗakin wanda shi ke ɗan rage musu masifeffen sayin tayis ɗin,
komai na ɗakin pinch colour ne sai ɗan ratsin fari.
Cikin jagulewar zuciya ta kwanta bisa gadon tare da lumshe manyan Idanunta dake cike da ruwan hawaye.
Allah ya sani sam bata ƙaunar zuwa Jauro Yaya ko kaɗan, ya zame mata dole ta newa kanta mafita.
Ɗan gajeren tsaki taja tare da mirginawa ta juya tsakiyar gadon, kana ta lumshe idanunta, da wannan tunani bacci ya ɗauke ta...
Cikin nutsuwarsa da kuma sanyinsa kamar koda yaushe yake tuƙa motar, yayin da M Jameel ke gefen hagunsa kamar wanda akace ya dubi madubin dake gefensa se kuma yayi saurin kallon Moddibo dake Driving cike da mamaki yace.
“Kai A.J kaga kamar binmu akeyi fa ko?”.
Kai Moddibo ya jinjina tare da ɗan yamutsa fuska anitse yace.
“Eh binmu akeyi sai munje gidan Ummi zan tsaya”.
Cikin sauri M Jameel ya juyo gareshi tare da ɗan ware idonsa yace.
“Kama san ana binmu kuma shine ka ƙi tsayawa? Idan kuma wanda zasu cutar da mune fa A.J?”.
Kai Moddibo ya girgiza yana mai cigaba da tuƙinsa tare da buɗe lips inshi a sanyaye yace.
“Ai nasan wanda ke binmu fa Alhaji Bashir ne”.
Da sauri M Jameel yace. “Waye Alh Bashir?”.
Ɗan juyow Moddibo yayi tare da ɗan kallonshi kafin yace.
“Babban yaron Malam Arɗo ne”.
Cikin sauƙe Numfashi M Jameel yace.
“Ok to Meyesa ba zaka tsaya ba?”.
Ba tare da ya juyo ba yace.
“Nasan magana ce mai yawa yazo dashi, koda na tsaya ma, ba zamu gama ba kuma kaga agefen titi muke baya ga hakama na masa signal ya fahimta”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da faɗin.
“Ok shikenan”.
Daga nan sukaci gaba da tafi.
Suna isa ƙofar gidan Ummi M Jameel ya buɗe ƙofa ya fita dai-dai lokacin da Alh Bashir ya ƙara so fuskarsa ɗauke da murmushi ya miƙa wa Alh Bashir hannu sukayi musabaha cikin sakin fuska Alh Bashir yace.
“M Jameel Ko?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa mishi tare da cewa.
“Ya gida ya iyalai ya kuma Baba Arɗo?”.
Cikkn sakin fuska Alhj Bashi yace.
“Duk Suna lafiya”.
Murfin motar M Jameel ya buɗewa Alh Bashir tare da cewa.
“Bismillah kashiga”,
Sannan ya zagaya gefen da moddibo yake wanda har zuwa lokacin bai fito ba yace.
"Bari nashiga ciki sai ka shigo”.
Kai Moddibo ya gyaɗa cikin yanayin sanyin magarsa yace.
“Nima Ina Shigowa yanzu”.
“To sai ka shigo”.
Ya fadi tare da juyawa ya nufi cikin gida yashiga bakinsa ɗauke da sallama.
Ba lefi madedecin gida ne mai kyau daga farkon gidan ze iya ɗaukan motoci biyu se tank na ruwa dake can gefe tsakar gidan shimfiɗe yake da interlock sai babban sashe guda ɗaya cikin gidan zagaye yake da fulawa wi masu kyau wanda keda alaƙa da Moddibo dan duk inda yake da dama sai ya ƙawatasa da fulawowi, sabida suna samishi farin ciki.
Tsarin ginin yayi matuƙar kyau duk da cewa ba babba bane amma komai fess dashi haka zalika madedecin falon nasu da befiye girma ba yayi matuƙar kyau falon na ɗauke da manyan setin kujeru kalar ash da baƙi cai Centre table dake tsakiya da kuma ƙaton TV dake maƙale abango daga gabar da TV akwai ƙaton fanka bayan AC dake maƙale da bango daga yamma da TV zagaye yake da wasu flowes masu kyau da ɗaukar hankali sai tattausan carpet mai ɗan kare kyau dake malale a tsakiyar falon...
Cike da so kulawa ƙauna irin ta uwa Ummi ta kalli Jameel dake shigowa tare da sakar masa da murmushin da bata san ya subce mata ba,
bayan ta amsa sallama.
Cike da farin ciki Asma'u ta miƙe tare da gyara wuyan abaya ɗan baby himar dake zage da fuskarta da ɗauke da murmushi cike da jin daɗi ta rungume M Jameel da faɗin.
“Oyoyo Yaya Jameel na Ina yini”.
Kanta ya shafa cike da son yar uwar tasa yace.
“Lafiya lau my blood ya karatu?”.
Cikin murmushin ta amsa da.
“Alhamdulillah”.
kana ta zauna daga ƙasa kusa da ƙafafunsa,
Ummu kuwa miƙewa tayi tana ɗan leƙan bayansa.
Murmushi M Jameel yayi domin ya fahimci Moddibo take leƙawa ganin basu shigo tare ba.
Cikin yanayin fara'arsa yace.
“Kai Ummina ki bari mugaisa kafin ki tambayi 'yan biyun nawa??”.
Ka ta girgiza tare da cewa.
“A'a gwara in tambaya naji, domin shi yace na muku dambun couscous shiya keso kaga kuwa ai bazan ji daɗi ba in ban ganshi ba”.
Murmushi M Jameel yayi yana mai jin daɗin yadda mahaifiyarsa ke nunawa amininsa ƙauna tamkar ita ta haifeshi, yana murmushi jin dadi yace.
“To yana mota”.
Da sauri ta sake dubansa tare da cewa.
“To me yakeyi amota da bai shigo ba?”.
Ashagwaɓe yace.
“To Ummina mu gaisa mana”.
Dawowa tayi ta zauna bisa kujera 2 str,
shi kuwa M Jameel zamewa ƙasa yayi zauna daɓas bisa carpet kana ya ɗaura kansa acinyarta murya a sanyaye yace.
“Ummina daga shigowa ko gaisawa ba muyiba sannan baki samin albarka ba kika tsareni da tambayar Moddibo”.
Hannunta ta ɗauka bisa tsakiyar kasan tare da shafa kansa tana mai cewa.
“Ubangiji Allah ya Albarkanci rayuwarku! Allah ya dafa muku acikin dukkan lamuranku!!
Ubangiji ya tsareku daga sharrin abinƙi tsakanin mutum da aljan!!!
Allah ya baku 'ya'ya masu biyayya tamkar yadda kuke mana kaida Amininka”.
Cike da tsananin jin dadi da sassayan salama yace.
“Ameen thumma Ameen Yah Ummi”.
Hannunta ta ɗan janye daga kansa tare da sake tambayar sa.
“Ina Moddibo?”.
Ƴar dariya mai sauti yayi tare da miƙewa ya zauna akusa da ita kasancewa kujeran 2sitter ne.
gyara zamansa yayi yana fuskantar ta yace.
“Moddibo zai shigo amma ba yanzu ba”.
Da sauri tace.
“Meyasa?”.
Cikin saurin shima yace.
“Bari dai in miki bayani hankalinki ya kwanta.
Muna tahowa ne Alh Bashir babban yaron Malam Arɗo ya biyo mu to suna mota suna tattaunawa.
Nasan bazai wuce ƙorafi ya kawo akan mahaifinsu ba”.
Tsaresa da ido Ummi tayi kana tace.
“ƙorafi akan Babansu kuma?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Eh Ummi saboda Malam Arɗo wani irin mutum ne wanda zamuce mai dukiyar lukudi gashi dai Allah ya bashi dukiya na ban mamaki amma babu wanda ya isa yaci wannan kuɗin kamar abin masifa”.
Gyara zama Ummin tayi tare da cewa.
“Ikon Allah to sabi da me?”.
Numfashin M Jameel ya ɗan fesar tare da cewa.
“Tun bayan rasuwar mahaifinsa abubuwan suka ƙazanta.
Domin baya sauraron shawarar kowa koda kuwa ƙannensa ne domin shine babba acikinsu dan haka babu mai tanƙwarashi.
To fa saidai Allah ya ɗaura masa son Moddibo a zuciyarsa duk abinda Moddibo yace ko kuma ya kawo shawara akai to zaiyi koda kuwa ransa baya so.
Duk da wani lokaci zakiji yana yiwa Moddibon ma faɗa akan cewa zaisa shi kashe kuɗi amma koda ya gama surutun daga baya zakiga yayi abin da ya fadan.”
Gyara zama M Jameel yayu tare daci gaba da cewa.
“To fa wannan dalilin ne yasa muddin 'ya'yansa suna buƙatar wani abu saidai su biyo ta hannunsa Moddibo”.
Ka saƙe Ummi tayi tana kallon Jameel din kana cikin sanyin murya tace.
“To kada fa hakan yasa yayi baƙin jini awajen 'ya'yansa kasan ɗan adam”.
Dariya M Jameel yayi kana yace.
“Ummi me Moddibo zai buƙata awajen Malam Arɗo me zeyi da dukiyarsu? Mutumin da baiwa yayansa Bama me zai bawa Moddibo wanda baida shi".
Kai Ummi ta gyaɗa tare fesar da numfashi a sanyaye tace.
“Hakane kam al'amarin Moddibo da Innayi akwai al'ajabi, domin ko nasan baza su taɓa buƙatar wani abu awajensa ba, duk da kuwa anayi musu kallon basu da wani cikekken jigo acikin rayuwarsu.
Amma kuma yanda suke tafiyar da rayuwarsu cikin tsari da hikima da wadata yana bani makaki”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cewa.
“Kinga Koda motar da Malam Arɗo ke hawa tsohuwa ce aƙalla zata kai shekaru ashirin da biyar ko ashirin da takwas amma har zuwa yau ya kasa can zawa, anyi-anyi dashi yaƙi duk yanda akayi dashi ya sauya wata yaƙi kuma kullum ciki bashi ciwon kai takeyi.
har kyautar Mota ɗansa Alh Bashir ya bashi amma yaƙi amsa domin atunaninsa daga baya zai fanshe kuɗin sa.
Ko gidansa da kike gani yanzu ga gini dai yayi mai kyau amma ɗakunan matansa kamar zauren haka suke babu kujeru bare wani abu shi Tv.
Yanzu haka kwanan ake gyaran makarantarsa wanda da taimakon Moddibo akeyinsa kuma adalilinsa ne yake biyan Malamai albashi mai tsoka inba haka ba baki ɗaya makarantar ta koɗe sannan babu albashin kirki saboda Moddibo yanzu aka rushe makarantar ake gyarawa yanzu hutun da aka kara ma gani yake kamar za'a yi masa asara shiryasa yace adawo ko ba'a gama gininba to bayan an dawo yanzu dole aka sake komawa hutu saboda ba'a gama gyaranba yanzu ma cewa yayi dole kada a wuce wata ɗaya da ƙyar Moddibo ya lallaɓasa aka tafi hutun kafin adawo angama gini da kuma tsare tsare sa duk ya buwaye mu da cewa Moddibo na sashi kashe kudinsa”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Masha Allah shiko wannan wani irin mutum ne?”.
Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.
“Ummi haka 'ya'yansa ke fama dashi, kin san ku fulani”.
Murmushi Ummi tayi tare dayi masa daƙuwa.
Aɓangaren Moddibo kuwa.
Zaune suke da Alh Bashir bayan sun gama gaisawa shiru na wasu daƙiƙu ya wanzu atsakaninsu kafin.
Cikin kulawa Moddibo ya ɗan juyo ya kalli Alh Bashir cikin kulawa yace.
“Alh ya akayi?”.
Numfashin mai nauyi Alh Bashir ya sauƙe kana a hankali yace.
“Mitsss Moddibo Agaskiya al'amarin Babanmu yana matuƙar ɗaure mana kai?”.
Lumshe idanunsa yayi kafin yace.
“Meya faru!?”.
Kai ya girgiza cikin yanayin damuwa yace.
“Modobbo wallahi Mahaifiyata bata da lafiya, ance sai anfitar da ita waje, gashi duk cikin mu babu wanda yake da halin biya afita da itan.
Kasan halin Babanmu kuma, duk iyakar iyawata yaƙi amincewa.
Ni kuma bani dashi”.
Cikin sanyi Moddibo yace.
“Alh baka dashi kuma”.
Kwaffa Alh Bashir yayi tare da cewa.
“Wallahi Allah Moddibo wasu lokuta idan akace min Alh Bashir ba ƙaramin ɓaci raina yake ba domin bafa mahaifina ne yabiya min Makka ba.
Sannan ba nine na biyawa kaina ba dukiyata bace yasa naje ba.
Dalilin Surukina naje wato mahaifin Matata fa ya biya min na samu naje duk wani abu da nake buƙata sai dai Inje wajensa wanda kuma hakan da kunya da kuma zubar da girma.
amma mahaifina Allah ya hore masa fiye dana surkina amman bazai taimaka manaba ayanzu ga jinyar mahaifiyarmu dole sai anfitar da ita waje an mata dashen ƙoda.
shi kansa yana ɓuƙatar canjin mota lokuta da dama yana tafiya Atsakiyar titi zakaga ta lalace, idan shi baya damuwa da zaginsa da akeyi a gari da rayuwarsa to mu muna buƙatarsa ba mason wani abu ya sameshi kuma bama jin dadin habaice-habaicen da akeyi mana.
Shiyasa nazo wajen ka.
Dan Allah da Manzonsa kayi masa magana ya kai mahaifiyarmu asibiti. Sannan ya canza motarsa bayan wannan akwai kannen mu mata da suka gama secondary akwai buƙatar su tafi jami'a amma yaƙi sasu domin aganinsa za'a cajesa kuɗi masu yawo dan Allah katemaka kayi masa magana akan waɗan nan abuvuwan”.
Ya dire ayar mgnar da haɗe tafin hannunsa alamun roƙo da neman al'farma.
Moddibo kuwa ajiyar zuciya ya sauƙe tare da buɗe idanunsa dake lumshe kana a hankali yace.
"Insha Allah zanyi masa magana, amma ayanzu da ƙyar zai amince domin da mun zauna zance ɗaya yake nanata min wai na sashi kashe kuɗi amakaranta wai zan talautashi”.
Murmushi mai ciwo Alh Bashir yayi tare da cewa.
“Muma ko agida haka muke shan complain Koda kudin cefene da sauran abubuwa aka tambayesa zaice Ni bani da kudi wannan yaron Moddibo duk yasa na kashe kuɗaɗenna aginin makaranta”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara fitar da ainihin kyawunsa cikin sanyi yace.
“Uhufm Malam Arɗo kenan.
Ba matsala Insha Allah zanyi magana dashi duk yadda mukayi dashi zakaji”.
Ya kare mgnar yana shafa tattausan sajensa.
Godiya Alh Bashir ya masa sannan su kayi sallama Moddibo yashiga cikin gida.
Shi kuma ya juya ya tafi.
Tattausan murmushi Ummi tayi ganin Moddibo cikin kulawa tace.
“Babana na kaina sannu da zuwa”.
Kasancewar sunan mahaifinta garesa.
Cike da ladabi ya zauna yana cewa.
“Ummi fatan mun same ku lafiya ya yara?”.
Da murmushi afuskarta tace.
“Duk muna lafiya ya jikin Innayi?”.
“Alhamdulillah Ummi jiki kam da sauƙi sosai ma".
Ya kare mgnar yana mayar da kallonsa ga Asma'u data fito daga Bedroom da alama muryarsa taji ta fito, har ƙasa ta tsugunna tare da cewa.
“Yah Moddibo ina yini”.
“Lafiya Asma'u ya karatu da hadda?”.
“Alhamdulillah”.
Kai Ya jinjina tare da faɗin.
“Meyesa yau bakije hadda ba?”.
Kanta aƙasa tace.
“Yah Moddibo bani da lafiya ne zazzaɓi ke damuna”.
Kallonta yayi na daƙiƙu uku, kana yace.
“Asmau kadafa ki biyewa wannan mashiririciyar ƙawar taki, ki dena harƙa da ita sam banason alaƙarta dake tsakaninku.
Domin yarinyar bata ji kona misƙala zarratin, bana son ganinki tare da ita dan gaba ɗaya sunanta ya zagaye makarantar saboda rashinjinta sam bata da nutsuwar da za'ayi abota da ita.”
Ita dai Asma'u kai take jinjina mishi.
M Jameel kuwa ido ya zuba mishi yayinda Ummu kuwa ke murmushi.
Shi kuwa Moddibo gyara zamansa yayi tare daci gaba da cewa.
“Domin shin abota anaso ayi da na gari, bi ma'ana idan za kayi abota kayi da mutum na gari domin kamar dai misalin:
meyin abota da me saida turarene koda ba azata masa ƙamshi ba to baza azata masa wari ba, sannan misalin: mai abota dame zuga-zugi koda yana da haske to ba za'ayi masa zaton haske ba".
Ɗan kishingiɗan M Jameel yayu tare da lumshe idanunsa.
Shi kuwa Moddibo cikin nitsuwa yaci gaba da cewa.
“Manzon Allah (S.A.W) ya kwaɗaitar damu da yin abota da mutanen ƙwarai domin abokin ƙwarai yana daga cikin wanda Allah yayi alƙawarin zai sasu acikin inuwar alarshinsa ranar tashin ƙiyama, amma kuma duk abotar da ba'agina sa saboda Allah da manzo ba to ƙarshensa nadama ce sam wannan FATTANAH bata dace da zama abokiya a garekiba”.
Itade Asma'u kanta na ƙasa batare data ɗago ba tace.
“Toh Yah Moddibo”.
M Jameel dake kishin giɗe idanunsa lumshe kuwa a hankali ya miƙe tare da buɗe idanunsa akan Moddibo dake cigaba da yiwa Asma'u nasiyya akan tarabu da Khausar cikin tsareshi da ido yace.
“Wai dan Allah A.S meye haka? kana tayiwa Asma'u huɗubar watsar da aminiyarta shin ita Khausar ɗin sheɗan ka ɗauketa ko kuwa dujjal?”.
Ɗago kai Moddibo yayi tare da tsuke fuska yana kallon M Jameel yace.
“Kusan haka domin sam yarinyar bata da ɗabi'un kirki”.
Kai M Jameel ya girgizi kana yace.
“Haba Moddibo yarinyar nan tana fahimtar karatu duk wasu abubuwa da ake koyarwa tana ganewa fiye da duk yan ajinka,
kawai rawan kai da ƙuruciya ke damunta, da zaran ta mallaki hankalinta zata dena, amma ka zauna kana ƙoƙarin cusa ƙiyayyarta azuciyar Aminiyarta sam hakan ba dai-dai bane yoh ba ita cema ke taimakawa ƙanwar taka da kake zugawarba ita me take ganewa ma tana nan kai kamar na kifi”.
Itade Asma'u kanta na ƙasa tana wasa da yatsun hannunta.
Wani kallo mai cike da manufofi Moddibo yayiwa M Jameel tare da taɓe baki kana yace.
“Ina ruwanka? bansa bakinka ba da Asma'u ƙanwata nake magana”
Kana ya juyo ya kalli Asma'u da har zuwa lokacin kanta ke sunkuye yace.
“Maganata kika ɗauka zakiyi amfani dashi ko nasa?”.
Da sauri tace.
“Naka Yah Moddibo”.
Murmushi yayi da faɗin.
“Ɗayyit Allah ya miki albarka”.
Ɗago kai M Jameel yayi dai-dai lokacin Asma'u ta ɗago kanta,
ido yakashe mata ita kuma murmushi ta sakar masa.
Ummi dake sauraronsu kuwa sai yanzu tace.
“Yawwa Moddibo ka cigaba da samun Ido akan yaran nan dan yaran saida sa ido”.
Moddibo kuwa ido ya lumshe tare da gyaɗa kai kana yace.
“Insha Allah Ummi na lura J da wannan fitinanniyar yarinyar kusan halinsu ɗaya shima kullum fama nake dashi ya nutsu yaƙi nitsuwa”.
Wara ido M Jameel yayi tare da cewa.
“Nine bani da nutsuwar A.S?”.
duk dariya suka sanya banda Moddibo da yayi murmushi.
Abinci Ummi ta bawa Asma'u umarnin ta kawo musu fita tayi ba daɗewa ta dawo hannunta ɗauke da warmers ta ajiye musu M Jameel ne ya buɗe murmushi Moddibo ya saki yana kallon yanda dambun yayi kyau sai tashin ƙamshi albasa da kuma ƙamshin man shanu.
Ummi da kanta ta zuba musu tare da mimmiƙa musu plate ɗin.
Bismillah sukaui kafin suka fara ci suna