Showing 216001 words to 219000 words out of 262297 words
wuri saboda ya fara siyan pampers".
A cikin satin Takawa yaje maiduguri nemarwa Amir auren Aishan sa, ai kuwa iyayenta jiki na karkarwa suka ce sun bayar. Tare da sultan suka tafi. A bauchi suka sauka sannan suka hau motoci zuwa maidugurin, suka kuma dawowa bauchi igan sarki suka yi taro sannan suka dawo Abuja. Tun a hanya sultan yayi min waya wai ya gaji, shi ya dade rabon dayayi irin wannn gajiyar. Yana dawowa kuwa da kyar na samu yaci abinci duk kuwa da soyayyar sultan da abinci. Dakinsa ya wuce yana tafiya yana hada hanya saboda bacci. Ina kallonsa ina dariya a raina. Allah ya nuna min ranar da zan rama abinda sultan yake yi min a gidan nan, yau zai gane shayi ma ruwa ne, zai ji yadda nake ji idan ya hanani bacci. Dakina na tafi nima naje na tsalala wanka, na shafe jikina da turaruka da mayuka irin duk wanda sultan yake so, na dauko wata rigar bacci na da tun da nazo gidan ban taba saka taba saboda kallonta ma kadai in nayi kunya nake ji, na saka, na dauko jan jambaki da nasan yana ruda sultan na shafa a lips dina, na zura hijab a raina ina cewa sultan yau ka kade har ganyenka. Ina shiga dakin na ganshi ya bararraje akan gado daga shi sai three quarter wando, ya kure ACn dakin kamar ka shiga freezer, na taba jikin sa naji sanyi kalau, naje na rage ACn na dawo ina kallonsa, a hankali na hau kan gadon na fara shafa fuskarsa, "sultan? Sultan?" Amma sultan shiru kamar gawa, nayi masa chakulkuli a kafa irin yadda yake min amma bai san ina yi ba, a raina nace aikuwa sai ka tashi yau. Na shiga toilet na dauko cotton bud, nazo na fara sosa masa kunne a hankali, yayi juyi ya janyo pillow ya dora akan sa. Haushi kamar ya kashe ni amma naki hakura, na fara shafashi duk inda nasan yana so amma maimakon ya farka sai jikin sane yake farkawar. Naji tsoro na daina. Na koma kiran sunan sa da dan karfi, sai a lokacin yayi juyi ya dauke pillow daga kansa, na kara volume din kirana, ya dan bude idonsa da suka yi ja sosai saboda bacci ya kalleni kamar zaiyi kuka, nace "pay back time" ya kwabe fuska ya gane me nake nufi yace "dan Allah Moon ba yau ba. Ki bari wata rana kya ramar, you have no idea irin baccin da nakeji yau" nace "nima lokacin da kake tashina you had no idea irin baccin da nake ji" bai ce min komai ba ya juya baya ya ja bargo, na tsallaka ta samansa na yaye bargon ina dariya, hankali na ya kwanta, ko a haka na barshi nima na rama. Ya dago yana kallona ina dariya, a hankali naga baccin idonsa yana washewa lust yana replacing baccin, idonsa akan rigar dake jikina, nayi sauri na daina dariyar nace "shikenan ma babu wani abu na hakura kwanta kayi baccinka" ya dago yana kallon fuskata yanayinsa yana chanzawa, yana min rikitaccen kallo yace "no thank you, na fasa baccin kuma, I got something sweeter than bacci" da sauri na ja da baya, yau na kunto wa kaina ruwa kuma bani da lema, ai kam kafin in sauka ya kamo ni yana kare min kallo, na fara bashi hakuri "kaga ka gaji da yawa, dan Allah ka kwanta kayi baccinka kawai, kaga gobe zakaje office kar kazo ka makara" yayi dariya yace "a da kenan, yanxu na chanza shawara" ya kawo bakinsa dai dai kunnena yace "tunda har kika tambayeni bashin da kike bina, dole ki karba".
Nasha kama Sultan yana kallon picture din Ummee a waya ta, sai nazo kuma sai ya basar yayi kamar wani abin yake yi daban, shi a dole wai bai damu da ita ba. Ni kuma da naga haka sai ba saka hoton nata a screen saver dina, yana dauka ya gani ya juyo yana kallona da alamar tambaya, na daga masa kafada nace "for easy viewing" ya ajiye wayar yayi tafiyar sa irin baya son maganar nan. A bangaren Hafsat kuwa har suka gama zaman su a Riyadh Ummee bata fada mata wata maganar da zata dangantata da Nigeria ba ko kuma da Sultan. Rannan kawai sai ga Hafsat ta kirani tace zasu koma Riyadh Abban Zayed baya jin dadi zasu je su duba shi. Kuma tayi min alkawarin insha Allah wannan karon zata samo labari ko da kuwa a gurin Ummeen zayed ne. Kwana uku bayan nan muna zaune da Asmau tana yi min kitso sai ga wayar Hafsat na dauka ina addu'ar Allah yasa labari mai dadi ne, tace "Moon she talked to me" nace "how managed? Ya kika yi mata?" Tace "zama nayi ina ta bata labarin Nigeria da Abuja, na kuma bata labarin Mommyn mu da yadda take son mu bata son rabuwa damu ko kadan. Irin heart to heart talk din nan. Daganan kawai sai tace min ai itama tana da da, kuma tana sonsa fiye da komai a duniya, tana nan kuma tana jiran ranar da zai zo gurinta. All these years zaman jiran yazo gurinta take yi, all these dukiyar da take tarawa, shi take ajiyewa dan tasan komai daran dadewa zai zo gurinta" nayi shiru inajin hawaye yana taruwa a idona, tace "yanzu kina ganin in gaya mata nasan shi ko kuma me kike so in ce mata" na danyi tunani kadan sannan na tsarawa Hafsat duk abinda nake so ta gayawa Ummee. A ranar da daddare muna zaune a palon Sultan, ina kwance akan kujera ina game a wayarsa shi kuma kan study table dinsa yana zane, sai ga kiran Hafsat a waya ta, sai da na jera adduoi sannan na dauka, na daga murya yadda zan calling attention din sultan nayi mata sallama, tace min da fulatanci "na gaya mata duk yadda kika ce" ina jin haka na saka waya ta a hands free, Hafsat ta koma turanci "Maimunatu this is zayed aunt, she wants to talk to you about her son" ina kallon sultan ya ajiye pencil din hannunsa, nima sai da na hadiye yawu saboda bakina naji ya bushe, ina jin Hafsat tana bata wayar tana mata bayanin ga sister din tata, naji muryarta ta larabawa tace "As Salaam-o-Alaikum" na amsa mata murya ta na rawa, idona akan na sultan wanda ya juyo yana kallona, ta fara magana da turancin ta mai accent din larabawa "Am sorry to disturb you. What is your name?" Nace "Maimunatu" tace "Nice name you get, I always wanted to name my daughter that, but I didn't get a daughter I got a son. I talked to your sister about him she said she didn't know him, but she said you might. His name is Sultan, he is a Prince in Abuja. Very handsome and very strong. I only want to know how he is doing" sai da na tattaro dukkan jarumtata sannan na iya magana, still idanuna a cikin na sultan wadanda suka chanja kala, nace "I don't only know him, he is my husband, Ummee"
MAIMOON
By
Maman Maama
Episode Eighty Seven : Riyadh
Sai da naji daukewar numfashinta ta cikin wayar, sai kuma ta fara maganar da sauri cikin rawar murya kamar mai shirin yin kuka "what? What did you just said? Sultan is your husband? Yana ina ? Yana kusa dake?" Nace "yana jin duk abinda kike fada ummee" ta sake cewa "what? Sultan? Kana jina? My son are you there?" Sultan ya taso da sauri ya taho inda nake zaune ya kwace yawar daga hannuna, ban ankara ba sai gani nayi ya buga ta da jikin bangon dakin, a take ta tarwatse a kasa, ya tsaya yana kallona yana numfashi sama sama tamkar wanda yayi gudu, sannan kuma ba tare daya sake cewa komai ba ya juya ya shiga kofar corridon da zata kaika bedroom dinsa, yana shiga ya bugo kofar da karfi har sai da dakin yayi motsi. Na mike tsaye ina kallon kofar, dama nasan sai munyi drama da sultan akan ummeen sa, amma na shirya damarar sai na daidaita su, so help me God. Na karasa inda pieces din wayata suke na durkusa na tsince, wannan wayar ta gama yawo sai dai kuma wata ba ita ba, na zare sim card dina da memory card na tattara sauran na zuba a wastebasket, na kashe kayan wutar dakin na rufe koina na bishi dakinsa, ina shiga na tarar dashi a kwance a kan gado ko kayan jikinsa bai cire ba, idonsa a rufe kuma nasan ba bacci yake ba, na shiga toilet nayi shirin kwanciya nazo na saka wata T-shirt dinsa babba wacce tazo min har chinya ta, har yanzu yana nan a yadda yake, na kashe fitilar dakin na hau gadon nayi addu'ah sannan na jawo pillow na can nesa dashi na kwanta na juya masa baya, ko minti biyu banyi da kwanciya ba na jishi ya mirgino ya dawo jikina, ya saka hannuwanshi ya zagayo ni ta baya, bance masa komai ba, mun jima a haka sannan naji yace "why did you call her bayan na gaya miki I want nothing to do with her?" Nace "bani na kirata ba ai, ita ta kirani" yace "amma ai ke kika saka har ta kira ki din, kina sane ai" nace "afuwan, ayi hakuri" yace "please don't call her again" nace "I don't even have her number ta yaya zan kirata? Besides, ka fasa min wayar ma" yace "I will get you another one tomorrow. Ko ta kuma kiranki kar ki dauka, am doing perfectly fine without her" na juyo ina kallonsa na bata rai duk da nasan duhu ne ba gani zaiyi ba, nace "why are you blaming her wai? Bayan kasan bata da laifi" yace "she left me, shine laifinta" nace "she didn't, a gaba na Takawa ya gaya maka a ka aka dauke ta aka fita da ita, what is her fault in that?" Yace "she should have come back for me, why didn't she look for me all these years?" Nace "bansani ba sultan, amma nasan dole tana da dalilin ta, uwa tafi gaban komai a duniyar nan. Ba zaka san dalilin da yasa bata dawo ta neme ka ba har sai ka bata chance, har sai kayi magana da ita, idan kunyi maganar kaji cewa hujjarta is not good enough nayi maka alkawarin ba zan sake yi maka maganar ta ba" na daure shi da jijiyoyin jikinsa, bashi da amsar da zai bani sai cewa yayi "maganar ta isa haka. Let's sleep".
Washegari na daura niyar fara abinda zan yiwa sultan, dan haka dana hada mana breakfast sai naci nawa a kitchen na kawo masa nasa coffee room dinsa, na tafiyata dakina, ina zaune a palo ya shigo, naji kamshin turarensa amma ban dago na kalleshi ba, yace "me yasa baki zo munci abinci tare ba?" Na bawa iska ajjiyarsa, ya karasa shigo wa dakin ya tsaya a gaba na, ya shirya alamar office zai fita, kallo daya nayi masa na dauke kaina, yace "magana fa nake miki Moon" na yamutsa fuska nace "naji ai, nafi son cin abincin ni kadai ne shi yasa" ya saka hannu ya juyo da fuskata yace "wai duk akan maganar wayar ne? Yanzu kafin inje office ma zan siya miki wata" bance masa komai ba kuma ban kalle shi ba. Ya dora lips dinsa akan nawa yana kissing, na kwace fuskata na mike na bar gurin ina juya masa bombom, ina shiga daki na bugo kofa ta da karfi irin yadda yayi min jiya.
Ranar Amir ne yazo daukar musu abinci, yana zuwa ya miko min waya yace "gashi inji oga kwata kwata, yace yayi miki charge, kuma dan Allah ki kirasa yanzu" na karba nace "to nagode" yace "ki kirashi fa, dan tun safe yana can ya kasa zana komai, yace rashin jin muryarki ne" na kirkiro murmushi nace "zan kira ai" Amir yana fita na jefar da wayar akan kujera nayi tafiya ta daki. Ranar sultan bai kai yadda ya saba kaiwa a office ba sai gashi ya dawo, ya tarar dani na tasa gyada mai gishiri a gaba ina ci, na daga kaina nayi masa sannu da zuwa na cigaba da abinda nake yi, yazo ya zauna a gaba na ya harde kafa yana leka fuska ta yana murmushi, saura kadan in mayar masa amma na daure na bata fuska, yayi ajjiyar zuciya yayi tagumi da hannu biyu yace "wa ya baki gyada?" Nace "ai kawa nayi aka siyo min" yace "amma kinsan duk abinda kike so ba tare muke zuwa mu siyo ba?" Nace "na hutashshe ka" yace "ina wayarki?" Nace "bana bukatar waya ni, tunda babu wanda zan kira da ita" Har ya tashi ya tafi kuma sai ya dawo ya sunkuya ya dauke ni chak ya tafi dani bedroom dinsa. Ban hana shi komai ba amma barinsa nayi yayi abinsa shi kadai, shi kadai yayi kidansa kuma yayi rawarsa, kamar zaiyi kuka yace "Love menene hakan ne kike yi wai. Please come back to your normal self, I don't like this new you" ba tare dana kalleshi ba nace "kai ka siya ai da kudinka" ya danyi shiru sannan yace "yanzu me kike so ayi?" Na juyo ina kallonsa nace "ka shirya mu tafi Riyadh" da sauri ya girgiza kai "no way, babu inda zamu je" na mike na dauki riga ta ina sakawa nace "ok, suit yourself" ina jin yana kirana nayi tafiyata ba tare dana waigo ba. Haka na cigaba da gasawa sultan gyada a hannu, he is beyond frustrated yanzu, ban hana shi taba ni ba amma shi kansa ba jin dadin abin yake yi ba, murmushi kuwa rabon da inyi masa tun kafin muyi waya da Ummee. Na kunna wayata na saka sim card dina saboda kar mutane suyi ta nema na, ban jima da kunna wa ba kuwa Hafsat ta kira ni "Moon me ya faru ne ranar nan? Wayar ta dauke kuma munyi ta kira shiru bata shiga? Na gaya mata duk yadda mukayi da sultan, tace "ai kuwa ta tayar da hankalinta, ranar kusan kwana tayi tana kuka, har sai da nayi nadamar tayar da maganar nan. Yanzu menene abinyi?" Nace "kin san halin sultan, and he is probing harder than I thought, amma zan cigaba da ganin yadda zanyi dashi. Ki kwantar mata da hankali, ki san abinda zaki gaya mata". Ranar hankali na ya kara tashi akan maganar ummee, na yanke shawarar zan shigar da Takawa cikin maganar. Yana zuwa da daddare na riga sultan zuwa, naje na gaishe shi ya amsa da fara'arsa yana min godiyar kokarin da nake gurin yi musu hidimar abinci. Na dauko waya ta na buda hoton Ummee na ajiye masa a gabansa ina kallon fuskarsa, ga mamaki na sai naga banga changin komai ba, ya dagi kai yana kallona yace "Hafsat ce ta turo miki?" Mamaki ya kara kamani nace "eh" ya gyada kai yace "tun washegarin ranar dana dawo hayyacina na aika har can Riyadh din nace a binciko min labarinta, an kuma bani labarin komai, nasan dan wanta ne yake auren yayarki Hafsat, har number dinta an turo min, what I lack is the courage to call her" na kalleshi da mamakin wai kamar shi ne zai ce bashi da courage, yace "yes, after all we went through together sannan kuma na tura mata da takardar saki kuma na kwace mata danta tsahon shekaru talatin, I don't know me zance mata in na kirata ko kuma na je wajanta" na sunkuyar da kaina, yace "sultan yaga picture din?" Nace "eh ya gani" yace "me yace?" Nace "he didn't say anything yet" yace "kina ganin zaije?" Nace "maybe, amma ba yanzu ba" yace "yayi fushi ko?" Kai kawai na gyada masa, kafin ya sake cewa komai sultan ya shigo dakin, ya bimu da kallo yana kallon waya ta a gaban Takawa, bai ce komai ba na mike na bar gurin, ina kallon sultan yana harara ta a raina nace yau akwai daru kenan. Ai kuwa Takawa yana tafiya sai gashi har dakina, "zancan me kuke yi dazu kafin inzo?" Nace "zancen Ummee muke yi" cikin fushi yace "dama dashi kuka hada baki kenan" na girgiza kaina nace "bamu taba maganar dashi ba sai yau, yanzun ma kuma ni ce na fara yi masa maganar, ashe duk abinda nake son in fada masa ya sani, yana da address dinta da number wayarta da komai amma ya kasa kiranta saboda bai san me zai ce mata ba" ya zauna a kusa dani yace "me yace?" Na juyo ina kallonsa nace "ya tambayeni in ina ganin zaka iya zuwa gurinta" ya mike tsaye da sauri "no, I am not going to be dan aiken soyayyar su, if he want his wife he should go get her by himself" nace "then go as her son, ba wai dan aiken takawa ba" ya sake cewa "NO, ita me yasa ba zata zo Nigeria ba? In tana son gani na tasan a inda nake, abinda zatayi kawai shine ta je airport ta shiga jirgi ya kawo ta Nigeria. Tunda kika ga tsahon shekara talatin bata zo ba to bata son ganina, ba zanje ta wulakanta ni inzo in ji haushi ba, maybe tayi wadansu yayan and she don't need me in her life" yana maganar yana zagaye dakin, nace "bata yi wadansu yayan ba, in fact vata kuma yin wani auren ba tun barinta Nigeria" ya tsaya da zagayen da yake yi ya kalle ni yace "then why didn't she come for me?" Na mika masa wayata nace "call her and ask her, ni bansani ba" ya karbi wayar ya ajiye a gefe, at least wannan karon ba'a fasa min waya ba. Na mike tsaye na karasa gabansa, na saka hannu biyu na riko fuskarsa nace "Sultan she has been crying tun ranar da muka yi waya da ita, ta gane abinda ya faru, ta gane kai ka kashe wayar saboda ba kason magana da ita, ta gane cewa fushi kakeyi da ita. Sultan mahaifiyar kace fa, kar ka bari ubangiji yayi