Showing 63001 words to 66000 words out of 176046 words
gyara kayansu da Raudat ta burkitasu.
Siririn tsaki ta saki tare da kallon tulin kayansu dake burkice kamar basu taɓa ganin ninkiba bare guga stool taja ta zauna tana ninke kayan.
Acan falo kuwa yunƙurawa Mommy tayi da faɗin.
“Bari na ɗauko Plate".
Da sauri Hajiya Bunayya ta mike tare da cewa.
“A'a bari na ɗauko Miki”.
Ta Faɗa tare da shiga kichen ɗin.
Ita kuwa Mommy murmushi tayi aranta tana jinjinawa ƙaunar da Hajiya Bunayya ke nuna mata tabbas samun irinta acikin kishiyoyi sai antona.
Hajiya Bunayya kuwa nashiga kichen ta fashe da dariya mai ɗan sauti tace.
“Shegiyar mata zaki ci Ubanki atunaninki har ƙasan raina nake sonki”.
Sai kuma ta sake tun tsirewa da wata dariya mai sauti can ƙasa, kana ta ɗauki cup ta zuba mata Tea kana ta ɗauki Plate da spoon ta fita.
Miƙa wa Mommy plate ɗin tayi tare sa faɗin.
“Naga kamar kwana biyu bakyajin daɗi”.
Ya mutse fuska Mommy tayi kana tace.
“Wallahi kuwa gaba ɗaya bana jin daɗin jikina wannan karon kuma da laulayi sosai yazo min”.
Cike da tausayawa Hajiya Bunayya tace.
“Ayyah sannu Ubangiji Allah ya inganta”.
Aranta kuwa cewa tayi Allah ya tarwatsa matsiyaciya.
Ita ko Mommy tace.
“Ameen ya Allah”.
Miƙewa Hajiya Bunayya tayi tare da ɗaukan Plate din ta ɓude perpesoup ɗin dake tururi yana tashin ƙamshi ta zubawa Mommy tare da miƙa mata da kofin shayin.
Lumshe idanu tayi sosai ƙamshin ya bugeta, a take yawunta ya tsinke abinka da mai cike lokaci ɗaya taji ranta yabiya da Perpesoup ɗin hannu tasa ta amsa tare da ajiye plate ɗin bisa cinyarta kana tasa spoon ɗin da sauri ta ɗebo sokar hanta da rokon ta perpesoup ɗin takai bakinta.....!
*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA
_By_
*GARKUWAN MARUBUTA*
[19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇
*SAKAYYAH*
_Page 11_
_NA_
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*FREE PAGE fa ya kusa ƙarewa*
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine wannan Free page ne ƴar uwa 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Sai in saki a Group ɗin.*
*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*
_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._
🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,
Cikin lumshe Ido Mommy ke cin perpesoup ɗin yayin da daɗinsa ke ratsa ilahirin jikinta,
kallonta Hajiya Bunayya dake murmushi tayi tare da ɗiban romon da cokali takai bakinta kana ta buɗe Idanunta dake lumshe.
Tace.
“Gaskiya Yaya Nagode wallahi bakiji yanda naji daɗin Perpesoup ɗin nan ba, dama sai tunanin a binda zanci nake tuntuni sai kuma gashi Allah ya kawo ki”.
Murmushi mai cike da Ma'anoni Hajiya Bunayya tayi kana ta muskuta tare da gyara zamanta tace.
“Lallai de kam aidama sanyin nan saida abu mai ɗumi da ɗan yaji-yaji”.
Yayin da aƙasan ranta wani irin farin cikine mara misaltuwa wanda har yakasa ɓoyuwa asaman fuskanta.
Ita kuwa Mommy Sosai take cin perpesoup ɗin tana mai lumshe Idanunta yayin da daɗin sa ke ratsa har ƙwaƙwalwar kanta tace.
“Yaya perpesoup ɗin nan yaji kayan yaji”.
Dariya Hajiya Bunayya tayi tace.
“Dama Alhaji nayiwa nace bari na zubo miki dan nasan zaki ji daɗin sa”.
Kai Mommy ta gyaɗa da faɗin.
“Aikam gashi yamin daɗi sosai”.
Acan ɗaki kuwa miƙewa tsaye Khausar tayi daga kan stool tare da riƙe ƙugunta ta bayan ta gama nin ke kayan asaman laɓɓannta ta furta.
“Wash Allah!, Gashi yanzu na gama gyara kayan nan, amma Raudat na zuwa ɗaukan abu ɗaya zata wargaza shi kab, ya zama kamar ba'a taɓa gyarashi, amma Insha Allah next time, Idan ta ƙara har gitsashi, sama Zan mayar dan kayanta, ta yanda idan tazo baza ta iya ɗauka ba sai ta kirani in bata yafiye min sauƙi”.
Ta Ida maganar tare da fitowa falon tana riƙe da ƙugunta da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke dafe asaman wuyanta.
Cike da mamaki take kallon Hajiya Bunayya dake zaune yayin da Mommy ta ke shan perpesoup ɗin da kaɗan ya rage asaman Plate ɗin.
Cikin yanayin tashin hankali da razana Khausar ta ɗaga Muryanta tace.
“Mommy me kike ci?".
Anitse Mommy ta ɗago kanta dan sam batasan ta fito ba sai da taji muryanta, gyara rikon Plate din Mommy tayi kafin tace.
“Perpersoup ne ko zaki cine?”.
Ita kuwa Khausar kai ta girgiza cikin rawan murya tace.
“A'a nikam bazan ciba Mommy kekam Komai kika samu sai kinci, ba zaki tsaya ki duba ingancin sa da kuma rashin ingancin saba”.
Baki Mommy ta sake tana kallon Khausar da Mamaki.
Ita kuwa Hajiya Bunayya wani mugun Harara ta galla mata cike da tsanarta tace.
“Komai ta samu saita ci ke kin isa ki hanata cine?, Khausar!, Khausar!!, Khausar!!! ki kiyayeni fa”.
Ta Ida maganar tana dariya irin abin awasa takeyin sa, yayin da kuwa azuciyarta ba haka bane.
Ita kuwa Mommy taɓe Baki tayi tace.
“Yaya rabu da ita itama kanta kwaɗayin ya kawota ƙilan so take in bata”.
Fuska Khausar ta ɓata cike da damuwa tace.
“Wallahi nikam ba zanci ba Mommy kema Meyesa zakici, kema daga ganin abu saiki hau ci, batare da kin duba ingancin sa ba Allah ma dai yasa kinyi Bismillah”.
Dafe kai Mommy tayi tace.
“Aikuwa de Wallahi kwaɗayin sa yasa na shafa banyi Bismillah ba, Anma bari nayi.
Bismillahi feh Auwalihi Wa'ahirihi”.
Ta faɗa tare da cigaba da shan perpesoup ɗin.
Wani banzan kallo me cike da tsana Hajiya Bunayya ta watsa wa Khausar aranta tace, shegiyar yarinya, wannan yarinyar saina bi takan ta tukunna zata gane kurenta, bari dai ingama da matsalolin dake gabana”.
Ita kuwa Khausar kallon mahaifiyarta da har zuwa yanzu take shan perpesoup ɗin tayi tace.
“Wai Mommy ba zaki haƙura dasha haka ba?".
Girgiza Kai Mommy tayi kana tace.
“Kema Idan zaki ci ga shican akula Khausar ban hana kiba, amma wannan tambayoyin naki sun fara isata”.
Ƙwafa Hajiya Bunayya tayi tace.
“Ƙyaleta bare ma ni bazan bar mata ba ina kedai ya isheki?”.
Cikin sakin fuska Mommy ta gyaɗa kai tare da faɗin.
“Eh Alhamdulillah ya isheni”.
“Aiko buƙatar maje haji salla, ba zan bar matashi ba, tunda dai ke kinsha ai hikenan, idan tanaso ta biyoni ɗakina”.
Ta ida maganar tare da ɗaukan kularta ta fice bayan ta yiwa Mommy sai anjima.
Zama Khausar tayi agaban mahaifiyarta cikin raunin murya da yanayin damuwa tace.
“Mommy meyesa!?, Rayuwar nan fa ba yanda kika ɗauke ta da yanda zuciyarki take ace haka na kowa yake da munji daɗin duniyar nan fa, amma Mommy meyesa daga kawo miki abu zaki ɗauka kici yanzu kuma idan abin cutarwa ne fa?”.
Kallonta Mommy tayi cikin tsukr fuska kana cikin fushi tace.
“Khausar ki kiyayeni fa, bana son wannan baƙin halin da kike ɗaurawa rayuwarki fa. Ni bakiga ina nunawa matar nan baƙin hali ba haka zalika itama da zuciya ɗaya take zaune damu, zaman lafiya mukeyi babu kishi bare tsangoma ko hassada, amma meyesa zaki sawa ranki rashin yarda akan n
Me kike zaton zata cutar dani, babu abinda zata yimin dan haka ki kiyaye”.
Ita kuwa khausar hawaye da ya cika mata Idanunta tashiga ƙoƙarin mayarwa sabida takaici, mahaifiyarta ta ɗauki duk kan yarda da amana ta basu, amma sukuma da wannan damar suke amfani ganin sun cutar da rayuwarta.
Ƙasa Tayi da kanta kana tace.
“Shikenan Mommy Komai na faɗa miki ba zaki yarda dani ba, amma babu komai Ubangiji Allah yatsareki ya kuma kareki".
“Ameen”Mommy ta amsa a kufule.
Ita kuwa Khausar cikin mutuwar jiki ta miƙe tare da wucewa Bedroom ɗinta tana maijin wani irin zafi azuciyarta.
Da kallo Mommy tabi bayanta tana ayyana abubuwa da yawa akanta, tarasa ina Khausar ta ɗauko wannan halin baki ɗaya bata da yarda muddin Hajiya Bunayya zata kawo mata abu ko Haiydar saita tsaya tana musu tambayoyi akai, da faɗin kada suci kada suyi kaza da kaza.
Jin ƙiran sallah magriba yasa ta miƙe tashiga Bedroom ɗin ta dan gabatar da Sallah.
Aɓangaren Khausar kuwa tana shiga ɗaki ta lumshe Idanunta tare da manna bayanta da jikin ƙofa.
Hawaye masu ɗumi suka zubo mata jikinta na bata da wani makircin da Hajiya Bunayya ta shiryawa mahaifiyarta sam bata yarda da wannan perpesoup ɗin da takowo mata ba,
shin wai ma ta wani hanya zatabi ta fahimtar da mahaifiyar?.
Sosai ta zurfafa acikin tunanin da take har aka shiga Masallaci sai, asannan ta sauƙe gauron numfashi tare da nufar toilet cikin nutsuwa ta ɗaura alwala kana ta fito, tare da shimfiɗa darduma duk da yanayin zullumi da take ciki bai hanata tattara nutsuwarta zuwa ga Ubangiji mabuwayi gagara Misali ba,
bayan ta sallame ta ɗaga hannayenta biyu zuwa sama kana tace.
“Ya Allah baka zalinci sannan kai ka hana zalunci atsakaninmu ya Allah baka gyan-gyaɗi bare bacci ya Allah kada ka bawa wannan baiwar taka daman cutar damu ya Allah ka kare mahaifiyata al'farma Annabi da al'ƙur'ani”.
Kana ta shafa addu'ar tana mai zubar da hawaye har aka idar da Isha'i bata fita ba saima miƙewa da tayi ta kwanta agado lamo cike da tunanin rayuwa da haka bacci mara daɗi ya ɗauke ta.
Cikin ikon Allah haka Mommy ta kwana lafiya lau batare da wani mugun abu ba, tun Khausar na jira taji Mommy tace wani wajen nayi mata ciwo ko kuma taga zubewan cikin Mommy kamar yanda Hajiya Bunayya ta faɗa taji shiru,
hakan yasa ta watsar da abin aranta yayin da Aɓangaren Hajiya Bunayya baki ɗaya kunnenta ke sauraron jin wani labari daga bakin Mommy sai dai shiru amma tace bari ta kara jira kaɗan ta gani.
Yau kwanan Mommy uku da cin perpesoup ɗin da Hajiya Bunayya ta kawo mata tana zaune a Bedroom ɗin ta cike da kasala.
Cikin rumtse idonta ta zabura tare da dafe ƙasan maranta da yayi wani masifan murɗawa ahankali ta furta.
“Wash! Allah na”.
Sai kuma ta koma ta zauna tare da lumshe Idanunta yayin da hannunta na dama ke dafe asaman maranta sai ka ta miƙe tare da fitowa falon tana takawa ahankali.
Khausar dake zaune a asaman 3sitter Jikinta sanye da half gownt na bacci yayin da ta tura tulin sumar kanta acikin hular Net Idanunta na kan takardan Geography dake riƙe ahannunta yayin da Nahawu ke ajiye gefe ta ɗago manyan Idanunta ta zubasu akan Mommy dake ya mutse fuska alamar bata jin daɗin jikinta, zama tayi akan 1 sitter kana a hankali tace.
“Khausar har yanzu baki shiga ba?”.
ta ida mgnar tana mai cije lips ɗinta.
Ita kuwa Khausar kai ta gyaɗa mata tace.
“Eh Mommy karatu nakeyi, gobe Idan Allah ya kaimu zamu fara Exam ɗin First term, lokacin ai ya tafi amma Mommy lafiya na ganki haka?”.
Ta ƙare mgnar tana kafe mata ido.
Ya mutse fuska Mommy tayi tare da lumshe Idanunta still cikin na damƙarta tace.
“Wallahi cikina ke ɗan min ciwo Khausar”.
Cike da tausayawa Khausar tace.
“Cikin ki kuma Mommy?”.
Kai Mommy ta gyaɗa tace”.
“Eh”.
Ita kuwa Khausar ajiye takardan hannunta tayi tare da tsirawa mahaifiyarta ta Ido cikin tausayawa tace.
“Mommy kodai in faɗawa Abba Azo atafi Asibiti ne?".
Kai Mommy ta girgiza kana tace.
“A'a ai beyi tsanani har haka ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da sauƙe numfashi tace.
“Toh Allah ya sawwaƙe”.
Mommy da hannunta ke dafe asaman cikinta still Idanunta na lumshe tace.
“Ameen”
Miƙewa Mommy tayi ta koma kan 3sitter ta kwanta kamar minti biyu da kwanciyarta ta sai kuma sake miƙewa ta zauna tana yamutse fuska.
Ita kuwa khausar cikin yanayin damuwa tace.
“Sannu Mommy kode in Kira Abba ne?”.
Girgiza kai Mommy ta kumayi sannan tace.
“A'a tashi ki koma ɗaki nima yanzu zan shiga na kwanta”.
Girgiza kai Khausar tayi tace.
“A'a Mommy Zan zauna dake”.
Lumshe idanu tayi tare da cije laɓɓanta na ƙasa tace.
“Kada ki damu kije ki kwanta na faɗa miki naji sauƙi kuma nima yanzu zan shiga na kwanta”.
Cikin sanyin jiki ta mike kana tace.
“Saida safe Allah yaƙara sauki”.
Mommy ta amsa da “Ameen”.
Ita kuwa Khausar tana shiga ɗaki ta zube akan gadonta tare da faɗa wa duniyar tunanu, a haka bacci ya ɗauke ta kasancewar dare yaja batayi bacci ba ga kuma gajiya.
A ɓangaren Mommy kuwa haka ta kwana cikin mawuyacin hali tare da murƙusoso cikin matsanancin ciwon ciki.
Washe gari.
Da safe bayan Khausar na idar da Sallah tayi Azkhar ta nufi ɗakin Mommy bakinta ɗauke da sallama.
Mommy dake kishingiɗe kan darduma ta ɗago kanta tare da amsa sallamar Khausar.
Kusa da ita Khausar ta tsugunna tare da riƙe hannunta tace.
“Mommy ina kwana ya cikin naki?”.
“Murmushin Ƙarfin hali Mommy tayi kana tace.
“Naji sauƙi Khausar kije ki haɗa muku abin Breakfast kada lokaci ya ƙure”.
Kai Khausar ta gyaɗa kana tace.
“Amma da sauki Mommy kodai daurewa kike yi?”.
Murmushi Mommy tayi tace.
“Eh jeki shirya muku”.
Kai ta gyaɗa sannan ta fice kai tsaye kichen ta nufa.
Tana shiga tasa ruwa kadan atukunya yanda zai wadatar mata bayan ya tafasa ta ɗan zuba mai kana ta zuba Couscous kamar minti goma ta buɗe taga ya dahu yayi sar gwanin kyau, amfanin ɗiga man kenan.
Sauƙewa tayi sannan ta buɗe fridge ta ɗauko miyan stwe da yaji naman kaza ta ɗumama sai kuma ta dauko lunch box din Raudat, Ramadan da Haiydar da kuma nata