Showing 141001 words to 144000 words out of 176046 words
motar Abba.
Cikin sauri ya ƙarasa jikin motar tare da cewa.
“Abba kaine?”.
Jinjina kai Abba yayi asanda ya ƙarasa fita daga motar kana cikin raunin murya yace.
“Eh Nine Aliyu ina tsammanin Jameelu yana nan to idan ba nan ba ina Jameelu zai je adaren nan.
Amma anya ka bin cika baya gidan Umminsa ba wasa take mana ba?”.
Girgiza kai Moddibo yayi cikin mutuwar da jiki da rauni yace.
“A'a Abba baya can tunda nayi magana da Ummi kuma yanzu da muka gama waya da kai ma na kirata nace baya can itama kuka fa takeyi”.
Cikin ruɗu da rashin sanin madafa Abba yace.
“Toh kazo muje can ɗin mu duba may be ko motarsa ta ɓaci ahanya can ya nufa”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da faɗin.
“To bari in ɗauki motata dan nasan Innayi ma bazata zauna ita kaɗai agida ba”.
Ya faɗa tare da shigewa cikin gida kai tsaye falonsa ya nufa ya ɗauki key sannan suka fito da Innayi acikin motar.
Motar Modibbo ce ta shiga gaba na Abba na biye da ita tuƙi kawai Moddibo yake amma baki ɗaya baya cikin nutsuwarsa.
Acan gidan Ummi kuwa tunda Moddibo ya sanar mata M Jameel baya gidan Abba hankalinta yayi masifar tashi ta fito coumpund ta tsaya tana kuka yayinda Asma'u da Bashir ke taya ta cikin tsanananin kaɗuwa.
Cikin rarrashi da nasiyya Malam Ahmad ke tausanta dasu Asma'u.
Cikin sauri Ummi ta ɗaga kanta ganin hasken motoci abakin gate ɗin gidan su.
Aruɗe ta kallesa tare da cewa.
“Ka kalli hasken mota Malam ko dai Jameelu ne?”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ki kwantar da hankalin ki Fatima dan Allah ki nutsu Insha Allah babu komai, ba abinda zai samu Jameelu”.
Kai ta girgiza kana tace.
“A'a to ai naga hasken mota ne”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da riƙe hannunta ganin yanda ta firgice kana yace.
“Toh bari naje na duba naga ko waye ne”.
Kai ta girgiza kana cikin raunin murya tace.
“A'a to muje dai”.
Kai ya gyaɗa tare da yin gaba kana tabi bayansa Malam Ahmad na buɗe ƙaramar ƙofa yaga motar Moddibo daf da bakin gate Dai-dai lokacin Moddibo ya buɗe Murfin motar ya fito.
Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da leƙa motar dake bayansa kana tace.
“Babana”.
Cikin sanyin murya yace.
“Na'am Ummi J bai zo nan ba dagaske?”.
Cikin muryan kuka ta girgiza kai kana tace.
“A'a bai zo bafa Babana idan yazo ya za ayi in ɓoye muku”.
Cikin mutuwar jiki Abba ya buɗe Murfin motar tare da fita kana ya kalli Ummi da hawaye ke bin kuncinta yace.
“Fatima”.
Saurin Kallonsa Ummi tayi tare da cewa.
“Abban Jameel”.
Cikin yanayin tashin hankali yace.
“Da gaske Jameelu bai zoba?”.
Kai ta gyaɗa Masa still Hawaye na bin kun cinta tace.
“Bai zoba kuma nata kiran wayoyinsa basa shiga”.
Cikintashin hankali da ruɗu suka haɗa baki wajen furta.
_“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha”_.
Cikin sanyi Moddibo ya kalli Abba da idanunsa suka sauya launi saboda tashin hankali kana yace.
“Abba mu koma ta hanyar gidaku mu duba ko dai motarsa ta samu matsala ne ko kuma yayi hatsari ne?”.
Kai suka gyaɗa cikin sauri Ummi ta juya tare da kallon Moddibo kana tace.
“Bari na ɗauko hijabina muje tare”.
Bata jira jin abinda zasu ce ba ta juya da sauri ta koma tare da ɗaukan hijabinta ta fito coumpund ɗin kallon Asma'u da Bashir tayi wanda har zuwa lokacin suna cikin ruɗani, cikin Muryan kuka tace.
“Asma'u ku kula da kanku zamu duba hanya ko Allah zaisa mu gansa”.
Cikin sauri Asma'u tace.
“Ummi zamu biku”.
Girgiza kai Ummi tayi tana tafiya tace.
“A'a ku zauna kada ku fito”.
Daga haka ta fice Malam Ahmad na ƙoƙarin ɗauko mota Moddibo yace.
“Ummi kuzo ku shiga motata kawai”,
Kai ta gyaɗa kana tashiga bayan motar kusa da Innayi.
Malam Ahmad kuwa a gaba, kana suka fara tafiya koda da irin tunanin da yake Aransa duk wani inda suke tunanin mota zai iya maƙalewa ko kuma hatsari sun duba amma babu M Jameel da motarsa babu dalilinsa har unguwar su Abba suka koma amma still Babu shi babu dalilinsa.
Cikin yanayin gajiyawa da ɗimuwa Abba ya buɗe Murfin motar ya fito kana Moddibo da sauran ma duk suka fito.
Cikin raunin murya me nuni da razani Abba yace.
“Gashi mun biyo har nan ma amma baya nan, to mu gwada zuwa asibiti mu duba ko dai yayi hatsari ne ko yaya”.
Cikin raunin murya Moddibo ya Girgiza kai kana yace.
“Abba hatsari kuma? Ai da hatsari ne da munga mota kuma da ankira mu”.
Kafin Abba yace wani abu Innayi ta kalli Moddibo tare da cewa.
“Eh muje dai asibitin saboda Kore shakku”.
Jinjina kai sukayi tare da shiga motar kana suka nufi Asibitin.
Ahankali Moddibo ya kalli Innayi kana yace.
“Toh wani asibitin zamuje kin san dai bawasu manyan asibiti muke dasu ba”.
Cikin sanyi malam Ahmad yace.
“Mu fara zuwa babban asibitin idan yaso sai mu duba sauran daga baya”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da nufar babban asibitin Abba na biye dasu.
Suna isa suka tarar da gate din asibitin arufe kasancewar har biyu tayi,sauran asibitin suka shiga zagayawa amma ko wanne arufe in sun buga an buɗe musuma in sun shiga bashi ba lbrinsa.
Cikin han zari Abba ya cewa Moddibo su nufi Private hospital ɗin Abba haka kuwa akayi.
Suna isa Moddibo ya sauƙa tare da nufar cikin Hospital kana ya tambayi Norse dake aiki ko M Jameel yazo suka ce a'a juyawa yayi ya shiga motar kana suka ci-gaba da nemansa.
Wasa gaske fa babu Jameel ba dililinsa ba motarsa, gaba ɗaya sun shiga ruɗu da zulumi gamida tsoro.
Misalin ƙarfe uku hankalin su ya kai ƙololuwa wajen tashi baki ɗaya sun cika da damuwa zuwa wannan lokacin sun tabbatar ba lafiya domin M Jameel baya yawo sannan Gembulan ba wani babban gari ne da keda charking point ba bare su kai report.
Moddibo kuwa banda tasbihi da kiran sunan Allah babu abinda yake Aransa yayin da kasala da mutuwar jikinsa ke ƙaruwa fiye da farko kana ga hadarin da zuwa yanzu yayi gangami asama da alamar ruwa na gab da sakƙowa, dan tuni aka fara yayyafi.
Abba kuwa tunda suka fito a asibiti ya kifa kansa ajikin motar zuciyarsa na bugawa da masifaffen ƙarfi cikin raunin murya yace.
“Acikin wannan daren ga hadari na kira layukan Jameeluna duka basa shiga a wannan yanayin ina Jamilu na ya shiga”.
Cikin raunin murya mai cike da karaya Modibbo ya fesar da numfashi mai zafi kana yace.
“Yanzu acikin daren nan ina J yake?.
Wani hali yake ciki?.
Wani irin yanayi yake cikin a wannan daren da kuma hadarin da yake tasowa ina J ɗina yake!?”.
Cikin ƙarfin hali Malam Ahmad ya numfasa kana yace.
“Insha Allah ba komai mu bari muga zuwa safiya abinda Ubangiji zai yi”.
Cikin tsanananin rauni Ummi ta kife kanta da jikin kujeran Motar kana ta fashe da wani Marayan kuka mai gunji”.
Cikin damuwa da kuma tausayawa Abba ya juya tare da kallon Malam Ahmad kana yace.
“Malam ku tafi gida kaima Moddibo ku koma gida da Innayi kada ruwan nan ya saƙƙo muna nan duk inda ya kamata mu duba mun duba baya nan bari mu gani zuwa safiya”.
Girgiza kai Moddibo yayi Araunane yace.
“Abba ya za ayi mu koma mu shiga cikin gida mu samu mafaka bayan bamu san halin da J yake ciki ba. Abba ina kake tunanin zamu koma mu samu nutsuwa acikin wannan yanayin bayan bamu san ina J yake ba!?”.
Kallonsa Abba yayi cike da rauni yace.
“Toh Aliyu ina zamuje mu duba?, Duk inda ya kamata mu duba mun duba sannan wayoyinsa basa shiga wannan shine babban tashin hankalina mu koma gida muyi alwala mu sanar wa Ubangiji halin da muke ciki Aliyu”.
Jinjina kai sukayi atare cike da gamsuwa da abinda yace sam tashin hankali da ruɗanin da suke ciki yasa sun kasa samun nutsuwar da zasuyi addu'a.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana yace.
“Toh Abba”.
Sannan suka shiga mota Abba yaja ya nufi gidansu cikin tashin hankali da ɗimuwa yayin da Hajiya Karima ke kuka Abba kuwa ko da kallonta ya gagara yi bare kuma ya iya lallashin ta.
Ya yinda Moddibo ya nufi gidan Ummi babu abinda ke tashi acikin motar banda sheshsheƙan Kukan Ummi ta rasa shin wani irin tunani zata yi shin ina Jameelunta yake awannan tsohon daren Akuma irin wannan lokacin.
Moddibo kuwa cikin tsananin damuwa da zulumi da macewar jiki ya cigaba da Driving har ya isa kofar gidan yayi Parking.
Fita Malam Ahmad yayi Ummi ma ta sauƙa suka nufi cikin gidan.
Ganin hasken mota yasa Bashir miƙewa da sauri tare da buɗe ƙaramin gate ɗin.
Cikin sauri Asma'u da har zuwa lokacin take zaune ta ɗago kanta tare da miƙewa ta riƙe hannun Ummi kana tace.
“Ummi Ina Yaya Jameel Ummi kunga Yah Jameel?".
Cikin sanyi Ummu ke jujjuya mata kai.
Ita kuwa a ɗimauce tace. “Ummi to ina yashiga awannan daren dubi hadari fa wani hali yake ciki?”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da fashewa da kuka kana tace.
“Ban saniba Asma'u Bansan inda Jameelu na yake ba, bansan halin da yake ciki ba Asma'u zuciyata zafi take jinake tamkar kaina zai rabe gida biyu!”.
Aruɗe Asma'u tace.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_, nashiga uku Yah Jameel”.
Cikin sauri Malam Ahmad ya riƙe hannun Asma'u ganin kamar bata hayyacinta kana yace.
“Subhanallah Asma'u da iliminki kike kirawa kanki shiga uku kada ki sake haka Addu'a ya kamata mu masa kunji ko?”.
Kallonsa ya mayar kan Bashir kana yace.
“Kuzo mushiga muyi masa addu'a ayanzu ba kuka Jameelu yake da buƙata daga wajen muba face adduoi”.
Kai suka gyaɗa sannan ya sake hannun Asma'u ya riƙe na Ummi Bashir kuma yarike hannun Asma'u suka shiga ciki kai tsaye ko wannensu toilet yashiga ya ɗaura Al'wala kana ya fito suka shimfiɗa Sallaya tare da fara jera nafillah suna roƙon Allah daya fitar da M Jameel aduk halin da yake ciki.
Moddibo kuwa suna isa gida yayi Parking tare da rufe ƙofar kana ya wuce falonsa yayin da Innayi ma tashige sashen ta yana shiga kai tsaye toilet dake falon ya shiga ya ɗaura alwala kana ya fito ya shimfida Sallaya cike da nutsuwa ya fara Sallah kana duk sujjadar da zaiyi sai ya roƙi Ubangiji ya kare J ɗin sa aduk inda yake”.
Baki ɗaya su haka suka raya wannan daren cike da bautar Ubangiji tare kuma da rokon Allah daya bayyanar da M Jameel kana Allah yaraba sa da duk kan sharrin Mutum da Aljan.
Bayan an kira Assalatu Moddibo ya fito ya nufi masallaci ana idar da sallah kai tsaye gidan Abba ya nufa.
Yana isa kiran Ummi na shiga wayarsa ciki. Sanyin jiki ya ɗaga wayar tare da kaiwa kunnensa kana yayi Sallama.
Cikin dashashshiyar murya Ummi ta amsa Sallamar sa kana tace.
“Babana ya labarin Jameelu na?”.
Cikin sanyin murya yace.
“Ummi nima gashi yanzu nazo wajen Abba naji ko ya dawo gida”.
Dai-dai lokacin Abba ya buɗe gate ya fito ganin Moddibo tsaye yasa ya isa wajensa ahankali Moddibo ya zare wayar daga kunnensa bayan yace anjina zai kirata.
“Aliyu dama yanzu zanje wajenka”.
A hankali Modibbo yace.
“Abba to yanzu ya zamuyi”.
Numfashi Abba ya fesar tare da cewa.
“To mu tafi police station Jiya Baki ɗaya ba muyi tunanin zuwa can ba”.
Kai Moddibo ya gyaɗa kana suka shiga motarsa yaja Abba kuwa jingina da jikin kujera yayi baki ɗaya zuciyarsa ta tushe ya rasa wani irin tunani zaiyi yayin da Idanunsa suka tsats-tsafo da ruwan hawaye.
Moddibo kuwa Driving yake amma baki ɗaya baya fahimtar komai ko gilmawar mutum ya gani sai yaga kamar J ɗin sane.
Suna isa yayi Parking atare suka fito daga motar tare da shiga station din Dpo dake ƙoƙarin fita yayi Murmushi tare da cewa.
“Alh Bashiru maidala Barka da zuwa kaine da kan ka?”.
Jinjina kai Abba yayi kana cikin sanyin murya yace.
“Na kawo report ne ɗana Jameelu ne bamu ganiba”.
Cike da mamaki da kuma al'ajabi Dpo da sauran folisawan suka ce.
“Ɗan ka Jameelu kuma?”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Eh tun jiya ba agansa ba kuma babu motarsa sannan akira layukan sa basa shiga”.
Cike da jimami Dpo yace.
“Subhanallah Alhj mai yasa baku kawo report tun dare ba!?”.
Numfashi Abba ya fesar kana yace.
“Yanayin hadari ne sannan baki daya hankalin mu baya Jikin mu sai mukayi tunanin bari muyi addu'a mu kaiwa Ubangiji kukan mu”.
Daga nan yayi miki bayanin dukkan abinda ke tafiya.
Kai Dpo ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan Alhj insha Allah yanzu zamu kira hedquater mu na cikin Taraba afaɗa musu halin da ake ciki”.
Kai Abba ya gyaɗa kana yace.
“Toh shikenan mun gode”.
Moddibo kuwa tun da suka shiga ya jingina da jikin bango Ya Lumshe Idanunsa yana motsa laɓɓansa alamar tasbihi bai ce komai.
Wunin wannan ranan baki ɗaya haka gidaje uku sukayi sa cikin zullumi,fargaba da kuma tsantsar tashin hankali Moddibo kuwa duk bayan minti biyu sai ya kira Number M Jameel aƙalla daga Jiya da daddare zuwa yau ya kira wayarsa yafi sau ɗari.
Acan ɓangaren Ummi ma haka yakasance bini-bini zata kira layin sa amma amsar ɗaya ake basu shine Switch off.
Haka zalika Abba time to time zaiyi try number M Jameel amma akashe Wunin wannan ranan baki ɗaya sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasancewa suna cikin tsananin tashin hankali da ɗimuwa duk inda ya kamata su nema ko su bincika duk sun nema sun bincika amman ba lbri.
Abba kuwa zama yayi afalonsa tare da kira duk wani danginsa ko kuma abokin arziki ko zaiji Jameelu yaje amma kowa amsa ɗaya yake basa baije ba.
Haka zalika Ummi baki ɗaya ta kira danginta ko M Jameel yaje amma suma dai amsar ɗaya ce baije ba.
Wunin wannan ranan har dare babu M Jameel babu labarin sa zuwa wannan lokacin tsananin tashin hankali da ruɗun da suke ciki ba zai misaltuba.
Da daddare Misalin ƙarfe goma Moddibo ne zaune a falon Abba kansa aƙasa yayinda idanunsa suka kaɗa sukayi ja jawur kana jijiyoyin kansa sun tashi sunyi ruɗu ruɗu rabonsa da bacci tun daren shekaran jiya haka zalika yauma koda runtsawa ne yakasa kana ya sanya duka hannunsa biyu ya dafe kansa dashi zuwa lokacin baki ɗaya ya kasa control ɗin kansa kife kansa yayi ajikin kujera tare da fashewa da kuka mai gunji.
Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da karkarwa yace.
“Abba ina J yake? Abba ina J ya tafi ya barni Abba wani hali J yake ciki?”.
Hajiya Karima ce tashigo falon bakinta ɗauke da Sallama tare da kallon Moddibo dake kuka tamkar ƙaramin yaro lumshe Idanunta tayi tare da cewa.
“Haba Aliyu kuka kuma kai da ya kamata ka tausashi Mahaifinsa sannan kuma ka zauna zakuyi ta kuka atare kenan?”.
Karo na farko kenan arayuwar data yi masa magana cikin taushin lafazi.
Ahankali Moddibo ya ɗago kai ya kalleta still yana kuka yace.
“Aunty Karima ina J yake Ina J ɗina yashiga ya barni?”.
Cikin rauni Abba ya ɗago idanunsa da hawaye ke zuba Akuma dai-dai lokacin wayar Abba ta ɗauki ruri yana ɗagawa yaga number ce ba suna sai ya mayar ya ajiye.
Kallonsa Moddibo yayi tare da faɗin.
“Abba waye ne?".
Ciki Sanyin Abba ya kalli wayar kana yace.
“Numbar ce ba suna”.
Cikin muryan kuka Moddibo yace.
“Toh Abba ka ɗaga mana ko za'a faɗa mana anga J ne”.
Cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da cewa.
“Assalamu Alaikum”.
Daga ɗaya ɓangaren cikin wata bauɗaɗɗiyar murya aka amsa da.
“Wa'alaikum Salam kaine Alhaji Bashiru Maidala mahaifin Malam Jameelu?”.
Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da miƙewa tsaye kana yace.
“Eh nine mahaifin Jameelu”.
Cikin sauri Moddibo ya miƙe tsaye,
itama Hajiya Karima cikin sauri ta miƙe tsaye.
Gyaran murya yayi kana yace.
“Toh Jameelu yana wajen mu”.
Cikin rawan baki Abba yace.
“Jameelu yana wajen ku yana cikin halin lafiya? To a ina kuke?”.
Kai tsaye yace.
“Eh gashi ma kaji muryarsa”.
Ya faɗa tare da miƙawa M Jameel wayar.
Cikin sauri Abba yace.
“Jameelu”.
M Jameel kuwa cikin wata raunan'niyar murya me cike da galabaita da tashin hankali kamar wanda yayi kuka yana sauƙe ajiyar zuciya yace.
“Abbana”.
Cikin rawan jiki da rauni Abba yace.
“Na'am Jameelu Meye sameka?,Aina kake?”.
Ajiyar zuciya mai nauyi M Jameel ya sauƙe cikin rauni da yanayi wahala yace.
“Abba nima ban sani ba bansan inda nake ba Abba ina A.J”.
Cikin muryan kuka Abba ya kalli Moddibo da jikinsa ke rawa kana yace.
“Gashinan".
Ahankali M Jameel dake sakin ajiyar zuciya yace.
“Abba ka bashi wayar”.
Miƙawa Moddibo wayar Abba yayi cikin sauri Moddibo ya amsa tare da mannawa akunnensa kana Yace.
“Jyyyyyy”,yaja sunan cike da taraddadi.
Fesar da numfashi M Jameel Yayi tare da cewa.
“AJ”.
Cikin yanayin rauni da tausayawa ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“J ina kake?”.
Girgiza kai M Jameel Yayi kana yace.
“AJ ban sani ba bansan inda nake ba, ban san ida suka kawoni ba”.
Cikin sauri aka Fisge wayar daga hannun M Jameel kana cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya akace.
“Ka bawa mahaifinsa waya”.
Ahankali kuma cikin sanyi Moddibo yace.
“Waye kai ina J yake?”.
Cikin wata razananniyar tsawa yace.
“Kabawa mahaifinsa waya ba da kai muke son magana ba?".
Moddibo kuwa Girgiza kai yayi kana yace.
“Toh me kuke so ku faɗa min ko mameye”.
Cikin sauri Abba ya janye wayar daga kunnensa tare da sa wayar a handsfree kana yace.
“Gani mahaifin Jameelu".
Daga ɗaya ɓangaren mutumin yace.
“Jameelu yana hannunmu bawai mun sace sa dan mu kashe sa ko wani abu bane amma idan kuka yi mana taurin kai zamu iya kash”...
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci ba haƙƙin wani a kanki 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA. Sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276*
*By*
*GARKUWAR MARUBUTA*
[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin SAKAYYAH na kuɗine ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, sai in saki a Group ɗin*
“Idan har kana son rayuwar ɗanka to.
Kabi sharaɗin mu kabi tsarinmu, sannan kabi dukkan dokokin, muddin kana so Jameel ya rayu idan kuma ka kuskura kayi mana taurin kai kayi mana gardama kan sharuɗan da muka ginda ya maka to zakaga abinda zai biyo bayan gardama”.
Cikin tsanananin kaɗuwa Abba ke girgiza kai yayin da bakinsa ke rawa ya gaza furta komai.
Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya mutumin ya cigaba da cewa.
“Dama kai tsaye mu aikin kashe sa aka bamu. Toj amma saboda nagartansa da mutuncinsa yasa mukaji bama buƙatar kashe Malam Jameelu munfi ɓuƙatar abada kuɗi musakeshi domin shi Jameelu na kowane, kauda irinsu a doron kasa asarace data shafi, dukkan