Showing 123001 words to 126000 words out of 262297 words
ya faru dani tun sanda ya Walid ya dauko ni daga gurinsa, tafiyar mu niger da duk abinda ya faru acan har taimakon da musbahu yayi min na samu na kira daddy na. Nace "yanzu Mommy ce kadai matsala, ita ma kuma insha Allah zata sauko" na sauko daga kan kujerar nima nayi irin zaman da yayi na cigaba da bashi shawarwari akan sabon companyn sa, na bashi shawarar ya bude branch a New York tunda yana da mutane sosai acan, naga alamar yaji dadin shawarar, nan yace in zabarwa companyn suna wai dama ni yake ta jira in dawo in fadi sunan da nake so, nace zan zaba amma ba yanzu ba sai nayi tunani. Nan kuma na sake bashi shawarar yake zuwa palace yana gaishe da babanshi, ya dan bata fuska yace "why?" Nace "because he is your father" Ya Habeeb ne ya shigo palon, ya tsaya yana kallon mu da mamaki yace "wai ke har yanzu kina nan? Mu duk mun dauka kinyi bacci by now?" Na kalli wall clock din palon 12:49, da sauri na mike ina rufe bakina da hannu, na shiga uku, duk dariya suke min, Allah yasa Mommy bata shiga dakina ba, dan tunda muka dawo gidan ban kuma ganinta ba, kar in kara wani laifin akan wani. Ya Habeeb yace "soyayya dadi, wayo ku baku ma san lokacin ya tafi ba ko?" Da sauri nayi hanyar waje ina jin Sultan ya biyo bayana yana kirana, a bakin kofa na tsaya ya karaso ya miko min wani abu a leda, na kalle shi da alamar tambaya yace "it is a phone, ba zan iya hakura da jin muryar ki ba, dazu na siyo na yi miki charge dinta na saka miki sabon sim" na dan yi shiru amma kuma nima ina son muke wayar ai. Na karba nace "thank you" bai ce komai ba, na juya na cigaba da tafiya ya sake biyoni ya sha gabana yana tafiya da baya da baya yana kallona kamar wacce zan gudu, har muka je kofar palon mu, na kama handle din kofar yace a hankali "love" na juyo na kalleshi, a hankali ya sake cewa "thank you for loving me" bance komai ba sai murmushi da nayi, shima murmushin yayi min, and in that moment ji nayi duk hawalar da nasha is nothing, for him, I can do it all over again, ko da wacce tafi ta baya ce ma.
A bangaren Mommy kuwa tunda suka dawo ta shiga dakinta ta rufe kofa, ta kwanta a kan gado zuciyarta tana yi mata zafi, mai yasa wai kowa ba zai fahimce ta ba? Wannan yaron ba yaron kirki bane, bai dace da Moon dinta ba, her perfect daughter deserves someone like her. Wannan yaron is too strong for her daughter, in anyi auren ma cin zalinta zai tayi yana lallabata ita kuma da raguwar zuciya tayi ta yafe masa. That's is ko da ace ya gyaru ma, in kuma bai shiryu ba yaje ya sha giyarsa yazo ya lakada mata dukan tsiya. Ta runtse idonta, bama zata iya tunanin 'yarta wani katon gardi yana dukanta ba. Ta tashi ta dan daga labule ta leka waje, shi ta fara gani akan mota tare da habibin ta, ta rasa wanne irin charm yayi using akan 'ya'yanta da mijinta, ita yanzu abin kunya ne ma kawayenta su shigo su ganshi a gidanta bayan duk irin maganganun da suke yi a office akansa, da akwai cases dinsa da yawa da ake kawo musu amma sai kuma azo a janye saboda iyayensa sun bata shi, ita ta kasa gane wanne irin so iyayensa suke masa da har suka barshi ya lalace haka, wannan ai ba soyayya bace. Ta shiga toilet tayi wanka ta fito tana shiryawa, wai har ita yau dear ya zauna ya wanke ta agaban iyayenta, abinda bai taba yi mata ba kuma duk akan wancan shegen ruwa biyun. Ta saka kayanta ta fita ta leka dakin Moon ta jita a bandaki tana wanka, ita kunyar 'yar tata ma take ji, me zata ce mata bayan tayi failing, yanzu ga yaron nan an kawo shi har gida yadda zaiji dadin lalata mata 'ya a gidan ubanta. Ta sauka kasa tana bada order abincin da za'a dafa, a kitchen din ta zauna kamar yadda ta saba akayi aikin abincin tare da ita, sai da ta tabbatar komai ya kammala sannan ta koma sama tace akawo mata nata sama, bata son wannan tsageran yaron ya shigo ya same ta a kasa, da wasu idanunsa a tsatstsaye irin na marasa kunya. Ta koma dakinta tayi sallolinta sannan ta jawo abincinta taci, duk abincin ma babu dadi, sam yanzu bata iya cin wani abin kirki, she is suppose to be downstairs with her family, kamata yayi ace tana can ta tabbatar Moon taci abinci ta ko shi. Amma sam dear yaki sauraronta, ita ba zata iya zama da yaron nan ba, shi kuma direct ya gaya mata shi fa ba zai kore shi daga gidan saba sai ranar da shi da kansa yace zai tafi. Kuma yaran ma babu wanda ya hawo yayi mata magana, irin Mommy mai yasa ba kya saukowa mu ci abinci tare? Ji tayi wani hawaye ya zu bo mata, ta goge tare da jawo wayarta ta duba time, safiya ce yanzu a England, tayi dialing number din Hafsat.
Hafsat ta gama sallamar Zayed tana shirin shiga wanka taji shigar kira daga Mommy, ta zauna da kyar saboda nauyi da ta fara, ta daga da sallama. Mommy ta amsa da daskararriyar murya, suka gaisa sannan mommyn tace "Moon ta dawo gida" da yake tuntuni Hafsat tasan duk abinda yake faruwa, da sauri Hafsat tace "Haba? Tana ina? Dan Allah Mommy bata mu gaisa" Mommy tace "tana kasa tare da daddyn ku da brothers dinku, da kuma wannan yaron" Hafsat ta gane wa take nufi. Sun jima shiru sannan Mommy tace "Hafsat ke kinfi kowa sanin Moon, dan ina ganin kamar hatta ni da na haife ta kinfi ni sanin ta, please tell me, where did I go wrong a tarbiyyar dana bata? Me yasa tayi choosing ta bakantamin ta tozartani a cikin jama'a? Me yasa ta zabi sultan? Me yasa tun farkon ganin ta dashi ba ta fahimci cewa ba sa'an auren ta bane ba?" Hafsat ta danyi shiru sannan tace "Mommy kaddara ce, destiny, Sultan destiny din Moon ne haka itama Moon destiny din Sultan ce. Allah ya riga ya rubuta cewa sai sun hadu kuma sai hakan ta faru a tsakanin su. Mommy babu inda kikai wrong a tarbiyyar mu dan ba mu kadai ba duk wanda ya san mu yana yabawa da irin tarbiyyar da kika bamu, wannan shi yasa ko da yaushe muke kokarin mu zama perfect saboda kar muyi failing dinki, but no body is perfect. Duk abinda Moon tayi tayi shine because she is afraid of failing you Mommy. Sultan ba shine saurayin Moon na farko ba, tayi Ibrahim, she loved him so much amma haka tayi ta kumbiya2 saboda tasan ba lallai ne in ta kawo muku shi ku karbe shi ba, sanda tayi summoning courage kuma ta kawo shi gida shi kuma ya kasa summoning courage yayi facing Daddy. Sai da tayi spending five years kafin ta cire ran dawowarsa. So you understand why she is holding tightly unto Sultan. Shima haka tayi ta hiding dinsa daga gurinku saboda tasan shima ba zaku amince da shi ba. Tsoron da take yi na cewa zaku rabata dashi shi yasa take going behind your back take ganinsa. Na sha bata shawarar ta kai ku gurinsa but she kept saying she is waiting for the right time, she was afraid, afraid of not being the perfect girl you want her to be. So tayi ta dan gyara shi kafin ta kawo muku shi, amma sai gashi kun ganshi in his worst" tunda ta fara magana Mommy bata ce komai ba, sai da taji tayi shiru sannan tace "yanzu me kike ganin ya kamata inyi" Hafsat ta sake cewa "Mommy ni personally i don't like sultan, but tunda har Moon tayi falling for him, kuma Daddy ya dauko shi ya hada shi da 'ya'yansa gudan jininsa, suma kuma a cikin 'yan watanni har suka saba dashi then there must be something Good about him. Ni ina ganin Mommy give him a chance, you might even like him too"
Bayan sun gama wayar Mommy ta jima a zaune tana digesting maganganun Hafsat, tasan Hafsat tsintar kalmomi tayi wajan yi mata bayani amma abinda take so ta gaya mata shine 'she is too strict' kuma tasan haka ne, takurawar ta da son su zama perfect ne ya saka Moon take zuwa gurin Sultan a boye. Yanzu badan Allah ya kare mata yarinyar bama da sai dai ta ganta da ciki ta rasa a ina sa samu. She was wrong before, but now she is going to correct her mistakes. Ta tashi ta kwashe kayan abincin da ta gama ci ta fita dasu kitchen, babu kowa a palon duk sun fita, ta koma daki ta sake wani wankan tayi shiri na musamman, she is going to take back her family. Tana jin Daddy yazo ya wuce ta gaban dakinta amma ko lekowa bai yi ba, sai da ta bari ya dan jima da shiga sannan ta bi bayansa. Tana shiga taga ya fito daga wanka da towel a jikin sa yana kokarin shiryawa, kallo daya yayi mata ya dauke kansa, ta zagayo gabansa ta dauko mansa ta fara kokarin shafa masa, ya ture ta ya matsa, ta ajjiye man ta dauko turarensa ta biyo shi inda yake kokarin saka pajamas dinsa ta karasa saka masa ta fara fesa masa turaren hannunta, ture ta ya sake yi ya tafi kan gado yana shirin kwanciya, ta saka hannayenta ta baya ta rungumo shi, ya chire hannun nata ya matsa. Ta shagwabe fuskar ta kamar zatayi kuka tace "am sorry fa" bai kula taba ya hau kan gadon, ta bi bayansa ta kwanta a kirjinsa tare da sauke ajjiyar zuciya, sun jima a haka sannan a hankali ya dora hannunsa a bayanta yana shafa ta kamar mage, ita kuma ta kara narkewa a jikin sa, can kasan makogwaronsa a furta "I miss you"
Episode Fifty Eight : For You, Only You
'Yan # teamibrahim ina jin duk abinda ake yi muku, believe me, i will surely reward your loyalty. Bature yace "he who laugh last.......
Washegari da sassafe Sultan ya kira ni yace min ya tafi office, yana da meeting very early, dan haka nima ban tashi da wuri ba, ina jin Mommy kusan shigowarta uku tana dubani, sai kusan karfe 12 na tashi, shima kuma yunwa ce ta tashe ni, nayi wanka na shirya cikin wasu riga da skirt english wears tunda duk kayana sunyi min yawa yanzu, nayi packing gashina a tsakiyar kai na sauko kasa, a kitchen na samu su Mommy already suna aikin abincin lunch, na gaishe da Mommy ta amsa tana kallon kayan da na saka, na jawo kujera na zauna nace "Ma'u ki kawo min taimako, yunwa na ke ji" da sauri Asma'u ta ajiye aikin da take yi ta fara hado min tea, na karba na fara sha sannan ta zubo min farfesun naman ragon da suka gama hadawa ta hado min da bread, na karba ina ci ina santi, Mommy tace "aikin kenan, amma in akace kiyi garki ba zaki yi ba sai dai a girka ciki, ni ban taba ganin macen da bata son girki ba sai ke Moon" Furaira ta karba "kuma gashi gwanin nata gwanin abinci ne ba" a tare muka watsa mata harara ni da Mommy, tayi sauri taja bakinta tayi shiru, can Mommy tace "ke furaira ya akayi kikasan saurayinta ne?" Furaira tace "nima Mommy wallahi a gurin 'yan waje nake ji, shi yake gaya musu" a raina nace "zai aikata" Asma'u tace "kar ki damu mai sunan daada, duk sanda akayi bikin ki gidan ki zan koma inyi ta dafa miki abinci ke da mijin ki" nan itama ta karbi nata rabon hararar daga Mommy" sai da na gama cin abinci na sannan Mommy tace "ku bata suyar friend rice din nan tayi" na fara yarfe hannu ina kallon Mommy kaman zanyi kuka "Mommy wallahi kone wa zanyi, ni kuba ni in yanka muku wani abu, ni zafin wutar ne bana so" asma'u ta biye min "dama wannan jikin naki haka babu tsoka ina zaki iya juya shinkafa? Bara dai in baki ki hada fruit salad" nan na kama murna na zauna dishen a kasa na nade kafa, maryam tace "so take fa ta gudu, ai tana zuwa kitchen zata ce a bata yanka, daga nan zata yanke hannu sai kuma ta tashi ta fita shikenan ba zaki kara ganin taba sai akan dining" duk suka saka dariya, na bata rai nace "ke Maryam har zaki nuna min aiki da wuka? Da likita fa kike magana" daga nan sai na fara basu labarin yaddda muke buda kan mutun mu bude kwakwalwarsa mu yi masa aiki sannan mu mayar mu rufe, ban ankara ba ina ta surutu sai gani nayi ana juye fruit salad din a bowl, har an gama hadawa, na dauko cup aka zuba min na koma gefe na fara sha ina cigaba da labari na. Tsayuwar mota muka ji a waje, Mommy ta kalleni tace "madam ki je ki chanza wadannan kayan na jikin ki, dan wannan tsageran yaron bashi da linzami a gidan nan, har kitchen din nan zai iya shigowa" nace "Mommy kaya na duk sunyi min yawa ne wallahi" tace "to sai ki saka wadanda suka fi wadannan girma ko kuma ki saka dogon hijab" nace "yes Mommy" har zata fita tace "kar ki yadda fa inzo dining in tarar dake da kayan nan sai ranki ya baci" da sauri na mike na riga ta hawa saman. Sai da nayi alwala na saka dogon hijab dina bayi sallah sannan na dan gyara fuskata na sauka kasa, ya Habeeb na tarar a palo, na zauna muka fara hira sai da ga Daddy, ya Walid da Sultan sun dawo, daga gani daga masjid suke. Ko kallon inda Sultan yake banyi ba na gaishe da Daddy, duk da ina jin idanuwansa a kaina. Daddy ya fara yi mana zancen convocation din mu da za'a yi next week, kuma duk tare za'ayi har dasu Faruk. Nan muka kama murna. Saukowar Mommy ce ta katse mana hayaniyar mu, gaba daya muka juya muna kallonta, tasha ado tun daga sama har kasa, tayi kyau sosai dan bazaka kalleta ba kace ta haife ni ma ballantana ya Walid daya doshi 30 years. Tana zuwa ta gaishe da Daddy, su kuma duk suka gaishe ta har Sultan, ta amsa ba tare da ta kalle shi ba, sannan tace "ga abinci nan a dining" ta mike ta tafi, muma duk muka bi bayanta. Muna zama na tashi na fara zubawa kowa abinci, sakara ce da miyar vegetables, fried rice da hadin salad sai farfesun naman rago, sai kuma fruit salad. Kowa farfesu na fara zuba masa sannan kuma sai in tambaye ka me kake so a cikin sakwara da shinkafa sai in zuba maka, amma da nazo kan Sultan ban tambaye shi ba na xuba masa fried rice da salad da yawa amma na ciccire tumatir din cikin salad din, duk abinda nake yi idon kowa akaina yake, ina gamawa yace min "thank you" ban amsa masa ba na koma na zauna. Ya Habeeb ne ya kasa shiru yace "shi Sultan mai yasa ba'a tambaye shi abinda yake so ba? Idan kuma ransa yafi son sakwarar kuma fa?" A hankali nace "baya cin sakwara ai" ya Walid yace "wow, yanzu kai zama kayi kai ta lissafa mata abincin da kake so da wanda baka so?" Daddy yayi gyaran murya duk kowa yayi shiru. Ina lura da Sultan gaba daya a takure yake, kuma nasan ganin Mommy a gurin ne. Daddy ya cigaba da maganar zuwan mu England ita kuma Mommy ta gaya mana cewa in munje zamu taho tare da Hafsat saboda tana son tazo ta haihu a gida, nan muka kara yin wata murnar. Sultan ne ya fara tashi yace wa Daddy zai koma office saboda ya baro aiki sosai a can. Yana tafiya su Daddy da yaya Walid suka fara maganar irin cigaban da company n Sultan yake samu, yaya Habeeb yace "yanzu fa a cikin 'yan watanni har ya fara zancen sayan building din kusa dashi zai kara wasu offices din ya kara expanding din gurin. He is a real hustler. Baya zama sam, baya kuma gajiya da aiki" ni da Mommy kawai jin su muke bamu ce komai ba. Sai da suka gama sannan Mommy tace da ya Habeeb "kai da kake ta celebrating success din wani kai ina taka success din? Tunda aka samar maka aikin nan ka fara ni banga ko hula ka saya wa kanka ba, baka da aiki sai kashewa 'yammata kudi ko? Ka san Allah Habeeb ka fita daga ido na in rufe, kana ganin walid ya sayi filin sa yana kokarin fara gini amma kai ko ajikinka sai ana maganar wani ka iya cewa 'he is a real hustler' bayan kai yanzu da zan duba account dinka babu wani abin kirki a ciki" yadda kokayi maganar ya Habeeb ne saka mu muka yi dariya ni da ya Walid, ta juyo tana hararar ya Walid tace "kai kuma ka iya taya wani murna cewa budurwarsa tasan abinda yake so da wanda baya so amma kai kaki yin budurwar ballantana ka gaya mata kai me kake so din, you are not getting any younger fa, ya kamata kai ma ka san me kake ciki tun kafin hajja ta juyo kanka ta samar maka mata" na rufe bakina ina dariya ganin yadda ya Walid ya bata fuska, ta juyo kaina tace "ke kuma a ina kika samu wannan wayar ta hannun ki?" Cikina ne ya bada kululu, na fara in ina, tace "shine ya baki ko?" Na gyada kai, tace "ce masa akayi ba zamu iya saya miki waya