Showing 126001 words to 129000 words out of 176046 words
murya kana yace.
“Ayyah Mommy am gobe abarni kar Inje makaranta mana”.
Kallonsa Mommy tayi tare da cewa.
“Toh Meyesa Ramadan?”.
Kai ya Girgiza kana ya marairaice murya tare da cewa.
“Mommy nidai kawai bana son zuwa Makarantar nan”.
Hankalinta ta mayar kansa kana tace.
“A'a Babana ba yadda za'a yi haka ace baka son zuwa makaranta. Ai yanzu ka fara zuwa ma”.
Araunace ya kalli Mommy tare da cewa.
“Dan Allah Mommy Gobe kawai.
Na goben nan dan Allah Mommy na kada Inje Mommy na goben nan kawai kada abarni Inje makaranta kada inje”.
Girgiza Kai Mommy tayi cike da kulawa tace.
“A'a Ramadan ya za'a yi inbarka ba kaje makaranta ba ai bazai yuwu ba dole ne kaje makaranta kam”.
Jan zuciya yayi tare da dafe kuncinsa kana yace.
“Mommy shikenan kin yarda in tafi?”.
Jinjina masa kai tayi tare da cewa.
“Na yarda mana kaje”.
Miƙewa yayi daga wajenta ya koma kusa da Khausar tare da riƙe Hannunta cikin yanayin roƙo ya langwaɓar da kai tare da marairaice murya yace.
“Addah Khausy ki tayani bawa Mommy haƙuri gobe kada Inje makaranta kice tabarni gobe kar Inje makaranta mu zauna da ita bana son zuwa makarantar nan Addah Khausi bana so ki faɗawa Mommy”.
Khausar kuwa Kallonsa ta riƙa yi har ya kai ƙarshe, ajiyar zuciya ta sauƙe tare da riƙe tafin hannunsa acikin nata kana tace.
“Toh Ramadan tun daga yanzun ka kana primary 3 sannan kace bakason zuwa makaranta Primary mafa yanzu kayi rabin gamawa ai Ramadan ka fara da wuri”.
Araunace Ramadan ya kalleta tare da cewa.
“Yanzu Addah Khausi zaki bari inje”.
Cikin rashin ɗaukar maganarsa da muhimmanci Khausar tace.
“Eh Sosai ma”.
Haiydar dake kwance kan 3sitter ya ɗago kansa tare da kallon Ramadan kana yace.
“Eh dolenka. Dolenka ma kaje”.
Sai kuma ya maida kallonsa kan Mommy dake kallon Ramadan kana yace.
“Allah Mommy Idan aka sakewa Ramadan ma bazai yi karatu ba”.
Tura baki Ramadan yayi tare da sake hannun Khausar ya koma jikin Mommy kana yace.
“Mommy ki faɗa masa ƙoƙarin da nake a hadda ai yasani ko.
Gasa akaje ni nake zuwa mana na ɗaya a sate ɗin mu”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da cewa.
“Na sani Ramadan kana ma da kokari kawai dai da kake cewa kar abari kaje gobe abarka ka hutane bai yi ba. Idan ka tuna ma gobe Laraba ne idan kaje gobe jibi Alhamis zaka huta gata Friday shima zaka huta kaji ko Ramadan”.
Girgiza kai yayi still Idanunsa akan Mommy yace.
“Ayyah Mommy ni Banason zuwa ki barni mana”.
Khausar ne ta kallesa cike da mamaki tace.
“Ohh Ni Khausar yau kam naga ikon Allah da nacin yaro”.
Taɓe baki Haiydar yayi tare da cewa.
“Rabu dashi duk zai gama kuma dole gobe sai yaje makaranta”.
Acan Bedroom ɗin Hajiya Bunayya kuwa kwance take akan makeken gadonta daya ji shimfiɗa na alfarma kana kunnenta maƙale da babbar waya ta gyara kwanciyarta tare da cewa.
“Nama gama ɗaukar wannan matakin in Allah ya yarda in dai wannan anyi angama ya wuce Babban shima Insha Allah za asan abinda za'a yi akai”.
Daga ɗaya ɓangaren Hajiya Lami dariya tayi kana tace.
“Da dai yafimiki in ba Haka ba kina gani ƴaƴan ki zasu zama bayi, dan da zaran sarautar nan ta fita ahannun ku kinyi bankwana da ita ƴaƴan ki kuwa sun zama tamkar ba ƴaƴan Sarauta ba, duk da cewa Masarautar ba wata babba bace ai baka so ya wuce kaba ya fita ahannunka!”.
Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta sauƙe kana tace.
“Hakane”.
Murmushi Hajiya Lami tayi tare da faɗin.
“Kinga ai Gimbiya Fadeela ta cikin Taraba Aminiya tace duk iya ƙoƙari tanayi dan ganin sarauta ya zauna ahanununta ke kanki kinsani ai ina faɗa miki saboda iya na cinka iya samun abin ka”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi kana tace.
“Hakane ai ma duk na gama shi in faɗa miki”.
Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace.
“Ai haka yafi kam kada ki tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa”.
Dariya Hajiya Bunayya ta sheƙe dashi kana tace.
“Kede ki bari zaki sha kallo”.
Hira suka sake taɓawa daga haka Hajiya Bunayya ta katse kiran.
Washe gari.
Da safe baki ɗaya yaran aka shirya su cikin Uniform Bayan Khausar ta gama shirya Ramadan cikin Uniform ɗin sa tamiƙe ta shiga kichen dan ɗauko masa Lunch box ɗin sa.
Ramadan kuwa yana ganin fitan cikin sanɗa ya fice daga sashen nasu zuwa sashen Hajiya Bunayya ya ɓoye.
Khausar kuwa kai tsaye Bedroom ɗin su ta nufa bakinta ɗauke da Sallama Cak ta tsaya ganin Ramadan bai ciki ƙara sawa ciki tayi tare da kiran sunan sa amma shiru toilet da Wadrope ta buɗe still baya ciki.
Cikin sauri ta fito tare da nufar Bedroom ɗin Mommy kana ta kalli Mommy dake zaune gefen gado tace.
“Mommy na gama shirya Ramadan da Raudat kuma ga Raudat amma banga Ramadan ba har munje wajen mota bamu gansa ba”.
Miƙewa Mommy tayi tare da cewa.
“Ikon Allah to ina kuma yashiga?”.
Buɗa hannu Khausar tayi da faɗin.
“Allahu A'alam”.
Falon suka fito tare da duba ko ina amma baya nan.
Kallon Khausar dake leƙa bayan Kushin Mommy tayi kana tace.
“Khausar jeki duba ɗakin Haiydar ko yaje ya ɓuya acan yau, Bansan meke damun Yaron nan ba tun jiya baya so ayi masa batun zuwa makaranta abinda bai taɓa yi ba”.
Taɓe baki Khausar tayi kana tace.
“Iyayi mana Mommy daga anyi masa wasa shikenan ya ɗauka”.
Ta ida maganar tare da fita zuwa ɗakin Haiydar.
Abakin ƙofan ta tsaya tare da ɗan ɗaga sautin Muryanta kana tace.
“Ramadan kafito fa?”.
Shiru ba amsa jin haka yasa ta buɗe ƙofar ɗakin tashiga shiru ba kowa da mamaki take kallon ko ina dake kimtse tsaf har toilet ta ɓude still baya ciki siririn tsaki taja tare da ficewa ta koma sashen Mommy.
Ƙugunta ta riƙe da hannu ɗaya kana ta kalli Mommy dake tsaye tace.
“Mommy ban gansa ba fa”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da faɗin.
“Toh kije ki duba sashen Ummanku ko yaje ya ɓuya acan kinsan itama zata iya ɓoyesa”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana ta juya ta fice.
Bakinta ɗauke da Sallama tashiga falon zune ta samu Hajiya Bunayya akan 1sittee.
Kallon ta Khausar tayi tare da cewa.
“Ummah Ramadan yazo nan?”.
Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da gyaɗa kai kana tace.
“Eh gashi nan yazo ya ɓuya wai yau baya son zuwa makaranta”.
Ƙwaffa Khausar tayi kana tace.
“Aikuwa dole sai yaje”. ta faɗa tare da wuce Bedroom Kana tace.
“Wallahi Ramadan kafita idona”.
Jin muryan Khausar yasa Ramadan miƙewa tare da hawa can karshen gadon Hajiya Bunayya kana ya ɗaga sautin muryansa tare da cewa.
“Dan Allah Ummah ki hanasu kice yau dai kawai subarni kada Inje makaranta”.
Murmushi Hajiya Bunayya tayi tare da haɗa hannunta biyu waje ɗaya kana tace.
“Dole sai kaje maza ka fito ka tafi nikam kasan bazan hanaka zuwa makaranta ba, Ramadan dole zaka je”.
Dai-dai lokacin Sulaiman ya fito tare da faɗin..
“Ikon Allah yau Ramadan da kanka kake cewa baka son zuwa makaranta duk ƙoƙarin kan nan?”.
Shi dai bai ce komai ba Khausar na ƙoƙarin za gayawa gefen gadon ta riƙo sa yayi saurin ɗirƙa ta ɗaya side ɗin gadon ya fice waje da gudu.
Dafe kai Khausar tayi tare da bin bayansa yana cewa.
Ramadan kazo mu tafi Sulaiman duk sun shiga mota saura kai ka ɗai ake jira”.
Shi kuwa Ramadan sashen Mommy ya nufa da gudu yana shiga ya ɓuya abayan Mommy.
Muryarsa na rawa tamkar wanda ke shirin fashewa da kuka yace.
“Mommy dan Allah kar inje”.
Hararansa Mommy tayi kana tace.
“Sai kaje Meyesa ba kason zuwa Ramadan ka faɗa min dalili”.
Rau-rau da idanunsa yayi kana yace.
“Ni dai bana so bazan jeba Mommy”.
Dai dai nan Khausar ta shigo kansa ta nufa tare da miƙa hannunta da niyyar kamasa tayi saurin damƙe maranta tare da rintse Idanunta kana tace.
“Wayyo Allah na!”.
Cike da kulawa Mommy ta kalleta tare da cewa.
“Yau kuma ciwon cikin ki ko?”.
Kai ta gyaɗa mata cikin sanyi murya ta kalli Ramadan kana tace.
“Ramadan kazo mana kai kaɗai fa ake jira”.
Maƙale kafaɗa yayi dai-dai nan suka jiyo hong ɗin mota cikin sanyin murya Khausar tace.
“Mommy kin jifa shi kaɗai ake jira zasuyi letti fa Allah zaija idan sunje azanesu kinsan, Moddibo ba ruwansa ko yara sawa yake aci ƙaniyarsu!”.
Ta ida magansr tare da miƙa hannu da niyar janyo sa.
Cikin sauri Ramadan ya sake Matsawa baya tare da riƙe ƙafafun Mommy tare da fashewa da kuka kana cikin raunin murya yace.
“Mommy dan Allah kice abarni ni dai yau bana son zuwa makaranta bana so Mommy dan Allah ki barni”.
Mommy kuwa Kallonsa tayi lokaci ɗaya taji jikinta yayi masifar sanyi janye ƙafafunta tayi tare da Kallonsa kana tace.
“Kai Ramadan wai meyesa bakason zuwa makarantar?”.
Cikin kuka sosai yace.
“Ayyah Mommy dan Allah yau ɗin nan kaɗai ki barni kada Inje makaranta nafi so yau In wuni ina kallonki kina kallona”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ramadan kaje yau kaga gobe idan Allah yakai mu Alhamis ne baza kaje makaranta ba zamu wuni agida juma'a ma zamu wuni tare kaga har Asabar ma baza ka jeba”.
Girgiza kai yayi still hawaye na bin Fuskarsa yace.
“Mommy ni dai bana so”.
Miƙewa Khausar tayi tare da kama hannunsa tana jansa shima hannun Mommy ya riƙe yana kuka Khausar na jansa yana jan Mommy da ƙar ta fincike sa suka fita kana ta sanya shi amota tana kallon Haiydar dake hararan Ramadan tace.
“Gashi ku tafi”.
Kana ta juya ta koma ci.
Da yake shi Haiydar haddan safe suke zuwa na maza.
Kusa da Mommy ta zauna tare da riƙe mararta tana yarfe hannunta kana ta runtse Idanunta tare da faɗin.
“Wayyo Cikina ciwo Mommy!”.
Mommy kuwa jikinta ne yayi sanyi kallon Khausar dake riƙe da marar ta tayi tare da cewa.
“Ke tashi kijeki ɗauko min Yarona, bana so yau abar minshi kada yaje makarantar nan, tunda tun jiya da daddare yake Matsawa kada abarshi yaje nima raina baya so kawai abarshi ya dawo yafi min tashi ki ɗauko min ɗana”.
Ahankali Khausar ta ɗago tare da kallon Mommy kana cikin sanyin murya tace.
“Ayyah Mommy cikina ya kama bazan iya ba kuma Mommy meyesa zaki biye mishi?”.
Girgiza kai Mommy tayi tare da cewa.
“Khausar naji kawai bana so ya tafi ɗauko min shi”.
Dai-dai lokacin kuma suka ji Girinirin alamun an rufe gate Kallon Mommy Khausar tayi kana tace.
“Toh Mommy kin jin anrufe gate sun tafi”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe tare da lumshe Idanunta kana tace.
“Toh shikenan Allah ya tsare Allah ya dawo dashi lafiya”.
Khausar kuwa Ameen tace tare da kwanciya akan 3sitter still Hannunta na dafe saman maranta.
Kallonta Mommy tayi cike da kulawa tace.
“Yau kuma cikin ki yau nawa ga wata ne?”.
Ahankali Khausar ta buɗe Idanunta tare da cewa.
“Yau Sha biyar Mommy”.
Jinjina kai Mommy tayi kana tace.
“To aima kusan saura kwana huɗuma Period ɗinki yazo date ɗin da saura?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da matsa saman maranta kana tace.
“Eh Mommy haka dama yake min kafin kwanakin su cika yana min yawan ciwon ciki”.
Numfashi Mommy ta fesar kana tace.
“Allah dai ya sawwaƙa kije ki haɗa ruwan zafi da zuma kisha”.
Ahankali Khausar ta motsa laɓɓanta tare da faɗin.
“Toh”.
Kana ta yunƙura zata tashi tayi saurin komawa saboda yanda cikin ya murɗa.
Ganin haka yasa Mommy ta miƙe tare da zuba mata Zuma da ruwan zafi akofi ta kawo mata amsa tayi tasha tare da gyara kwanciyar ta akan kujeran tana jin ciwon na sauƙa ahankali Mommy kuwa zaman ta ta gyara akan kujeran tare da lumshe Idanunta...
Acan mota kuwa bayan sun isa bakin makarantar Amina dake baya ta kalli Driver tare da cewa.
“Malam Habu ka sauƙe su ba sai mun shiga cikin gate ba sai ka wuce ka kaini unguwar Waziri gidansu Samira Sani”.
Anutse Malam Habu ya juya ya kalleta kana yace.
“In dai shigar dasu kinga Yara ne ba zasu iya tsallaka wa daga kan titin nan ba bare yanda motoci suke wucewa”.
Wani kallon ta watsa masa tare da cewa.
“Yau suka fara zuwa makarantar kuma ga Haiydar ai zai riƙe su”.
Kai Malam Habu ya gyaɗa tare da sauƙe su kana yaja motar ya tafi.
Haiydar kuwa juyawa yayi tare da ɗaukar Raudat kana ya juya da nufin zai riƙe hannun Ramadan kawai ya hangosa Atsakiyar titin Aminu kuwa tuni ya tsallaka.
Kamar daga sama wata baƙar mota jeep ta taho aguje.
Cikin tsananin tashin hankali da ruɗu Haiydar yace.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Ramadannnn”.
Motar kuwa da mugun gudu tazo tare da nufar kan Ramadan...!
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k ne 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*
_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._
🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,
*By*
*GARKUWAN MARUBUTA*
[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta, cikin Aminci domin ko kin gashi a wasu wuraren toh na satane na Allah ya isane, Yaseen kuwa wlh na Allah ya isan ne duk ƙanƙatar haƙƙina ban yafeba, yake yar uwa mai tsoron Allah da kikaye haƙin wani ki biya 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group ɗin, ku kuma masu fitar da littafina ki da Allah, Allahu Rabbi ya isarmin wahalata da nasha kusan tsawon shekara ina rubutu. Dan ki biya 1k kudin karatu kike fitarwa mutun sama da ɗari, toh yadda kika tozarta min kasuwanci ne kema Allah ya haɗaki da mai miki fiye