Showing 48001 words to 51000 words out of 176046 words
Ƙarfe nawa zamu tafi can jauro yayan sannan mai zakaje yi?”.
Cikin sanyi yace.
“Wata Rugar Fulani ce amma gaskiya akwai tafiya zamu tafi da yanzu tun da kaga ƙarfe tara zuwa sha ɗaya zamu isa Insha Allah,Yawanci ina zuwa karatu can wajen wani Malam Aliyu limamin Rugar tasu sannan kuma anyi masa rasuwa shine nakeso Inje inyi masa ta'aziyya to kaga motata ta samu matsala”.
Jinjina kai Moddibo yayi da faɗin.
“Allah yajiƙan musulmi toh ba matsala muje tunda dama yanzu babu abinda nake yi, amma dai zamu dawo da wuri ko tunda kasan akwai ‘yan hadda?”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa yace.
Toh ba matsala Allah dai ya kaimu lafiya”.
“Amin”. Yace
Sannan ya miƙe suka shiga mota suka fice kasancewar Ashirye suke.
Moddibo kuwa ƙira'ar Sheykh Jabeer ya kunna suna tafiya yana saurara tare da bin bakinsa tafiya mai ɗan nisa sukayi a haka.
Malam Arɗo ne ya katse shirun da faɗin.
“Gaskiya wannan tsarin ginin Makarantar yayi kyau Moddibo kayi ƙoƙari”.
Murmushi Moddibo yayi yace.
“Uhum Masha Allah”.
Haka suka cigaba da tafiya suna taɓa hira jefi-jefi wanda mafi yawan hiran Malam Arɗo keyi shi dai Moddibo daga Uhm sai um-um. Koko yace Masha Allah ko Alhamdulillah.
Suna dosan Rugar Moddibo yaga wajen kamar Rafi hayaƙi na tasowa lokaci ɗaya wani irin sanyi mai ratsa jiki ya ratsa gaba ɗaya ilahirin jikinsa Atake ya lumshe idanunsa tare da cije laɓɓansa na ƙasa.
Ahankali ya juya ya kalli malam Arɗo yace.
“Kai Malam garin nan akwai sanyi”.
Murmushi malam Arɗo yayi yace.
“Sosai ma kuwa garin akwai sanyi”.
Kai ya jinjina tare da jan numfashi kana ya fesar da huci mai ɗan karen ɗumi.
Dai-dai lokacin yayi parking a ƙofar gidan malam liman kana yana motsa laɓɓansa alamar Tasbihi yake.
“Subahanallahi”. Ya furta a hankali sabida tsarin garin yayi matuƙar ratsa shi.
Yaya Abba da shigowarsa kenan ya isa garesu tare da miƙawa Moddibo hannu sukayi musabaha kana yace.
“Sannun ku da zuwa fatan kunzo lafiya?”
Kai Moddibo ya gyaɗa da faɗin.
“Alhamdulillah".
Kallon Malam Arɗo Yaya Abba yayi yace.
“Tsoho mai ran ƙarfe”.
Murmushi Malam Arɗo yayi da faɗin.
“Ya akayi ɗan saurayi”.
Cikin alamun sanayya yayi musu jagora, har cikin ɗakin Malam Liman.
Cike da mutuntaka daddataku Malam Liman yake musu marhabin da zuwa.
“A'a Malam Arɗo kaine tafe, sannu da zuwa, on laleko mon njabɓa ma mon laleko bagare”.
Sai kuma ya juyo ya kalli
Yaya Abba kana yace.
“Jeka kawo musu abin taɓa wa”.
Kai yaya Abba ya gyaɗa sannan ya miƙe ya shiga cikin gida.
Ba jimawa ya dawo hannunsa riƙe da Akwashi guda biyu akan faranti sannan ya koma ya sake ɗauko kofi guda biyu ya buɗe akwashin daya fi girma Gashesh-shen naman ragone da aka masa gashin ruwa ruwa yayin da ɗaya akwashin ke ɗauke da madaran shanu mai ɗumi Yaya Abba yace.
“Bismilla kuci”.
Bai jira jin mai zasu ceba ya miƙe yabar wajen.
Shi kuwa Moddibo lumshe idanunsa yayi sakamakon ƙamahin naman daya ratsa hancinsa da kuma yanda gashin yayi kyau a ido da farko baiyi niyyan ciba amma ganin yanda gidan yake atsaftace da kuma masu gidan ga wani irin ƙamshi dake tashi yasa ya fara cin naman cikin nutsuwa tare da zuba madaran sosai yaci dan baƙaramin daɗi naman yayi ba, gashi dama baiyi breakfast ba.
Malam Arɗo ma sosai yaci sannan yasha madaran wanda shi kuwa kirtansa ke hamada ci sai yazo nan yake kashe tsatsan haƙoransa shiyasa ba cika fashin zuwa duk wata yana zuwa sai biyu.
Bayan sun kammala ne Malam Liman yashigo ya zauna daga gefen Malam Arɗo ya bashi hannu sukayi musabaha.
Malam Arɗo yace.
“Fatan mun same ku lafiya ya kuma muka ji da ƙarin haƙuri?”.
Kai Malam Liman gyaɗa tare da faɗin.
“Hakuri mungode Allah”.
Malam Arɗo yace.
“Allah ya jiƙansa da rahma da kuma dukkan musulman da suka rigamu gidan gaskiya”.
“Ameen ya hayyu ya ƙayyum”.
ya amsa.
Shima Moddibo cike da girmamawa yace.
“Malam ya mukaji da haƙuri Ubangiji Allah ya jikansa da Rahman Allah ya haskaka makwancinsa”.
Malam Liman ya amsa da.
“Ameen”.
Baffa Liman ya kalli Malam Arɗo yace.
“Muje ka gaida Babbar Addarmu wacce take madadin mahaifiyarmu”.
Kai Malam Arɗo ya gyaɗa kana yace.
“Toh ba matsala muje”.
Ya ida Maganar suna miƙewa.
Baffa Liman da malam Arɗo na gaba yayin da Moddibo da yaya Abba ke bayansu Moddibo na ƙarewa yanayin garin kallon sosai garin ya burgesa ko ina ka duba tsaf-tsaf babu alamar ƙazanta ko datti.
Bakinsu ɗauke da Sallama suka shiga gidan Hajja Nana lokacin tana zaune atsakar gidan kan ta burma.
Baffa Liman ya kalli Hajja Nana yace.
“Ga Yayana kuma ɗalibina yazo zai gaisheki”.
Tace.
“Ayyah sannunku da zuwa”.
Sannan ta miƙe ta shimfiɗa musu darduma dake tsaf dashi babu alamar datti ajiki komai na gidanta tsaf babu datti duk da stufanta amma komai nata tsaf yake.
Sosai garin da mutanen garin suka burge Moddibo komai na garin akimtse.
Gaisawa sukayi da Hajja Nana sannan suka yi mata ta'aziyya madara mai ɗumi tasa aka kawo musu. Koda sukace Alhamdulillah fir tace dolefa susha ita baƙo baya zuwa wurinta ya fita baici komaiba.
Madarar kawai Moddibo yasha kasancewar ya ƙoshi agidan malam Liman Aransa kuwa sai yaba karamci da dattakon mutanen yake.
Aɓangaren Khausar kuwa tana can rafi tare da Dije da Sadik sunje ɗiban ƙwan Zabbi da kuma kayan lambu dake hannun Khausar bayan sun gama suka fito kallon Sadik da Dije Khausar tayi tace.
“Tunda wayar yaya Abba na hannu na zanje Bishiyar ƙare zancenka in Kira Mommy na”.
Kai suka gyaɗa mata da faɗin.
“Muje toh”.
Bayan fitowarsu daga gidan Hajja Nana Moddibo ya ciro wayarsa da niyyar kira sai yaga ba network kallon Yaya Abba yayi yace.
“Baku da network ne?”.
Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace.
“Eh bamu dashi amma akwai inda zaka samu idan kana da buƙata sai muje in kaika wajen akwai service ta nan nede babu”.
Kai Moddibo ya gyaɗa yace.
“Eh inada buƙata gaskiya muje”.
Sai kuma ya juya ya kalli Malam Arɗo da Baffa Liman yace.
“Bari zamuje ya rakani in sami network ina so zanyi kira”.
Baffa Liman yayi Murmushi yace.
“Yau ka shigo Rugar Fulanin da basu da network sai anje annema ko?”.
Dan murmushin Moddibo yayi tare da shafa sajensa zuwa gyamunsa daya ƙawata kyawun fuskarsa.
Malam Liman ne yace.
“Abba in kunje ku karasa cikin Rafi Modibbo yayiwa Jauron garin nan ta'aziyya sannan kuce yazo munada boƙo ne”.
Jinjina kai Abba yayi sannan suka fita shi kuma Malam Arɗo da Baffa Liman suka wuce can gida domin ƙara karatu.
Suna fita Moddibo ya kalli Yaya Abba yace.
“Kai sanyin garin kun nan yayi yawa bari na ɗauki Jacket nasa”.
Ya faɗa tare da nufar motar ya buɗe ya ɗauki farin Jacket ya ɗaura akan Army green ɗin jallabiyarsa da yayi masifar yi masa kyau.
Murmushi Yaya Abba yayi Aransa yana yaba baiwar kyawunsa da kuma iya Dressing ɗin sa.
Ta cikin wata siririyar hanya dake ɗauke da korayen ciyayi masu kyau da ƙamshi suka ratsa.
Sai wani lumshe ido Moddibo keyi yana jin kamar ya tabbata awajen saboda yanda garin ya tsaru komai nasu mai kyaune.
Ta Cikin wannan Hanyar suka ɓulla har Rafi Yaya Abba nata yi masa hira shi dai daga Uhm sai Um-um saiko Masha Allah.
kasancewar sa ba mutum nai me surutu ba.
Suna shiga cikin Rafin Moddibo ya dunƙule hannunsa waje ɗaya jin sanyin wajen yafi na cikin garin juyawa yayi ya kalli Yaya Abba kana yace.
“Muma muna da sanyi amma sanyin ku yafi namu sosai”.
Kai Yaya Abba ya gyaɗa yace.
“Sosai ma ai tanan kam munfi sanyi”.
Jinjina kai Moddibo yayi yace.
“To ku riƙa rage Bishiyoyi mana sanyin be damun ku?”.
Yaya Abba yace.
“Aikuwa mu munajin daɗin sanyin”.
Moddibo yace.
“Masha Allah”.
Acan cikin rafi kuwa Sadik riƙe yake da ƙwan Zabbi mai yawa yayin da Khausar ke riƙe da ma daidaicin kwando ahannunta wanda ke ɗauke da,Inabi,Tuffa, Mangoro,Abarba,Kwakwa, Lemo,da sauran kayan itatuwa yayin da ɗaya hannunta ke riƙe da wayar Yaya Abba tana dannawa Sadik ya juya ya kalleta yace.
“Khausar da kin haƙura da danna wayar nan sai mun tsallake wannan ruwan dake gudu kinga akwai duwatsu aciki”.
Still hankalinta na kan wayar tace.
“Kada ka damu ai ina kallo”.
Kai ya gyaɗa mata sannan suka cigaba da tafiya.
Yaya Abba kuwa yana ƙoƙarin karya kwanar da zai sadasu da Bishiyar ƙare zancenka ya hango Baffa Jauro acikin Rafi juyawa yayi ya kalli Moddibo yace.
Gacan Baffa na Jauron garin nan da Malam yace mubiya kamasa ta'aziyya”.
Kai Moddibo ya gyaɗa yace.
“Toh mu ƙara sa".
Kai Yaya Abba ya gyaɗa sannan suka nufi wajen Moddibo kuwa wayarsa ya ciro a aljihu yana duba ko akwai network ata wajen Dai-dai lokacin da Khausar ta iso wajen baki ɗaya hankalinta da nutsuwar ta nakan wayar tana saka number Mommy.
Kallon Dije Yaya Abba yayi wacce tuni ta tsallake ƙoramar ruwan yace.
“Dije har kun ɗebo ƙwoyin?”.
Kai Dije ta gyaɗa masa kana tace.
“Eh Ya Abba".
Moddibo kuwa sam bai lura da mutum agabansa ba, ya ɗago ƙafarsa na dama zai tsallaka yashiga rafin kenan, ita kuma Khausar ta ɗago ƙafarta na hagu zata tsallaka tafita a rafin ji kake gub suka bugi juna da ƙafafunsu.
Tagal-tagal Khausar tayi baya zata fadi yayin da shikuma Moddibo da ƙyar ya tsaida kansa daga faduwar da zai yi.
Ita kuwa khausar Atsorace ta saki kwandon kayan Marmarin dake hannunta tare da kai hannu ta riƙe rigarsa da hannu ɗaya yayin da ɗaya hannun ke riƙe gam da wayar Yaya Abba.
A kuma lokaci guda ta rumtse idanunta tare da sakin kara.
Shi kuwa Moddibo cikin hanzari yakai hannu ya riƙota sai alokacin idanunsa suka sauƙa akan fuskarta ita.
Ita kuwa Khausar sassayan numfashi ta fesar jin an riƙeta bata faɗiba yasa ta ɗago kan Idanunta ne suka sauƙa akan fuskar Moddibo.
Lokaci ɗaya jikinta ya ɗauki rawa na tsananin tsoro da firgicin ganinsa kawai sai ta sake hannunsa tare da rintse Idanunta tayi baya zata faɗa cikin ruwan,Cikin zafin nama yasanya Lallausan tafin hannunsa ya riƙo hannunta tare da fisgota ta tsallaka sai yayi wucewarsa batare daya juya ya kalleta ba.
Ita kuwa khausar banda rawa babu abinda jikinta keyi cikin rawan murya tace.
Ka-ka-kayi ha-ƙuri ban gankaba shiyasa, shi kuwa Moddibo ko juyawa baiyi ba bare yaji abinda take faɗa yabar wajen.
Sai alokacin Yaya Abba ya lura da yayan itatuwan ta data zubar yace.
“Ya haka Khausar mai yasa bakya kallon gabanki in kina tafiya?”.
Cikin rawan murya tace.
“Tsautsayine”.
Tafaɗa tare da barin wajen aranta kuwa tunani take yau kuna Moddibo Arugar mu me ya kawo sa? kuma mai ya haɗa sa da yaya Abba? to me ya zoyi? da wannan tunanin ta isa Bishiyar ƙare zancenka tana isa ta hau kan dutse. dake farko ta zauna tare da sa hannunta ta riƙe reshen, kana ta kiran number Mommy.
Shi kuwa Moddibo bayan sun karasa wajen Baffa Jauro.
yace.
“Ina yini Baffa fatan mun same ku lafiya ya kuma ƙarin haƙuri?”.
Baffa Jauro kuwa cikin yanayin sauƙin kansa da kuma dattako ya amsa da.
“Haƙuri Alhamdulillah fatan kunzo lafiya?”.
Moddibo ya amsa da. “Lafiya Ubangij Allah yajiƙan sa da rahma idan kuma tamu tazo Allah yasa mu cika da Imani”.
Baffa Jauro ya amsa da.
“Ameen”.
Yaya Abba ya kalli Baffa Jauro da faɗin.
“Bari muje na rakasa Bishiyar ƙare zencen ka kuma Baba Yace kaje tare suke da Malam Arɗo".
Kai Baffa Jauro ya gyaɗa kana yace.
“Adawo lafiya”.
Miƙewa sukayi suka nufi Bishiyar ƙare zancenka tun kafin su isa Moddibo ke jiyo suturatai da dariyar mutane Aransa yace to lafiya dai.
Suna ƙarasawa yaga tsoffi,Matasa,maza,da mata kowa maƙale da waya akunnensa ahankali kunnuwansu ke jiyo masa kamar sautin Muryan Khausar da mamaki ya ɗaga kansa gefen yamma idanunsa suka sauƙa akanta saman dutse kana kanta na bisa reshen Bishiyar.
Aransa yace to ashe ga inda ta samo ɗabi'ar hawa bishiya wato garin ne dole sai akan bishiya ake waya wannan shine gado.
Ya juya tare da kallon yaya Abba yace.
“Dole sai na hau kan Bishiya zanyi wayar?”.
Girgiza kai Yaya Abba yayi yace.
“A'a ko akan dutsen ma zaka samu network”.
Jinjina kai Moddibo yayi yace.
“To ku maida ƙa'ida mana mata su hau kan duwatsu maza su hau kan Bishiya idan ya kama dole ne sai an hau kan Bishiya ko kuma ku maida lokacin yin wayar mata daban lokacin yi. Wayar maza da ban kusa tsari da ƙa'idar musulunci ku dena gwamutsuwa haka”.
Jinjina kai Yaya Abba yayi yace.
“Gaskiya ne kabamu shawarar data dace Insha Allah za'ayi haka zan faɗawa Baffa Jauro ayi haka”.
Moddibo kuwa cewa yayi.
“Ai ya kamata ayi haka yanzu Meye amfanin ga mata asama sannan ga maza aƙasa ko kuma duk suna gwamutse maza da mata ko da duk kan ku 'yan uwane ai yakamata ayi abu duka bisa tsarin Addini ko ba haka ba bai dace ba duk da cewa yawancin ku ’yan uwane amma akwai auratayya atsakanin wasu”.
Cikin jin daɗin Nasiyyar da ya masa da gamsuwa Yaya Abba yace.
“Hakane Insha Allah za'a gyara malam”.
Ita kuwa khausar sam batasan Moddibo sun zo wajen ba.
Bayan sun gama gaisawa da Mommy.
Mommy tace.
“Khausar kwana biyu baki kira ba kuma kinsan ba zai yiwu na kira kiba”.
Araunane Khausar da mutuwar Baffa Umaru ya dawo mata sabo tace.
“Mommy ankashe Baffa Umaru har gida aka kashesa Mommy agaban idanuna aka kashesa!”.
Shi kuwa Moddibo hankalinsa na kan yiwa Yaya Abba magana bai san mai take faɗa ba juyawar da zai yi yaji tana cewa.
“Mommy har anyi sadakan bakwai hankalina ne bai kwanta ba”.
ta faɗa hawaye na zuba daga idanunta.
Shi kuwa Moddibo ido ya zuba mata ganin yanda hawaye ke kwaranya daga idanunta.
Khausar tace.
“Mommy ai zakizo kiyi mana ta'aziyya ko?”.
Mommy da mutuwar ya kashe mata jiki tace.
“Insha Allahu zamu zo, nasan idan na faɗawa Abbanki ba zai hana ba, ki shirya idan nazo zamu taho tare, dan Asma'u tazo tayi min magana batun zaku koma makaranta, kishirya kayanki idan muka zo zamu tafi tare idan Hajja Nana ta yarda”.
lumshe Idanunta tayi tace.
“Baza ma ta hana ba Insha Allah idan kunzo zamu tafi tare dan dama tace zanje Ɓadamaye wajen Baffa na nacan kuma sunzo ta'aziyya mun haɗu dasu, sannan ma Addata Ikki tazo mun haɗu da ita sai wani lokaci zanje Ɓadamaye nama karɓi number su, suma sunce dan suna sauri ne kuma mun haɗu amma da zasu je su duba ni anma munyi canjin number”.
Cikin sanyi Mommy tace.
“Toh shikenan babu damuwa ki shirya idan nazo zamu taho Insha Allah gobe zamu zo ta'aziyya”.
Sallama Mommy ta mata.
Juyawar da zatayi Idanunta suka sauƙa akan Moddibo daya tsareta da ido saida ta kusa faɗuwa saboda tsoron ganinsa.
Da ido ya mata alamar ta saƙƙo kafin ƙiftawa da Bismillah kuwa ta diro ƙasa.
Kallon Dije dake jiranta tayi tace.
“Mu tafi”
Yaya Abba ya miƙa mata kwandon kayan Marmarin ta data zubar yace.
“Gashi kin zubar dasu na ɗebo miki”.
Kamar wacce aka fisgo maganar daga bakinta tace.
“Banaso ka bashi na bashi”.
Sai da ta rufe bakinta asannan ta tuna mai ta faɗa hannu Dije ta fusga tace.
“Mutafi".
Shi kuwa Yaya Abba gyara riƙon kondon yayi.
Shi kuwa Moddibo ɗaya daga cikin duwatsun wajen ya samu ya zauna tare da kiran wayar M Jameel.
M Jameel na ɗagawa Yayi Sallama.
Amsawa Moddibo yayi tare da faɗin.
“Kada kaje kata nemana nasan zaka ne meni bana nan sannan ka kira wayata kaji akashe ina wani ƙauye ne da mukaje da Malam Arɗo amma Insha Allah zamu dawo kafin Azahar".
M Jameel yace.
“Toh meyasa baka gaya min ba tun ɗazu”.
Cikin yanayin shaƙuwa yace.
“Nima zuwan ba zata ne, kuma lokacin nasan kana bacci”.
Cikin sauƙe numfashi M Jameel yace.
“Toh badamuwa Allah ya dawo daku lafiya”.
“Ameen”. Yace tare da katse kiran.
Bayan ankira sallan Azahar sun idar kai tsaye wajen motarsu suka nufa Yaya Abba ne ya zo ya miƙa masa kwandon kayan Marmarin da Khausar tace abashi.
Cikin yanayin nutsuwarsa da kuma sanyin murya sa yace.
“A'a Nagode amma ka ajiye awajenka”
Murmushi yaya Abba yayi yace.
“To ai bani ce na baka ba Khausar ce tace abaka”.
Yana gama faɗa ya buɗe bayan motar ya saka masa.
Malam Liman ma ya basu Zabbi Baffa Jauro kuma ya aiko musu da ƙwan Zabbi Hajja Nana kuma ta aiko musu da zuma sannan suka yi musu sallama suka tafi Moddibo kuwa yaba karamci ci halaccin mutanen sukayi.
Suna shiga cikin gari ya wuce da Malam Arɗo gidansa ya ajiye sa sannan ya sauke masa ƙwan Zabbin da kuma Zabbin da goran zuma.
Malam Arɗo yace.
“Ka ɗauki Zabbin da kuma ƙwoyin mana”.
Kai Moddibo ya girgiza yace.
“A'a wannan zumar ma ya isheni”.
Ya ida maganar tare da jan motar ya fice zuwa gidansa.
Acan ɓangaren Mommy kuwa da daren ta samu Lamiɗo ta faɗa masa maganar rasuwar da kuma son zuwanta suyi ta'aziyya, Cikin jimami yace toh Allah ya kaimu gobe zasu zo.
*WOHOHO IN KAJI ANA ƘI GUDU TABBAS SA GUDU NE BEZO BA*
_Ina kuke Ma'aurata masu sha'awar ganin sun zama taurari kuma fitilu a idanun mazajensu Uwar gida,Amarya,Tsakar gida,hadda tan kaɗen gida Shararriya kuma ƙasaitacciya data saba kawo muku nau'ikan sirrin sahihan magungunan ma'aurata wato *AYSHA ALIYU GARKUWA* Garkuwar Marubuta ayau ma ta dawo muku da Ingantattun magungunan mata masu kyau da inganci domin gyara kanki ki zamto tauraruwa a idanun mijinki...Muna da Ingantattun Abubuwa kamar haka_ :_Munada Garin mallaka, garin maɗi, garin Hakkin mayi, garin ɓelɗamhi Garin ilanwaddihi, Gumbar da ba'a baiwa mai kishiya, Gumbar kolli mai kellin al'khairi, Gumbar Riɗi wato 3 in 1, Gumbar makwaranyi, Masin Maliƙi mai masifar ƙarfi da matse mace, ka masin Daɗi har Maɗigan Akwai, kwanon ƙasaitacciyar mace mai masifar kyau da ratsa jiki da samar da inƙantacciyar ni'ima yanada abubuwa masu kyau haɗinsa, Zumar goron tula mai masifar kyau, tsumin dabino, mai ratsa jiki, tsumin Riɗi mai ƙarfi, Furar Mata mai tsastsafo da ni'imantaccen damshi, Cida kaza, Ciccibi Abodi, Tsumin Ɓaure, tuwon ɓauren, kana akwai maganin sanyi sadidan, da dai sauransu...Se kuma fannin ƙamshi kasance da Shu'umin ƙamshi wanda ze gigita ƙwaƙwalwar Oga tare da jin ko wacce mace bata kaiba...._ _Shin ko kina da labarin Miskilinci da ƙasaitar Rayyan Naaan amma lokaci ɗaya ya zamto zautacce sakali akan soyayyar Jannart bakomai Jannart ta riƙe ba face sirrinkan gyara da kuma shu'uman humran da kulaccar sirri na Aysha Aliyu Garkuwa(Tubali) tabbas taga tasirin haka domin Naanunta ya zame mata tamkar bawa_
_Shin ko kinsan sihirtaccen haɗin da Aysha ke sha kenan ta zamto tauraruwa a idanun Hamma Yusuf(Miwasmiti)...Tabbas Mahmud ya zamto zautacce kuma makaho akan sauyayyar Bazawara wato khadijarsa duk da kuwa gashi da budurwa(Namiji Baya Kaɗan) ko kinsan hakan nada alaƙa da amfani da sahihan maganin da kuma shu'uman humran Aysha Aliyu Garkuwa??.Nasan ba zaka ku manta da irin kima da kuma darajar da Aysha ke dashi acikin Idanun Sheik Jabeer ɗin ta duk da kuwa shekaru sunja anma jinta yake tamkar budurwa 'yar sha bakwai(Garkuwa) sirrin hakan na tare da Ingantattun kuma