Showing 66001 words to 69000 words out of 176046 words
ta zuba musu, sai kuma ta koma ɗaki tashiga toilet tayi wanka Agurguje ta fito ɗaure da towel mai ɗan girma sannan ta cirewa Raudat kayanta tayi mata wanka bayan sun fito tashafa mata mai kana ta sanya mata Uniform sannan itama ta shirya cikin Uniform da yayi matukar amsar jikinta hannu Raudat taja suka fita dai-dai lokacin da Haiydar suka fito da Ramadan cikin shiri ko wannensu ya nufi inda lunch box ɗin da yake ya ɗauka kana suka fice harabar gidan suka shiga mota.
Kamar ko yaushe motar na parking Khausar ta fito riƙe da hannun Raudat,
Sai da ta kaita ajinsu sannan cikin sauri ta juya ta kama hanyar koma ajinsu daga baya taji ankira sunan ta da faɗin.
“Lelewal ke kullum sai kowa ya riga ki shiga cikin aji ko?”.
Ahankali ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta akan Malam Isa dake tsayi murmushi tayi da faɗin.
“Ba haka bane Malam na tsaya kai Raudat ajinsu ne shiyasa”.
Kai ya gyaɗa still Idanunsa akanta hakanan yarinyar ke burgesa ahankali yace.
“To ki tafi kar araba musu questions paper ba kyanan”.
Kai ta gyaɗa tare da juyawa cikin sassarfa da sanin darajar kanta take tafiya har ta isa cikin ajin.
Aɓangaren Amina kuwa koda M Jameel yashiga class da niyyar raba musu questions paper ƙasa tayi da kanta ta amsa batare data kalli fuskarsa ba domin koda gaishesa ne ta dena tunda ta lura da baya buƙata kallon fuskanta, to shima M Jameel Sosai yaji daɗi da yarinyar ta daina gaishesa, dan ko kaɗan baya ƙaunar kallon fuskarta, bare kuma wata magana ta haɗa su.
Acan gida kuwa tun bayan tafiyar su Khausar Makaranta cikin Mommy ya tsananta da ciwo da ƙyar ta yunƙura ta miƙe tana mai rintse Idanunta jini taga yana bin ƙafafunta da sauri ta dafe cikinta da ƙyar ta iya furta.
“Ya Allah wannan ciwon cikin kuma na menene?”.
Da ƙyar taja ƙafanta zuwa jikin beside drawer ta ɗaga wayarta tare da kiran number Hajiya Bunayya, kafin ya katse Hajiya Bunayya tayi picking tare da Sallama.
Mommy kuwa cikin azaban ciwon da cikinta ke mata ta rintse Idanunta kana tace.
“Yaya”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katseta da faɗin.
“Ƙanwata lafiya naji muryanki haka?”.
cike da yarda ta rintse Idanunta cikin yanayin azaban ciwon da cikinta keyi tace.
“Wallahi Yaya cikina ciwo yake tun daren jiya, haka na kwana banyi bacci ba yanzu kuma gashi jini ya ɓalle min!
Dan Allah ki faɗawa Alhj mutafi asibiti”.
Hajiya Bunayya kuwa da damuwa amuryanta tace.
“Subhanallahi! bari na faɗa masa yanzu ma kuwa”.
Sannan ta katse wayar ta nufi ɗakin Lamiɗo ranta fari Sol burinta ya cika abakin ƙofa suka haɗu yana shirin fita.
A take ta wani marairaice fuska kana cikin yanayin damuwa tace.
“Yanzu Mommyn Khausar ta kirani.
Wai jiya da ciwon ciki ta kwana yanzu kuma jini ya ɓalle mata”.
Ai bai ma gama sauraron abinda zata faɗa ba ya ratsa ta ya wuce sashen Mommy cike da damuwa.
Hajiya Bunayya kuwa da harara tabi bayansa kafin taja siririn tsaki ta mara masa baya.
Tana shiga Bedroom ɗin ta samu Lamiɗo tsugunne akan Mommy da sauri ta tsugunna daga gefensa ta riƙo hannun Mommy.
Cike da tausayawa kamar za tayi kuka tace.
“Sannu Aysha ciwon ciki amma baki yi magana ba, gashi har ya tsananta jini na zuba”.
Ta ida maganar zufa na karyo mata wanda in kagani zakayi zaton na tsananin damuwa ce, nan kuwa na tsananin farin cikin burinta ya cika ne.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi tare da naɗe hannun rigarsa zai ɗauke ta Ganin haka ne yasa Hajiya Bunayya tayi saurin miƙewa tare da tallafo Mommy jikinta suka fita,
agidan baya suka zauna Lamiɗo kuma ya shiga gefen mai zaman banza Driver yaja suka tafi Hajiya Bunayya sai faman sannu take yiwa Mommy.
Suna isa asibitin aka karɓe su kai tsaye emergency aka nufa da ita ganin cikin ya riga ya zube yasa likitoci suka nufi wani ɗaki da ita tare da yi mata wankin ciki kana suka yi mata allurai nanda nan bacci wahala ya ɗauke ta Lamiɗo kuwa kasa Matsawa daga kusa da ita yayi ya cike da kulawa ya zauna a bakin gadon tare da riƙe tafin hannunta cike da tausayinta.
Hajiya Bunayya data shaƙa ta cika kuwa.
Wani lalataccen harara ta watsawa ƙeyansa cikin ranta tace, tabbas sai tayi wani abu akan wannan rawan jikin da yake mata.
A zahiri kuwa dafa kafaɗar sa tayi, ahankali ya ɗago kansa ya kalleta da idanunsa dake cike da damuwa amma baice komai ba.
Cike da kirsa ta ƙirƙiri murmushin da bai kai zuciba kana tace.
“Dan Allah ka rage damuwar nan, babu yanda zamuyi da ƙaddara haka Ubangiji ya tsara wannan ɗin ma ba rabo bane, ayanzu addu'ar lafiya take da buƙata awajenmu”.
A hankali ya sauƙe nannuyar Ajiyar zuciya tare da mayar da Kallonsa ga Mommy dake bacci tamkar babu abinda ke damunta.
Lumshe idanunsa yayi yace.
“Ina matuƙar tausayawa Aysha tun bayan haihuwar Haiydar take fama da wannan matsalar sannan ko wanne cikin sai ya wahalar da ita kafin ya fita”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta katsesa da faɗin.
“Ya zamuyi da rubutacciyar ƙaddara, ai kaga da Ubangiji yaga dama ai cikin Raudat da Ramadan ya zauna”.
Kai ya jinjina amma baice komai ba.
Ita kuwa cikin ɓoye farin cikinta ta sauƙe ajiyar zuciya da faɗin.
“Zan koma gida kafin ‘yan makaranta su dawo, naga lokaci yaja amma Insha Allah anjima zan dawo”.
Kai ya gyaɗa ba tare da yace komai ba still Idanunsa na kan Mommy.
Hajiya Bunayya kuwa ficewa tayi ranta fari fess kana tasa Driver ya maida ta.
Acan Makarantar su Khausar kuwa koda suka gama Exam ba abasu damar tafiya ba bayan sunyi sallar la'asar suka shiga haddar Alkur'ani sai ƙarfe biyar aka tashe su, kana suka shigo mota suka nufi gida, motar na parking Raudat ta fice da gudu ta nufi sashen su
Tana shiga falo ta fara kiran.
“Mommy! Mommy!! na mun dawo”.
Jin shiru yasa ta nufi Bedroom ɗinta da gudu ta buɗe ta shiga tana kiran.
“Mommy!, Mommy!!, Ina kika shiga”.
Still Bata ganta ba da gudu ta juya ta fito falon dai-dai lokacin Khausar kuma ta shigo ƙara sawa kusa da Khausar tayi ta riƙe hannunta kana tace.
“Addah Khausy Ina Mommy?”.
Kallonta Khausar tayi kafin tace.
“Bata ɗaki ne?”.
Kai Raudat ta gyaɗa mata alamar Eh,
Sake hannunta Khausar tayi kana ta nufi kichen ta buɗe wayam tagani alamar bata nan komawa tayi ta shiga Bedroom din ta ɓude still ba tanan jikin toilet ta nufa ta manna kunnenta ajiki tare da faɗin.
“Mommy Mommy kina ciki kuwa?”.
Jin shiru yasa ta tura ƙofar toilet din still bata nan fitowa tsakiyar falon Khausar tayi tare dasa hannun damanta ta riƙe ƙugunta tana tunanin ina Mommy ta shiga haka, bayan tasan bata fiye fitar yamma ba kuma koda zata fita tun safe kafin su tafi makaranta zata faɗa musu bare kuma yau da suka barta bata jin daɗi.
Da sauri ta kalli Raudat sai kuma tace.
“Jirani anan ina zuwa”.
ta faɗa tare da ficewa kai tsaye sashen Hajiya Bunayya ta nufa bakinta ɗauke da sallama tana faɗin.
“Ummah”.
Shigar ta yayi dai-dai da lokacin da Hajiya Bunayya ke riƙe da waya tana cewa.
“Kedai Hajiya Lami bari buƙata ɗaya ta biya saura ɗaya, tana can kwance a asibiti cikin ya zube yabi makwarari, saura ɗayan daman jira nake inga ya zata kaya ne ki shirya jibi zamu koma”.
Komai Hajiya Lami ta faɗa ohon musu, ita dai Hajiya Bunayya cikin jin dadi ta kece da wata mahaukaciyar dariya mai nuni da tsantsar farin ciki.
Lokaci ɗaya kuma dariyar nata ya tsaya ganin Khausar tsaye, sai kuma ta katse kiran tare da kallon Khausar.
Kafin tace wani abu Khausar tayi saurin cewa.
“Ummah ina Mommy mu?”.
Hajiya Bunayya ta wani langwaɓar da kai kana tace.
“Ayyah Khausar am Mommy ku tana asibiti bata da lafiya wallahi cikinta ya zube”.
Da sauri Khausar da kanta ke ƙasa ta ɗago ta kalli Hajiya Bunayya tana sake maimaita kalmar cikinta ya zube akasan ranta lokacin ɗaya hawaye masu zafin gaske suka cika kwarmin Idanunta.
Sai kuma tayi saurin maida hawayen ta kafin tace.
“Shikenan ɓuƙatar magauta tabiya hankali ya kwanta. Allah ya raya mata wa anda ta haifa. Ubangiji ya tsaresu daga sharrin mai sharrin”.
Ta ida maganar tana ƙoƙarin fita.
Da sauri Hajiya Bunayya tace.
“Ke Khausar zo nan Me kike nufi?”.
Anutse Khausar ta juya tare da sauƙe manyan Idanunta da suka sauya launi zuwa ja ta zubawa Hajiya Bunayya kana tace.
“A'a Ummah babu abinda nake nufi, kawai dai addu'a ce nayi”.
Cikin tsuke fuska Hajiya Bunayya ta watsa mata Harara da faɗin.
“Sannan su waye ne Magautan?”.
Ware hannu Khausar tayi tare da faɗin.
“Nikam ban sansu ba, amma dai nasan Allah Mabuwayi gagara Misali ya sansu kuma zaiyi maganin su, domin ai bahaushe yace rana dubu ta ɓarawo rana ɗaya ta mai kaya, suji tsoron ranan da Ubangiji zai musu kamun talala!”.
Cike da Mamaki Hajiya Bunayya tace.
“Wai Khausar me kike magana kamar habaici kike min ko kuma hannunka mai sanda!?.”
Ware ido Khausar tayi tace.
“Haba Ummah in Miki habaici kuma ayanda kike ƙaunar Mommyn mu kinfi ƙarfin habaici ko hannunka mai sanda kin wuce haka sai dai mgnar ce tazo kamar zaurance”.
Ɓoyeyyen Ajiyar zuciya Hajiya Bunayya ta saki domin tayi zaton yarinyar ta gano lagonta ne.
Khausar kuwa murmushi tayi tare da faɗin.
“Bari na tafi asibitin kar dare yayi”.
Da sauri Hajiya Bunayya ta gyara zamanta Idanunta akan Khausar tace.
“Toh kibari in ƙara sa abinci mana sai ki tafi dashi”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh amma bari na shiga gidan Aunty Ruƙayya kafin ki ƙarasa”.
Kai Hajia Bunayya ta gyaɗa tare da faɗin.
“Toh ki gaisheta”.
Kai kawai Khausar ta gyaɗa Sannan ta wuce sashen su.
Tana shiga Bedroom direct toilet ta wuce ta cire Uniform ɗin ta sannan ta watsa ruwa bayan ta fito ta dauki dogon rigar material pinch colour ta sanya, kana ta nufi kichen Agurguje ta dafawa su Haiydar jollof ɗin shin kafa da yaji bushesh-shen kifi da kayan ƙamshi nan da nan kichen ɗin ya ɗauki ƙamshi Warmers ta ɗauka ta juye sannan ta tafasa musu tea kana ta ɗura musushi, sannan ta fita falon dai-dai lokacin da Haiydar ya shigo.
Kallonsa Khausar tayi tare da kiran sunansa tace.
“Haiydar”.
Ya amsa da.
“Na'am”.
Cikin sanyi tayi ƙasa da muryanta tare da faɗin.
“Dan Allah Haiydar ka kwana anan kai da Ramadan, Raudat kuma zamu tafi da ita asibiti sai mu kwana da Mommy”.
Kai ya gyaɗa mata sai kuma yace.
“Nima ai inaso naje na dubata”.
Jinjina kai Khausar tayi tace.
“Ba damuwa kazo mutafi dukan mu amma yanzu zan fara shiga gidan Aunty Ruƙayya in sanar mata, idan yaso kai da Ramadan ku taho tare da Ummah,
In yaso sai ku dawo tare amma kubar min Raudat dan zamu kwana tare”.
“Toh shikenan Allah ya bata lafiya”.
“Ameen”,
Tace kana ta juya ta tafi har ta kusa fita ta sake juyawa ta kalli Haiydar dake tsaye Ahankali tace.
“Dan Allah Haiydar ka kula, bakomai za'a baka kaci ba, akwai abinci na dafa muku sannan duk wani abu da zaku buƙata akwai”.
Da sauri ya dafe kansa tare da faɗin.
“Ke dai jeki da rashin yardan ki kedai haka Allah ya halicce ki baki da yarda”.
Cikin sanyi ta girgiza kai kana tace.
“Shikenan ni dai ban san sai yaushe zaku yarda dani ba”.
Ta ida maganar tare da ficewa”.
Kai tsaye gidan Aunty Ruƙayya ta nufa.
Tare da Sallama tashiga Babban falon da yaji kayan alfarma kujerun set biyu aciki Black and Ash sai kuma babban tv plasma dake Manne abango daga ƙasansa kuma horm teater ne ƙasan falon kuma shimfiɗe yake da chanis capet.
Aunty Ruƙayya dake bedroom ta fito fuskarta ɗauke da murmushi tace.
“Khausar kece sannu da zuwa, shigo ciki”.
Da sauri tace.
“A'a Aunty sauri nakeyi ai”.
Cikin kulawa tace.
“Yo yasu Mommy ki?”.
Murmushi Khausar tayi tace.
“Wallahi Aunty Ruƙayya Mommy ce ke asibiti bata da lafiya, shine nace bari nazo na faɗa miki, Ni yanzu ma zan wuce ko za muje tare?”.
Cike da tausayawa Aunty Ruƙayya tace.
“Ayyah Allah ya bata lafiya zanje bari ina zuwa mu tafi tare”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Toh”.
Aunty Ruƙayya kuwa bedroom ta shiga tare kiran mijinta a waya, bayan ya bata izinine, ta ɗauko key mota da mayafinta suka fita,
suka shiga mota,
jingina kai Khausar tayi da jikin motar kalaman Hajiya Bunayya nayi mata suwwa akunne.
Juyawa Aunty Ruƙayya tayi ganin yanda Khausar ta zurfafa cikin tunani yasa tace.
“Ki riƙa yi mata addu'a”.
Kai kawai Khausar ta iya gyaɗa mata.
Cikin Mintuna kaɗan suka isa Asibitin bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga ɗakin da aka kwantar da Mommy saboda Hajiya Bunayya ta faɗa mata.
Kwance akan gado suka tarar da ita yayin da Lamiɗo ke gefenta akan kujera hannunsa riƙe da kofin tea yana miƙa mata da faɗin.
“Ki tashi kisha”.
Yana jin Sallamar Khausar ya juya yana kallonta har ta isa kusa dashi.
Cike da kulawa yace.
“Khausar har kun dawo?”.
Kai ta gyaɗa kana tace.
“Eh Abba ya jikin Mommy!?”.
Sai da ya ɗan kalli Mommy dake jingine da pillow sai kuma ya mayar da Kallonsa kan Khausar yace.
“Da sauƙi”.
Sai asannan ya lura da Hajiya Rukayya ya ɗan yi murmushi da faɗin.
“Hajiya Ruƙayya sannu da zuwa”.
Zama tayi akujeran dake kusa da ita tana cewa.
“Yawwa ya Hajiya Aysha da jikin kuma?”.
Ɗan Murmushi yayi kana yace.
“Da sauƙi”.
Tana kallon Mommy tace.
“Ubangiji Allah ya ƙara sauki”.
Ya amsa da.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
Khausar kuwa bakin gadon ta ƙarasa ta riƙe hannun Mommy acikin nata.
Cikin raunin murya tare da tausayawa mahaifiyar tata tace.
“Sannu Mommy ya Jikin?”.
Lumshe idanu Mommy tayi kana ta buɗe su a hankali tace.
“Da sauƙi Khausar bana jin komai in dan ta nice ma, da su sallame ni in koma gida mu kwana tare, dan bana jin ciwon cikin yayi sauƙi babu inda yake min ciwo!”.
Ajiyar zuciya Khausar ta sauƙe tare da faɗin.
“Masha Allah Mommy Allah yaƙara sauƙi Ubangiji ya ƙara tsarewa ya kare”.
A ranta kuwa cewa tace.
Ayyah da ace duk addu'o'in da takeyiwa Mommynta tun randa taci ferfesun da ace tana haɗa addu'ar da yaron cikin wata ƙil da bai zube ba.
Shafa kanta Mommy tayi cike da ƙaunar ta tace.
“Ameen Khausar ki kwantar da hankalin ki ba najin Komai”.
Ta faɗi hakan ganin yanda Khausar tayi zuru-zuru da ita.
Hajiya Ruƙayyance ta kalli Mommy kana tace.
“Hajiya Aysha ya ƙarfin jikin!?”
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Dasauƙi Hajiya Ruƙayya ya ‘Yar taki ya kuma rigima a makaranta!?".
Kallon Khausar Hajiya Ruƙayya tayi kana tace.
“A'a yanzu ai ta daina ta fara girma!”.
Jin haka yasa Khausar tayi murmushi.
Lamiɗo kuwa miƙewa yayi idanunsa akan Mommy yace.
“Toh shikenan bari na tafi dama ganin babu kowa ne yasa nake zaune bari na samu naje nayi wanka dan tunda muka zo ban samu na koma gida ba”.
Hajiya Ruƙayya tace.
“Ayyah ai babu komai Alhaji kaje”.
Jinjina kai Mommy tayi tace.
“Allah ya tsare”.
Ya Amsa da.
“Ameen”sannan ya juya ya fice.
Tafiyar Lamiɗo babu daɗewa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka zo Raudat na riƙe da hannunta.
Suna shiga Hajiya Bunayya ta zauna daga gefen gadon tare da kallon Mommy tace.
“Sannu ƙanwata ya ƙarfin jikin?”.
Murmushi Mommy tayi kana tace.
“Ai naji sauki Yaya”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cikin yanayin tausayawa tace.
“Allah ya baki lafiya”.
Hajiya Ruƙayya kuwa kallo ɗaya tayi wa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami taji sam basu kwanta mata arai ba musanman ma Hajiya Bunayya dake wani shish-shugewa Mommy.
Ta dai daure tace.
“Sannunku da zuwa”.
Hajiya Bunayya da Hajiya Lami suka haɗa baki wajen cewa.
“Yawwa ya mai jikin”.
Ataƙaice Hajiya Ruƙayya tace.
“Da sauƙi”.
Hajiya Lami kuwa jikin gadon ta matasa Idanunta akan Mommy tace.
“Ayyah Sannu Hajiya Aysha Ashe ga abinda ya faru kuma? Amma wannan abu yayi yawa ai gwara Alhj yayi ƙoƙari ya fitar dake waje wannan matsalar ko yaushe da ansamu ciki ya zube ai babu daɗi!”.
Kafin Mommy tayi magana Hajiya Bunayya tayi saurin cewa.
“Kede bari Hajiya Lami abin nan yana damun mu, gaba ɗaya mun kasa gane menene ainihin matsalar, amma hankalinmu na tashi kullum cikin yanayin nan, abin babu daɗi yanzu ciki takwas kenan yana zubewa abin ai babu daɗi!”.
Taɓe baki Khausar da Hajiya Rukayya sukayi alokaci ɗaya.
Ahankali Mommy ta gyara matashin data kishingiɗa akai kana tace.
“Uyummm ya za'ayi da abinda Allah ya tsara, amma ni inaga nin ba wani matsala bane, tun da gashi na haihu bayan haihuwar Haiydar ma haka nata fama da ɓare-ɓaren nan, kuma daga baya da Allah ya kawo Ramadan da Raudat an haifesu ba komai ai”.
Cike da kirsa Hajiya Bunayya tayi yaƙe kana tace.
“Hakane kam, toh Allah ya kawo masu albarka”.
Hajiya Lami kuwa harara ta gallawa Mommy tare da taɓe baki aranta tace shegiya me iyayin jaraba keda haihuwa sai dai kiga anayi.
Idanun Hajiya Ruƙayya da Khausar na kan Hajiya Lami alokacin data taɓe baki ta harari Mommy,
Juyawa Hajiya Ruƙayya tayi ta kalli Khausar tare da jinjina kai itama Khausar kai ta jinjina.
Miƙewa Hajiya Ruƙayya tayi tare da kallon Mommy tace.
“Toh Hajiya Aysha Ubangiji Allah ya ƙara sauki sannan Allah ya tsareki daga sharrin abin ƙi ni zan wuce!”.
A hankali Mommy ta ɗan yunƙura tare da lumshe Idanunta kana tace.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum Hajiya Ruƙayya Nagode”.
Hajiya Lami da Hajiya Bunayya kuwa baki suka saki suna kallon Hajiya Ruƙayya da Mamaki aransu suka ce kaji shegiyar mata da iyayi uban wa takewa wannan addu'ar.
Miƙewa Raudat tayi tare da riƙe hannun Hajiya Ruƙayya tace.
“Aunty Ruƙayya ni zan biki gidanki, Inje in kwana dasu Salman tun da gobe babu makarata”.
Da sauri Khausar ta kalli Raudat dake riƙe da hannun Aunty Ruƙayya tace.
“Ayyah Raudat am baza mu kwana ba?”.
Girgiza kai Raudat tayi tare da langwaɓar da kai kana tace.
“ Ni dai Ina tsoro ni bazan zauna ba”.
Kai Khausar ta gyaɗa da faɗin.
“Shikenan kibi Aunty Ruƙayya”.
Murmushi Aunty Ruƙayya tayi tare da jan hannun Khausar dake cikin nata
Har sun kai ƙofa Hajiya Bunayya ta ƙirƙiri murmushi tana kallon bayan Raudat tace.
“Oohhh Raudat ba zaki bini mu tafi gida ba?”.
Kafaɗa Raudat ta maƙale tace.
“A'a ni zanbi Aunty Ruƙayya”.
Aunyty Ruƙayya kuwa jan hannun Raudat tayi suka fice batare data sake jiran jin Abinda Hajiya Bunayya zata ceba.
Bayan tafiyar Aunty Ruƙayya babu da ɗewa Hajiya Bunayya ta miƙe tare da kallon Mommy tace.
“Toh ƙanwata zamu wuce Allah yaƙara sauƙi”.
Murmushi Mommy tayi da faɗin.
“Nagode Yaya ahuta gajiya”.
Hajiya Lami tace.
“Babu Gajiya”.
Sannan suka fice Khausar kuwa jinginar da kai tayi kamar mai bacci.
Da daddare Khausar ta miƙe daga kan dogon kujeran asibitin da take kwance ta dubi Mommy da bacci ya fara fisgarta tace.
“Mommy”.
Buɗe idanu Mommy tayi tare da kallon Khausar tace.
“Na'am Khausar ya akayi?”.
Ajiyar zuciya Khausar ta saki tana wasa da yatsun hannunta tace.
“Mommy baki zargi perpesoup ɗin nan da kika ci azubewar cikin nan ba!?”.
Sosai Mommy ta tsira mata ido na second uku zuwa biyar sai kuma ta miƙe daga kwanciyar da take Atake fara'ar