Showing 93001 words to 96000 words out of 176046 words

Chapter 32 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete


_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*In sha Allah daga gobe zan gama free page, ƴar uwa baki makara ba ki biya ki karanta cikin Aminci littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 daga wannan page ɗin sai na gobe mun gama free page, ki biya yafi sauƙi tsira ba haƙƙin kowa kanki.*



*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*

Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.

Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.

Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA

Shiko M Jameel Wani irin tsuma ilahirin jikinsa keyi sakamakon tuni da ayoyin sukayi mishi na jin azabar da Ubangiji ya tanadar wa da duk wanda ya kashe ran mumini da gangan ba tare da wani haƙiba.
Cikin raunin murya me cike da tsananin tsoron Ubangiji M jameel É—in ya kawo fassarar aya na 90 da kuma 91, tsit gaba É—aya masallacin yayi babu abinda ke tashi sai sautin kukan M Jameel daya kasa ci gaba, yayinda kukansa yasa da dama cikin mutanen yin kuka.
Middibo kuwa kife tafukan hannunsa yayi kan fuskarsa yana maiyin wani irin sassayan kuka mai masifar sa rawan jiki, gaba É—aya fuskarsa tayi jazir.
Cikin ƙarfin hali M Jameel ya fara mgn cikin rawan murya yace.
“A cikin suratul Nisa, Aya ta 92 Allah ma ɗaukakin sarki na cewa, 92:
-:Baya halasta ga mutum da ya kashe ran mumini, sai dai idan ya kasance kuskure ne.”.
Sai kuma ya tsagaita tare da sayan tafin hannunsa ya share hawyen daketa kwaranyowa da idanunsa, cikin rawan murya yaci gaba da cewa.
“Duk wanda kuma ya kashe! Mumini da kuskure toh, zai ƴanta wuyan Muminin, sannan ya bada Diyya ga iyalan wanda ya kashe”.
Sai kuma ya dire ayar mgnar tare da rushewa da zazzafan kuka mai cike da tashin hankalin da raunata zukata aya ta 93.
Cikin rauni yasa hannu ya karɓi hankicif ɗin da ɗan agajin dake bayansa ya miƙa masa, sharce hawayensa yayi tare da juyowa ya kalli Moddibo da gaba ɗaya jikinsa rawa yake sai sheshsheƙan kuka mai fuzge numfashin da yakeyi, bazai iya hana kansa kuka ba, bare ya samu iko da damar hana aminin nasa.
Cikin sheshsheƙan kuka M Jameel ya gyara zamanshi tare da cewa.
“Huymmmm, a kuma cikin suratul Nisa ɗin ayata 93, Allah madaukakin sarki nacewa-:
(Duk wanda ya kashe Mumini bisa ganganci, ko Mugunta da zalumci. Toh Sakamakonsa shine wutar Jahannama”.
Sai kuma ya sake sakin wani irin raunataccen kuka mai cike da tsoro kana yaci gaba da cewa.
“Allah madaukakin sarki cewa yayi-:
Duk wanda ya kashe ran mumini zai dawwamane cikin jahannama, kuma Allah yayi fushi dashi, sannan kuma ya tsine masa”.
Kawai sai ya kife kansa bisa Table ɗin dake gabansa, shar-shar haka hawayensa ke kwaranyar babu ƙaƙƙautawa.
Modibbo kuwa cire tafukan hannunsa yayi bisa fuskarsa tare da dafa kafaÉ—ar M Jameel É—in kawai saka sufashe da kuka a tare, cikin kukan murya na rawa M Jameel ya buÉ—e baki da nufin zaiyi mgn amman ina ya kasa.
Haka yasa Moddibo rumtse idanunsa kana murya na rawa yace.
“Bayan fushi da tsinuwar ubangiji Allah Mabuwayi da komai baya ɓuyar masa yace.
-:Wa ahdalahun Azaban Azeeymah).
Ma'ana ya tandarwa duk wanda ya kashe ran mumini da ganganci Azaba mai girma!!!!.”
Zuwa lokacin wasu daga mutanen cikin masallacin kuka sukeyi da sheshsheƙan mafi akasari kuma duk jikinsu yayi sanyi.
Shi kuwa Moddibo cikin rauni da sanyi yace.
“Duk waɗannan ugubobin sun ta'allaƙane ga wanda ya kashe ran mumini da ganganci, sakamakonshi Jahannama, kuma a cikinta zai tabbata, sannan Allah yayi fushi dashi, kana ya tsine masa, kuma ya ƙara masa da azaba mai girma.
Wannan masifa har ina ɗan adam zai kaishi koda iyayenka ne sukayi fushi da kai taɓewa kakeyi bare Ubangijin talikai, koda iyayenka ne suka tsine maka lalacewa kakeyi bare tsinuwar Allah, sannan azaba koda ta tururin tea ne tsoronsa muke bare kuma tabbata ta jahannama sannan da tanadin azaba mai girma”.
Kawai sai lips inshi suka fara rawa kar-kar shima É—in ya kasa ci gaba.
Ganin hakane yasa M Jameel sharce hawayensa tare da cewa.
“Aramma kawo mana dukkan wata Ayar Al,qura'ani da Ubangiji yayi magana akan duk wanda ya kashe ran mumini”.
Cikin tsumar jiki tare da wata raunatacciyar murya mai cike da tsananin tsoron Ubangiji da kuma sanin hukuncin wanda ya saɓa masa Moddibo yayi gyaran murya dai-dai zai fara karanta Ayar manyan Malaman dake wajen suka nuna musu agogon dake liƙe a can bayansu a jikin gini.
Wanda hakan ke musu nuni da alamar lokaci yayi.

Nan-nauyan ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe tare da share ƙwallan da suka zuba masa kana cikin raunin murya yace.
“Lokaci yayi sai dai idan Allah ya kaimu gobe zamu ɗaura daga inda muka tsaya”.
Ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Ya Allah Ubangiji yabamu zaman lafiya ya Allah karabamu da sharrin ƴan bindiga daɗi Ubangiji ya tsare mu da sharrin kidnappers Ubangiji ya bamu zaman lafiya Allah yajiƙan iyayen mu da duk kan musulman da suka rigamu gidan gaskiya.
Wa subhanakallahumma wabi hamdika ash shahadula'ilahu. nastagfirka wanatuubu Ilaik”.
Tunda ya fara addu'ar suke Amsawa da Ameeen har aka shafa.
Mata ne suka fara fita kafin maza.

Acan ɓangaren Khausar kuwa, bayan ta koma gida kai tsaye Bedroom ɗinta ta wuce batare data shiga wajen Mommy ba, tana shiga ta kwanta lamo akan gado hawaye na tsiyaya daga kyawawan Idanunta sosai.
Tafseer ɗin da M Jameel Yayi ya riƙa ratsa jikinta har ƙwaƙwalwar kanta Muryar Modibbo kuwa har yanzu yana ratsa kunnuwanta, da haka bacci ya ɗauketa batare data shirya ba.
Washe gari Da safe still haka Khausar ta tashi cikin mutuwar jiki Anutse ta fito daga Bedroom É—in ta zauna agefen Mommy dake falo.
Lumshe Idanunta tayi kana cikin sanyin murya tace.
“Mommy ina kwana”.
Anutse Mommy ta maida kallonta gareta tare da na zartan yanayin ta batare data amsa gaisuwar data mata ba ta jefo mata tambya tare da cewa.
“Meke damunki Khausar na lura tun jiya jikin ki Asanyaye”.
ĆŠago Kai Khausar tayi Idanunta cike da ruwan hawaye kana cikin sanyi murya tace.
“Wallahi Mommy tun jiya da muka je wajen tafsir ɗin da Malam M Jameel yayi jikina ya mutu hankalina ya tashi gaba ɗaya na rasa mai yasa tsoro ya kamani”.
Miƙewa Mommy tayi tare da matsowa kusa da Khausar ta shafa kanta kana tace.
“Babu komai wannan masiface-masiface ne da Allah ya jarabci Al'umma wannan ƙarnin saidai mu dage da addu'a Allah ya yaye mana ya kuma tsaremu da faɗa wa mummunar ƙaddara Allah ya rufa mana asiri ya karemu da zamewa sanadin mutuwar koda kadagare ne”.
Jinjina kai Khausar tayi tare da cewa.
“Ameen”.

Acan gidansu Moddibo kuwa Innayi ce zaune atsakar gida ta zabga tagumin tunda taji tafsirin da M Jameel sukayi jikinta yayi masifar sanyi wani irin tsoron Allah mara misaltuwa tashiga hakan fargaba ya rufeta.
Washe gari.
Da hantsi A hankali Moddibo da M Jameel suka fito, Moddibo na sanye cikin Shigarsa as Usual Jallabiya Sky blue mai yauƙi da santsi kansa ɗaure da farin Hirami kana takalmamsa farare jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi turaren Oud Khareem na tashi.
Shima M Jameel sanye yake cikin irin shigar Modibbo jikinsa na fitar da sanyayyan ƙamshi kai tsaye sashen Innayi suka nufa,Innayi dake zaune gaban barandar akan kujera ƴar tsugunno ta ɗago kai ta kalli Moddibo da M Jameel kawai sai taji Idanunta na tsats-tsafowa da ruwan hawaye.
Tsayuwa Moddibo ya gyara kana yace.
“Ya dai Innayi”.
Idanu ta zuba masa batare data iya furta komaiba kawai sai hawaye suka shiga kwaranya daga idanunta.

Cikin yanayin tashin hankali Moddibo ya tsugunna agefenta na dama yayin da M Jameel ya durƙusa agefenta na hagu kana suka haɗa baki tare da cewa.
“Innayi ya dai me yasame ki?”.
Kallonsu tayi hawaye na cigaba da kwaranya daga idanunta ta sauƙe numfashi kana tace.
“Wa'azinku na jiya ya ratsa jikin mutane wa'azin yasa mutane acikin ɗimuwa wa'azinku na jiya ya tunatar sannan yasa tashin hankali kuma wannan zamanin muna fama da Masifa Allah dai ya yaye mana jiya hankalina atashe yake domin ire-iren abubuwan akeyi!”.
Jinjina kai M Jameel yayi tare da sauƙe numfashi kana yace.
“Hakane sosai ma Innayi amma mu cigaba da addu'a babu abinda ya gagari Ubangiji ga dama yazo watan Ramadan muyita addu'a Allah ya yaye ya taƙaita ya sauƙaƙa mana”.
Atare Modibbo da Innayi suka amsa da.
“Ameeen”.
Miƙewa M Jameel da Moddibo suka atare kana M Jameel ya Kalli Innayi tare da cewa.
“Toh Innayi zamu tafi Tafseer A masallacin makarantar mu”.
Jinjina kai Innayi tayi kana tace.
“Ubangiji Allah ya tsare ku ya kuma sake ɗaukaku”.
Ameeen suka amsa tare da juyawa zasu fita har sun kai ƙofa Innayi ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da cewa.
“Yauwa wai niko ya batun tafiyar mu ne?”.
M Jameel ya juya tare da cewa.
“Komai ya kammala na tafiyar mu Insha Allah ranan sha biyar ga wata zamu tashi misalin sha biyu da rabi na dare jirginmu zai tashi jibi kenan ba in sha Allah, kuma sai munyi tafsir ɗin ranan ma zamu tafi Taraba”.

Kai ta gyaÉ—a kana tace.
“Allah ya nuna mana Ubangiji Allah ya kaimu lokacin lafiya amman kuma kace sai kunyi tafsirin ranar?”.
Kai ya jinjina tare da cewa.
“Eh kinga Tara na dare zamu fara, goma zamu tashi, dama kuma kafin mu tafi zamu gama shirin mu duka, tsananin mu Gembulan da taraba kuma tafiyar awa ɗaya da rabine, kinga kenan sha ɗaya da rabi zamu isa, zamu samu awa ɗaya ma acan kafin mu tafi, Abba na kuma su gobe nema zasu tashi”.
Cike da gamsuwa Innayi ta jinjina kai tare da amsawa.
“Allah ya kaimu lfy”.
Ameeen suka amsa a tare kana suka fice mota suka shiga M Jameel ke Driving cikin nutsuwa har suka isa masallacin.

Suna shiga suka fars gabatar da tafsirin kamar yanda suka saba ƙarfe ɗaya da rabi dai-dai suka gabatar da sallah Moddibo yayi limanci bayan sun idar suka cigaba kiran sallar La'asar yasa suka dakata da karatun tare da miƙewa suka gabatar da sallah bayan sun idar suka fito suka shiga mota awannan lokacin ma M Jameel ke Driving har suka iso gida.
Hong M Jameel Yayi Modibbo ne ya fita ya buÉ—e musu.
Anutse suka fito tare da furta Bismillahi,
Ahankali Moddibo ya gyara tsayuwarsa tare da fesar da sassayan numfashi.
Ido ya tsirawa bishiyar Ayaba da iska ke kaɗawa har na tsawon sakonni goma, sai kuma ya maida kallonsa kan Bishiyar mangoro Idanunsa ya lumshe domin Allah ya sani ganin sirrai ya fiye mishi ganin komai daɗi. sannu ahankali ya riƙa tuna lokacin da yarinyar tashigo gidan har tayi nasaran hawa reshen bishiyar mangoro mai girma da tsawo, da kuma sanda ta faɗo akan yatsun ƙafarsa.
Da sauri ya buÉ—e idanunsa
Tare da jan dogon tsaki mai cike da tsanar lamuran yarinyar. Idanunsa ya juya jin M Jameel na cewa.
“A.J tunanin mai kakeyi haka ka tsiwara Bishiya ido?”.
Sanyayyar Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da furzar da iska mai sanyi daga bakinsa kana yasa hannu ya shafa kwantaccen Sajen fuskarsa ya maida kallonsa kan M Jameel da har zuwa lokacin shiyake kallo,Ya mutse fuska yayi kana yace.
“Babu komai”.
Daga haka ya wuce gaba Kai M Jameel ya Girgiza tare da bin bayansa suka shiga Babban falon Moddibo da komai ke kimtse sai tashin ƙamshi yake.

Zama M Jameel Yayi akan 3sitter tare da faÉ—in.
“Wash' Allah!”.
Kallonsa Moddibo yayi amma bai ce komai ba Bedroom ya nufa tare da janye Hiramin kansa kana ya cire jallabiyar dake jikinsa ya buɗe ƙofar toilet da addu'a
Kana yashiga shawer ya sakarwa kansa yashiga cuɗe jikinsa ya ɗauki kusan minti ashirin kafin ya fito zama yayi agaban Dressing mirrow ya shafa Mai sama-sama kana ya miƙe ya sanya Jallabiya Maroon colour da farin hirami. Feshe jikin sa da turarukansa masu daɗin ƙamshi yayi. shima M Jameel wanka yayi tare da sauya kan jikinsa zuwa Jallabiya fari kana ya ɗaure kansa da Maroon Hirami Sosai sukayi kyau atare suka fito zuwa farfajiyar gidan anan suka samu Innayi da Asma'u na aikin abin buɗa baki kallon Innayi dake soya ƙosai yayi sai kuma ya maida kallonsa kan Asma'u dake dama kunun sadaka na masallaci har ta gama ta rufe sai kuma suka bita da ido.
Kallon Asma'u dake kwaɓa fulawa, kuka, da kanwa M Jameel Yayi yace.
“Yau kuma ɗan wake ake mana ne Asmeey?”.
Kai ta jinjina kana tace.
“Eh dan naji jiya Yaya Moddibo nacewa ɗan wake mukayi ne shiyasa yau nace bari ayi”.
Murmushi Moddibo yayi ya mai binta da wani irin amintaccen yace.
“Kai kin kyauta mun kuwa, kwana biyu bamuci ba inaga tunda azumi ya kama kamar baku yimana shiba”.

Kallonsa Asma'u tare da ce wa.
“A'a munyi amma ranan baka ciba agidan Ummi kuka sha ruwa ranan”.
Jinjina kai yayi yace.
“Toh yau kam Insha Allah zamu dawo muci ɗanwaken nan”.
Murmushi tayi ta na jefa É—an waken da cokali tace.
“Allah ya dawo daku lafiya”.
Ameeen suka amsa kana suka mayar da Kallonsu kan Innayi dake musu gashin Zabbi sai tashin ƙamshi yake.
Idanu M Jameel ya lumshe yace.
“Innayi zamu wuce”.
Da murmushi afuskarta ta kallesu tace.
“Ubangiji Allah ya tsare”.
“Ameen”,Suka amsa sannan suka fice atare kai tsaye masallacin Juma'ar da suke limancin suka nufa cike da nutsuwa da kuma kamala suka gabatar da tafsirin Alkur'ani acikin Suratul Zariyat yayin da Moddibo ke jan baƙi M Jameel na tafsiri ƙarfe shida dai-dai suka tashi.

Anutse suka fito daga cikin masallacin suka shiga mota akuma dai-dai lokacin wayar M Jameel ya hau ruri cike da nutsuwa ya gyara zamansa tare da ciro wayar daga aljihun sa Sunan Abban sa ke yawo a screen É—in kallon Moddibo da idanunsa ke lumshe yayi yace.
“Kaga Abba ke kira”.
Ya ƙara sa maganar tare da Amsa kiran yakai kunnensa tare da cewa.
“Assalamu Alaikum”.
Daga ɓangare Abba yace.
“Wa'alaikum Salam Babana”.
M Jameel Yayi murmushi tare da cewa.
“Na'am Abba na”.
Gyaran murya Abba yayi kana yace.
“Nikam laifin me mukayu mukune da kai da Moddibo da baza kuzo mu samu ladan baku buɗa baki agidan nan ba”.
Murmushi M Jameel Yayi yace.
“Ayyah Abba na laifin me zaku mana mukam a duniyar nan gama A.J ɗin yana jinka”.
ĆŠan Matsawa kusa da M Jameel É—in Moddibo yayi kana yace.
“Abbah mai zaku mana A duniya ko kun yi mana abu baza muyi fushi da kuba waye zaiyi fushi da iyayensa?”.

Murmushi Abba yayi yace.
“Toh tun da akayi azumi baku zo kunsha ruwa a gidan nan bafa, abin yana damuna yau fa kwana goma sha uku kenan da baku zo kunsha ruwa agidan nan ba fa”.

Dariya M Jameel Yayi yace.
“Abba ka dai manta mun zo ranan da akayi azumi biyar agidan muka sha ruwa fa”.
Gyara zaman wayar Abba yayi akunnensa kana yace.
“To ai bana nan ba asha ruwan dani ba yau dai so nake kuzo musha ruwa tare”.

Gyara zama Moddibo yayi yace.
“Abba baza mu bari sai gobe ba?”.
“A'a yau nakeson ganinku kuzo musha ruwa anan”.
Cewar Abba.
Jingina kai Moddibo yayi tare da lumshe idanunsa kana yace.
“Toh shikenan Abba zamu zo insha Allah amma bari mu fara zuwa gida”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.
“A'a karfa ku makara kuzo komai ya kammala ku kawai ake jira ga kun lokacin ya ƙarato”.
Atare suka haÉ—a baki wajen cewa.
“Toh shikenan Abba ga munan zuwa”.
Kallon Moddibo M Jameel dake Driving Yayi kana yace.
“Muje?”.
Moddibo kuwa Idanunsa dake lunshe ya buÉ—e yace.
“Eh muje mana J”.
Kai M Jameel ya gyaɗa kana ya juya akalar motar zuwa Unguwar su Abba ba abinda ke tashi acikin motar face ƙira'ar Alkur'ani acikin Suratu Yusuf tare da Sanyayyar ƙamshin tularensu, Wayar Moddibo dake gaban aljihu ne ya hau ruri Anutse yasanya lallausan tafin hannunsa mai zagaye da gashi ya ciro wayar tare da kallon sunan mai Kiran Malam Arɗo amsa kiran yayi tare da kai wa kunnensa.
Daga ɗaya ɓangaren Malam Arɗo yayi gyaran murya kana yace.
“Wai kai baza kazo kasha ruwa agidana ba ko sau ɗaya ne Moddibo?”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi tare da shafa kwantaccen Sajensa kana yace.
“To Malam ka gayyace mune ai baka gayyace mu shan ruwa ba”.
Da sauri Malam ArÉ—o yace.
“To na gayyace ku xo yanzu”.
Girgiza kai Moddibo yayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login