Showing 150001 words to 153000 words out of 176046 words

Chapter 51 - Sakayya 1 Hausa Novel Complete

yiwa Ummi jaje bayan sun koma gida.

Baki ɗaya Khausar ta kasa nutsuwa kafin ta kwanta taje tayi alwala kana ta ɗauki Kur'ani tana ta karatu tare da tawassali dashi da niyyan Ubangiji ya bayyana M Jameel aduk inda yake.

Misalin ƙarfe goma na dare kamar lokacin da aka dauke M Jameel Moddibo dake gefen Abba ya miƙe da niyyar tafiya Akuma dai-dai lokacin wayar Abba dake gabansa ta hau ruri.
Atare Abba da Moddibo suka kalli wayar cikin sauri Abba yayi Picking call ɗin tare da kaiwa Kunnensa.
Daga ɗaya ɓangaren akace Alhj Bashiru mahaifin Jameel ko!?”.
Cikin sauri Abba ya gyaɗa kai tare da cewa.
“Eh nine nayi ta kiran layinku baya shiga”.
Cikin fusatacciyar murya Mutumin yace.
“Dama ce maka mukayi idan ka kira zai shiga?”.
Girgiza kai Abba yayi tare da faɗin.
“A'a to menene sharaɗin ku na biyu kaga ban faɗawa kowa ba!”.
Cikin bauɗaɗɗiyar murya Mutumin yace.
“Kuɗin fansa zaka biya shine sharaɗin mu na biyu”.
Kai Abba ya gyaɗa tare da cewa.
“To nawa kuke buƙata?”.
Kai tsaye mutumin yace.
“Milion ɗari biyu”.
Atsorace Abba ya dafe hannunsa aƙirji kana ya zare ido cikin tsanananin firgici yace.
“Milion ɗari biyu!?”.
Atare Hajiya Bunayya da Moddibo da maganar ya dakesu suka haɗa baki atare wajen cewa.
“Milion ɗari biyu?”.
Cike da gadara Mutumin yace.
“Toh idan ba zaka bada ba sai ka shirya karɓan gawar ɗan ka!”.
Cikin sauri Abba ya Girgiza kai tare da cewa.
“Kuyi hakuri dan Allah dan darajar Annabi kada ku kashe wayar”.
Cikin Yanayin ɓacin rai Mutumin yace.
“To ai mun riga mun faɗa muku abinda ake buƙata idan ka shirya gobe zamu sake kiran ka muji ko ka shirya”.
Yana gama fadar haka ya katse kiran...!






By
*GARKUWAR MARUBUTA*


[30/07, 1:40 PM] Halimatu A/rahman Sadeeya: *Littafin SAKAYYAH dai na kuɗi ne ba free book bane 1k ne kacal ki biya ki karanta cikin Aminci kada ki karanta na sata na Allah ya isa. 0661110179 GTBank AISHA ALIYU GARKUWA sai ki turo min shaidar biyanki ta WHATSAPP 09097853276 sai in saki a Group ɗina*


Cappande. Acikin tafin hannunsa ya ɗebo sulallan Gwal ɗin da wasu yan guntu-guntun sanduna tare da birbiɗin yashin kana ya shiga jujjuyasu, ahankali ya maida kallonsa kan Innayi data gyaɗa masa kai alamar ya fito dasu hannunsa ya zura acikin tukunyar yashiga kalato salullan wanda na ainihin Gwalne aƙalla sun kai guda ashirin, karkaɗe yashin yayi tare da fitowa dasu kana ya ɗaura su akan rigarsa tare da gyara zaman sa abakin ramin ya tsura mata Ido Innayi ma ido ta zuba masa ganin yanda ya zauna yasa tashiga maida yashin ta rufe ramin kana ta sanya duwatsun ta rufe tare da tura fantekar kan ramin kallon Moddibo dake binta da kallo tayi kana tace.
“Ɗaura min randan nan akai”.
Ajiyar zuciya Moddibo ya sauƙe still Idanunsa na Kanta cikin sanyin murya yace.
“Innayi wannan kamar Gwal?”.
Kai ta gyaɗa masa kana tace.
“Eh Gwal ne”
Still ba tare daya motsa ba ya sake kallon Gwal ɗin kana yace.
“Ina kika same su Innayi?”.
Girgiza masa kai tayi kana tace.
“Wannan ba lokacin tambayar ina nasamu gwala-gwalai bane. Moddibo lokacine daya kamata ace ka lissafa su muga adadin su kana musan nawa za'a samu mu haɗa mu karɓo Jameelu yanzu tashi mubar wajen nan mushiga ɗaki kaga dare ya tsala”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
“Toh”,Kana yabi bayanta tare da tsira mata idanu cike da ɗumbin mamaki tare da tarin tuhuma ahankali ya sake kallon sulallan Gwal ɗin dake haɗe da waɗanan sanduna guntaye aciki asaman laɓɓansa yayi sallama tare da shiga ɗaki.
Wutan ɗakin Innayi ta kunna Atake haske ya zagaye ɗakin bayan Moddibo ta ratsa tare da rufe kofar ɗakin kana ta dawo kusa dashi ta tsaya tare da sanya hannunta ta tsistsince ƴan guntulayen sandar ta shiga haɗawa kasancewar akwai wajen haɗawa ajiki Moddibo kuwa Idanu ya zuba mata cike da mamaki.
tana cigaba da haɗawa ga mamakinsa sai yaga ya zama sanda irin wanda manyan Limamai ke riƙe wa suna tafiya dashi sanda ce mai masifar kyau da tsari wacce da ka gani kasan mai tsadace.

Kallonsa Innayi tayi tare da cewa.
“Wannan sanda ce samansa inda ake riƙewa ne kaɗai keda Gwal sai kuma ƙasan sa inda ake dogara wa amma wannan bazan baka shiba saboda ba zaiyi daraja sosai ba. Saboda ahaɗe yake da sanda kana sandar kuma bazan siyar ba, sulallan dai zaka haɗa ka duba sai dai sunzo mana alokacin da bashine ba saboda sulallan baki ɗaya sun ƙare”.
Ido kawai Moddibo ya zuba mata still da shock atare dashi.
Innayi ta cigaba da cewa.
“Baki ɗaya nauyin karatunka.
Cin mu, shan mu, suturar mu, tun kana ƙarami da duk wani abinda ya kama su nake ɗauka in siyarwa Alhaji Hashim mai sayan gwala-gwalai shiyasan farashin sulallan duk yanda suke zan faɗa masa adadin da suke yazo ya siya muyi lissafi muga nawa za'a samu”.
Kai Moddibo ya gyaɗa tare da cewa.
“Toh shikenan”.Yayi mgnar tare da lumshe idanunsa, baki ɗaya damuwarsa asamu kuɗin bawai tunaninsa ya tambayi ina tasamu gwala-gwalan nan ba sannan bashida kuzarin da zai iya tambayar ta, sandar na menene, kana bashi da ƙarfin zuciyar jin mai yasa baza asayar da sandar ba, ayanzu burinsa bai wuce asamu ahaɗa kuɗaɗen akarɓo J ba.
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da kallon Innayi kana yace.
“Toh zan tafi dasu ɗakina”.
Kai ta gyaɗa masa kana ya miƙe ya fita yana jin confidence da farin ciki yasan Gwal nada daraja duk da cewa ƴan ƙananun sulallane amma yasan da izinin Ubangiji zasuyi daraja.

Acan gidan Abba kuwa bayan tafiyar Moddibo Hajiya Karima ta kalli Abba daya zurfafa acikin tunani kana ta ɗan ya mutse Fuska tace.
“Alhji wai yanzu baza ka sake ƙara neman ragi ba? yanzu sai ka ɗauki Million ɗari da hamsin ka basu mai kake tunanin zai faru gaba idan sunji daɗi za'a sake ɗaukan ƴaƴanka ne fa!”.
Anutse Abba ya ɗago kansa tare da kallonta kana cikin sanyin Murya yace.
“Karima to me kike tunani?”.
Ba yabo ba fallasa tace.
“Ka nemi ragi”.
furzar da iska mai zafi yayi still Idanunsa na kanta kana yace.
“Karima kamar baki ji me yace ba, cewa fa yayi muddin aka nemi ragi akan rayuwar Jameel”.

Cikin sauri tace.
“Bafa za'a kashe Jameel ba, kawai Alhj idan zaka nemi ragi ka nemi ragi, sai kace baka sha zafin neman kuɗin ba zaka ɗauka agabtale ka basu kamar ba kasan darajar suba, amma babu yanda zaka ɗauki wannan maƙudan kuɗin ka bayar akan Jameelu!”.

Cike da mamaki Abba ya kalleta kana cikin ɗaga sautin murya yace.
“Karima to idan ban bada kuɗi akan Jameelu ba akan wa kike so in bayar? Shin Karima anya Karima?”.
Wani irin kallo ta masa kana cikin sauri tace.
“Anya me?”.
Dai-dai lokacin Hajiya Turai ta shigo baki ɗaya ta hargitse babu walwala afuskarta ta kalli Hajiya Karima kana tace.
“Ai dai kam abin nata da mamaki, idan bai ɗauki kuɗi ya bayar akan Jameelu ba akan wa kike so ya bayar?”.
Sai kuma ta maida kallonta kan Abba da idanunsa ke lumshe kana tace.
“Aini Alhj naga ƙoƙarin ku ma da har kuka iya neman ragin da suka rage muku, kuma ai sunyi ƙoƙari ni dai anawa tunanin kada ku kuskura kada ku sake yin batun ragin wasu kuɗin, suje su kashe mana yaro abanza idan aka kashesa mai son sa keda asara wanda bai sonsa kuma bai damu ba”.
Ta ida maganar hawaye na ciko kwarmin Idanunta.

Hajiya Karima kuwa wani kallo ta watsa wa Hajiya Turai tare da cewa.
“To mekike nufi?”.
Taɓe baki Hajiya Turai tayi kana tace.
“To ai gaskiya ne duk mai son Jameelu ba zai so ace za'a sake neman ragi ba”.
Taɓe baki Hajiya Karima tayi tare da watsa mata kallon banza kana tace.
“Kenan kina nufin Ni bana son Jameelu?”.
Hannu Hajiya Turai ta buɗe kana tace.
“A'a wannan ke ki kafaɗa da bakin ki amma dai shawaran da kika kawo ba shawara me kyau bace”.
Hannu Abba ya ɗaga musu tare da kallon Hajiya Karima dake kumfar baki kana yace.
“Bana son hayaniya ya isheku.
Dan Allah kubarni inji da abinda ke damuna”.
Kai Hajiya Turai ta gyaɗa tare da tsuke bakinta alamun itama ba hayaniyar take soba.
Cikin sanyi ta kalli Abba tare da cewa.
“Alhj ga Million biyu a Account ɗina zan bayar ahaɗa”.
Wani shegen kallo Hajiya Karima tabi Hajiya Turai dashi kana cikin taɓe baki tace.
“Hmmm munafurci dai da neman gindin zama haddasu kaza acikin cin danƙo”.
Cikin sanyi Abba yace.
“Nagode Turai Allah ya saka da alkhairi ayanzu kyauta koda na Naira biyar aka bani ita ina buƙatar ta, xansa acikin tumunin kudin da za'a karɓo Jameel”.
Cikin sauri Hajiya Karima tace.
“Nima Allah ya bani in bayar”.
Kai ya gyaɗa kana yace.
“Ameen”.
Juyawa tayi ta fice Hajiya Turai kuma ta zauna gefensa tana sake tausansa.

Acikin kwanaki biyu Moddibo ya saida gwala-gwalan da kuma motocinsa dana M Jameel Yayi total ɗin kuɗin sun kama Million ashirin da biyar ya turawa Abba cikin account ɗin sa Alhamdulillah yanzu akwai Million casa'in da biyar acikin account ɗin Abba Aɓangaren Abban ma yana cigaba da fafutuka ganin ya samu kuɗi.
Acikin kwanakin baki ɗaya abubuwa sun kankama baki ɗaya sun sake maida hankalinsu kan neman kuɗin suga sun samu sun haɗa yau ya kama kwanan M Jameel goma kenan awajen Kidnappers din kana yau kwana biyu rabon Abba da Moddibo suyi waya da M Jameel Misalin huɗu na yamma Moddibo ya bar gidan Abba ya nufi gidansu bayan sun sake tattauna wa.

Acan ɓangaren Boka Kar'uzu kuwa Hajiya Bunayya da Hajiya Lami ce gurfane agabansa cikin wata sandararriyar murya Boka Kar'uzu ya kece da wata mahaukaciyar dariya tare da jujjuya gashin dake wangamemen tafi hannunsa kana ya ɗago kansa tare da Kallon Hajiya Bunayya da jajayen Idanunsa da suka tara kwantsa yace.
“Kin tabbatar gashin yaron ne dai ko?”.
Cike da ƙwarin gwiwa Hajiya Bunayya ta jinjina masa kai tare da faɗin.
“Tabbas na tabbatar Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye tsinanne Uban tsinannun wannan gashin kan Ramadan ne domin dana shafa turare na shafa kansa bayan na fita naga gashi ya manne ahannu shine na tattare na kawo maka kamar yadda ka umarceni.
Wata mahaukaciyar dariya. Boka Kar'uzu ya sheƙe dashi wanda yasa bukkan da suke ciki ya hau girgiza cike da jin daɗin kirarin data masa yace.
“Hhhhh magana ta ƙare Ƙaramar la'ananniya me kafirar zuciya aiki ya riga yayi anwuce babinsa saura na Babban”.

Girgiza kai Hajiya Bunayya tayi tare da cewa.
“Agama da batun Ramadan ɗin kafin ayi na Haiydar to babu matsala wannan ba damuwa bace”.
Ajiyar zuciya Hajiya Lami ta sauƙe kana tace.
“Ni kuma Boka yanzu Abban Samira na nan amma nanda sati biyu masu zuwa zai tafi aikin Umrah, shiyasa nayi shiru da batun zuwan Samira nan mu bari sai mahaifinta ya tafi kaga ba kowa agida da banaso daga gidan Hajiya Bunayya arika zuwa ana daukan ta saboda sa idanawa. Amma Alhj na tafiya idan ya kama ma ta dawo gidan ka idan kuma kaine ma zaka rinƙa kwana idan gari ya waye ka dawo to duk daya”.
Wata dariya mai masifar ƙara Boka Kar'uzu ya kece dashi kana buga ƙafarsa na hagu wanda baki daya ƙura ta buke wajen kana yace.
“Hhhhh saishi Boka Kar'uzu Uban bokaye La'anannen Uban La'anannu Mugu Uban mugaye tsinanne Uban tsinannun shaiɗani Uban shaiɗanu babu wata matsala da zaran ya tafi zan zo Ni da kaina dan zamu fi sakewa agidan naku acan ma zan tare in ragargaji sabon budurci”.
Kai Hajiya Lami ta gyaɗa tana murmushi kana tace.
“Yanda kake so haka za'ayi”.
Daga nan suka miƙe suka fita ta baya kamar yanda suka shigo suka nufi gida ransu fari soll musamman Hajiya Bunayya.

Acan ɓangaren Khausar kuwa sanye ta fito cikin hijabi maroon mai facemaks kafadarta rataye da jaka fari sol jikinta na fitar da sanyayyan ƙamshin turaren Oud Ma'aruf cikin yanayin sanyin ta da tun ɓatan M Jameel bata dawo dai-dai ba ta kalli Mommy dake zaune kan 2sitter kana tace.
“Mommy zan tafi”.
Kai Mommy ta gyaɗa kana tace.
“To kice ina gaida Ummi”.
Kai Khausar ta gyaɗa cike da nutsuwa ta fita tare da sanya Platshoe fari Anutse ta nufi coumpund ɗin dai-dai lokacin da Amina da Uncle Naseer suka shigo hannunsu sarƙafe da juna kallo ɗaya Khausar ta musu ta kawar da kanta gefe kana ta lumshe Idanunta.

Ido Uncle Naseer ya zuba mata tare da shafa kansa kana cikin sakin fuska yace.
“A'a Khausi ina zuwa da yamma nan?”.
Batare data sake kallon inda suke ba kana cikin sanyin murya tace.
“Zanje gidan su Asma'u ne”.
Langwaɓar da kai yayi kana yace.
“Ai haka dai maganar bata haɗa muba Khausar, ashe wai Malam Jameel aka sace Agaskiya garin nan ya fara bada tsoro bari muje na kaiki in jajantawa Ummi”.

Girgiza kai Khausar tayi kana tace.
“A'a kabari kawai”.
Cikin sauri Amina ta watsawa Khausar harara kana ta maida kallonta kan Uncle Naseer Shima ta hararesa.
Uncle Naseer kuwa ganin kallon da Amina ke jifansu dashi yasa ya ware idonsa tare da sakar mata da lallausan murmushi kana yace.
“Ohh Baby Colm down mu nayin Auren mu zan ɗauke ki mu gudu mubar ƙasar nan, kafin muma Akinnafemu tunda kinga anfara tsincr ƴaƴan masu kuɗi an ɗauke Malam Jameel next target ɗin su ni za'a ce za'a saɓe ko ke, kafin ma su ankara zamu gudu abinmu.
Dariya Amina ta ƙyalƙyale dashi tare da manna kanta ajikin damtsen hannunsa.
Khausar kuwa cikin sauri ta kawar da kanta gefe tare da lumshe Idanunta.
Ahankali Uncle Naseer ya ɗago kansa tare da tsura wa Khausar Ido tabbas soyayyanta acikin jininsa yake har yau har gobe zuciyarsa na muradin Khausar, itace burinsa Kawai zai Auri Amina ne domin cikar Burinsa amma Khausar itace muradinsa.

fesar da iska mai sanyi yayi yana jin wani irin yanayi agame da ita kana yace.
“Khausi jirani in ɗauko sakon Uwaniyona inzo in kaiki?”.
Da sauri Amina ta janye kanta dake manne adantsensa kana tace.
“Ka kaita kuma?”.
Kai ya gyaɗa tare da yimata raɗa akunne yace.
“Yes My dear wife ai jaje ne".
Ashagwaɓe ta girgiza kai tare da cewa.
“Gaskiya Ni dai Uncle Naseer bana so ka tafi ka barni”.
Shafa fuskarta yayi kana yace.
“Bafa daɗewa zanyi ba”.
Khausar kuwa cike da takaicin abinda sukeyi tace.
“A'a Uncle Naseer ka bari ganan Haiydar ma zai kaini da mashin ɗinsa”.
Kai ya gyaɗa still Idanunsa na kanta yace.
“Ok”.
Dai-dai lokacin Haiydar ya fito daga sashen Abbansu hannunsa riƙe da key mashin dinsa.
Kallon Uncle Naseer da Haiydar yayi da murmushi afuskarsa yace.
“Uncle Naseer yau dai Addah Khausy ta yarda in jata amashin ɗina”.
Cikin alamun so Naseer yace.
“To ayi a hankali dai banda fifita”.
Dariya Haiydar yayi tare da cewa.
“Uhmm aikam zata sha fifita”.
Murmushi Uncle Naseer yayi tare da cewa.
“Dan Allah ka jata ahankali kada kayi mana asara”.
lumshe Idanunta tayi baki ɗaya bata da wani kuzari ɓatan M Jameel yayi masifar ratsata hakan yasa ko magana bata fiye yiba daga Um-sai Um-um.
Haiydar kuwa mashin ya ɗauko tare da ɗaukar ta suka fice kana Amina da Uncle Naseer suka shiga ciki.

Haiydar na isa kofar gidan Ummi yayi Parking ahankali Khausar ta sauƙa tana gyara zaman hijabinta kana atare suka shiga cikin Falon Ummi bakinsu ɗauke da Sallama.
Ummi dake zaune riƙe da carbi ahannunta Asma'u da Bashir na zaune gefenta suka Amsa Sallamar.
Cike da ladabi Haiydar ya gaisheta tare da sake yi mata jaje kana suka gaisa da Bashir tukunna suka fice atare.
Khausar kuwa cike da sanyin tace.
“Ummi ki kwantar da hankalin ki insha Allah yaya Jameel zai bayyana babu abinda zai sameshi da izinin Ubangiji addu'a mu bazai tafi abanza ba".
Jinjina kai Ummi tayi cikin yanayinta kamar mara lafiya tace.
“Ameen ya Allah”.
Cikin sanyin murya Asma'u da Muryanta ya dishe da kuka tace.
“Babbar matsalar mu yau kwana biyu kenan Basu sake kira ba gashi baki ɗaya kuɗin Million Casa'in da biyar aka samu aka haɗa”.
Kallonta Khausar tayi tana cire hijabinta tace.
“Haka dai kika cemin jiya har yanzu kuɗin basu haɗuba”.
Kai Asma'u ta gyaɗa mata kana tace.
“Basu haɗu ba Khausar damuwar dake damunmu kenan wlh, baki ɗaya hankalinmu ya kasa kwanciya sai dai Yah Modibbo yace Abba ya nemi bashin banki amman sunce yau ko gobe zai samu kuɗin”.
Cikin sanyin murya Khausar tace.
“Insha Allah kuɗin zasu haɗu da izinin Ubangiji Allah ya karesa ya tsare lafiyarsa”.
Atare suka amsa da Ameen.
Shiru Khausar tayi tare da tallafe kuncinta kana ta kalli Ummi da Asma'u sai kuma ta fesar da numfashi kana buɗe jakarta tare da kwaso ƴan kunnaye da sarƙa da kuma zobe kala biyu da alamun nata dana Mommy ne, hannun Ummi ta kama tasasu a ciki kana ta rufe hannun Ummin tare da cewa.
“Gashi inji Mommy na, tace Dan girman Allah da Manzonsa kada ki ƙi karba Ummi dan Allah kada kice komai a saidashi a haɗa kuɗin.
Cikin tsananin jin dadi Ummi ta kalli girman Gwal ɗin musamman na Mommy wanda a ƙalla shi kadai zai iya kai one Million da yan ɗori.
Hawaye na tsiyayo mata tace.
“Bazan ƙiba Khausar kicewa Mommynki ngd matuƙa ubanji yayi mata sakayya da gidan al'janna mai girma”.
Cikin sanyi duk suka amsa da Amin.
Cikin sanyi Khausar ta fesar da numfashin kana a hankali tace.
“Amma Ummi Meyesa ba asa Police acikin maganar ba?”.
Cikin raunin murya Ummi tace.
“Sunce muddin Akasa police acikin maganar to abakin ransa”.
Cikin sauri ta dafe ƙirjinta tare da cewa.
“Innalillahi akan ransa kuma?”.
Kai Asma'u ta gyaɗa Tare da cewa.
“Kuma batun kuɗi ma da suka ce da farko Million ɗari biyu sukace yanzu ya zama Million ɗari da hamsin saboda ragin da aka nema to yanzu sunce muddin aka sake neman ragi akan ransa”.
Aruɗe Khausar ta rintse Idanunta tare da cewa.
“Innalillahi wa'inna ilahi rajiu'n”.
Sai kuma ta juya tare da kallon Ummi cikin sanyin murya tace.
“Ummi kinsan wani abu?”.
Kai Ummi ta girgiza kana tace.
“A'a”.
Lumshe idanu Khausar tayi tare da cewa.
“Ummi ranan da Yah Jameel ya mai dani gida da muna tafiya munga wata mota tana ta binmu abaya”.
Sai kuma tayi shiru alamar tunani ajiyar zuciya ta sauƙe kana tace.
“Ummi shine fa dama nace da za'a faɗawa hukuma zan iya bada number Motar saboda na zargi motar duk inda mukayi motar na biye damu wataƙil da hukuma zasu shiga za'a iya kama wa anda suka sace Yah Jameel, domin tun fitar mu motar ke bibiyanmu har saida muka kusa gidanmu suka daina binmu”.
Cike da mamaki Asma'u tace.
“Kai Khausar?”.
Kallonta Khausar tayi tare da gyaɗa mata kai kana tace.
“Wallahi kuwa Asma'u amma lokacin bamu kawo komai aranmu ba shima kuma Malam Jameel Bai kawo komai ransa ba”.
Girgiza

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login