Showing 162001 words to 165000 words out of 176046 words
Allah ahaɗa Abba abasu azo a karɓe ni”.
Cikin rauni ya runtse Idanunsa da hawaye suka cika kana yace.
“Abba bana son zaman nan babu daɗi ba Ummina ba A.J sannan kaima ba kai wuri ba daɗi dan Allah Abba ka basu duk abinda suke so kazo ka karɓe ni ku saida komai nawa a haɗo kuɗin”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da ƙoƙarin hana hawayen sa zubowa kana yace.
“Babana Insha Allah zan zo in karɓe ka koda raina suke so zan basu amadadin ranka”.
Modibbo kuwa tuni wasu irin hawaye masu masifar zafi ke kwaranyo mishi tamkar mace.
Fisge wayar sukayi daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.
“Toh kaji dai abinda ɗan ka ya faɗa zamu baka dama ta karshe”.
Cikin sauri Moddibo da idanunsa ke rintse ya buɗe tare da cewa.
“Dan Allah! Dan Allah!! Dan girman Allah!!! dan darajar Annabi Muhammad (S.A.W) badan muba kamar yanda kuka ce J nada mutunci da kamala toh dan Allah saboda wannan kamalar tasa ku rage mana kuɗin zamu yi muku duk kan biyayya amma ku faɗa mana abinda zamu iya kawo wa”.
Daga ɗaya ɓangaren shiru mutumin yayi ba tare da yace komai ba kana bai katse kiran ba.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Dan Allah kuyi haƙuri ku rage mana Insha Allah ba zamuyi gardama ba, amma kuɗin hannun mu munyi munyi sun kasa kai adadin da kuke buƙata mu samu su kai adadin da kuke buƙata wannan shine matsalar mu ku temaka ku ragar mana”.
Ajiyar zuciya mutumin ya sauƙe tare da cewa.
“Wannan Moddibo ne ke magana ko?”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana cikin sanyin murya yace.
“Eh”
Cike da gadara Mutumin yace.
“Toh shikenan ku bada Million ɗari da hamsin”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Mungode amma dan Allah ba zaku ƙara rage mana ba?”.
Cikin wata razananniyar tsawa Mutumin yace.
“Dan ubanka dan ka samu na zabge Million hamshin.
Atake to wallahi acikin Million ɗari da hamsin Naira biyar ba zamu rage ba kuma wallahi idan ku ka yarda kuka sake yi mana batun ragi kuɗi to wallahi akan ran Jameel domin kuɗi ne dai mu ki ya rayu ko ya mutu zamu samesu”.
Cikin tsanananin tsoro da kaɗuwa Moddibo ya dafe ƙirjinsa yayin da kansa ya sara da masifan ƙarfi.
Cikin tsawa Mutumin ya cigaba da cewa.
“Yanzu Moddibo gashi kayi magana dashi na ƙarshe wanda ko bacci yake yana kiran sunan ka gashi kayi magana dashi dan wataƙil shine maganarka na ƙarshe kenan dashi matukar dai baku haɗa kuɗin nan ba ku kasake yi mana batun ragin kuɗin to kayi magana dashi na ƙarshe kenan”.
ya faɗa tare da wurgawa M Jameel wayar.
Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da maƙalawa akunnensa kana cikin raunin murya yace.
“A.J”.
Cikin sauri da zaƙuwa Moddibo yace.
“J ina kake?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi tare da cewa.
“A.J ban san inda nake ba ina Ummina!?”.
Runtse Idanu Moddibo yayi tare da taune lips ɗinsa kana yace.
“Tana lafiya J?”.
Cikin sanyin Murya M Jameel yace.
“J ka tabbata?”.
Cikin raunatacciyar murya yace.
“Na'am”.
jin haka yasa yaci gaba da cewa.
“Kace mata kada tayi kuka tayi ta min. Addu'a A.J ina sonka Ina son Ummina Ina son Abbana Ina Son Asma'u Ina son Bashir”.
Da sauri Moddibo ya dafe ƙirjinsa dake harbawa da masifan ƙarfi cikin raunin murya M Jameel ya cigaba da cewa.
“A.J Ina son Khausar tashigo rayuwar mu”.
Cikin tsanananin rauni Moddibo yace.
“Na sani J nasan kana son mu muma muna sonka, kuma in sha Allah duk zamu kasance a tare, zata shiga rayuwarka J zan mutunta abinda kakeso J”.
Girgiza kai M Jameel Yayi still cikin raunin murya yace.
“Ngd A.J in kayi haka kayi min komai, kayiwa Ummina magana idan akwai wani abu a hannunta ta bayar ahaɗa azo a karɓeni awajen nan dan Allah katemaka min”.
Araunane Moddibo yace.
“Insha Allah J zan taimaka da duk kan iyawa ta da kuma duk kan damata J koda ace da raina ne zan fanshi ranka da rayuwarka Insha Allah zamu fito da kai”.
Jinjina kai M Jameel yayi tare da faɗin.
“Nagode Nagode A.J ina maka fatan al'khairi acikin rayuwarka ga Amanar Ummina, Asma'u, Bashir,Abba da.... ka kula dasu kafin in dawo sannan kada ka mance batun Kh”...
Fisge wayar akayi daga kunnensa tare da katsewa.
Dafe kai Moddibo yayi cikin wani irin azabebben rauni ya fashe da matsanancin kuka tare da miƙewa batare da yace komai da Abba ba ya fice yana fita ya shiga motarsa tare dayi mata key.
Kana ya ciro wayarsa tare da dearling number Ummi tana ɗagawa murya a raunace yace.
“Ummi”.
Cikin sanyin murya tace.
“Na'am”.
Cikin ƙoƙarin hana kansa kuka yace.
“Ummi munyi waya da J yanzu”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe kana tace.
“Dagaske Babana?”.
Kai ya gyaɗa kamar tana gabansa.
Cike da tsoro Ummi tace.
“Babana to Meyesa kake kuka?”.
Fashewa yayi da kuka kana cikin sheshsheƙa yace.
“Ummi ina kukan rashin J akusa dani ne Ummi wanda suka sai motarki Alhj Abdallah kice ya tura Azo aɗauki motocina da na J duka azo asiya ahaɗa kudin duka”.
Numfashi Ummi ta fesar tare da rintse idanunta kana tace.
“Sunƙi ragewa ko?”.
Girgiza kai yayi tare da cewa.
“A'a Ummi sun rage mana Million hamsin akai yanzu ya zama Million ɗari da hamsin suke buƙata”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Toh Alhamdulillah wataƙila zamu iya cin nasara".
Cike da rauni Moddibo yace.
“Insha Allah Ummi da izinin Ubangiji”.
Ya faɗa tare da katse kiran jin wani kuka na neman kufce masa.
Kai tsaye hanyar gida ya nufa ba abinda ke yawo acikin kunnensa face sautin Muryar J ɗinsa yana isa gida yayi Parking tare da rufe musu gate.
Kai tsaye sashen Innayi ya nufa yana isa ya zauna abakin baranda tare da riƙe kansa da hannu duka biyu,
Kana ya fashe da wani irin kuka mai masifar ciwo a zuciya.
Wani irin azaban zogi yaji zuciyarsa na masa hadi da zafi da raɗaɗi yayin da wani masifaffen rauni ya lulluɓesa.
Innayi da bacci ya fara fisgarta ne, ta miƙe da sauri jin kamar sheshsheƙan Kukan Moddibo kana ta fito tare da Kallonsa yayin da gaba ɗaya ilahirin jikinta ya ɗauki rawa cikin sanyin murya tace.
“Ya dai Moddibo lafiya kuwa mai ya faru da Jameelu?”.
Cikin matsanancin kuka yace.
“Innayi ya zamuyi taya zanyi in.
Samu in taimaki J duk kan tattalina ya ƙare babu abinda zan samu in saida cikin gaggawa.
Zan saida tsohuwar motar da kika siya min da wannan sabuwar da kuma na J duka za'a siyar sannan Innayi nasan koda an siyar dasu duka, kuɗin ba zasu ciki Million ɗari ba”.
Sai kuma ya kife kansa bisa guiwowinsa ya sake fashewa da sabon kuka kana yace.
“Innayi sunce idan muka sake neman ragi akan kuɗin kamar mun nemi akashe J ne”,.
Jingina kansa yayi jikin fillan dake gefenta tare da fashewa da matsanancin kuka hadda sheshsheƙa.
Cikin Sanyin jiki Innayi ta zauna kusa dashi batare da tace yayi shiri ko kuma ya daina kukan ba, domin ta tabbata duk abinda yasa Moddibo kuka ba ƙaramin abu bane, kana idan har bai yiwa wannan abin kuka ba to mai zai yiwa kuka arayuwarsa.
Moddibo kuwa kuka ya cigaba da yi tamkar ransa zai fita har shidewa yake.
A ƙalla ya ɗauki Mintuna masu tsawo yana kuka kafin ahankali ya ɗago kansa tare da kallon Innayi kana yace.
“Innayi”.
Cikin sanyin murya tace.
“Na'am Moddibo”.
Cikin Muryansa daya dishe da kuka yace.
“Innayi ta wace hanya ce wace damace wane daliline kike samu kike mana duk kan buƙatun rayuwarmu?
Innayi in dai har adana kuɗi kikayi in dai har basu ƙare ba Innayi ki fito mana dasu ki taimakeni aceci J dashi”.
Jinjina kai tayi kana tace.
“Moddibo gaba ɗaya tattalin da mukayi na zaman rayuwar mu awannan yanki awannan gari a wannan ƙasar anje matakin da gaba ɗaya tattalin namu yazo ƙarshe sabida lokacin komawa muhalli ya kusan cimmmana”.
Sai kuma ta kalli Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke bin Fuskarsa kana tace.
“Na tanadi komai ne domin sanin cewa muna da bukatar su kama daga karuntaka, ci, sha, Jinya, sutura.
Da dai sauransu to yanzu kuma lokaci ya tafi rayuwa ta juya abubuwa sun tafi baki ɗaya tattalin namu yayi ƙasa tsadan rayuwa ya cinye kaso mafi tsoka”.
Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Innayi koma wani irin tattaline shin babu ragowa ne ko kaɗan ne?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Akwai ragowa”.
Cikin kuka yace.
“Menene amfanin ragowan duk tattalin arzikin da kike dashi matukar dai ba zai fito atemaki J ɗina da shiba Jamelunki fa ya fito daga inda yake fa”.
Ya ƙare mgnar cikin ƙunan rai, domin gani yake kamar ma duk duniya ba'a damu da J ɗinsa ba.
Ita kuwa Innayi cikin tafiya wani sashi nazarin Jinjina kai tayi tare da cewa.
“Bashi da amfani Indai bazan fito dashi ba, amma bari na fito dashi amma yanzu ka fara yin shiru tukunna kana kayi min al'ƙawarin cewa bazaka tambayeni komaiba akan duk abinda zaka gani”.
Kai ya gyaɗa mata kana yace.
“Innayi muga abinda zan fara samu awajenki tu kunna zanfi jin sanyi, ni yanzu a duniya babu tambayar da ke bakina daya wuce ina J yake , wanne hali yake ciki”.
Sai kuma ya fesar da zazzafan numfashi tare da cewa.
“Wallahi Allah ji nakeyi tamkar naje na zauna abakin masallacai inyita bara asamu ahaɗa kudi in cikata in karɓo J Innayi ya zanyi”.
Cike da rauni Innayi tace.
“Ba zakayi bara ba Moddibo Bari muga abinda Allah zai mana”.
Kai ta gyaɗa tare da jan hannunsa suka nufi bayan ɗakinta inda randunan ƙasa ke ajiye.
Kallon Moddibo da har zuwa lokacin hawaye ke zuba a idanunsa tayi kana tace ɗaga min randan nan”.
Sauri kallonta yayi kana ya Kalli randan ƙasan tare da cewa.
“In ɗaga miki randa kuma?”.
Ba tare data kallesa ba tace.
“Kada kayi min musu idan na baka Umarni kabi”.
Kai ya gyaɗa cikin sanyin yace.
“Toh”.
Tare da ɗaga randan ya matsar gefe.
Ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Toh ɗaga fantekar”.
Kai ya ɗaga tare da matsar da fantekar dake cike da ƙasa gefe.
Yana janye fantekar yaga ƙasan wajen alailaye.
Ahankali Innayi ta zauna agaban wajen Moddibo kuwa cikin sanyi jiki ya durƙusa agefenta.
Itako Innayi hannunta ta sanya ta fara tono ƙasan dake wajen ganin duhu agarin yasa Moddibo sanya hannunsa acikin aljihu ya ciro wayarsa tare da kunna tochligt ya haska mata inda take tonawan.
Innayi kuwa ahankali ta cigaba da tono ƙasan bayan ta gama kwashe ƙasan ya rage sauran wasu manyan duwatsu ahankali ta ciresu duka.
Cike da mmki Moddibo ya tsaida idanunsa akan fafakekken rami an lailayeshi da siminti yana rufe da murfin tukunya kamar na lamba uku, da ɗan ƙarfi ta ɗago Murfin tukunya.
Cikin sauri Moddibo yayi saurin rintse idanunsa da karfu sakamakon wani haskene mai masifar sheƙi daya ɗauke masa idanu daya kashe masa idanu,
A hankali ya kuma saƙe buɗe inadunsa, da sauri ya mitso ganin yadda cikin ramin ke sheƙi da ƙelƙeli mai ɗauke ido yake fitowa daga cikin ramin, acan ƙasan ramin kuwa cike yake da ƴan ƙananan sulallan gwala-gwalai wanda basu fiye yawa ba sosai hasken ya ɗauke masa idanu saboda hasken wayarsa daya haske cike da tsanananin mamakin ya sunkuyo tare haska cikin ramin da kyau kana ya sanya tafin hannunsa acikin ramin ya ɗebo guda huɗu tabbas sulallan Gwalne...!
Littafin SAKAYYAH na kuɗine ko kin ganshi a wani wurin na satane. Ki biya ki karanta cikin Aminci 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA.
By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:42 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin nan dai ba free book bane, na kuɗine ko kin gashi a wasu wuraren da ba Group na da ake biya insa mutum, littafin 1k ne kacal in sha Allah zaki karanta shi daga forko har ƙarshe akan 1k kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki yar uwa*
Sbpndegoo. Lamiɗo kuwa cikin yanayin, tausayi da jinƙai da ƙauna mai haɗe da taraddadi da tsoro, ya sanya tafin hannunsa na dama ya tallafo, fuskar Ramadan ya juya gefe da gefe ga mmkinsa gaba ɗaya uwayan yaron ya koma lagob-lagob cikin yanayi da kiya da son aro Jarumtaka ya runtse Idanunsa tare da maimaita kalmar Hasbunallahu wani'imal wakil. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n.
Cikin sauri Hajiya Bunayya dake zaune ta buga hannunta aƙirji tare da kallon Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido tace.
“Mai Martaba ya rasu ko?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da ɗago ido ya kalleta kai ya girgiza mata batare da yace komai ba.
Da sauri Mommy dake tsaye tayi baya tare da zama da ɓas akan kujeran dake bayanta, baki ɗaya jikinta ya saki Atake ta fara Maimaita kalmar.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin”,ta faɗa hawaye na bin kuncinta Shar-shar.
Khausar kuwa juyawa tayi ta kalli Hajiya Bunayya kana ta mayar da kanta kan Mommy da hawaye ke bin kuncinta ahankali ta sake maida kallonta kan Lamiɗo da yayi shiru yana jan yatsun Ramadan alamar yana dai-dai-tasu.
Cikin wani irin yanayi tace.
“Abba mu tafi dashi asibiti,Abba mu kaisa asibiti”.
Jujjuya kai Lamiɗo yayi kana yace.
“Khausar ki nutsu”.
Kallon Hajiya Bunayya da Idanunta ke kan Ramadan yayi yace.
“Hajiya Bunayya kama khausar ki zaunar da ita”.
Mommy kam tana zaune akan kushin babu abinda take maimaitawa face kalmar Innalillahi still hawaye na bin kuncinta.
Ganin haka yasa Lamiɗo fesar da numfashi kana ya miƙe tare da ɗaukar Ramadan awuyansa ya fice.
Da sauri Khausar ta miƙe tare da bin bayansa tana cewa.
“Abba inzo mu tafi Asibitin ne!?”.
Tsintsiyar hannunta Hajiya Bunayya ta riƙe tare da gyara zamanta tace.
“Khausar ki nutsu mana ki dawo ki zauna?”.
Kai khausar ta girgiza cikin rawan murya tace.
“Ki sake ni zamu tafi asibiti ne kiga Ramadan fa”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da faɗin.
“Ki zauna mana ba kiji Abbanku yace ki zauna ba.
Kai ta gyaɗa cikin wani irin yanayi ta koma ta zauna.
Lamiɗo kuwa yana fita kai tsaye sashen Gimbiya Dadu ya shiga bakinsa ɗauke da Sallama zaune ya samu Gimbiya Dadu afalon.
Ganinsa Rungume da Ramadan yasa cikin sauri tace.
“Ya dai lafiya Lamiɗo meke faruwa?”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ramadan ne fa ki duba min shi”.
Kai ta gyaɗa tare da Matsawa gaban Ramadan dake kwance ƙasan ɗakin yatsunta biyu ta kai saitin hancinsa sannan ta riƙe jijiya hannunsa kallon Lamiɗo tayi cike da mamaki tace.
“Ha'a bashi da rai ai ajikinsa?”.
Araunane Lamiɗo ya ɗago idanunsa da suka kaɗa sukayi jawur jijiyoyin kansa ya tashi cikin raunin murya yace.
“Nima dai kamar haka na gani ahannuna na ya cika kamar babu rai atare da shi.
Jinjina kai Gimbiya Dadu tayi cikin rawan murya tace.
“Tabbas ba Rai atare dashi Ramadan ya rasu fa”.
Ta ida maganar tare da ɗago hannunsa ta juya sangalam duk ta inda ta juya sai ya tafi luuuu zai fadi kana ga bakinsa dake aɗan buɗe idanua kafe.
Ahankali Lamiɗo ya sunkuyar da kansa akan Ramadan hawaye masu ɗumin gaske suka shiga zubo masa asaman kincinsa, suna ɗiga kan fuskar Ramadan tal-tal yayinda jinkinsa ya shiga tsuma.
Gimbiya Dadu kuwa bayanta ta jingina da jikin kujeran cikin sanyin murya tace.
“Allah sarki Ramadan ashe dai ciwon kan nan na ɗauka ne? Ciwo lokaci ɗaya!?”.
Akuma dai-dai lokacin Uncle Naseer ya shigo falon ganin yanayin da suke ciki ne yasa ya zauna gefen Gimbiya Dadu tare da cewa.
“A Lafiya meke faruwa?”.
Ahankali Gimbiya Dadu ta ɗago kai tare da Kallonsa tace.
“Wallahi Ramadan ne Allah ya masa rasuwa!”.
Arazane Uncle Naseer ya Kalli Gimbiya Dadu tare da kallon Ramadan dake kwance cikin wani irin yanayi yace.
“Ha'a wani irin magana ne Gimbiya Dadu ya zakice Ramadan ya rasu!? Ko ke Dr ce ya za ayi kice ya rasu taya kika gane hakan?”.
Kallonsa ya mayar kan Lamiɗo daya zubawa Ramadan ido kana yace.
“Yah Lamiɗo mu kaisa asibiti”.
Kallonsa Lamiɗo yayi tare da Girgiza masa kai still Idanunsa na nan ja jawur ruwan hawaye na kwance acikinsu yayinda jikinsa ke cigaba da tsuma zuciyarsa na harbawa da masifan ƙarfi.
Uncle Naseer kuwa hannu yasa a aljihu tare da ciro wayarsa yayi dearling number family Dr su yana ɗagawa yace dan Allah yazo ya duba yaro agida Dr ya amsa da toh.
Bayan minti 16 minute Dr yazo bayan ya duba ya tabbatar musu da Ramadan ya rasu kimanin minti talatin da suka wuce.
Sai asannan Uncle Naseer ya yarda kana ya raka Dr ya tafi yana dawowa.
Sashen Gimbiya Dadu ya hadu da Lamiɗo ya fito da Ramadan Rungume akafaɗarsa bayansa yabi Lamiɗo kuwa kai tsaye Falonsa ya nufa yana shiga ya kwantar da gawar Ramadan Atsakiyar ɗakin kana ya cire masa suturar jikinsa ɗen oh foɗimo.
Cikin rauni da tsinkewar zuciya ya nufi ɗakin Mommy a inda yabar Mommy zaune anan ya dawo ya sameta still Idanunta na zubar da hawaye masu zafi da ƙuna a zuciya.
Khausar dake gefenta ta kalleta tare da cewa.
“Mommy Meye faru me yasamu Ramadan?”.
Ahankali Mommy ta janyota jikinta tare da kwantar da ita akan cinyarta kana ta sanya hannunta akanta tana shafawa cikin sanyin murya mai cike da rauni tace.
“Khausar muyi haƙuri Ramadan kam ya tafi ya barmu.
Ubangiji Allah yajiƙan sa Allah ya masa rahma Allah yasa mai cetone”.
Cikin tsananin tashin hankali Khausar ta fashe da matsanancin kuka me tsuma zuciya yayin da ta shiga girgiza kanta kallon Mommy tayi Muryanta na rawa tace.
“Mommy Ramadan kike cewa ya rasu!? Mommy wannan wani irin magana ne!?
Dan Allah Mommy kice mafarki nake Mommy kice ba gaskiya bane!”.
Girgiza kai Mommy tayi still Hawaye na bin fuskarta amma ta gaza furta komai.
Cikin sauri Khausar ta toshe bakinta jin wani matsanancin kuka ya taho mata.
Ajiyar zuciya Lamiɗo ya sauƙe tare da ƙarasawa cikin falon ya zauna kusa da Mommy, kasancewar akan 3sitter take.
Cikin sanyi murya yace.
“Khausar kiyi haƙuri kinji ko?”.
Kallonsa tayi da jikaƙƙun Idanunta kana tace.
“Abba da gaske wai Ramadan ya rasu!?”.
Nunfashi Abba ya fesar tare da jinjina mata kai yace.
“Da gaske ne Khausar ya muka iya da hukunci Ubangiji, dama shi ya bamu Ramadan kuma shi ya karɓesa, kiyi haƙuri ki daina kukan nan kinji ko!?”.
Girgiza kai tayi tare da sake fashewa da matsanancin kuka mai gunji.
Dafa kanta Lamiɗo yayi cike da tausayawa yace.
“Kiyi haƙuri yanzu ma Naseer ya kira Dr yazo ya dubasa sannan ya tabbatar min da cewa ya rasu!”.
Cikin wani irin yanayi mai cike da ruɗu Khausar ta miƙe da gudu tare da shiga Bedroom ɗinta ta faɗa kan gado tare da sakin marayan kuka.
Lamiɗo kuwa bayan ya sake rarrashin Mommy tare da bata haƙuri da kuma nuna mata muhimmanci tawakkali