Showing 138001 words to 141000 words out of 176046 words

Chapter 47 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete

da Mayyar wannan yaro mai ƙwala-ƙwalan ido daya karye nake son kawar dashi tun da shi wancan mai kama da Brolas ɗin Uwarsa ta shayar dashi saɓani, tunda kinga wannan hatsarin ma shi na shiryawa abi takansa amma, ba'a samu babban ba akabi takan ƙaramin”.
Sai kuma ta sauƙe numfashi tare da jan dogon tsaki kana tace.
“Dole saina koma na samu boka Kar'uzu da maganar ayi duk abinda za ayi nikam Haiydar shine babban matsala ta tunda shi Ramadan shine ƙarami akan Aminu, babu yanda za ayi Aminu na raye aɗauki Sarauta abawa Ramadan dole dai sai ɗana ɗin dai”.
Cikin sauri Hajiya Lami ta katseta tare da cewa.
“Kul-Kul Hajiya Bunayya kada kiyi la'akari da wannan ƙaramin tunanin naki, ba kiji Malam Bahaushe na cewa ɗan hakin daka raina shike tsole maka Ido ba?.
To ki rufa wa kanki asiri ki kawar dasu duka biyun hankalinki ya kwanta ki samu nutsuwa da salama aranki”.
Kana ta saki wani murmushi tare da cewa.
“Kinga idan kika gama dasu ɗaya ce zaki samu nutsuwa akanta itace Raudat da kuma Khausar.
Kinga Khausar kuwa ba ƴar gidan bace babu yanda za ayi agola tavi gadon Sarauta koda na mijine bare kuma mace. Raudat kuwa ƙarama ce kuma mace.
Amman Haiydar da Ramadan dai kaudasu, da kike batun Ramadan shine ƙarami a kan sulaiman, sau nawa manyan Yayu ke zaune ake bawa ƙannen su Sarautar, ni dai shawarar da zan baki yanda zaki gama da Haiydar haka zaki gama da Ramadan”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi tare da gyara zaman wayar akunnenta kana tace.
“Haka ne fa kuma aini duk wannan tunanin bai zo min ba, atunanina idan na kawar da Haiydar shikenan”.
Girgiza kai Hajiya Lami tayi tare da faɗin.
“A'a tsaya kallon ruwa kwaɗo ya miki ƙafa, har kina wani batun shine ƙaramin akan Aminu ai ba'a wannan zancen kima rufawa kanki asiri, kigama dasu gaba ɗaya to asannan hankalin zai kwanta, ki samu nutsuwa anan ne zaki tabbatar sarauta ahannun Aminu take, ke kuma kin zama Gimbiyar Gembulan Matar sarki Uwar sarki amma muddin ƴaƴan wancan koɗaɗɗiyar matar na nan keda Saurauta saidai hange daga naisa”.
Jinjina kai Hajiya Bunayya tayi cike da gamsuwa kana tace.
“Aikuwa hakane Nifa duk wannan tunanin bai zomin ba shiyasa nake alfahari dake ƙawata.
Insha Allah zanje muyi magana da boka Kar'uzu asan yanda za'a ɓullowa lamarin”.
Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh nima Insha Allah gobe idan muka je zan faɗa masa ya tsaida rana da Samira zata fara zuwa wajensa suyi satin, tunda dai yace idan ya kusance tama zai mayar mata da budurcinta ai shikenan”.
Atare suka sheƙe da dariyamai cike da farin ciki da annushawa kana Hajiya Bunayya tace.
“Ai dai haka yafi shiyasa na yarda da aikin Boka Kar'uzu kamar yankan wuƙa dan sha yanzu magani yanzu ne tun yaushe muke bin boka bursunu tsawon shekaru ba biyan buƙata sai asaran kuɗi”.
Jinjina kai Hajiya Lami tayi kana tayi mata Sallama suka katse wayar.

Aɓangaren Abban M Jameel kuwa tsaye yake ajikin window falonsa ya tsirawa harabar gidan Ido tun bayan fitar Motar M Jameel ya kasa motsa wa daga wajen.
Hajiya Karima data fito daga Bedroom ɗin sa ta dubesa cike da kulawa tace.
“Ya dai Alhj tun tuni kana tsaye ana ka gaza motsa sama da awa biyu kenan tun bayan fitar motar Jameel kake tsaye lafiya kuwa?”.
Cikin wani irin yanayi ya lumshe idonsa.
Haka nan yaji ruwan hawaye na tsats-tsafo masa a hankali ya sauƙe ajiyar zuciya tare da furzar da iska kana yace.
“Haka nan dai narasa me nake tunawa awajen nan”.
Ajiyar zuciya ta sauƙe tare da dafa bayansa kana tace.
“Toh kazo ka zauna mana”.
Girgiza kai yayi tare da fesar da numfashi kana cikin sanyi murya yace.
“Ina ga ko dan garin dana gani da alamun hadari ne ko yaya ne ban sani ba”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Toh kadawo ka zauna dan Allah tsayuwar tayi yawa”.
Kai ya gyaɗa lokaci ɗaya yaji wani irin masifaffen rauni mai haɗe da bugun zuciya ya rufe sa Atake yaji Idanunsa na tsats-tsafo da ruwan hawaye masu ɗumi yayin da zuciyarsa ya cigaba da tsinkewa jikinsa na mutuwa tamkar ana zare masa laka cikin sanyi jiki yaja ƙafafunsa da yaji sunyi masa mugun nauyi ya zauna akan kujera tare da kwanciya akan 3sitter kana ya lumshe Idanunsa.
Cike da kulawa tace.
“Ya dai lafiya kuwa kashiga ciki mana?”.
Girgiza kai yayi still zuciyarsa na cigaba da bugawa yayinda muryarsa ke ɗauke da rauni yace.
“Please Karima ki barni in kwanta inaji kamar kaina na ciwo”.
Cikin sauri tace.
“Alhj kad dai BP kane?”.
Girgiza kai yayi still Idanunsa na lumshe yace.
“A'a ba BP na bane bari dai mu gani”.
Zama tayi daga hannun kujeran kana tace.
“Toh kasha maganin ka kuwa?”.
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
“Eh sosai ma yan zun nan kafin Jameelu ya fita ya bani nasha”.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
“Eh ƙwarai kuwa hakane toh Allah ya sawwaƙa”.
Ahankali yace.
“Ameen”, Miƙewa tayi tare da shiga Bedroom ɗin sa ta kwanta.

Ɓangaren Moddibo kuwa har Misalin sha biyu da kwata yana zaune dafe da ƙirjinsa dake cigaba da bugawa ahankali ya ɗago kansa tare da shafa gefen wayarsa haske ya bayyana tare da nuna masa ƙarfe 12:15 afili ya furta.
“Har yanzu J bai zoba”.
Yayi mgnar tare da shiga Call log yayi dearling number M Jameel amma ga mamakinsa sai yaji Swich off.
Cikin yanayin damuwa ya dafe kansa tare da cewa.
“Ikon Allah lafiya kuwa wayar J arufe?”.
Kallonsa ya mayar kan babbar wayarsa tare da ɗauka kana ya fito da ɗaya number M Jameel ya kira Shima still Swich off.
Miƙewa tsaye yayi ido a lumshe yace.
“Ha'a ya wayar J akashe kuma dai J baya kashe wayarsa, to amma mai yafaru yau wayarsa akashe toh me yake faruwa bayan ya faɗa min yau zai dawo!?”,l.
Yayi maganar cikin zulumi
“Ya ilahi ya mujabat da'awati, to kuma ko kafin J ya fito sai da ya kirni yace zaije wajen Abba ya sallame sa sannan yazo amma kuma har yanzu bai zoba”.

Atake wata zuciyar tace kasani ko yazo suna tare da Innayi suna can suna ƙus-ƙus atake ya amince da abinda zuciyarsa ya raya masa cikin mutuwar jiki ya nufi ƙofan falonsa tare da buɗewa.
Wani sanyayyan iska ya hurasa ahankali ya ɗaga kansa sama gani yayi hadari ya fara haduwa sai walƙiya dake haskawa can ƙasa alamun yanzu hadarin ya fara, garin ya danyu duhu sakamakon rashin wuta ga kuma hadarin,
ahankali yabi sararin samaniyar da kallo ganin yanda hadarin yayiwa garin zobe kana aƙasan ransa yace to kodai wannan hadarin ne ya hana J zuwa sai kuma yace to kodai yana ɗakin Innayi ya faɗa yana taka step ɗin ahankali.
Cikin sauri Innayi ta haske masa ido da touch light mai masifar haske cikin han zari ya Janye hannuunsa dake danne da J ɗinsa ya tare Idanunsa dashi saboda hasken touchlight daya haska masa ido.
Cike da kulawa Innayi tace.
“Moddibo ya dai lafiya ina zuwa Atsakiyar adaren nan?”.
Ahankali ya sake sakƙowa daga kan step ɗin tare da jingina bayansa da jikin filan barandarsa, kana hannunsa na dama na kan flowes dake gefe yace.
“Kece fa kike ganinsa tsakiyar dare ne, dudu shabiyu da rabi ne fa yanzu”.
Kallonsa tayi tare da cewa.
“Tsakiyar dare ne mana Moddibo yanzu fa ƙarfe shabiyu harda rabi ai tsakiyar dare ne, to amma me kafito yi lafiya dai ko?”.
Cikin sanyin murya yace.
“J ne har yanzu bai zo ba kuma ya fito akan zai zo ma ya kirani awaya kan cewa yanzu zai shiga wajen Abbansa ya masa saida safe ya fito, kuma har yanzu bai iso ba sannan nata kiran layukan sa basa shiga”.
Ya ida maganar akasalance.
Ajiyar zuciya Innayi ta sauƙe tare da cewa.
“Toh dan bai zoba Moddibo ai ba abin tashin hankali bane, kaga yanayin wannan hadarin daya haɗu zai iya hanasa zuwa wataƙil daya shiga wajen Abban nasa zaice dare yayi kuma ga hadari ya bari sai gobe”.
Da sauri ya katseta da cewa.
“To ai Innayi wayarsa bata shiga fa”.
Saurin Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.
“Ka kira layinsa duka?”.
Kai ya jinjina mata.
“Eh na kira layukansa duka fa basa shiga”.
Cikin yanayin bacci ta kalli Moddibo tare da sakin hamma kana ta aro Jarumtaka tare da cewa.
“To ko dai network ne?”.
Lumshe Idanunsa yayi tare da Girgiza mata kai kana yace.
“A'a ba network bane cemin akeyi akashe kuma fa Innayi J baya kashe wayarsa, ko zai kwanta komai yaya kuma nasan wayar J baya rasa caji”.
A hankali Innayi ta rufe idonta jin kamar tsinkewar zuciya ya ziyarci ta.
Amma sai ta daure kana tace.
“To amma kaga jiya ma kace min wajen Umminsa ya kwana to ko dai yauma yaje canne ne ya kashe wayarsa dan kada kayi ta kiransa?”.

Jinjina kai yayi tare da faɗin.
“Ok ba mamaki fa bari na kira Ummi”.
Cikin sauri Innayi ta kallesa tare da cewa.
“Aƙarfe ɗaya saura zaka kirasu?”
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh Innayi in dai har wurin Ummi yake nasan yanzu zasu ganshi kamar takwas na dare ne, saboda nasan yanzu suna hira ba suyi bacci ba.
Kai Innayi ta gyaɗa tare da gyara tsayuwar ta kana tace.
“Toh shikenan ka kira”.

Dearling number Ummi yayu.
Acan ɓangaren Ummi kuwa kwance take yayin da idanunta ke lumshe cikin tsananin tsinkewar zuciya da kasala jin rurin wayarta yasa ta miƙe firgice cikin yanayi sanyi sanya hannunta na dama ta janyo wayar tare da ƙurawa screen ɗin Ido sunan Moddibo ke yawo.

Cikin sauri tare da rawan jiki tayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnenta batare data amsa Sallamar daya mata ba tace.
“Babana Lafiya?”.
Cikin ƙoƙarin danne damuwarsa yace.
“Ummi lafiya ya naji kamar kin razana?”.
Ahankali ta koma ta jingina bayanta da jikin kushin ɗin tare da lumshe idanunta kana cikin wata raunan'niyar murya mai cike da kasala da tsoro ta fesar da numfashi tare da cewa.
“Gaba ɗaya ma ai. Arazanen nake Babana”.
Moddibo kuwa cikin kasala da mutuwar jiki ya yaja numfashi tare da fesar wa kana yace.
“To Ummi me yafaru?”.
Buɗe Idanunta dake lumshe tayi tare da dafe ƙirjinta da still yake bugawa kana tace.
“Ban saniba amma gaba ɗaya ina jina wani irin gani nan dai kamar mara lfy, kuma ba zance ga abinda yake damuna kai tsaye ba”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe kana yace.
“Toh amma Ummi lafiyar ki lau?”.
Kai ta gyaɗa masa kamar yana gabanta kana tace.
“Lafiya ta ƙalau,Amma Babana lafiya ka kira yanzu?”.
Numfashi ya sauke tare da lumshe idanunsa kana ya sake jingina bayansa da jikin step ɗin tare da cewa.
“Eh lafiya lau babu komai dama zan tambayeki ne ko dai J yazo yana wurinki ne munyi dashi tun ɗazu akan zai zo har yace min gashi ya fito amma zai sallami Abbansa ne kawai ya taho”.
Sai kuma ya lumshe idanunsa tare da cijan lip ɗin sa na ƙasa kana yace.
“Amma har yanzu be taho ba, inata jiran sa ko ƙofar gida bamu rufe ba, shiyasa nace bari na kira koya biya wajenki, da yake jiya ma nan ya kwana!?”.
Rumtse ida nunta tayi da masifar ƙarfi k cikin wani azabebben tsinkewar zuciya da faɗuwar gaba ta buga hannunta na dama aƙirji tare da cewa.
_“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n. Allahumma Ajirni fii musibati wa'ahlifli khairan min_
bai zo ba kuma yace maka zai zo?
Abbansa kaɗai zai Sallama?”.
Gyaɗa kai Moddibo yayi tamkar yana gabanta kana cikin raunan'niyar murya mai cike da sanyi yace.
“Eh Ummi”.

Cikin wani irin yanayi na taraddadin zuciya da rauni Ummi tace.
“Ya Ubangiji Allah ka dubeni da Idon Rahma. Ya Allah ka tsare wannan bawan naka, aduk inda yake Alfarman Annabi da Alkur'ani”.
Jin salatin da kuma yanayin da Ummi tayi Magana cikin firgici ya farkar da Asma'u, Bashir da Malam Ahmad Aruɗe Asma'u ta miƙe tare da dafe kanta da taji yayi masifar sarawa ta sauƙa daga kan gadon.

Acan ɗakin Bashir kuwa Hasbunallahu wani'imal wakin ya furta tare da sauƙa ƙasa kusan atare suka fito falon ko wannensu zuciyarsa na bugawa da kaso tamanin cikin ɗari.
Moddibo kuwa cikin sanyu da ruɗu yace.
“Ameen ya Allah Ummi ameen ya rabbil Izzati”.

Cikin zulumi Ummi ta runtse Idanunta kana tace.
“Amma Babana ka kira Abbansa mana”.
Numfashi Moddibo ya fesar tare da kallon Innayi data tsaresa da ido cikin yanayin razani yace.
“Eh Ummi nayi tunanin kiran Abbansa amma sai nace bari na fara kiranki tunda jiya yazo na, sannan Ummi nasan J baya kashe wayarsa rashin shigar wayarsa nema yafi damuna!”.
Girgiza kai Ummi tayi yayinda ruwan hawaye masu masifar ɗumi suka cika kwarmin Idanunta kana cikin raunan'niyar murya tace.
“Tabbas baya kashewa ka kira Abbansa kaji”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Eh dama zan kirasa amma Innayi tace ko Abbansa ne ya hanasa zuwa ganin hadari”.

A hankali tace.
“Anya?,Ka kira sa dai”.

“Amma yanzu dare baiyi ba Ummi”.

Cikin sauri tace.
“A'a ka kira Babana ka kira Abbansa ɗin duk yanda kukayi ka kirani ka sanar min”.
“Toh”.
Moddibo yace kana ya katse kiran.

Asma'u da Bashir kuwa zuru-zuru sukayi da ido domin suna iya jiyo sautin muryar Modibbo.
Durƙusa wa Asma'u tayi tare da toshe bakinta kana tashiga.
Girgiza kanta tare da cewa.
“Ya Allah kada ka jarabcemu da abinda baza mu iyaba ɗaukaba Allah ka tsare Yaya Jameel aduk inda yake ya Allah kada ka bari wani abu na cutarwa ya sameshi”.
Cikin raunin murya Ummi ta kalleta Atake taji wasu hawaye masu masifar ɗumi sun zubo kuncinta.
Ahankali Malam Ahmad da jikinsa yayi masifar sanyi ya ƙarasa kusa da Ummi.

Moddibo kuwa yana katse kiran ya shiga contact tare da fito da Number Abban M Jameel.
Kana ya Kalli Innayi cikin sanyin murya mai cike da tashin hankali yace.
“Kin gani ko Innayi baya can. J baije gidan Ummi ba. Innayi ina J ya tafi bayan yasanar dani cewa zai taho”.
Lokaci ɗaya wani masifaffen tsoro da tashin hankali ya ziyarci Innayi wanda ta kasa ɓoyewa har hakan ya bayyana asaman fuskarta dake nuni da tsantsar ruɗu.
Cikin dakiya da kuma nuna masa babu komai insha Allah ta gyara tochligt dake hannunta kana tace.
“Ka dai kira Abbansa muji wataƙil yana can tare dashi hadarin ne ya hanasa fitowa”.
Kai ya gyaɗa mata tare da dearling number Abban M Jameel yana jin yanda zuciyarsa ke cigaba da bugawa da masifar ƙarfi yana bada sautin dif-dumm-dif dumm.
Abba dake kwance kan 3sitter Idanunsa arufe bacci ya fara fusgarsa yaji suwwan wayarsa Atsakiyar kansa afirgice ya miƙe tare da zama kana ya duba screen ɗin wayar nan yaga sunan Moddibo na yawo cikin rawan jiki yayi Picking.
Atare Abba da Moddibo sukayi Sallama.
Ahankali Moddibo ya sauƙe numfashin tare da ƙoƙarin dai-dai-ta nutsuwarsa kana yace.
“Wa'alaikum Salam Abba”.
Cikin yanayin firgici da ruɗu Abba ya sauƙe ajiyar zuciya tare da cewa.
“Na'am Aliyu ya akayi?”.
Numfashi Moddibo ya fesar kana yace.
“Lafiya Abba”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da jingina bayansa da jikin kushin kana yace.
“Ya gida kowa lafiya dai?
Jameelun yaƙara so yana lafiya ko?”.
Lokaci ɗaya zuciyar Moddibo ya buga da masifar ƙarfi kana yayi saurin dafe ƙirjinsa tare da cewa.
“Abba baya gidane”.
Wani irin azabebben bugawa zuciyar Abba yayi kana yace.
“A'a bakwa tare ne tun 10:15 ai ya sallameni yace min zai taho wurinka”.
Moddibo kuwa da sauri ya rumtse idanunsa tare da dafe jikin step ɗin yana mai jin kansa na masifar sarawa tamkar zai rabe gida biyu cikin raunin murya yace.
“Abba tun ƙarfe 10:15 ya fita kuma yace wajena zai zo? Abba tun ɗazu fa nake jiransa ko ƙofar gida bamu rufe ba har yanzu J bai zoba sannan fa nata kiran layukan basa shiga”.

Cikin tsananin razani da tsinkewar zuciya Abba ya miƙe tsaye kana yace.
“Aliyu mai kace?”.
Araunane Moddibo da Idanunsa ke juyawa ya dafe kansa kana cikin sanyin murya yace.
“Abba na yita kiran layinsa baya shiga”.

A ruɗe Abba ya miƙa tsaye tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n to lafiya Aliyu?”.
Girgiza kai Moddibo yayi tare da gyara tsayuwar sa kana yace.
“Toh Abba kuma yace waje na ɗin zai taho?Abba J bai zoba bafa”.
ya ida maganar cikin raunin murya mai cike da tsantsar tashin hankali.

Atake zufa ya wanke wa Abba jiki duk da iskar dake kaɗawa d ƙarfi ya haɗiye wani abu mai ɗaci kana yace.
“Ko dai gidan Ummin sa yaje”.
Da sauri Moddibo ya girgiza kansa muryarsa na rawa yace.
“Um-um Abba baya can yanzu nayi waya da Ummi itace ma tace in Kira ka Dan ni Ina tunanin dare ma yayi bazan kira ba”.

Cikin tsinkewar zuciya Abba ya nufi ƙofar falon Hajiya Karima da sautin muryansa ya farkar da ita tayi saurin fitowa daga Bedroom ɗin Aruɗe ta kallesa kana tace.
“Lafiya Alhj?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da cewa.
“Jameelu ba agansa ba wai baije wajen Moddibo ba sannan baije wajen Umminsa ba”.
Da sauri ta dafe ƙirjinta kana tace.
“Ba agansa ba kuma gashi yanzu ƙarfe ɗaya”.
Kasa cewa komai Abba yayi ya nufi ƙofa da sauri.
Tare da cewa.
“Miƙo min key mota”.
Cikin sauru tabi bayansa tare da Kallonsa ganin Gajeren wando da single ne kaɗai ajikinsa yasa tace.
“Toh yanzu ina zaka je adaren nan??”.
Cikin raunin murya yace.
“Karima ina zanje kike tambaya ta? Jameelu na fa baya gidansu Aliyu sannan baya gidan Umminsa to ina Jameelu yaje kinsan waye Jameelu da in dai baya nan yana gidansu Aliyu ko gidan Umminsa tabbas da akwai abinda yake faruwa”.
Cikin sauri ta juya tare da komawa Bedroom ta dauƙa Masa Jallabiya da key mota kana ta sanya hijabinta ta fito tare da miƙa masa.

Karba yayi yana tafiya yana saka jallabiyar kana ya nufi inda Motarsa yake ya shiga cikin sassarfa tabi bayansa yana shiga mazaunin Driver itama tayi saurin buɗe gefen mai zaman banza ta Zauna.
Kallonta yayi tare da cewa.
“A'a ki koma”.
Girgiza kai tayi tare da cewa.
“A'a Alh ya za'ayi in barka ka tafi kai kaɗai muje dai”.
Kai ya gyaɗa batare da yace komai ba ya figi motar.
Suka tafi bayan mai gadi ya buɗe masa ahankali ya fara bin hanyar Yana dudduba gefen titin kana cikin sanyin murya yace.
“To ko dai motarsa ta samu matsale ne?”.
Girgiza kai Hajiya Karima tayi kana tace.
“Idan ma motarsa ta samu matsala Alh ai saidai ya kira akawo masa wata”.
Kai ya jinjina still Yana cigaba da Driving ɗin yayin da zuciyarsa ke cigaba da bugawa da kaso Cassa'in cikin ɗari suna cikin tafiya har suka isa gidan su Moddibo.

Moddibo dake tsaye coumpund ɗin har zuwa lokacin ya gagara koda ƙoƙƙwaran motsi yayi saurin kallon gate ɗin ganin hasken mota Itama Innayi dake tsaye tayi saurin bin wajen da kallo zuciyarta na cigaba da bugawa.
Cikin sauri tare da rauni yace.
“Toh waye wannan ko dai motar J ne?”.
Ya faɗa tare da nufar gate ɗin Innayi kuwa ido ta zuba masa har ya buɗe gate.
Moddibo kuwa yana buɗe gate din idanunsa suka sauƙa akan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login