Showing 159001 words to 162000 words out of 176046 words
yayi tare da girgiza kai kana yace.
“A Malam ayi haka”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.
“Asiyar Moddibo menene Jameelu baiyi mana ba aduniyar na, kasancewar sa atare damu shiyafi mana komai”.
Ahankali Ummi ta ɗago kanta tare da tsira masa ido hawaye na bin kuncinta ta sani fili dai filinsa ne halalinsa mallakinsa, amma baki ɗaya ginin dake ciki Jameel ne ya musu bayan yasa an buge tsohon ginin taɓon.
Girgiza kai tayi cikin rauni tace.
“A'a ba sai anyi haka ba bari muga abinda Mahaifinsa zai samu”.
Girgiza kai Malam Ahmad yayi tare da kallon Asma'u da Bashir da har zuwa lokacin suke kuka a hankali ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ni dai na sadaukar da wannan gida ga.
Jameelu wallahi na yafe masa shi duniya da lahira na amince asa shi akasuwa muddin za a samu masu siya, to asa shi akasuwa mu samu muga aƙalla dai awajen mu ace an samu Million goma kuɗin zaifi gwaɓi”.
Sun kuyar da kai ƙasa Ummi tayi hawaye masu masifar zafi suka zubo mata.
Hannunta Moddibo ya riƙe cikin sanyin murya yace.
“Ummi dan Allah ki daina wannan kukan idan kina kuka muku ma ya zamuyi Ummi babu abinda J ke buƙata awajen mu face addu'a ganin ki awannan yanayin naya sake raunatamana zuciya”.
Kai Malam Ahmad ya gyaɗa kana yace.
“Sosai ma wannan kukan da kike Fatima saidai ya haddasa miki wani ciwon amma babu amfanin da zaiyi dan Allah ki daina ki cigaba da yi masa addu'a. shi kansa ba zaiso ace kina masa kuka ba”.
Kai ta gyaɗa tare da share hawayen ta kamar yarinya kana tace.
“Na daina Insha Allah zan cigaba da yimasa addu'a Ako da yaushe”.
Saida Moddibo ya tabbata ta daina kukan kafin ya mata sallama ya fice cike da tausayinsu Driving yake ahankali har ya isa gida yayi Parking kana ya fito ya rufe gate din tare da wucewa sashen Innayi bakinsa ɗauke da sallama.
Kwance ya samu Innayi cikin Yanayin damuwa gefenta da Radio tana sauraro wanda ɓatan M Jameel ake sanarwa.
Miƙewa tayi ta zauna tare da amsa Sallamar sa kana tace.
“Moddibo ya labarin Jameelu?”.
Cikin sanyin murya yace.
“Innayi sun sake kira ɗazu”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da cewa.
“Toh kunyi magana dashi yana cikin ƙoshin lafiya?”.
Girgiza mata kai yayi kana yace.
“A'a Innayi bamuyi waya dashi ba amma bisa duk kan Alamu J baya jin daɗin zaman wajen can”.
Ahankali Innayi ta jingina bayanta da jikin bango kana ta matsar da Radio gefe tare da cewa.
“Dama Moddibo ya za ayi yaji daɗin zaman wannan wajen. kasan yanayin da yake ciki ai dole bazai ji daɗin zaman wannan wajen ba amma me suke buƙata?”.
“Innayi kuɗi suka nema”.
“Kuɗi suka nema to aisai abasu aje a karɓe shi”.
“Innayi kuɗin da suka nema na fitar hayyacine!”.
“Kuɗi har nawa suka nema? Da zai zama na fitar hankali”.
Dafe goshinsa yayi kana yace.
“Innayi Million ɗari biyu suka nema kuma cikin ƙanƙanin lokacin fa”.
Ita kam Innayi baki ɗaya lissafin ta sincewa yayi jin maƙudan kuɗin tama rasa nawane, kallon Moddibo tayi tare da cewa.
“Dubu ɗari biyu?”.
Kai Moddibo ya Girgiza tare da cewa.
“A'a ba dubu ɗari biyu bafa Million fa Million ɗari biyu”.
Daga kanta sama tayi alamar tunani sai kuma ta kallesa tare da cewa.
“Million biyu?”.
Still girgiza mata kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Million ɗin goma, ashirin, hamsin, ɗari, ɗari da hamshin har ɗari biyu”.
Dafe kirji tayi kana tace.
“Million ɗari biyu?”.
Jinjina mata kai Moddibo yayi.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ban gane lissafin ba Aliyu”.
Lips ɗinsa duka biyu ya cije a lokaci guda kana yace.
“Ba zaki gane lissafin ba Innayi kuɗi ne masu tarin yawa suke nema”.
Cikin sanyin murya Innayi ta jujjuya kanta kana tace.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n Hasbunallahu wani'imal wakin Layukalliful nafsi illa wusɗaha_
Toh yanzu mai Baban nasa yace?”.
“Innayi Abbansa bashi da wannan kuɗin a ƙasa kwanan nan dama ya gama yi mana ƙorafi bashi da kuɗi”.
Lumshe idanu Innayi tayi kana tace.
“Ya Salam ya Ubangiji Allah ka dube mu da idon rahama, ya Allah ka yayemana ya Allah ka sauƙaƙa mana ya Allah ka tsare Jameel ka kare mana shi, Allah ka tseratar da wannan bawan naka”.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Ameen”.
Kallon second biyar zuwa bakwai Innayi ta yiwa Moddibo kana tace.
“To amma kai Moddibo mai kake ganin zakayi akai?”.
Still hannunsa na dafe akansa yace.
“Innayi akwai kuɗi awajena zan tattara su in haɗa su muga nawa za'a samu awajena”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Yafi kam”.
Bayan sun sake tattauna ne Moddibo ya miƙe tare da yi mata Sallama kana ya nufi Sashen sa ahankali ya tura Murfin Kofar shiga tare da mayarwa ya rufe.
Kana ya jingina bayansa da jikin da kofar tare da rintse idanunsa sautin murya M Jameel ya farayi masa kai-komo AJ bansan idan nakeba,
Lumshe danunsa yayu zuciyarsa na bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dif-dif cikin sauri ya buɗe Idanunsa jin muryan M Jameel na yawo a kansa yana cewa A.J A.J Kallon kan 3sitrer kurui ji yake kamar zaiga J dinsa a wurin, cikin raunin murya yace.
“J Why are you?, Zuciyata zata fashe ya Allah kaji ƙaina ya rabbil Izzati ka dawo da J garemu cikin aminci da salama ya Allah kada ka bawa waɗɗanan azzaluman daman cutar dashi”.
Ya kai 15 minutes yana mai jero Addu'o'in cike da rauni, kafin ya miƙe kamar wanda aka mitsina ya nufi Bedroom ɗin sa kai tsaye toilet ya shiga ya watsa ruwa kana ya ɗaura alwala ya fito ya kwanta bisa gadonsa yayi rigingine duk da yasan cewa da wuya bacci ya ɗauke sa amman ya lumshe idonsa domin yau kwana uku rabon da ya samu wani wadataccen bacci sai wani irin azabebben ciwon kai da yakeji tamkar kansa zai rabe da ga wani irin sarawa da yakeyi yana bada wani irin sauti mara daɗi gau-gau-gau!.
A hankali ya bude idon sai kuma yayi saurin
Lumshe Idanun sabida sarawa da kan yayi masa.
Cikin zazzaƙan muryansa mai cike da rauni ya fara raira ƙira'ar Suratul Yusuf hawaye masu ɗumi suka riƙa fita daga idanunsa suna shiga kunnensa cikin wannan yanayin da cikar Sa'adatu da karatun Alqur'ani mai girma ya samar masa, wani irin kiɗimemmen baccin da bai shirya masa ba ya sace sa.
Acan cikin baccin sa kuwa zaune ya hangosa akan wata.
Tattausan shimfiɗa cikin wani masha'hurin falo mai masifar kyau da ƙawa.
Sai dai kima yana ta dariya hartada karketawa, yayinda idanunsa kuma sunyi jawur jikinsa na rawa jin.
A hankali ya fara jujjuya kansa yana mai ci gaba da dariyar ya juyo kansa gabansa, jin alamar tafiya tare da wani ƙamshi daya ratsa hancinsa yasa ya ɗaga manyan idanunsa da sukayi luhu-luhu ya sauƙe ganinsa akan Khausar dake zuwa garesa cikin wata iriyar ƙasaitacciyar shiga, ido ya zira mata ko ƙebtawa bayayi har ta isa garesa, a hankali ta zauna gefensa.
Tare da tsira masa manyan Idanunta masu haske wanda ke ciki da ruwan hawaye kana ta miƙa masa wani hankief fari ƙall mai masifar ƙamshin turare.
Ƙin karba yayi saima lumshe idanunsa da yayi wanda sai lokacin ya samu wasu irin tafasassun hawaye suka samu damar kwaranyowa, hakan yasake kawar da kansa gefe tare da sakin sheshsheƙa.
Ahankali Khausar ta matsa gabansa har suna shaƙan nunfashin juna kana ta sanya hankief ɗin ta shiga share masa hawayen cikin wata Sanyayyar murya mai cike da nutsuwa da kuma rauni tace.
“Yah Jameel Addu'ar mu yake buƙata ba kuka ba idan kai kana kuka.
Toh Ni kuma ya zanyi addu'a za muyi masa kaji ko Abu J”.
Ta ida mgnar da kiransa da sunan da ta raɗa masa, tare da faɗawa jikinsa ta fashe da sassayan kuka dai-dai lokacin kuma ya farka.
Kansa ya dafe tare da miƙewa ya shiga toilet ya ɗaura al,wala kana ya dawo ya shimfiɗa Sallaya ya fara nafillah yana cigaba da yiwa M Jameel addu'a.
Ba tare da yabi ta kan mafarkinba, domin yanzu kam idan da sabo ai yaci ace ya saba da yawan ziyarar kutse da nacin da Khaisar keyi masa cikin rayuwar baccinsa.
Washe gari Ummi ta tattara baki ɗaya Sarkoƙi, ta da ɗan kunnen zobe da awarwon Gwal nata dana Asma'u ta shirya ta tafi Tarata.
Tana isa kai tsaye babbar kasuwar su ta wuce kana tashiga shagon saida gwala-gwalai ta bayar aka gwada cikin sa'a ta samu sunyi farashi sosai kasancewar Manyan Sarƙoƙine nata dana Asma'u wasu nata tun tana gidan Abban Jameel ne, suka haɗa mata kuɗin ta Naira Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin sukayi mata transfer dinsu.
Daga nan gidan kai tsaye gidan Ƙawarta Hajiya Salma Wanda mijinta ke saida Motoci yawanci awajensa M Jameel ke siyan mota ko kuma can zawa.
Mai A dai-dai-tan na sauƙeta ta miƙa masa kudinsa kana ta shiga cikin tangamenen coumpund ɗin daya tsaru kai tsaye ciki ta nufa tare da Knowking ɗin ƙofar kana ta murɗa handle ɗin tashiga bakinta ɗauke da sallama.
Hajiya Salma dake zaune akan kujera ta miƙe cikin sauri kana tace.
“Hajiya Fatima sannu da zuwa ga wajen zama”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da cewa.
“Yawwa Nagode”.
Sannan ta zauna tare da sakin Ajiyar zuciya.
Bayan sun gaisane.
Cikin sanyin murya Hajiya Salma tace.
“Ayyah Hajiya ashe ga abinda ya faru da ɗana Jameel kuwa?”.
Cikin yanayin sanyin ɗaya zamewa Ummu jiki, ta gyaɗa mata kai tare da cewa.
“Ummm bari ke dai Hajia Salma duniya tayi min zafi”.
Cikin tausayawa Hajia Salma tace.
“Ba komai in sha Allah, kada ki damu Hajia Fatima.
Ubangiji Allah ya bayyanar da Jameel aduk inda yake Ubangiji ya karesa daga sharrin mai sharri”.
Cikin sanyin Murya Ummi tace.
“Ameen ya Allah ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Cike da tausayawa Hajiya Salma tace.
“Wallahi Koda wasa banji ba sai ɗazu da safe Alhj na duba jarida ya gani shine yake sanar min”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana tace.
“Allah sarki ai yanzu anshiga kwana na huɗu kenan.
Uhmmm dama nazo kiyiwa Alhj Abdallah magana ne akan ya duba motata ya siya”.
Ajiyar zuciya Hajiya Salma ta sauƙe kana tace.
“Ubangiji Allah ya tsare Malam Jameel aduk inda yake”.
ta faɗa tare da shigewa ciki tsaye ta samu mijin nata yana ƙoƙarin fita Kallonsa tayi kana tace.
“Alhj Hajiya Fatima ce ta zo mahaifiyar Malam Jameel”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Ikon Allah muna shirin zuwa kuma sai gata”.
Ya faɗa tare fitowa a tare, a inda Hajiya Salma ta barta anan suka sameta tayi ta gumi.
Ahankali Ummi ta ɗago jai tare da cewa.
“Alhj Abdallah ina kwana ya gida”.
Zama yayi kana yace.
“Lafiya lau Hajiya ashe kuma ga abinda ya faru da Malam Jameel”.
Kai Ummi ta gyaɗa kana cikin sanyin murya tace.
“Eh”.
Ajiyar zuciya Alh Abdallah ya sauƙe kana yace.
“Wallahi bamu da labari sai ɗazu ina karanta Jarida na gani nake faɗawa Salma tace itama bata da labari dake akwai wani fitar gaggawa daya kamani nace idan nadawo zan kaita da yamma ta gaishe ki”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da gyada kai kana tace.
“Allah sarki dama Motata ce nazo ka tura adauƙa maka ka ga lafiyarta zan saidata in zaka siya”.
Ɗagowa yayi tare da kallonta kana yace.
“Motar da Malam Jameel ya siya miki nan?”.
Kai ta gyaɗa masa tare da cewa.
“Eh shi”.
Zaman hular kansa ya dan gyara kana yace.
“Amma ai motar bata daɗe ba Hajiya Fatima”.
Kai ta gyaɗa Muryanta na rawa tace.
“Eh bata daɗe ba Uzurin gaggawa ne ya kama Ni shiyasa zan siyar”.
Jinjina kai yayi tare da cewa.
“Aikam dama mota ce mai kyau sannan bai daɗe da sayanta ba za tura yaro yaje ya ɗaukota kuma yanzu mugama magana tunda abu na gaggawa ne”.
Cikin sanyin murya tace.
“Tun baka gani ba”.
Girgiza kai yayi tare da faɗin.
“Baki da matsala Indai wannan ne zan baki Million shida”.
Cikin sauri Ummi tace.
“Alhj har Million Shida kuma dama motar yana da tsada kenan?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da zaro wayarsa acikin aljihu kana yace.
“Eh dama Million biyar ne haka ya siyeta toh nasiyeta biyar ɗin kamar yanda ya siya sannan Million ɗayan kuma na bada nawa gudunmawar Ubangiji Allah ya bayyana Malam Jameel”.
Ajiyar zuciya Ummi ta sauƙe tare da cewa.
“Ameen ya rabbil izzati, ngd Matuƙa".
Da sauri ta kalleshi jin yana cewa.
“Ki bani account number ki zan miki transfer”.
Kai Ummi ta gyaɗa tare da kiramasa number's ɗin.
Atake ya mata transfer.
Miƙewa tayi tare da yi masa godiya sosai kana ta fito, har ƙofa Hajiya Salma ta rakata kana ta Wuce.
Kai tsaye tashar motar Gembila ta nufa, tana zuwa kuwa tayi sa'a mutun ɗaya ya rage, haka yasa ta shiga motar ta tashi.
Alhamdulillah sun isa Gembila lfy.
A hankali Ummi ke tafiya tana jin wani irin sanyi a ranta tare da Comfedance ga Million ɗaya da dubu ɗari huɗu da dake account ɗinta ga kuma Million biyu da dubu ɗari huɗu da hamsin na Sarkoƙi kana ga Million Shida na mota ya zama tana da tsuran kuɗi ahannunta har Naira Million tara da dubu ɗari takwas kenan.
A hankali ta sauƙe wani zazzafafar ajiyar zuciya kana ta nufi gida.
Acan ɓangaren Moddibo kuwa ya haɗa duk wasu kuɗaɗe dake hannunsa ya samu Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamshin kai tsaye gidan Ummi ya nufa yana Parking ɗin motarsa mai A dai-dai-tan sahu na ajiyeta atare suka shiga falonta.
Suna shiga Bayan sun gaisa Ummi tashiga Alart massage tare da miƙawa Moddibo wayarta tare da cewa.
“Babana ka kalli kuɗi sunyi gwaɓi”.
Amsar wayar yayi tare da Kallon Alart massage ɗin kuɗin kana ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Masha Allah kuɗi sunyi gwaɓi bari na haɗa dana wajena”.
Kallonsa Ummi tayi haka nan taji hawaye na ciko mata kwarmin Idanunta.
Cikin sanyin murya Moddibo yace.
“Ummi na wurina na bashi da yawa Million huɗu da dubu ɗari biyu da hamsin ne”.
Cike da tausayinsa tace.
“Toh Allah ya biya. Babana Allah yabamu yanda zamuyi Ubangiji ya saka maka amma ka rage wani abu aciki ka samu na kashewa”.
Girgiza kai yayi cikin raunin murya yace.
“Ummi wani abu zan rage idan ina da abinda yafi wannan zan ɗauka in bayar akarɓo J naje. nayi magana da dillalai gidan mu na sashi akasuwa in dai za'a samu siyansa akan lokaci.
Cikin sauri Ummi ta kallesa tare da cewa.
“Gidan ku kuma Babana!?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Ummi Meye amfanin gidan mai zamuyi da gidan babu wani farin ciki acikisa.
Muddin J baya nan fa wanne farin ciki zamuyi. kuma komai da muka rasa zamu iya samu idan J ya dawo gare mu”.
Jinjina kai Ummi tayi, Account number dake wayarsa ya fito dashi ya mata transfer kuɗin tare da miƙa mata wayar karɓa tayi ta duba Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon kuɗin Naira Million goma sha huɗu kenan cib.
Numfashi ta fesar tare da kallon Moddibo kana tace.
“Alhamdulillah Babana kuɗi sun cika Million goma sha huɗu bari muje gidan Abban sa tare”.
A hankali yace.
“Amma Ummi ki bari sai gobe muje wataƙil yau ba zasu kira ba sai goben, amma ni yanzu idan nafi ta zanje wajen Abba muji nawa aka samu awajensa”.
Kai ta gyaɗa cikin sanyi tace.
“Toh shikenan Babana Allah yasa muji al'khairi”.
Kai ya gyaɗa tare da miƙewa kana yace.
“Amin.
Toh shikenan bari naje yanzu”.
Ya faɗa tare da ficewa.
Kai tsaye gidan Abba ya nufa bayan yayi Parking ya fito tare da shiga Falon bakinsa ɗauke da Sallama.
Abba dake zaune kan 2 sitter ya jingina bayansa da jikin kujera ya amsa masa Sallamar cike da tausayinsa ya zuba masa yana ganin yadda yake tafiya duk ya faɗa acikin kwanaki huɗu ya rame yayi shafal.
Ƙara sawa Moddibo yayi tare da zama gefensa kana yace.
“Abba ina yini ya kuma haƙurin rayuwa?”.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da cewa.
“Alhamdulillah Aliyu ya wajen su Innayi?”.
Kansa a ƙasa yace.
“Lafiya lau Abba basu sake kira ba ko?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da fesar da numfashi kana ya runtse Idanunsa cikin sanyin murya yace.
“Basu sake kira ba Aliyu”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Toh yanzu Abba kuɗi kimanin nawa aka samu awajenka?”.
Abba kuwa ahankali ya zame daga kan kushin ɗin ya zauna akan capet tare da fuskantar Moddibo kana yace.
“Aliyu na tattara duk abinda yake wajena kana duk wanda nake binsu bashi na tattarasu sannan na nemi temakon bashi duk wanda zan nemi temakonsu sunban bashi baki ɗaya kuɗin dana samu awajena Million hamsin da shida ne, iya adadin kudin dake hannu na kenan, duk ta inda zan buga na buga Aminaina ƴan uwana duk na nemi temako awajen su wasu sun bani kyauta wasu kuma aro na buga shine Million hamsin da shida”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Toh Abba kuɗi dai sun ɗanyi gwaɓi gashi awurin Ummi an samu Million Sha uku yanzu kenan muna da Million Saba'in dai-dai a ƙasa.
Ajiyar zuciya Abba ya sauƙe tare da fesar da numfashi kana yace.
“Alhamdulilah kuɗi sun fara taruwa Amma ɗari biyu fa suka ce gashi ko ɗari cikekke bamu samu ba”.
Cikin raunin murya Moddibo yace.
“Abba bari mugani idan sun sake kira sai mu rokesu su rage mana idan sun tallafa sun tausaya mana ko bashin banki ne zamu ci sai mu ƙara akai kuɗin ya cikata”.
Kallon sa Abba yayi tare da jinjina kai kana yace.
“Toh shikenan ba laifi Allah yasa mu dace”.
Ameen Moddibo ya amsa kana suka cigaba da hira har Misalin ƙarfe goma.
Abba najin ringing din wayarsa Yayi saurin zabura tare da picking kana yayi Sallama.
Daga ɗaya ɓangaren cikin bauɗaɗɗiyar murya mutumin yace.
“Alhj Bashiru ka haɗa kuɗin?”.
Cikin raunin Murya Abba ya gyaɗa kansa kana yace.
“Kuyi haƙuri bawan Allah dan Allah kuyi haƙuri wallahi kuɗin nan da kuka faɗa babu su awajena kwata kwata babu”.
Daga ɗaya ɓangaren mutumin ya juya tare da kallon M Jameel dake zaune a ƙasa kana cikin wata dakakkiyar murya mutumin yace.
“Da alama dai mahaifinka baya sonka”.
Jin muryan mutumin agefe yasa Abba saurin cewa.
“Don Allah ku bani inji muryarsa”.
Cikin wannan bauɗaɗɗiyar murya Mutumin ya wurga wa M Jameel wayar kana yace.
“Gashi kaji muryan sa”.
Cikin sauri M Jameel ya cafke wayar tare da kaiwa Kunnensa kana cikin sanyin mai cike da rauni mai tada hankalin ɗan Adam cikin murya mai cike da galabaita yace.
“Abbana”.
Cikin sauri Moddibo ya karɓi wayar a hannun Abba kana yasa a handsfree tare da danna record.
Cikin raunin Murya M Jameel yace.
“Abba kabasu kuɗin Abba dan Allah ka basu abinda suke so ka fitar dani awannan wajen mana Abbana”.
Runtse Idanu Abba yayi kana yace.
“Babana zan fitar da kai ina nan ina har haɗawa kuɗin insha Allah zan fitar da kai amma Jameelu duka-duka kuɗin da muka haɗa anan Million Saba'in ne su kuma sunce Million ɗari biyu suke so”.
Cikin wata raunan'niyar murya mai cike da masifaffiyar galabaita da neman jin ƙai M Jameel yace.
“Abba a saida motocina duka sannan aduba ɗakina akwai kuɗi amma bai cika Million biyu bama dan