Showing 198001 words to 201000 words out of 262297 words
duk da cewa da kyar ya danne zuciyar tasa ya yi ignoring din nasa, dan a lokacin babu abinda zai bashi satisfaction irin ya ga ya zubar masa da hakoran da yake using yake smiling at his wife, amma ya danne zuciyar sa saboda a lokacin yana ganin laifin moon ne kamar ita ce ta bada hanya, bayan sun fita kuma ya biyo su, why will he follow them in ba rainin hankali ba, waye suna tafiya da matarsa zai ga tsohon saurayinta yana binsu a baya kuma ace ransa ba zai baci ba? Laifin sa daya a lokacin, bai kamata yayi playing with rayuwar moon ba, kamata yayi yayi packing motar ya fito da Ibrahim da ga tasa motar ya babballashi ya zubar a gurin sannan suyi tafiyarsu.
Suna zuwa gida a part din Amir suka tsaya. Amir ya fito ya zagayo ya fito da sultan sannan suka shiga ciki, shi Amir duk a tunanin sa Sultan a buge yake, yana zuwa ya kwantar dashi a kan gado sannan ya debo ruwa mai sanyi ya kawo masa, yana fara sha yaji ruwan kamar madaci, ya furzar ya ajiye cup din a gefe. Amir ya zauba a gefensa yace "Sultan why do you do it? Ka samu good life with Moon why will you throw it all away saboda giya?" Wani takaici sultan yaji ya kama shi yace "fuck off amir" ya juya masa baya yayi kwanciyarsa. Amma babu bacci babu alamarsa sam, yadda jiya baiyi bacci ba haka yau ma da alama va zai yi baccin ba. Wata biyar kenan da aurensu da moon amma bai taba kwanciya ba tare da ita ba sai yau, bai taba tunanin kuma zai kwanta ba tare da ita dinba, amma yau gashi basa tare kuma duk suna raye, suna kuma gari daya. She even call the security on him tasa suka fita dashi ko kallon sa kuma bata yi ba, wannan ya tabbatar masa da cewa she means what she said, rabuwa zatayi dashi kamar yadda wadda ta haife shi ta rabu dashi, kamar yadda wanda ya haife shi ya rabu dashi, bai damu ba ko ya mutu ko yayi rai. Daddy daya ke kallo a matsayin sabon uba ma ya hade masa rai, daya gaishe shi kin amsawa yayi kamar yadda in ya gaishe da takawa baya amsawa. It is all over. He was a fool to even think it will work. Moon was right, rayuwarsu ba daya bace, they care about everyone hatta wanda ya bata musu, shi kuma va haka yake ba, they expect him to do the same, instead sai gashi ya kusa aikata kisan kai. He is a monster, shi ya riga ya dade da sanin hakan, idan zuciyarsa ta debe shi shi kansa abinda yake aikatawa sai daga baya yayi mamaki. Amma kuma yanzu har acikin zuciyarsa bai ji yayi nadamar abinda yayi wa Ibrahim ba, the bastard. Yanzu haka ma da zai ganshi da sai ya karasa shi, tunda shine yayi sanadin duk wannan abinda ya faru.
Shi kam yasan rayuwarsa ta kare, a kan gadon nan zaiyi ta kwanciya har sai mala'ikan mutuwa ya tuno dashi yazo ya dauke shi. Sai kuma ya tuno da halittar da take cikin marar Moon, wani nauyi yaji zuciyar sa tayi masa, his baby, yaci burin ya haifi 'ya'ya ya nuna musu soyayyar shi da ba'a nuna masa ba. Amma kuma Moon ta gaya masa cewa idan bai chanza zafin zuciyarsa ba 'ya'yansa ma gudunsa zasu ringa yi. Yaji wani irin daci a zuciyarsa, just the thought of his children resenting him ya saukar masa da wani mugun zazzabi. Ya jawo bargo ya kudunduna, maybe the baby will be better off without him.
Tun da assuba Amir ya taba shi yaji irin zafin da jikinsa yayi, da kyar ya tashi yayi sallah ya koma ya kwanta. Gaba daya hankalin Amir ya tashi, ya manta rabon da yaka Sultan a kwance babu lafiya, tun wata rashin lafiya da yayi suna America, sultan has always been healthy and energetic. Zuwa karfe goman safe yaga zagin jikin karuwa yake yi, duk uban bargunan daya loda masa amma karkarwa kawai yake yi hakoransa suna haduwa guri daya, a hankali yaji yana magana kasa kasa, ya sunkuyo da kansa dai dai fuskarsa yaji yana cewa "Moon am sorry, moon am sorry, dan Allah kiyi hakuri ba zan sake ba" wani irin tausayin abokin nasa yaji yana ratsa shi. Menene kuwa zai hada shi da Moon har haka? Shi yasan a rayuwarsa bai taba ganin soyayya irin ta Sultan da Moon ba, to menene kuwa zai saka su bata?. Ya dauko wayarsa yayi dialing number din Moon amma wayar a rufe, ya kuma kira har five times amma bai samu ba, yayi mata text "Sultan babu lafiya, kuma ke yake nema" ya tura mata. Daga nan ya kira number din doctor din gidan ya gaya masa halin da sultan yake ciki. Ba'ayi awa daya ba doctor din yazo ya duba sultan, shi kansa yayi mamakin zafin jikin sultan a take ya saka Amir ya taya shi suka cire masa bargonan daya lulluba suka cire masa riga da wandonsa suka barshi da singlet da gajeren wando sannan suka yi ta goge masa jikin sa da jikakken towel, amma suna dora towel din sai suga ya bushe saboda zafin jikin, a haka dai uka samu da kyar jikin ya danyi sanyi kadan, idan sultan gaba daya ya juye kamar ba nasa ba, doctor din da sauri yace a saka shi a mota su tafi dashi asibiti, suna zuwa aka tafi dashi private room likitoci suka hau kansa, Amir ya zauna anan shi kadai a waiting room, kawai ji yayi hawaye yana zubo masa, a ce mutum mai gata irin sultan, a Prince, da uwarsa da ubansa da matarsa a duniya amma an kawo shi asibiti babu kowa a gurin sai shi? Yana nan yana ta kukansa har doctor ya fito yana kallonsa yace "Haba Amir, kar ka badani mana, kana namiji kana kuka?" Amir bai kula da tsokanar da yake masa ba yace "doctor how is Sultan?" Yace "da sauki zamu ce. Fear dina shine brain dinsa, zazzabinsa yayi zafi da yawa in tsoron kar ya taba kwakwalwarsa, kuma yana tunani da yawa, wannan shi ya saka muka kasa stabilizing bp dinsa, amma for now mun yi masa allurar bacci, za mu jira kuma muga sanda zai farka. But please do your best ka ga ka kawo masa abinda zai faranta masa idan ya tashi daga baccin" Amir yayi masa godiya sannan ya shiga da sauri inda sultan yake kwance, tun kafin ya karasa kusa dashi ya hango irin ramewar da yayi da kuma farin da yayi, fatar bakinsa tayi purple alamar babu isashshen jini a jikinsa, kuma zazzabin ne ya kona jinin. Ya karasa ya rike hannunsa da yaji yayi sanyi kalau yanzu alamar zazzabin ya sauka, a hankali ya fara magana "Sultan ya zanyi? Me zanyi maka ka samu lafiya sultan?" Sai kuma ya mike kamar wanda aka tsikare shi yayi kissing hannun sultan ya fita da sauri, direct gidan su Moon ya dosa, tun daga bakin gate David ya tsayar dashi fuskar nan babu rahama a cikin ta ga bindiga a kugunsa yace "you are no longer welcome here" Amir yace "ba shiga zanyi ba ai, Moon nake son gani" David yace "bata son ganin ka ita" wata zuciya ta debi amir amma ya danne yace "ya akayi kasan bata son ganina, ka shiga ka gaya mata nine nazo zata fito" David yace "itace tace in kazo kar a barka ka ganta" Amir ya sake cewa "can you at least tell her that her husband is sick kuma yana bukatar ganin ta? Am sure in ka gaya mata haka zata ganni" ko kula shi David baiyi ba ya koma kofar gidan kawai ya tsaya yana kallonsa hannunsa a rike da bindigar sa. Amir yayi wishing ina ma yana da karfi irin na sultan da sai ya farfasawa david baki ya shiga gidan ya dauko moon aka ya kaiwa sultan ita. Amma babu damar yin hakan dan yasan tunkarar David will be like a suicide, kuma yasan bashi kadai bane akwai sauran a ciki. Dole ya koma yaja motarsa ya tafi, yanzu ya zaiyi kenan? Ya zaiyi da Sultan idan ya tashi? Wani tunani ne yazo masa, ya juya kan motar sai palace, yana shiga fada ya tafi direct, mutanen gurin sai kallonsa suke yi, sun san shi amma kuma basu taba ganin shi a fadar ba, ya tsaya yana facing Takawa da yake harde akan karaga, ga Abbas a zaune a hannun daman sa, ga sauran hakimai duk kowa ya juyo yana kallon Amir, da karfi amir yace "Your son is dying, yana asibiti kuma yana nemanka" kafin ya rufe bakinsa fadawa sukayi kansa, suka jashi suka fitar dashi waje, amma ko babu komai Amir ya isar da sakon sa. Ana fita da Amir Hakiman gurin suka fara magana, 'dama Sultan bashi da lafiya?' 'Me ya same shi?' 'Allah sarki yaron ya nutsu sosai wallahi' 'ni kam kwanan nan kullum na ganshi sai yayi ta bani sha'awa' da sarkin bai da makama, da madaki, wadanda sune ake kira da king makers, suka kalli juna suka mike a tare suka durkusa a gaban sarki "Allah ya taimaki sarki ai ya kamata muje muga jikin nasa" idon takawa ya kada yayi ja saboda bakin ciki, a ransa yana cewa "wannan yaron Amir yake kowa? Zaman sa ya kare a gidan nan" amma kuma a fili ba zai iya musa wa hakiman sa ba, musamman king makers, sune kamar shugabanni dan dattijai ne sosai, sune suka nada babansa, suka nada shi, sune suke da alhakin zaba da nada sarki. Dole Takawa ya mike, gab daya sauran hakimai suka mike, Galadima ne akan gaba. Amir yana ganin su yasan tarkon sa yayi kamu, ya shiga motarsa yayi gaba su kuma duk suka biyo bayansa. Gaba daya mutanen asibitin ranar sai da suka fito kallo, ga sarki da hakimansa gaba daya sunzo dubiya, direct dakin da sultan yake kwance suka nufa. Dakin bai dauke su gaba daya ba dan haka wasu ta taga suka leka suna gano sultan a kwance har yanzu yana bacci, Amir yaje kusa dashi yana shafa kansa yace "Sultan ka tashi ga Takawa yazo duba ka" a hankali idon Sultan ya fara budewa kadan kadan yace murya can kasa "Daddy? My Daddy?" Galadima ya rike hannusa yace "eh Sultan, babanka ne yazo ya ganka. Ya jikin nasa" Sultan ya kalle shi, ya dan hadiye yawu sannan ya fara kallon mutanen dakin, idonsa ya tsaya akan Takawa da yayi kicin kicin da fuska, ya karbe hannu sa daga na galadima ya mika gurin sarki yace "Daddy?" Gaba ki daya kowa idonsa yana kan Takawa dole ya karasa ya kama hannun sultan ya rike, hawayene ya fara gangarowa a idon Sultan, amir yaji wani iri a jikinsa, tun da suka girma, tun sanda aka kaisu lagos, bai taba ganin hawayen sultan ba sai yau, masu raguwar zuciya a gurin sai da suka taya sultan kokawa saboda babu wanda bai san kiyayyar da sarki yake yiwa sultan ba kuma babu wanda yasan dalili, a hankali sultan ya fara kukan kuma sai kukan ya fara karuwa har da sheshsheka, ya rike hannun Takawa yaki chikawa. Wani abu takawa yaji ya tsaya masa a zuciyarsa ya tokare, ya kasa hadiye koma menene, ya kasa fahimtar me yake ji. Muryar sultan yaji yace "Ummee na, Ummee na". Kan Takawa ne yayi bala'in sarawa, ya cika hannun sultan ya rike kansa da hannu biyu yana ambaton sunan Allah, ummee na, ummee na, a ina ya taba jin wadannan kalmomin, wani dan karanin yaro ya hango a idanuwansa wanda bazai wuce shekara biyu ba a hannun baba gaji yana ta zunduma kuka yana miko masa hannu yana cewa "Daddy na, Daddy na, ummee na, ummee na" a lokaci daya komai daya faru ya dawo masa tas a cikin kansa, take ya yanke jiki ya fadi sumamme a gaban gadon da sultan yake a kwance.
Hmm. Things are not always what they seem.
Episode Eighty one : The Skeleton in the Closet 2
A hankali Takawa ya fara dawowa haiyacinsa, ya bude idonsa da sauri yana kokarin ya dai dai ta tunanin sa, ya ilahi wannan wanne irin mugun mafarki yayi haka? A mafarkinsa wai an raba shi da khairat, a mafarkin sa kuma wai baya son Little Love, a mafarkinsa little love shine abinda yafi tsana fiye da komai, kuma wai har anyi shekaru da yawa har Little Love ya girma yayi aure. Oh wannan wanne irin mugun mafarki ne haka? Ya yinkura ya tashi zaune yana duba gefensa dan ya tashi khairat ya bata labarin mafarkin da yayi, amma sai me? Babu khairat a gurin, kuma wannan gadon ba nasa bane ba, ya kalli dakin shima, wannan dakin shima ba dakin sa bane ba, yayi kama da executive dakin asibiti, amma kuma haduwar dakin babu abinda ya raba shi da dakin gida sai drip daya gani a hannunsa. A karshen mafarkinsa an yi forcing dinsa ya je asibiti duba little love daga nan kuma bai san me ya faru ba sai ya farka daga mafarkin, to ko dai still har yanzu mafarki yake yi ne? Ya matsa ledar drip din yaji zafin shigar ruwan, mutum ai baya jin zafi a mafarki. Ya tashi zaune sosai ya cire drip din ya mike tsaye, gaban taga yaje ya daga labulen tagar, tabbas nan asibiti ne. Ya ilahi what is happening? Kofar toilet ya bufe ya shiga dan ya wanke fuskarsa maybe ko zai dawo haiyacinsa sosai, abinda ya gani a cikin madubi shine ya saka ya daskare a bakin kofa, he looks exactly like yadda yake a cikin mafarkinsa, older, thirty years older, ya karasa gaban madubin yana taba fuskarsa, shi din ne dai kuma tabbas wannan ba mafarki bane ba. Inna lillahi wa inna ilaihir rajiun. Yanzu duk abinda ya faru da gaske ya faru kenan? Yanzu shekararsa talatin rabonsa da khairat? Tana ina yanzu, shin tana da rai ko akasin haka? And Little Love, my poor innocent Little Love. A toilet din ya durkushe yana rusar kukan dashi kansa bai san ya iya irinsa ba.
30 years back
Tabbas Prince Sadiq Abdallah yayi soyayya da Khairat Faisal Abdallah a Oxford, England. Khairat full blood balarabiya ce kuma she too is of royal blood, born and raised in Riyadh, Saudi Arabia. Soyayya suka yi mai tsanani wadda har suke ganin cewa kamar they share the same soul but different bodies. Amma duk wannan soyayyar da suke yi iyayensu basu da masaniya a cikin al'amarin, wannan kuma ya faru ne kasancewar khairat balarabiya dan larabawa da wahala su dauki 'yar su su bada ita aure ga bakar fata, bahaushe. Khairat bata taba ganin anyi haka a familyn su ba, in fact a familyn su ma mostly auren dangi ake musu, dan already ma ita da akwai wanda aka riga aka ajiye mata zata aura in ta gama makaranta. Wannan shi yasa duk nacin da Sadiq yake yi mata akan ta barshi yaje gidansu taki yarda. Lalube kawai suke yi a cikin duhu. Sadiq yasan da irin kalubalen da yake gabansu amma shi bashi da tsoro sam, kuma ya riga ya saka a ransa cewa khairat tasa ce ko da kuwa sama da kasa zata hadu babu wanda ya isa ya raba shi da ita. A haka har suka gama makaranta, iyayen Khairat suka zo suka dauke ta suka mayar da ita gida. Wannan ba karamin tayar da hankalin Sadiq yayi ba dan ya san da maganar wancan hadin da ake so ayi mata a gida. Babu shiri shima ya tattaro ya dawo Nigeria gurin sarki Abdallah, ya shigar da maganar yana son sarki Abdullah yaje can Riyadh ya nemo masa auren Khairat. Sarki Abdallah yasan abinda dan nasa yake nema is close to impossible, ba zasu bashi auren khairat ba, musammam tunda an riga an yi mata miji, ba zasu karya alkawari ba, hakan yasa yayi kokarin tausar zuciyar dan nasa akan ya hakura da auren ya dawo gida ya nemi auren ko wacece a Nigeria zai nema masa aurenta, amma Sadiq was as hard as stone, dan haka ya tubure shi lallai ita yake so kuma ita zai aura. Da Sadiq ya fahimci cewa baban nasa bashi da niyyar honoring wish dinsa ga kuma time yana kurewa dan yasan a koda yaushe za'a iya daura wa khairat aure, dan a halin yanzu ma tayo masa waya tana kuka cewa maganar auren ta tashi kuma ta fadawa babanta cewa ita bata son wanda za'a aura mata kuma shi sadiq din take so, tana fadar haka baban ta ya saka aka kaita daki aka rufeta yace ko palo kar a barta ta ta kuma fitowa. Wannan ba karamin tayar da hankalin sadiq yayi ba, dan a lokacin ji yake yi da ace ya rasa khairat gwara ya rasa ransa, sai ya hada kayansa bada sanin iyayensa ba ya gudu daga gida. Riyadh ya tafi ya kama hotel ya zauna yana plan din abinyi, ba'a karbe wayar khairat ba dan haka suna waya da ita, ita take kara encouraging din sa ma akan yazo din, suka shirya plan dinsu sosai, plan A da plan B. Plan A shine zaizo gidan su ya nemi aurenta a gurin uncle dinta. Plan B kuma shine idan plan A yayi failing an hana shi auren nata zai salallabo cikin dare ya sace ta su gudu. Sadiq yasan cewa Saudi Arabia ba Nigeria ba ce ba, suna da tsatstsauran doka, idan aka kama shi zai iya rasa ransa, babu wanda zai kalle shi ya matsayin Prince tunda su a gurinsu he is not a Prince, amma soyayya ta rufe masa ido. Ya shirya tsaf yaje ya aiwatar da plan A, amma ko kyakykyawan kallo bai samu daga uncle din Khairat ba, in fact warning ma ya buga masa kuma yace ya bashi two days yabar kasar in ba haka ba zai turo masa askarawa suyi out dashi. Sadiq zuciya kamar zai mutu dan bakin ciki, wai yanzu saboda