Showing 87001 words to 90000 words out of 176046 words

Chapter 30 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete

ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.


GARKUWAR MA'AURATA


Anutse Moddibo da M Jameel suka fito daga motar dai-dai lokacin da Malam Ahmad ya fito daga harabar gidan ganinsu yasa ya faɗaɗa fara'ar fuskarsa tare da faɗin.
“A'a Masha Allah tagwayen Ummi kunzo?”.
Murmushi sukayi Atare kana suka ƙara sa kusa dashi.
Kallonsu Malam Ahmad yayi fuskarsa ɗauke da murmushi kana yace.
“Sannunku da zuwa ku isa daga ciki zan dawo mu gaisa”.
Kai suka gyaɗa masa atare kana suka nufi haraban cikin gidan shi kuma ya fice.
Bakin su ɗauke da Sallama suka shiga farfajiyar gidan,
Kusan a tare suka juyo suka kalli juna lokacin da idanunsu, ya sauƙa akan shimfiɗar ƙaton taburma da Ummi ta shimfiɗe asaman baranda kana ga wani lallausan Chanis capet dake fitar da ƙamshi da wasu manyan tuntuna guda uku ɗaya na tsakiya biyu na gefe da gefe sai manyan tire guda huɗu akai tiren farko na kayan fruit ne kama daga,Tuffa, Inabi, Gwanda, Dabino, Abarba, Ayaba, Kankana, Lemo duk anyi slinzing ɗinsu.
Ɗaya tiren kuma Flaks ɗin tea ne da ma dai-dai-tan kofina masu kyau sai gongomin madara da Bounvita.
Sai kuma ɗayan dake ɗauke da Flaks din kunu agefe, sai kuma na ƙarshe wanda yafi su girma manyan kulo-line masu kyau kula na farko Perpesoup ɗin jan naman rago ne daya dahu ligif yana fitar da ƙamshi sai ɗaya kulan kuma soyeyyen dan kalin ne da ƙwai gwanin ban sha'awa.
Jin Sallamar sune yasa Ummi saurin fitowa daga falo tare da faɗaɗa fara'ar dake Samar fuskarta kana tace.
“Lale marhaba sannunku da zuwa Babana”.
Murmushin gefen baki Moddibo yayi wanda ke ƙara masa kyawun fuskarsa kana ya lumshe idanunsa tare da faɗin.
“Barka dai Ummina”.
M Jameel kuwa baki ya tura cike da Shagwaɓa kana ya langwaɓar da kai Idanunsa akan Umminsa sai kuma ya kalli Moddibo dake ƙoƙarin zama akan shimfiɗar da Ummi tayi kana yace.
“Ni dai gaskiya na fara kishi Ummi mai yasa tun da har haka kike son Aliyun nan bakisa min sunan Babban naki ba nima ki riƙa cemin Babana?”.

Murmushi Ummi tayi Idanunta akansa ta zauna kana tace.
“To ai kaima Babana ne ko ka manta Kai takwaran kakan kane Baban-Babanka.
Dariya mai sauti yayi kana ya shafa sajensa tare da cewa.
“Ƙwarai kuwa haka Abbana ke kirana da Babana munyi raba dai-dai Ummi ta kiraka da Babanta Ni kuma Abba na ya kira ni da Babana”.

Gyaɗa kai Moddibo yayi cikin yanayin sanyin Muryansa ya Kalli M Jameel kana yace.
“Oho dai amma nine na hannun daman Ummi”.
Murmushi Ummi tayi cike da ƙaunarsu kana ta zauna daga gefensu Idanunta akan Moddibo dake motsa bakinsa idanunsa alumshe alamar tasbihi yake.
Ganin haka sai ta miƙe dan kar ta takura masa ta ɗan ɗaga sautin Muryanta tare da cewa.
“Bashir ga Yayanka sun zo baka zo kun gaisa ba”.
Cike da ladabi Bashir ya fito kana yace.
“Ummi kaya na nake gyarawa yanzu nake so in fito”.
Ya Ida maganar tare da zama agefen Moddibo kana yace.
“Yaya Moddibo ina wuni ya Ibada?”.
Moddibo kuwa buɗe idanunsa dake lumshe ya buɗe tare da ɗaura hannunsa akan Bashir yana shafawa kana yace.
“Lafiya lau Alhamdulillah ya karatu?”.
Bashir ya amsa da.
“Alhamdulillah”,Kana ya maida kallon sa kam M Jameel dake motsa baki da alama shima tasbihi yake ya kallesa tare da cewa.
“Yaya Jameel Ina wuni ya ibada?”.
M Jameel ya Amsa da.
“Alhamdulillah”.
Miƙewa Bashir yayi ya koma ya cigaba da aikin da yake.

Moddibo kuwa bayan yayi tasbihi sai ya koma Azkharul masa ƙarfe shida da minti Ashirin da biyu aka kira Sallar maghariba Plate din Dabino da Ummi ta ajiye musu agabansu Anutse Moddibo ya miƙe tare da ɗaukan ruwa ya kuskure bakinsa kana ya dawo ya zauna.
Shima M Jameel miƙewa yayi ya wanke bakinsa dabino Moddibo ya ɗauka ya buɗe sanan ya sanya abakinsa bayan ya furta.
“Zahabazzaba'u Wabitallatil,Uruƙu wasu batul Ajri Insha Allah”.
Anutse ya ke cin dabinon inda yaci sai ya sanya ƙwallon atafin hannunsa na hagu.
Guda bakwai yaci kana ya dakata.
M Jameel kuwa dabino Uku yaci kana ya janyo faranti kayan friut ɗin ya fara da Abarba.

Lumshe idanu Moddibo yayi tare da ɗaukar Inabi ya kai bakinsa sai kuma ya buɗe Idanunsa akan Ummin data ƙara so wajen zama tayi tare da tsirawa M Jameel idanu baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta yana kansa.

Iska Moddibo ya furzar daga bakinsa tare da jingina bayansa da jikin bangon ya lura da tun zuwansu wani irin kallon da Ummi ke bin M Jameel dashi kallone mai nuni da tsantsar so, da kuma ƙauna da shaƙuwa irin wanda uwa ke nunawa ƴaƴan ta.
Ƙasa da kansa yayi yayin da yaji ruwan hawaye masu ɗumi na tsata-tsafo masa saboda ganin shi ya rasa wannan damar bazai samu irin wannan ba arayuwarsa ba still Kansa na ƙasa ba tare daya ɗago ba ya dai-dai-ta muryarsa tare da faɗin.
“Ummi kiyi buɗa baki mana”.

Sai asannan Ummi ta lura da kallon da take bin M Jameel dashi, Malam Ahmad ma murmushi yayi domin ya lura da kallon da Ummi kebin M Jameel dashi Shikuwa M Jameel sai alokacin ya ɗago kansa ya lura da irin kallon da Umminsa ke binsa dashi.
Murmushi yayi mai cike da so da ƙauna.
Kana yace.
“Ya dai Ummina nayi kyaune ko muni kike ta kallona?”.

Ajiyar zuciya ta sauƙe kana ta ɗan lumshe Idanunta tare da girgiza kai kana tace.
“A'a kawai dai naga azumi ɗaya akayi ana biyu har ka rame”.
Murmushi yayi tare da gyara zamansa kana yace.
“Hmmm Ummi kenan ai kinga mu ba azumin ne kaɗai ba. akwai yawon zirga-zirga sannan abincinma bama nutsuwa mu cisa yanda ya kamata musamman ma idan na biyewa Babanki”.

Jinjina kai Ummi tayi kana tace.
“To yau kam anan sai kunci kuncika cikin ku sannan in dafa muku na Sahur ma ku tafi dashi”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana cikin sauri yace.
“A'a Ummi ki zauna Innayi na mana sannan ga can Asma'u na taya ta yanzu idan mun koma sai mun rasa inda zamu sanya abincin a cikinmu”.
Jinjina kai tayi kana tace.
“Toh shikenan Babana”.
Murmushi Moddibo yayi kana yace.
“Ummi kici abinci mana”.

Kai ta gyaɗa sannan ta janyo Plate ɗin dabinon ta ci guda uku Bayan tayi addu'ar buɗa baki.
Malam Ahmad ma danino uku yaci sannan Ummi ta ɗauki Flaks da niyyar haɗa musu tea Moddibo dake cin friut yayi saurin cewa.
“A'a Ummi bari sai munyi Sallah”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Toh shikenan sai kun dawo”.

Miƙewa sukayi M Jameel da Moddibo suka ɗauki buta kana suka ɗaura alwala suka fice Malam Ahmad kuwa ya riga su fita.
Kai tsaye masallacin ƙofar gidan su Ummi da Baban Asma'u ke limancin suka shiga. Suna idar da Sallar Maghariba bayan sun idar suka dawo cikin gida shigowarsu yayi dai-dai da rurin da wayar M Jameel keyi.

Kallon Moddibo M Jameel yayi kana yace.
“Innayi ce ke kira”.
Jinjina kai Moddibo yayi tare da cewa.
“Uhm”.
picking call din yayi ya kai kunnensa.

Daga ɗaya ɓangaren Innayi tayi gyaran murya kana tace.
“Jamilu lafiya baku dawo kunyi buɗa baki ba mai kuke yi har yanzu awaje?”.
Sajensa ya shafa kana yace.
“Innayi wallahi Ummi ce ta riƙe mu wai saidai muyi buɗa baki agidan ta”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Toh mu kuma na gidan mu ya zamu yi dashi”.

Kallon Moddibo yayi sai kuma yayi Murmushi kana yace.
“Innayi abawa Almajirai dai sai kibar mana na Sahur dan nasan kinyi miyarki mai daɗin nan miyar me kika mana ma tukunna?”.

Dariya Innayi tayi kana tace.
“Miyar roman da kake so na daddawa da ƙarago shi zanyi muku na Sahur”.
murmushi ya saki tare da faɗin.
“Yauwa ina son wannan miyar”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Toh shikenan sai kun dawo ka gaishe da Ummin”.
Ta faɗa tare da katse kiran.

Suna ida shiga gidan suka samu wajen suka zauna Ummi ta miƙe tare da ɗaukar Flaks da kofina ta haɗa musu tea mai kauri yana tururi kana ta zuba musu soyeyyen dankali da ƙwai.
Anutse suka fara ci kaɗan Moddibo yaci ya janye hannunsa daga ciki.
Kallonsa Ummi tayi kana tace.
“Ya dai Babana kaci mana”.
Murmushi Moddibo yayi tare da ɗaura hannunsa na dama akan shafefen cikinsa ya shafa kana yace.
“Ummi na ƙoshi”.
Girgiza kai Ummi tayi tare da cewa.
“Kai Babana me ma kuka ci?”.
Ɗan kwaɓe fuska yayi kana cikin sanyin murya mai kama da shagwaɓa ya lumshe idanunsa tare da cewa.
“Ummi kar muje muna sallah abinci yan fitowa ta hancin mu”.
Kallonsa Ummi tayi tare da murmushi kana tace.
“A'a Babana me ma kuka ci da zai zazzago ta hancinku?”.
Murmushi yayi tare da shafa sajensa zuwa gemunsa kana yace.
“Allah Ummi mun ƙoshi ko ba haka ba J?”.
Kai M Jameel ya gyaɗa tare da Hararan Moddibo ya cire hannunsa a Plate din dan kalin.
Hira suka sake taɓawa kana Moddibo ya miƙe tare da kallon Ummi kana yace.
“Ummi zamu tafi”.

Jinjina kai Ummi tayi tare da cewa.
“Idan kunyi sallah Isha'i zaku dawo ta nan?”.
Girgiza kai Moddibo yayi kana yace.
“A'a Ummi sai wani lokaci”.
Gyaɗa kai tayi tare da cewa.
“Toh ku tafi da kunun nan”.

Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe tare da gyara tsayuwar sa kana yace.
“Toh Ummi ina son kunun abamu zan tafi dashi”.
M Jameel ya juya ya kalli Ummi tare da langwaɓar da kai kana yace.
“Ummi Ni dai ba abani abinda nake so ba”.
Cike da kulawa da kuma so ta juya ta kallesa kana tace.
“Me kake so?”.
Murmushi yayi kana yace.
“Inabin za'a bani in tafi dashi”.
Saurin Kallonsa Moddibo yayi sai kuma ya juya ya kalli Ummi tare da cewa.
“Ummi kar ki basa yasha muna dashi agida”.
Tura baki M Jameel Yayi kana yace.
“Iyeee to na haƙura tunda ba aso ayimin kyautar”.
Ummi Kam murmushi take Cike da ƙaunar su, ji takeyi tamkar su duka biyu a cikinta ta rainesu ta haifesu.
Sallama suka mata kana suka fice suka shiga mota Moddibo ke mazaunin Driver yayin da M Jameel ke gefen mai zaman banza kai tsaye Masallacin da suke limancin na ƙofar gidan Sarki suka nufa sunyi tafiya mai ɗan tsayi kafin suka isa lokacin da suka isa ankira sallar Isha'i suka shiga Moddibo ne yayi limanci suka idar da Isha'i kana sukayi Asham bayan an watse kana suka fito suka shiga mota wannan karon M Jameel ke driving Kai tsaye gidan Innayi suka wuce.

Ƙarfe takwas da rabi suka isa gidan bayan sunyi parking sun fito kai tsaye sashen Innayi suka shiga bakinsu ɗauke da sallama a farfajiyar gidan suka tarar da Innayi da Asma'u zaune Innayi dake gashin nama akan mangal da tarin gawayi agefenta ta daga kanta tare da Kallonsu kana ta amsa Sallamar su.

Ƙara sawa kusa da ita sukayi M Jameel yaja kujera ya Zauna kana ya Kalli Innayi tare da cewa.
“Innayi ya dai mai ake gasa wasa ne?”.
Murmushi Innayi tayi kana tace.
“Nama nake dan gasawa nasanku da cin nama kamar kuraye!”.
Dariya M Jameel Yayi kana yace.
“Aikam Innayi kin kyauta gashi asalin gashi na gargajiya kike yi”.
Kai ta gyaɗa tana ɗaukar Plate tace.
“Eh ai nasanku”.
Ta ida maganar tare da miƙa musu naman data yayyanka ta zuba a Plate tare dasa musu yaji agefe sannan ta yaryara ɗa musu man shanu.
Kallon Asma'u dake yi musu sannu da zuwa tayi kana tace.
“Asms'u ɗauko musu capet su zauna”.
Cikin murza kai gefen dama da hagu Modibbo yace.
“Uhmm Innayi kin dai sanshi shi J ɗinki da son nama kamar kura”.
Murmushi M Jameel yayi dan yasan tabbas Modibbo bai cika damuwa da namaba, asalima in dai gasheshene ko soyayya in dai yaci yanka huɗu zuwa biyar zaice muƙa-muƙinsa sun gaji da taunawa, in kuma dafaffene wani lokaci da haƙorin gaba zai ɗan tattauna in yaji ya gaji sai ya tura masa naman gabansa.
Shi kuwa M Jameel Allah ya sani yana masifar son nama, shi kuwa Moddibo yafi bawa ƴaƴan itatuwa mahimmanci.
Cikin murmushin yace.
“Yoh in ban so namaba me zanso A.J Namafa shine maƙurar daɗi”.
“A wurinka ba, gashi kuma kana son koyamin”.
Cewar Moddibon,
Asma'u kuwa ganin Innayi na kallonta cikin mamakin tace.
“A'a Asma'u ɗauko musu abin zama mana”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta shiga falon ta ɗauko capet ɗin ta shimfiɗa musu awajen da yake agyare tass babu alamar ƙazanta.
Zama sukayi akai, Innayi ta sake kallon Asma'u tare da cewa.
“Haɗa musu Tea sannan kisa musu zuma yaji”.
Kai Asma'u ta gyaɗa kana ta miƙe ta zuba musu shayi tare da zuba wadataccen zuma aciki ta kawo musu.

M Jameel kuwa Anutse ya kai yankan naman bakinsa lokaci ɗaya ya lumshe idanunsa tare da buɗe su akan Innayi kana yace.
“Kai gaskiya gashin nan yayi daɗi sosai”.
Murmushi Innayi tayi tare da kallon Moddibo dake cin naman kamar ko yaushe kamar dai dole, yana ɗan taunawa kaɗan-kaɗan cikin kula tace.
“Kai kuma fa Moddibo?”.
Ɗago kansa yayi ya kalleta kana yace.
“Uhm yayi”.
Girgiza kai tayi kana tace.
“Wato kai dai baza ka iya Yabawa ba kenan?”.
Kansa ya sake ɗagowa tare da kallonta kana yace.
“Ai gashinan J ya yaba kuma danɗanon harshen mu ɗaya ne ai”.
Murmushi M Jameel da Asma'u sukayi.

Innayi kuwa baki ta taɓe M Jameel da Moddibo suka cigaba daci Ahankali Moddibo ya ɗago hannunsa tare da kallon tsadedden agogonsa kana ya mayar da Kallonsa kan M Jameel tare da cewa.
“Sai munyi sauri lokaci ya kusa J”.

Kai M Jameel ya gyaɗa tare da cire hannunsa a Plate din kana yace.
“Toh shikenan mu tafi”.
Miƙewa Moddibo yayi tare da kallon Innayi kana yace.
“Bari naje na canza kaya”.
Daga haka ya juya ya nufi sashen sa, shima M Jameel bayansa yabi.

Moddibo nashiga Bedroom ya sauya kayansa zuwa Jallabiya Coffee color tare da ɗaura farin hirami irin na samarin larabawa kana ya feshe jikinsa da turarukansa masu daɗin ƙamshi.
Anutse ya fito falo ya samu M Jameel da shima ya canza kayansa buɗe fridge M Jameel Yayi ya ɗauki goran faro mai sanyi sannan suka jera tare da Moddibo suka sauƙa.

Kai tsaye sashen su Innayi suka koma batare da sun shiga farfajiyar gidan ba .

“Toh Innayi mun tafi”.
Cewar M Jameel
Tana rufe roban yajin da suka ci nama dashi ta ajiye kana tace.
“Toh Allah ya tsare muma yanzu muna bayanku”.
M Jameel na gyara ɗaurin agogon dake tsintsiyar hannunsa ya kalleta kana yace.
“Toh idan za kuje kuzo mu tafi mana sai mu sauƙe ku”.

Girgiza kai tayi tare da cewa.
“Ai akwai Napep zamu hau”.
M Jameel kuwa kai ya Girgiza kana yace.
“A'a ai abin baiyi ba bayan tanan muke tafiya kuma kuce zaki shiga Napep kawai kuzo mutafi”.
Jinjina kai Innayi ta gyaɗa kana tace.
“To bari mu tattara da sauri sai mu tafi”.
“Toh”,M Jameel yace Shi kuwa Moddibo bai ce komai ba sai harɗe hannunsa da yayi aƙirji.

Cikin sauri Innayi da Asma'u suka tattare wajen sannan suka sanya hijabansu kana suka rufe kichen da gidan suka fice abayan Mota suka zauna ita da Asma'u yayin da M Jameel da Moddibo ke gaba.
Suna isa babban masallacin M Jameel yayi Parking Innayi da Asma'u suka fita suka nufi sashen mata su kuma suka shiga cikin masallacin daya cika sosai da al'umma.

Bayan sun zauna Kamar ko yaushe M jameel ya buɗe musu da addu'o'in kana Moddibo ya gyara system ɗin sa tare da ƙara rage girms Idanunsa kana yasa lallausan tafin hannunsa ya gyara zaman microphone din dake gabansa tare dayin gyaran murya cikin sanyayyar sautin muryansa ya fara kamar haka:
_“Auzubillahi Minal Shaiɗanir Rajim, Bismillahir Rahmanir Rahim.
(10) Innalazina ya'akuluna, Amwalal yatama zhulman innama ya'akuluna fiy buɗunihim naraa,wasayaslauna sa'irah”._
Jama'ar dake wajen masallacin cikin sassarfa suka ƙaraso cikin masallacin dan basa so koda harafi ɗaya ne su rasa daga cikin karatun Moddibo saboda baiwar muryarsa.

Moddibo kuwa sanyayyar numfashi ya fesar tare da jingina bayansa da kujeran kana ya cigaba kamar haka:
_“(11)Yusikumullahu fii auladikum,Lilzikri mislu hazzil unsaynan.Fa'in kunna Nisa'a fauƙasnatayni falahunna sulusa ma tarak,Wa'in kanat wahidatan falahannisf,Wali abwayhi likulli wahidin Minhumassudusu,Mimma taraka inkana lahuu waladun,Fa'in lam yakun lahu waladu wawarisahuuu abwahu fali ummihi sulus.Fa'in kana lahu Ikhwatun fali ummihi sudus min ba'adi wasiyyatin yusi biha audayn,abaukum wa'abna ukum latadruna ayyuhum aƙrabuna lakum naf',a,Faridatan Minallah,Innalaha kana aliman hakima”._
Ya dire ayar tare da jan numfashin sa da ya riƙe.
Jinjina kai M Jameel Yayi yayinda ayoyin ke ratsa sa cikin yanayin sakewa ya lumshe idanu kana yace.
“Aya ta gaba”.

Jinjina kai Moddibo yayi kana cikin zazzaƙan muryansa mai sanyi da ratsa jiki kana da nutsuwa ya cigaba da jan ayoyin saida ya kai aya ta Ashirin kana ya tsaya.
Shi kuwa M Jameel Cike da tsantsar ƙwarewa da nutsuwa kana da sanin makaman tafsir ya fara fassara ayoyin tare da cikekken kaddima da kowa amintattun haɗisai da suka da munasaba da ayoyin harma da sababul nuzur na ayoyi, lokacin ɗaya cikin masallacin ya sake samun nutsuwa tafsirin na ratsa su.

Ƙarfe goma dai-dai suka tashi tafsir ɗin mata suka fara fita ta ɓangarensu kafin maza suka fita acikin mota Asma'u da Innayi suka jira M Jameel da Moddibo goma da kwata dai-dai suka fito suka tafi.
Acan ɓangaren Khausar kuwa yauma kamar kullum taje tafsiri ita kaɗai ta dawo duk da masallacin a ƙofar gidansu yake bakinta ɗauke da Sallama tashiga cikin falonsu Anutse ta cire hijabinta tare da nufar kichen inda take jiyo motsin Mommyta kasancewar yau itace da girki yasa ko tafsir bata jeba.

Juyiwa Mommy tayi jin motsi abayan ta ganin Khausar yasa ta maida hankalinta kan aikinta kana tace.
“Kin dawo?”.
Kai Khausar ta gyaɗa tana kallon tuƙeƙken tuwon shinkafa da Mommy ke kwashe maran ƙarshe.
Ahankali Khausar ta matsa kusa da Mommy kana tace.
“Mommy ki bari zanyi miyar”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Ok to Miyar zogala za kiyi”.
Kai Khausar ta gyaɗa tare da ɗaukar.
Da fara aikin haɗa miyar zogalen.
Cikin abinda bai gaza awa ɗaya da rabi ba, duk ta haɗa ta sanya komai na buƙata kana.
Ta rufe nan danan kichen ɗin ya kaure da ƙamshin miyar sauran kayan da Mommy tayi amfani dasu ta haɗa ta wanke tare da sauƙe Miyar ganin tayi tik gwanin kyau.

Bayan ta gama ta buɗe miyar da yayi mugun kyau a ido ta ɗauki kular wani sashe ta zuba miya kasancewar babban gidana yasa kowa kaina nasa akeyi, na buɗa baki kuwa ki wacce a side ɗinta takeyi, mai girki zata sawa Lamiɗo, da Dadu, haka tsarin nasu yake.
Shigo wa Mommy tayi fuskarta ɗauke da murmushi ta kalli yanda kichen ɗin yayi fess ga ƙamshin miyar zogalan da yaki kifi da naman dariko, kallonta ta mayar kan Khausar kana tace.
“Sannu da ƙoƙari ki ɗauki na sashen Hajiya Bunayya ki kai mata”.
Kai Khausar ta gyaɗa sannan ta ɗauka kular Hajiya Bunayya ta wuce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login