Showing 51001 words to 54000 words out of 176046 words

Chapter 18 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete

sahihan magungunan Aysha Aliyu Garkuwa Wato Garkuwar Marubuta da kuma Ma'aurata na tabbata kunsan da cewa basirarta ba'a iya rubutun littafi ya tsaya ba hadda inganta rayuwar ma'aurata ta hanyar kawo musu Nagartattun abubuwa Ga duk wacce ta shirya saya seta tuntuɓi number ta 09097853276 muna iya tura kayan mu aduk inda kuke afaɗin Nigeria harma da ƙetare Dan Allah 'yar uwa idan baki shirya siyaba kada kiyi min magana muɓatawa kanmu lokaci...._



🤝🏻🤝🏻🤝🏻🤝🏻🥰😘sai.kunzo. sayan na gari maida kuɗi gida,

Washe gari Da safe suka ɗauki hanya zuwa Rugar Jauro Yaya sukayi ta'aziyya.
Bayan sun gama gaisawa ne Mommy tace.
“Hajja Nana zamu koma da Khausar dan gobe Insha Allah zasu koma makaranta”.

Kai Hajja Nana ta gyaɗa dan mutuwar ƙaninnata yasa tayi sanyi baki ɗaya.
Tace.
“Badamuwa ku koma da ita amma idan an kwana biyu ta riƙa zuwa saboda su saba da ‘Yan uwanta”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“Badamuwa Insha Allah zata zo”.

Kasancewar dama Khausar ta haɗa kayanta tun daren jiya yasa ta dauko jakarta sai kuma ta Rungume Hajja Nana tace.
“Hajja Nana zanyi kewarki ki riƙa zuwa bishiyar ƙare zancenka kina kirana dan Allah”.

Murmushi Hajja Nana tayi kana tace.
“Sai kace kin damu dani bayan rashin kunya kike min".
ƙaramin bakinta ta tura tare da ficewa tana cewa nidai zanyi kewarki.
Baki ɗaya Kakannints suka rakata jikin mota bayan sun haɗa mata tsaraba iri-iri Kama daga, Zabbi, Kaji, Ƙwan Zabbi, Nono jarka-jarka da kuma zuma man shanu.
Kawai sai Khausar ta fashe da kuka cikin raunin murya.
Tace.
“Aranan da nazo kamar haka da Baffa Umaru aka tareni yau kuma gashi babu shi!".
Hannunta Baffa Garga ya riƙe cikin rauni da zuba hawaye yace.
“Kiyi haƙuri Khausar haka rayuwar take idan kaini yau gobe ba kai bane, kuma in sha Allah zasuga SAKAYYAH”.

Hawayenta ta share tare da shiga mota tana ɗaga musu hannu Dije ma kan sosai tasha kukan rabuwa da Khausar.
Fatan sauƙa lafiya suka musu sannan suka ja motar suka tafi.

Khausar kuwa motarsu na isa harabar gidan Haiydar, Raudat da Ramadan suka taho da gudu suka rungumeta Ramadan ne yace.
“Addah Khausi nayi missing ɗinki”.
Kansa ta shafa tare da cewa.
“Nima nayi missing naku”.


“Addah Khausar Barka da dawowa daga zuwanki har gidan yayi haske, amma da bakinan duk saiyayi duhu”.
Cewar Haiydar
Ta wani wara manyan Idanunta tace.
“Kada kayi masu gidan suji”
ta faɗa tare da ɗaukar Ramadan suka shiga ciki afalon suka zube suna ta hiran bayan rabuwa.
Cikin sakin fuska Khausar ta kalli Raudat dake zuzzuɓura baki tace.
“A'a My happiness sis ya akayi ne?”.
Baki Raudat ta kuma turawa tare da cewa.
“Ba wani ai naga kinfi son Ramadan”.
Dariya mai sauti tayi tare da jawota ta ruggumeta.
Kana suka ci gaba da hirar yaushe gama. sallah kaɗai ke ɗagasu.

Bayan kwana biyu ya kama yau Asabar zasu koma makaranta kasancewar Asabar ne farkon satinsu Alhamis da juma'a kuma Weekend.
Tun wuri Khausar ta tashi bayan ta idar da sallar asbah tayi Azkharul sabah toilet ta shiga tayi wanka kana ta fito ta zauna gaban dressing mirrow ta shafe jikinta da lotion ɗinta kana ta shafa kajol a manyan Idanunta masu haske sai kuma ta shafa lips dinta Kaɗan tulin sumar kanta dake tsefe ta sanya farin Ribont ta kama ahankali ta buɗe duro ta ɗauki uniform ɗin ta dake goge maroon din wandon ta fara sanya wa sannan tasa ka farin riga sai kuma ta ɗauki farin ɗankwali ta ɗaura kana ta ɗauki maroon din hijab ta Sanya Wanda ya tsaya gwiwarta wani irin kyau tayi na ban mamaki sosai Uniform din ya amshets tamkar dan ita akayi.
A gaban Dressing mirrow ta tsaya ta ɗauki kwalban turare sun kai kala biyar ta feshe ilahirin jikinta dashi sannan ta ɗauki combos Fari ta Sanya tare da ɗaukar school bag ɗinta ta rataya kana ta fito falo.

Murmushi Mommy tayi tace.
“Manana kinyi kyau”.
Ta juya manyan Idanunta tace.
“Nogode Mommy na”.
Haiydar kam murmushi yayi yace.
“Yau za'ayi ruwa da ƙanƙara shugaban ’yan letti ta riga kowa shiryawa”.

Harara ta maka masa batare da tace komai ba ta shirya Raudat sannan sukayi Breakfast suka shiga mota Amina sai Harara take watsa mata ita kuwa khausar bata ma san tana yiba domin aƙasan ranta tunanin haɗuwarta da Moddibo take da kuma irin hukuncin da zai yanke mata.

Suna isa Makarantar lokacin har anfara shiga class cikin sauri sauri Khausar ta riƙe hannun Raudat suka nufi side dinsu Raudat ta ajiyeta a class kana da sauri ta juya, zata fita class ɗin kenan.
Taji Raudat ta saki ƙara tare da kiranta.
Da sauri ta juya tare da kamo Raudat ɗin da taga tana jujjuyawa, tsugunawa tayi tare da cewa.
“Raudat menene ya faru”.
Cikin kuka da yarfa hannu Raudat tace.
“Wayyo idona Adda Khausy ido, borkono".
Da sauri ta jawota tare da fara hura mata idon.
Sai kuma ta amshi goron ruwar da Antin su ke miƙa mata.
Wonke mata fuskar ta ta farayi tare da murza mata idon.
Cikin Sa'a kuwa ɗan abin da ta shiga idon ya fita.
A hankali ta buɗe idann nata, da tuni yayi jazir.
Cikin sanyi tace.
“Ayyah Raudy na sannu ko, yanzu dai ya fita ko?”.
Kai ta gyaɗa mata tare da kama hannun Antin nasu.
Ganin hakane yasa Khausar juyawa da sauri ta fito ta nufi harabar makarantar.

Shiru ba kowa a tsakiyar harabar alamun an gama shiga class kenan.

Cikin sassarfa ta fito daga side din ’yan nursery.
Kana ta nufi sude ɗinsu.

Da sassarfa ta nufi kan step ɗin.
Dai-dai lokacin kuma Moddibo ya fito daga class dinsu ya nufi ƙasa, a hankali yake take steps din yayinda hankalinsa baki ɗaya yana kan....!




Ki biya ki karanta, kiji ainin manufar labarin kiyi dariya kiyi shauƙi kibi haushi kiki tausayi kiyi kuka. Kiyi murmushi




By
*GARKUWAR MARUBUTA*
[19/07, 7:44 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: 📝🍇✨💫⏰🤴🏻👹❤️❤️❤️🍇

*SAKAYYAH*
_Page 9_

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*FREE PAGE NE ƴar uwa ki biya ki karanta abinki cikin Salamah, littafin SAKAYYAH 1k ne kacal 0661110170 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276. Kana in saki a Groups da na buɗe ba SAKAYYAH in da zaki karanta abinki salamun ƙaulum min rabbil rahim. Nama lfy fata lfy. Ba ruwan ki da jiran na sata na Allah ya isa*


Cikin nitsuwa yake tafiya, tare da taka steps ɗin a hankali, yana sauƙa ƙasa, yayinda hankalishi baki ɗaya ke bisa system nashi dayake kan hannunsa na dama yana daddanashi da hannun hagunsa, bisa dukkan alamu.
Abu mai mahimmanci ne yakeyi.

A dai-dai lokacin kuma Khausar ta iso bakin steps ɗin, cikin sauri take tafiya, da alamun tsoron kada malami ya rigata shiga aji ne.
Da sauri take tattaka steps ɗin tanayi sama.
Steps biyu ta taka ana uku, taji juyo da kanta da sauri dan jiyo muryar M Jameel na ce mata.
“Khausar sai yanzu?”.
Ba tare da ta tsaya ba, kana bata kuma juyo kanta ba taci gaba da tafiya a haka, hannunta na kan da ƙarfe dake gefen steps ɗin cikin yanayin sakewarta da M Jameel ɗin tace.
“Wallahi tun ɗazu muka iso fa Malam”.
Yana mai binta da ido yace.
“To kuma meya hanaki shiga class?”.
Still bata janye kanta daga kallonsa ba, kana bata tsaya daga haurawa saman da takeyi ba tace.
“Raudat ce ta tsaidani a side ɗin su”.
Da sauri yace.
“Da me ta tsaida ki?”.
Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa.
“Wai ƙwarone ya shiga idonta, shinefa tai ta ihu taƙi sakina dole saida aka cire matashi Allah sai kaga yadda idonta yayi jazir”.
Kanshi ya sunkuyar yana ɗan murza zaɓen azurfan dake yatsar yace.
“Ayya kwaro bai kyauta ba ya shiga idon Gimbiya Raudat”.
“Ai dai kam fa”.
Ta faɗina tana mai ƙoƙarin juyo kanta.
Cikin tsokana yace.
“Gashi kuwa har Malam Moddibo ya shiga ajinku”.
Cikin sauri ta kuma juyo kanta da dama bata gama juyashi ba cike da kaɗuwa tace.
“Da gaske?”.
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Tun ɗazuma kuwa”
Cikin yanayin tsoro ta ɗan zaro manyan udanunta tare da cewa.
“Na shiga ukuna”.
Murmushi M Jameel yayi tare da cewa.
“Ato kiyi sauri ki hau, in kinyi sa'a ya barki ki shiga”.
Jin haka yasa ta juyo da sauri tare da taka step ɗin gaba kana tayi kwanan haurawa kam steps ɗin da zai sadata da sama.
Wanda kuma dai-dai lokacin Moddibo ma ya taka step na ƙarshen kwanan.
Unexpected taji tayi karo da mutu.
Shi ma Moddibo ba zato ba tsammani yaji kanta ya bugi ƙirjinsa yayinda hannunta ya bugi System ɗin dake hannunsa ya subce ya tafi ƙasa da sauri ya sunkuyo ya cafe system ɗin da kana ya miƙe tsaye,

Ita kuwa Khausar cikin sauri ta ɗago kanta dai dai lokacin kuwa ya ɗago kansa shima ido cikon ido suka kalli juna kamar a fuzge ya furta.
“Again?”. a lokacin guda kuma, cikin tsananin takaici da zafin rai ya ɗaga tafin hannunsa na hagu ya yarfa mata wani irin gigitaccen mari mai masifar zafi gami da raɗaɗi.

M Jameel kuwa jin sautin sauƙan marin ne yashi ɗago kansa da sauri.

Ita kuwa Khausar wani irin gigitaccen ihu mai cike da rauni tare raɗaɗi ta saki, tare da dafe kuncinta kana ta rumtse idonta wanda duhu mai tarin yawa ya mamaye mata gani, kana tayi taga-taga ta koma baya zata faɗi, jin ta tafi suuuuu ƙafarta ta sule yasa takuma sakin wani ƙaran tare da buɗe idanunta, sai kuma tayi sauri ta medasu ta rufe sabida ganin wasu irin taurarin masu wutsiya da tartsatsi suna gilmawa ganinta sabida zafin marin da yasa suka mamayewa ganinta.

Gaba ɗaya ta sadakar domin tasan muddin ta faɗo nan to ita da karaya sun zama aminan juna.

M Jameel kuwa kanshi ya riƙe da hannu bibbiyu tare da faɗin.
“Innalillahi!!”.
Wanda faɗin hakane ya jawo hankalin Malam isa da yazo wucewa ta gefensa.
Shima ma Malam isa idonsa ya rumtse da ƙarfi tare da cewa.
“Yah Salam”.

Shi kuwa Moddibo cikin takaici yayi sauri miƙa hannunsa da nufin kamo hannunta amman ina tuni tayi nisa.
Sai yatsunta biyu ya samu ya riƙe da masifan ƙarfi.
Wanda saida suka bada sautin ƙas-ƙas.
Cikin zafin nama ya fincikota da ƙarfi wanda hakan yasa ta afka jikinsa.

Ita kuwa Khausar jinta a jikin mutum ne yasa tayi masa wani irin sahihin rugguma mai cike da razani dan gani take kamar dai har yanzu bata tsira ba.
Kanta ta cusa cikin ƙirjinsa tana mai shaƙan turarensa mai masifar ƙamshi.
Wanda a take nitsuwarta ta fara dawowa.

Shi kuwa Moddibo cikin tsoro da wani irin masifeffen abu da yaji ya soƙi tsakiyar kansa har zuwa cikin ƙahon zuciyarsa kana ya harba masa wasu irin masifaffun baƙin al'amuran a cikin jijiyoyin jikinsa da suka sa jikinsa sakin wani irin masifeffen karkarwa da sabauta aniyarsa, ya ware hannunsa tare da rumtse idanunsa da masifan ƙarfi.

M Jameel kuwa ajiyan zuciya mai ƙarfi ya sake tare da jingina bayansa da jikin ƙarfen.
a hankali ya kuma sakin numfashi tare da kallon yadda Moddibo ya buɗa hannayensa duka biyu kana ita kuma Khausar tana kwance bisa ƙirjinsa tayi lip tana ruggume dashi da masifan ƙarfi.

Wani irin shu'umin dariya mai sauti M Jameel ya sake.
Wanda hakan yasa Moddibo buɗe idanunsa kana dai-dai lokacin yaji gaba ɗaya tsikar jikinsa na tashi.

Malam isa kuwa sunkuyar da kansa yayi yana murmushi.

M Jameel kuwa dariya yake tare da nuna Modibbo da Khausar ɗin wacce tuni fuskarta tayi jazir shatin yatsun hannunsa sunyi ruɗu-ruɗu a farar fatarta.
Cikin sauri Moddibo ya ɓalle hannunta daga jikinsa tare da matsawa gefe da sauri.
Wani irin tsuke fuskarsa yayi tare da watsa mata kallon da yasa hantar cikinta kaɗawa.
Wanda cikin rawan jiki da rawan murya cike da rauni tace.
“Ana Aspet ya Mu'allim Allah mi larai ma on! Please! Kayi haƙuri”.
Ta ƙare mgnar cikin tsoro tare da gwamusa yaruka hudu duk a wuri ɗaya dan neman afuwa.
Shi kuwa Moddibo juyawa yayi tare da ratsa gefenta ya wuce kana cikin wata fusatacciyar murya mai matuƙar firgitarwa yace.
“Biyoni!”.
Cikin ɓarin jiki tace.
“Toh”.
Sannan ta miƙe tabi bayansa.

M Jameel dake riƙe da System ɗin yana juyawa yayi saurin bin bayansa da faɗin.
“Alhamdulillah kamar babu abinda ya samu System ɗin”.
Shi dai Moddibo ko juyawa baiyi ba bare kuma ya tankawa M Jameel.

Malam Isa kuwa dake ƙasa ido ya zirawa Khausar dake sauƙwa dafe kuncinta da kunne ya da tun da tasha marin ya bada sautin kauwww har yanzu ƙaran takeji, kana ga idanunta da suka kaɗa sukayi jawur asanda ta saƙƙo yace.
Fattanah sam bakya yin abinda ya dace a rayuwarki”.

Cikin zafin raɗaɗin marin da fuskarta keyi ta ɗago Idanunta da suke sake girma da ja ta kalli Malam Isa sai kuma tace.
“Wallahi bansa niba ne na juya ina kallon Malam Jameel ne dake yimin magana ne mukayi karo”.
Bata jira jin abinda zai ce ba tabi bayan M Jameel dake biye da Moddibo.

Cak Khausar ta tsaya daga bakin Office ɗin, karo na farko kenan arayuwarta da zata fara shiga Office ɗinsa, duk da cewa da basu da office da yawa, amma yanzu gyaran da akayi an haɗa Malamai biyu akan Office ɗaya Office din ba wasu masu girma bane, haka zalika ba ƙanana bane, sannan duk kusan ajere suke.
Ahankali Khausar ta maida Idanunta bakin office ɗin da akasa wasu irin flowes masu launi mai kyau da ɗaukar hankali aka jera suna fitar da wani irin sanyayyan ƙamshi.
Cikin Office ɗin kuwa Madaidaitan deks ne da kujeru ɗaya na fuskantar gabar ɗaya na fuskantar yamma daga gaban ko wanne kuma akwai kujeru guda biyu daga kan deks ɗin daga gefen damar sa akwai wani Cubet kamar kanta dake ɗauke da tarin littattafai na addini da kuma na boko cikin wajen kamar dai Library haka wurin yake.
Daga gefen hagunsa kuma flowes ne masu kyau da tsari daga jikin bangon kuma Room hitane ne maƙale abango yana fitar da ɗumi mai daɗi a jiki,
Sai kuma labulayen window da suka kasance farare sol Sanyayyan iska na kaɗawa daga bangon kudu dake kallon yamma TV ne maƙale abango daga tsakiya kuwa wani irin dakekken turkey carpet mai yawan gashi fari sai ratsin maroon kaɗan. sosai Office ɗin yayi kyau.

Shi kuwa Moddibo cikin nutsuwa da kuma zafin da zuciyarsa keyi masa ya zauna akan kujeran dake gabar yana fuskantar yamma yayin da M Jameel ya zauna akan kujeran dake yamma yana fuskantar gabar kana da sunan ko wannensu ajiki kujerarsa.

Ita kuwa khausar cikin tsananin tsoro ta ƙarasa shiga office ɗin tare da tsugunnawa agaban table ɗin da Moddibo ke zaune.
Ta riƙe kunnenta Muryanta Araunane wanda ke nuni da tsantsar tsoro da tashin hankali tace.
“Malam kayi haƙuri bansan kana tahowa ba”.
Shi kuwa Moddibo ko kallonta baiyi ba saboda yanda zuciyarsa ke tsananin ta farfasa ya tabbata idan yace zai daketa to zai iya karyata ko kuma ya sumar da ita hakan yasa ya janyo kujeran dake kusa dashi ya ɗaura ƙafafunsa akai kana ya lumshe idanunsa tare dasa hannu ya janyo Hiramin dake kansa ya rufe saman Idanunsa.

Cikin tsantsar nutsuwa da kuma sanyayyan sautin muryarsa mai zaƙi ya fara rara Ƙira'a acikin suratul Rahman yasan hakan shine kaɗai zai sanyaya masa ransa da zuciyarsa yasan muddin yace zai daketa ayanzu zai iya sumar da ita ko kuma karyata.
Saboda abubuwan da yarinyar ke masa yayi yawa.
Sabida tsabar raini da rashin kunya fa har gidansu ta bisa tayi masa rashin kunya sannan ta jima sa ciwo ayatsun ƙafansa wanda ya ɗauki tsawon kwanaki yana fama da ciwo.
Kana yaje ƙauyen su nan ma bata barshi ba saida ta bisa tayi masa rashin kunya ta nemi jefa shi acikin ruwa da wannan masifeffen sanyin garin nasu,
kana amakaranta ma bata barsa ba shin tsaranta ta mayar dashi kome?.

Ita kuwa khausar cikin Sanyayyar Muryanta me cike da tsoro tace.
“Ayyah malam na tuba kayi haƙuri wallahi bansani bane”.
Ƙin tanka mata Moddibo yayi ya cigaba da rera karatunsa cikin zazzaƙan muryansa.
Shi kuwa M Jameel Gyaran murya yayi hakan yasa Khausar tayi saurin Kallonsa da manyan Idanunta da suka kaɗa sukayi jawur.
Da ido yanuna mata Moddibo alamar ta cigaba da basa haƙuri.
Kai ta gyaɗa sannan ta cigaba da cewa.
“Ayyah Malam na roƙeka kayi haƙuri bazan sake ba”.

Acan sama ajinsu Khausar kuwa wani irin tsarin gini ne mai matuƙar kyau da ɗaukar hankali wasu irin windon Glass ne tsala-tsala masu tsayi da kyan tsari sannan ga flowes masu fitar da sanyayyan ƙamshi kana ga Room hita guda biyu gaba da baya daga farkon shiga class ɗin kuwa wani irin Black Board ne mai tsari irin wanda ake amfani dasu a manyan makarantu, kana ga wasu irin kujeru na zaman ɗalibai masu taushi da kyau, agaban ko wani kujeran ɗalibi akwai sunan sa ajiki, hakan yasa duk ɗalibar data shiga baza tasha wahala neman wajen zamanta ba wanda kuma manna sunan ake bisa alamu in an tashi kawai ɓarewa za'ayi a saka sunayen sabbin waɗanda zasu shigo ajin, kujeran Khausar shine na farko acikin jerin kujerun dake gaba da sunanta manne kamar haka _Khausar Usman Abubukar Lelewal._
Samira Sani ce ta ɗan juya Idanunta kan kujerar dake gefenta.
Wanda sunan Khausar dake manne kujerar afarkon.

Wani irin ya mutsa fuska tayi tamkar wacce taga wani abin ƙi cikin taɓe baki da tsanar mamallakiyar sunan tace.
“Ikon Allah wannan shine suna mai buƙatar hadda sunaye huɗu duk masu tsawo!”.
Ta Ida maganar tare da bankawa kujeran harara tamkar Khausar ɗin na kai, kana ta zauna daga baya inda sunan ta ke kai.

Asma'u dake gefe azaune tace.
“Ha'a sunane de ai ba wani abu ba kuma duk sunayene masu inganci da Kekkyawar nasaba naga dai sunanta sunane na ɗiya ga Annabi Muhammad (S.A.W) sannan sunan mahaifinta sune na sahabin Manzon Allah (S.A.W) haka zalika sunan kakanta sune na sahabin Manzon Allah (S.A.W).
Lelewal kuwa naga suna ne da kowa ke fatansa”.

Abeeda Sule ne ta watsa wa Asma'u harara tare da faɗin.
“Ke kuma wayasa bakin ki?”.
Taɓe baki Asma'u tayi kana tace.
“Ai gaskiyane daga kallon sunan baiwar Allah zata fara ƙanan magana”.
Ɗaya daga cikinsu manyan matan ajin nasu ne wacce bata fiye magana Hajia Khadija tace.
“Da wannan hatsaniyar da kukeyi tunda Moddibo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login