Showing 117001 words to 120000 words out of 176046 words
harbawa da yakeyi.
Acan ɓangaren Gimbiya Dadu kuwa cikin sanyi jiki Khausar ta buɗe ƙofar falon tare da Sallama tana shiga ta...!
*Littafin SAKAYYAH na kuɗine ƴar uwa ki biya ki karanta cikin Aminci da salama babu haƙƙin kowa a kanki littafin 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276, kana in saki a Group ɗin da zanke posting nashi, yar uwa koda kinga LITTAFIN SAKAYYAH A WAJE TO na satane, in dai kin san baki biya kadama ki karanta.*
*GARKUWAR* taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA
*By*
*GARKUWAN MARUBUTA*
[24/07, 6:14 AM] Halimatu A/rahman Sadeeya: Isreg'o. Cikin tsananin tsoro da mamaki Baba mai gadi ya juya gabas da yamma,r kudu da arewa acikin coumpund ɗin gidan amma babu mutum babu dalilin mutum, cikin tsananin kaɗuwa da ganin wannan abin al'ajabin yace.
“Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n. Cikin abinda bai wuce second ɗaya ba ace babu rago babu dalilinsa, kuma abu ayanke bawai da ransa ba bare ace ya gudu”.
Cikin kaɗuwa ya nufi cikin gidan tare da cewa.
“Ya Ilahi mai ya faru”.
Duk ya burkice ganin abin yake tamkar mafarki dai-dai lokacin da mai gidan ƙanin Lamiɗo yake fitowa.
Aruɗe Baba mai gadi yace.
“Alhaji ragunan biyu suna ɗaure amma yanzu naga ba ɗaya”.
Kallon Mamaki Alhj Musa ya masa tare da cewa.
“A'a ragunan biyu yanzu kuma babu ɗaya ƙafa ragon yake dashi Malam Idi?.
Aruɗe Malam Idi yace.
“Wallahi tallalahi Alhj da gaske yanzu-yanzu ragonan yana nan amma yanzu ya ɓace babu shi babu dalilinsa”.
Tsayuwa Alhj Musa ya gyara tare da cewa.
“Toh ragon ƙafa zaiyi ina zai shiga?”,.
Malam Idi daya gama shiga tashin hankali yace.
“Wallahi da gaske Alhj”.
ya faɗa tare da juyawa ya fice daga gate ɗin ganin su Khausar basu yi nisa ba yasa ya saki Ajiyar zuciya tare da cewa.
“Khausar!, Khausar!! Kuzo”.
A tsorace Khausar da Asma'u suka jiyo atare kana suka haɗa baki wajen faɗin.
“Ya dai Baba mai gadi”.
Hannu ya ɗaga musu tare da cewa.
“Kuzo dai”.
Cikin rawan jiki da tsoro Khausar tace.
“Lafiya?”.
Cikin ƙasa da murya Asma'u tace.
“Mun shiga uku kad dai ya gane?”.
Da ƙarfi Khausar ta haɗiye wani abu mai ɗaci tare da cewa.
“A'a Insha Allahu ma bai gane ba”.
Suna isa bakin gate ɗin yace.
“Khausar kushigo”.
Ƙara sa shiga sukayi zuciyar su na bugawa da mugun sauri.
Kallonsu Baba mai Gadi yayi tare da kallon Alhj Musa kana yace.
“Dan Allah dan Annabi ba ragunan biyu suna nan ba, har kuka tsaya kusa dasu suna ɗaure ba?”.
Atsorace Khausar ta gyaɗa masa kai kana Muryanta na rawa tace.
“Eh”.
Da sauri Baba mai gadi ya sake kallon wajen tare da cewa.
“Kawai ina zaune fa kamar abin wasa kamar amafarki kamar a Tv naga rago ɗaya ya ɓace”.
Khausar da jikinta ya fara rawane tace.
“Ya ɓace kuma?”
Cikin tashin hankali Asma'u da Idanunta sukayi zuru-zuru ta dafe ƙirjinta tare da faɗin.
“Ya ɓace kuma dai?”.
Jinjina kai Baban mai gadi yayi tare da cewa.
“Wallahi kuwa kun fita kenan ina juyawa naga ragon nan ya ɓace Khausar abin nan abin mamaki fa ina kuma kun gansu?”.
Shi dai Alhj Musa na tsaye ya harɗe hannunsa aƙirji yana sauraransu cike da al'ajabi.
Cikin tsananin tsoro mamaki da al'ajabi da kaɗuwa gami da kiɗima Khausar ta kalli Alhj Musa kana tace.
“Wallahi kuwa Baba ƙarami muma munga ragunan nikam mafa akusa dasu na tsaya. Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n yau mun shiga uku Meye faru ya akayi haka?”.
Jin hayaniya yasa mata dake cikin gida suka fara fitowa suna tambayar abinda yafaru duk wanda yaji rago ya ɓace sai yashiga cikin mamaki da al'ajabi.
Baba mai Gadi da abin ya tsaya masa arai ya kalli mutanen dake wajen tare da cewa.
“Wallahi ganin Idona ragon nan ya ɓace ɓat kamar a Film kuma babu kowa a farfajiyar gidan Khausar suna fita abin ya faru ina juyawa naga sun ɓace ɓat!”.
Atsorace Khausar ta jinjina kai tare da cewa.
“Wallahi kuwa Muma yanzu muka gansu mun samu ragu nan nan aɗaure”.
Ana haka Mommy tashigo nan ta samu labarin rago ya ɓace nan suka shiga jajantawa.
Khausar kuwa hannun Asma'u taja suka fice bayan sun fita Asma'u ta juya ta kalli Khausar tare da cewa.
“Khausar”.
Juyawa Khausar tayi tare da haɗiye wani abu mai Masifar ɗaci tace.
“Asma'u”.
Asma'u taja dogon numfashi kana tace.
“Khausar da kece zaki ɓace fa. Innalillahi wa'inna Ilahi rajiu'n”.
Khausar kuwa da jikinta yake rawan jitayi Idanunta sun ciko da hawaye cike da alhini tace.
“Asma'u mun shiga uku”.
Cike da rawan jiki suka ƙarasa gida kai tsaye ɗakin Khausar suka nufa tare da zama a ƙasa Capet ɗin duk sunyi zuru-zuru dasu kallo ɗaya zaka musu kasan cewa suna cikin ɗimuwa da tashin hankali mara misaltuwa.
Cikin rawan murya Khausar ta kalli Asma'u tare da cewa.
“To yanzu kam Uncle Naseer me yake nufi dani? Dama tsafi zaiyi dani, kenan Uncle Naseer ma tsafi ne Asma'u? ba kingani ba dama ni sam ban yarda da shiba, tsoronsu nake dama Gimbiya Dadu ya take bare kuma ƙanwarta mun shiga uku dama tsafi zaiyi dani Asma'u shikenan da kashe ni suke sonyi?”.
Cikin raunin murya Asma'u tace.
“Khausar wannan abin ya gigita ni na rasa ta yanda zan fassara shi”.
Ta gumi sukayi yayin da zuciyarsu ta cigaba da bugawa tsoro da tashin hankali ya bayyana atare dasu lokacin ɗaya zazzaɓi ya fara dirarwa Khsusar.
Ba jimawa Mommy ta dawo kai tsaye ɗakin Khausar ta shiga tana cewa.
“Ohhh Allah mai iko an duba fa ƙasa da sama babu ragon nan babu dalilinsa an duba ko ina babu shi ya ɓace!”.
Murya na rawa Asma'u tace.
“Mommy muma fa mun gansu”.
Mommy kuwa ahankali ta maida kallonta kan Khausar da jikinta ke rawa duk ta ruɗe cike da kulawa tace.
“Khausar ya dai?”.
Kuka Khausar ta fashe dashi tare da yarfe hannu kana tace.
“Mommy zan faɗa miki Mommy zan faɗi gaskiya”.
Kallon Mamaki Mommy tayi mata kana tace.
“Meya faru Khausar?”.
Cikin kuka sosai Khausar tace.
“Allah Mommy Zan faɗi”.
Zama Mommy tayi gefensu kana tace.
“Wai meke faruwa ne Asma'u”.
Cikin ƙoƙarin tsaida hawayen Khausar ta riƙe hannun Mommy acikin nata, kana ta zayyane mata duk yanda sukayi da Naseer da kuma shawarar da Asma'u ta bata sannan ta ɗaura da cewa.
“Mommy kuma nice ɗazun na dandala ƙyallen akan wuyan ragon, har muka ji tsoro kar Baba mai gadi ya ganmu kuma Allah wanda na shafawa ƙyellen ne ya ɓace”.
Aruɗe Mommy ta saki salati tare da sanar da ubangiji.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Hasbunallahu wani'imal wakil. La'ilah ha Illah anta subhanaka Inni kuntu Minal Zhalimin. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan minha_. Ohh Khausar am nashiga uku wannan rayuwa har ina Khausar kin tabbatar?”.
Kai ta gyaɗa tare da faɗin.
“Wallahi tallahi Mommy da gaske ne”.
Ta faɗa tare da cusa hannunta ƙarƙashin gado ta ciro mata ƙyallen data ajiye da niyyar idan Naseer yazo zata bashi”.
Cikin raunin murya tace.
“Mommy kingani Mommy kin gani ko wallahi shine ƙyallen”.
Jinjina kai Mommy tayi tare da kallon ƙyallen da ƙamshinsa ke bugun kanta kana tace.
“Nashiga Uku ni Aysha wannan masifa har ina?”.
Asma'u kuwa ta gumi tayi ganin abin take tamkar almara.
Khausar na share hawaye tace.
“Mommy ina dai yanzu kin gani kinga zahiri Mommy inaga yanzu kam zaki iya yarda su Mayu neko?”.
Girgiza kai Mommy tayi cike da jimami da kuma al'ajabi ta kalli Khausar tare da cewa.
“Toh su sukayi ko shi Allah am nashiga uku ba'a shaidar halin ɗan mutum”.
Girgiza kai Asma'u tayi kana tace.
“Nikam wallahi Uncle Naseer ya bani Mamaki duk da rawan kansa ban taɓa zaton zai aikata irin wannan abin ba”.
Ta gumi Khausar tayi duk abin duniya ya isheta Hausawa sunyi gaskiya da suka ce Mutum mugun Icce.
Ganin yanda suka ruɗe da al'amari yasa Mommy dai-dai ta nutsuwarta tare da cewa.
“Kar ku damu ku cigaba da addu'a domin addu'a takobin mumunice, sannan kada ku faɗa wa kowa wannan maganar ya zama sirri atsakanin mu”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Asma'u kana tace.
“Asma'u Allah ya miki al'barka, kin cika ƙawar kirki duk inda ake neman ƙawar arziki kin kai.
Allah Ubangiji ya Al'barkanci rayuwar ku ya kuma kare ku aduk inda kuke”.
Haɗa baki sukayi wajen faɗin.
“Ameen”.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauƙe kana tace.
“Wannan magana ya zama sirri atsakanin mu, kada ku fadawa kowa daga. Ni sai ku sai kuma Ubangijin daya halluccemu shi kuma Naseer zamu ga manufarsa.
Za muga iya gudun ruwansa sannan daga yau Khausar koda ya kira ki baza ki sake zuwa inda yake ba ko dai kina son shi!?”.
Zaro ido Khausar tayi cikin sauri ta shiga yarfe hannun tare da Girgiza kai kana tace.
“Allah Mommy bana sonshi, na tsane shi bani bashi har abada, me zanyi da matsafi ni dai bana sonshi Wallahi bana sonshi”.
Kai Mommy ta gyaɗa tare da kallon su kana tace.
“Toh shikenan ki kwantar da hankalin Allah ya tsare ku ya muku zaɓi da maza na gari, wannan ma ai addu'a ce tasa asirinsa ya tonu Allah ya ƙara tsaremu baki ɗaya ku kara riƙo da addu'a in sha Allah duk sharrin mai sherri sai dai yaga gadon bayanmu”.
Atare suka amsa da.
“Ameen”.
Haka dai akayi suna aka watse kowa na al'ajabi da ta'ajjadin ɓacewar ragon suna.
Acan gidansu Moddibo kuwa M Jameel zaune tare da Innayi Moddibo kuwa na tare da Malam Arɗo bai dawo ba.
Anutse M Jameel ya ɗago kansa tare da kallon Innayi dake zaune ta tanƙwashe ƙafafunta cikin sanyin murya yace.
“Innayi”.
Ahankali ta ɗago kanta tare da cewa.
“Na'am”.
Ajiyar zuciya M Jameel ya sauƙe kana yace.
“Innayi ni ko badan kar kice ina bincikar ki da tuhumar kiba.
Da zance da Allah Innayi ina ne asalin ƙasar ku tunda nan dai garin naji labarin zuwa kuka yi dan Allah Innayi ki faɗa min inane asalin garinku sannan, wai kwata-kwata mahaifin A.J bashi da dangi ne? Sannan Ina dangin Mahaifiyarsa”.
Ido Innayi ta tsira masa tana jin bugun zuciyarta na ƙawura.
M Jameel kuwa cigaba yayi da cewa.
“Sannan dan Allah kiyi haƙuri kada ranki ya ɓaci shin ke kakarsa ta wajen auwace ko kuma kakar sa ta wajen Uba ne?”.
Kallonsa kawai Innayi keyi tana jijjiga ƙafarta.
Ajiyar zuciya M Jameel ya saki kana yace.
“Dan Allah Innayi ki faɗa min ina son insan wannan abin kada ki ƙi faɗa min ke ta wani gefe ne kika kasance.
Kaka agaresa sannan kuma akwai abubuwa da dama da suke ɗaure min kai ina so insan su Innayi, idan har baki faɗa min suba Wallahi zan rayu da ƙumfa dan Allah ki faɗa min kada in mutu baki faɗa min ba”.
Sanyayyar Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da kallon M Jameel kana tace.
“Aaa to mutuwan nan Kam Jamilu am ai tana kan kowa, sannan ni tsohuwa ma ban ce kar in mutu ban faɗa muku ba, sai kaine zaka ce kar ka mutu ban faɗa maka ba!”.
Langwaɓar da kai yayi tare da karyar da murya cikin son karya logonta da batun zai mutu dan yasan bata son jin hakan yace.
“Ni dai ki faɗa min”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Jamilu bana son tone-tone ne Jamilu abar kaza cikin gashinta fa yafi, sannan kuma babu amfanin tone-tone da faɗe-faɗe!”.
Zamansa ya gyara tare da cewa.
“Innayi Ni dai inaso shi tone-tonen nan da faɗe-faɗen nan ina so afada min waye ne A.J Ina son insan Abu akan Abokina kuma Aminina ina so insan komai akanshi”.
Sauƙe numfashi tayi tare da kallon M Jameel kana tace.
“Toh nayi maka al'ƙawari ni kuwa zan sanar maka da komai in. Allah ya yarda zan faɗa maka abinda ya sawwaka duk da cewa bakomai zan faɗa maka ba”.
Jinjina kai yayi kana yace.
“Toh Innayi nagode amma ranan yaushe zaki faɗa min”.
Shiru tayi alamar tunani sai kuma tace.
“Duk ranan dana shirya zan faɗa maka sai kazo kai kaɗai”.
Jinjina kai yayi tare da cewa.
“Toh shikenan Innayi Nagode sosai”.
Bayan sun sake taɓa hira ne ya mata Sallama ya tafi.
Da daddare Misalin ƙarfe takwas Naseer ya shiga gidansu bayan yaje ya gama sharholiyarsa kai tsaye falon mahaifiyarsa ya nufa zaune ya samu Mahaifiyarsa da Yayunsa mata guda biyu dawowarsu daga gidan sunan kenan basu daɗe ba.
Zama yayi tare da gaishesu suka amsa cikin sakin fuska.
Aunty Hindu ce ta kallesa tare da cewa.
“A'a yau fa mun ga abin al'ajabi agidan Yaya Musa kawai ragon suna ya ɓace bat.
Ni dai gaskiya ban yarda da mai gadin nan ba da ƙyar idan bashine ya sace ragon ba yazo yana ihu da kururuwa wai rago ya ɓace rago zai ɓace shi tsuntsune ko abin tsafi ne?”.
Dariya Naseer yayi tare da kallon Addar tasa kana yace.
“Atoh ku dai bin ciki mai gadin nan rago zai ɓace haka nan ba dalili ne”.
Aunty Larai tace.
“Atoh abin dai akwai abin dubawa”.
Miƙewa Naseer yayi tare da miƙa yace.
“Bari na shiga ciki na watsa ruwa”.
Kallonsa Aunty Hindu tayi kana tace.
“Bari muje ka bani tsaraba ta da yake baka da kirki tunda kazo ba kaje gida na ba Naseer”.
Zaro ido yayi kana yace.
“Wallahi ranan naje Aunty Hindu akace min wai kinje kitso yara basu faɗa miki ba?”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Ai kuwa sun faɗa min ba shakka na tuna toh muje ka ban tsara bata”.
Ta faɗa tare da miƙewa gaba yayi tabi bayansa har suka shiga tsarerren falon nasa da komai na ciki ash colour da baƙi ne Bedroom ya wuce Aunty Hindu kuma ta zauna aɗaya daga kujerun cikin falon tana jiransa.
Naseer kuwa yana Shiga Idanunsa suka sauƙa akan yankekken rago Atsakiyar gadonsa Atsorace yaja baya cikin kiɗima da ruɗewa ya dafe kansa tare da furta.
_“Innalillahi Wa'inna Ilahi rajiu'n”_
Aunty Hindu kuwa jin Muryar sa Aƙiɗime yasa ta miƙe da sauri ta isa Bedroom ɗin Idanunta bai sauƙa ko ina ba sai kan ragon.
Dafe ƙirjinta tayi tare da cewa.
“Innalillahi ragon anan kuma?”.
Cikin sauri Naseer ya sanya hannunsa tare da rufe mata baki kana yace.
“Na roƙe ki Aunty Hindu Dan Allah ki rufa min asiri kada ki faɗa kada kiyi maganar”.
Cike da mamaki da kuma tsoro tace.
“Toh kenan Naseer kaine ka saci ragon?”.
Kallonta yayi tare da cewa.
“Kamarya in saci rago kamar wani almajiri. nima ganin sa kawai nayi akan gadona kamar yanda kika gansa”.
Harara ta watsa masa tare da kallon ragon dake kan gadon kana ta kallesa tare da cewa.
“Kai ka sace mana in ba Haka ba Naseer menene?”.
Wani shegen kallo ya watsa mata da alamun ɓacin rai atare dashi yace.
“Ba sacewa nayi ba idan ma satar zanyi ba zan saci mai raiba!? Ko ni matsiyacine da bazan iya saya ba, ko mun rasa wadatane a gidan”.
Sai kuma ya saki Ajiyar zuciya tare da dai-dai ta Muryar sa yace.
“Kawai dai akasi aka samu?”.
Cikin rashin fahimta tace.
“Kamar ya akasi aka samu?”.
Ƙugunsa ya riƙe da hannunsa biyu tare da furzar da Iska mai zafi daga bakinsa kana yace.
“Kawai an ɓata min aikina ne?”.
Cikin rashin fahimta tace.
“Aiki kamar ya?”.
Dafe kansa yayi alamun gajiya kana yace.
“Na haɗa ki da Allah da darajar Manzonsa, ni kar kiyi min tonon silili da tereren ban kaɗa dan Allah ki haɗiye wannan maganar ƴar uwa ki rufa min asiri wannan magana tsakanin mu ne kawai kin gansa magana ya ƙare”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da faɗin.
“Toh ka faɗa min menene sirrin?”.
Girgiza kai yayi tare da cewa.
“Ba zaki iya ɗauka ba”.
Kallonsa tayi kana tace.
“Ka faɗa min menene bazan iya ɗaukar ba?Abinda nasani Naseer idan ma maita ce duk mun tsotsa fa!”.
Sake ɗaure fuska yayi kana yace.
“Maita ku kuka tsotsa ni dai bana maita amma ina abin da yafi maita!”.
Zaro Ido tayi tare da cewa.
“Menene?”.
Ajiyar zuciya ya sauƙe kana ya sake kallon ragon lumshe idanunsa yayi tare da cewa.
“Bokana ne ya bani laƙani idan nayi aiki da al'adan mace zanyi kuɗi zanyi arziƙi mai tarin yawa da yake ba kisan kai bane shiyasa na bayar”.
Cije labɓansa na ƙasa yayi kana yace.
“Sannan kuma duk yarinyar data saka min jininta zan zo in same ta akan gado na”.
Furzar da iska mai zafi yayi daga bakinsa kana yace.
“Aunty Hindu ina fama da matsala tun da nadawo ƙasar nan ban samu nayi Sex ba. Ina dame ina cikin tsananin buƙatar Mace, toh kinga Khausar kuma ina sonta sannan nasan cewa nizan aureta shiyasa na bata mahaɗin maganin da aka bani ƙyallen akan ta samin jininta kinga da ita zanzo in