Showing 237001 words to 240000 words out of 262297 words
neman auren Amina da akaje yi 'yalleman, farko uncle Rufa'i yaki yarda, amma da yaga Daddy ne akan maganar sai yayi shiru, ansha dai rigima da Baffa dan cewa yayi shi bazai bawa bayarabe jikarsa ba, Daddy ne da uncle Ali suka dage, suka saka baffa a gaba da nasihohi ta lallami suna nuna masa irin tarbiyyar yaron, bashi da wani nakasu da addini zai ce kar a bashi aure, kuma suka nuna masa irin wannan intertribal marriages din shine zai kawo solution a rigin gimun kabilanci. Yanzu dai baffa ya yarda, an saka bikin Amina nan da wata biyu. Na lissafa naga kusan lokacin EDD na kenan. Sai shugabannin gwauraye na Abuja, yaya walid da yaya Habeeb, Daddy yace duk ya gaji da ganinsu suna zamar masa a gida, yace kowa a cikinsu ya fito da matar aure a hada dana Amina. Yaya Habeeb kam kamar danshi, dan sabofa yawan 'yammatansa sai da yayi ta ruwan ido kafin ya fitar da guda daya, wata Fadila 'yar Bauchi. A inda aka samu matsala shine gurin yaya walid, shi ko hanyar zuwa zance bai sani ba, ga 'yammatan kuma binsa suke yi kamar zasu kwanta masa, ga kuma kyan ga kudin, dan nesa ba kusa ba yaya Walid yafi yaya Habeeb kyau da iya daukar wanka, sai dai babu budurwa, da Daddy ya gaji da magana da kansa yayi wa Hajja waya yace ta samowa Walid mata a cikin 'yan'uwa, ai kuwa kamar an bawa kura ajjiyar nama, Hajja taji dadi sosai tana ganin Daddy ya huce mata haushin mu ni da Hafsat, kuma sai ta bawa kowa mamaki itama, mamar data zaba masa itace Zainab, 'yar autar uncle Ali. Yarinya ce karama dan wannan shekarar ta gama sec sch. Kyakykyawar bafulatana sosai ga hankali da tarbiyya irin ta uncle Aliyu, babu wasa. Uncle Aliyu bai ce komai ba sai ya tattara ta ya kaiwa hajja ita yace ita zata yi mata shirin auren, anan gurinta za'azo a dauke ta. Yaya walid kam farko cewa yayi bai yarda ba, wai shi tayi masa kankanta, sai da Daddy ya nuna masa bacin ransa sosai sannan ya hakura. Ni kam ina wata duniyar amma babu wanda ya kaini murna, dan dama can ina son yarinyar nan saboda nutsuwarta, sai dai ba tausaya mata an hada ta da shugaban bachelors na Abuja. Sultan kuwa da yaji labarin cewa yayi dai dai kenan, gwara da aka bashi karamar, dan yadda yake da shiru shirun nan in aka samo mai budadden ido aka bashi rakumi da akala zata mayar dashi. Jin labarin su Amina yasa na kira kawata Amira dan inji ya take ciki ita kuma, ta dauka da murnarta tace "maman baby shiru kin buya, wayarki ma bata shiga" nace "wallahi kuwa Amira, abubuwan ne sai a hankali" tace "dama nayi ta nemanki ne in gaya miki nagode da shawarar da kika bani, Ibrahim ya yafe min kuma sosai naji dadin yafiyarsa" nace "to me kike ciki yanzu?" Tace "ina kano yanzu. Bayan mun rabu da Ibrahim kawai sai naga cewa na bata wa mama rai itama da yawa, ta sha wahala sosai a kaina, dan haka na yanke shawarar zan huce mata haushin abinda nayi mata ta hanyar bar mata zabin mijin da zan aura, taji dadi kuma sosai, shine ta dauko ni muka dawo kano ta kawo ni gurin kanin baba, yanzu har ta saka gidan mu na abuja ma a kasuwa zata sayar ta sayi wani anan kano tayi zamanta, tace itama in ta samu miji aure zatayi" Nace "to zancen naki auren fa?" Tayi dariya tace "kinsan yadda tsarin yake ai, idan mace taki fitar da miji tayi aure sai a nemo dan uwanta shima wanda yaki aure sai a hada su. Yanzu dai wani cousin dina ne shima wai yaki yin aure, yana kasar waje karatu, shi akae cewa za'a hada mu, amma sai yazo munga juna tukunna" nayi mata fatan alkhairi muka yi sallama. Mommy tayi min waya tace "to bikin ma ba zaki zo ba sai surukan naki sun shirya?" Nace "ai bikin da saura Mommy, it won't take that long". Na kira Ummee ina son inyi tsegumi inji ya suke ciki, har muka gama hirar mu bata cemin komai ba, sai zancen kayan babies din da take yin order take min, har zamuyi sallama nace " Ummee is there any chance na zamu dawo gida nan kusa?" Ta yi shiru sannan tace "wato ku kuna son kuji status din mu amma mu ba zaku gaya mana naku ba ko? Tunda ba zaku gaya mana a ina kuke ba shikenan kowa ya rike labarinsa" but from her voice naji kamar things are going the right way. A bangaren sultan kuwa tunda muka zo Maldives ya kira Amir wanda shima duk shirye shiryen bikinsa sun sako shi a gaba, ga babban abokin ya gudu ya barshi, yace yake turo masa aiki yana yi daga nan, dama kuma aiyukan sun taro sosai, dan haka ya turo wa sultan da yawa. Haka sultan yake zama in his spare times yayi ta zane, ni kuma a lokacin nake samu inyi bacci, wani zanen in naga sultan yayi har mamaki nake yi, gaskiya zane baiwa ne ba kowa Allah ya bawa ba, dan in sultan yana zana gida ko mistake din measurement baya yi, wannan ya saka kullum contracts ne suke shigo masa ba sassautawa. Sultan is spending and making money at the same time.
Watan mu biyu a Maldives, ya zamanto cikina yana da wata takwas kenan. Ranar nan na kwanta ina ta bacci akan kujera, sultan kuma yana ta aikin zane a system dinsa, na farka naga 12:09 na dare, na shiga toilet nayo shirin kwanciya sai kuma naji ina son mijina, nace "wai wannan aikin ba zai kare bane ba?" Ya danyi tsaki yace "nima na gaji fa, the thing is complicated kuma wai gobe suke bukata zasu fara gini, dole yau zan kammala in tura musu. Nace "why not ka tura musu gobe su fara aiki jibi? Menene banbancin gobe da jibi?" Yace "I just want to finish it today, shikenan na huta, gobe sai fara wani" nace "OK" amma a raina nace "kayi aikin mu gani" na cire kayana na saka wata rigar baccina iya rabin cinya, babu komai a ciki, na zagayo ta gabansa na zauna a kujerar da take facing dinsa, ya dan dago kansa ya kalleni, ya danyi murmushi kadan ya cigaba da aikinsa, na dauko alawar tsinke na fara sha ina kallonsa, yana ta satar kallona ta saman system din gabansa, can yace "damn it, how do you want me to concentrate and finish this work on time while you are sitting there and looking like this?" Na cigaba da shan alawa ta nace "I don't want you to concentrate on that work, I have another work for you here" ya dan maida hankalinsa kan system din gabansa, na dauki kafa daya na dora akan daya, na jingina baya na da jikin kunerar, kallo daya yayi min sai yayi slamming system din ya rufe ta yace "fuck the work then, I will finish it tomorrow" ina dariya har ya karaso inda nake, nace "yanzu kayi magana" ya biyo ni kan kujerar yace "your wish is my command, master". Da safe muna baya wajan swimming pool, ina zaune na saka kafafuwana cikin ruwan shi kuma yana ta swimming dinsa sai wayar sa tayi kara, na dauka sai naga number din Zayed, ya karaso da sauri ya goge hannun sa ya karba ya saka a kunne, sum danyi magana sai naga ya kalle ni da sauri fuskarsa da damuwa, sai kuma ya kirkiri murmushi, amma nasan murmushin karya ne, da sauri ya karasa fitowa daga cikin ruwan ya shiga daki, bai damu da ruwan da yake diga daga jikinsa ba, daga gani bayaso inji abinda suke cewa ne, gaba na ne yayi muguwar faduwa har saida dan cikina ya motsa. Da sauri na tashi na bishi a baya. Ina shiga dakin yana kashe wayar, ya tsaya yana kallona, nima kallon nasa nake yi. Ya ajiye wayar yace "we are going to Nigeria" jiri naji ya debe ni, da sauri yazo ya rike ni ya kwantar a jikinsa, na bude bakina da kyar nace "waye ya mutu?" Ya dauke kansa daga kaina yace "kawai dan nace zamuje Nigeria sai kice wani ne ya mutu?" Na rike rigarsa nace "Hafsat ce ko? Zayed ne ya kiraka, Hafsat ce ta mutu ko?" Yace "in Hafsat ce ta mutu ta yaya zayed zai kira ni?" Sai na fashe da kuka nace "wayyo Mommy, wayyo Daddy, Na shiga uku" da sauri ya rike fuskata yace "ba Mommy da Daddy bane ba" nima na rike tasa fuskar nace "Faruk? Allah sarki faruk jiya mukayi waya dashi" ya dan bata rai yace "Moon, get yourself together, saboda an san abinda zakiyi kenan akace kar a gaya miki, you know your condition, gashi kina da high bp, kukan da zaki yi ba zai dawo da wanda ya mutu ba, sai dai kisa kanki dani da babyn mu cikin matsala. Ba Faruk bane ya mutu, ba Hafsat ba ba Mommy ba ba Daddy ba" a hankali nace "waye" ya jawo ni jikinsa ya rungume, na tsaya da kukana ina sauraron inji waye ya mutu.
Episode Ninety Four : RIP
Ya rike fuskata a hannunsa yana kallon cikin idona yace "kinsan dai da rayuwa da mutuwa duk na Allah ne ko? Kinsan babu wanda ya isa ya raya wani idan har Allah ya rubuta cewa kwanansa ya kare ko? Kuma kinsan babu wanda ya isa ya kashe wani in har kwanansa bai kare ba ko? Iyaye, 'yan uwa, miji ko mata, 'ya'ya dukka Allah ne yake bamu su kuma shi yake karbar su a lokacin da yaga ya dace. Duk lokacin da muka rasa wani abinda ya kamata muyi shine mu gode wa Allah daya bamu su tun farko, har muka rayu dasu muka ji dadinsu suma suka ji namu, dan daga mu harsu na Allah ne. Idan mutum ya riga ya mutu babban abinda yake bukata daga gare mu shine addu'ah, mu nema masa rahamar ubangiji tare damu baki daya, mu kuma yi fatan Allah ya sada mu dashi a aljannah inda zamuyi rayuwa ta har abada ba tare da tsofa ko mutuwa ba. Maimunatu Allah yayi wa Baffa rasuwa jiya da daddare, yau da safe akayi jana'izarsa aka kaishi gidansa na gaskiya." Wani sabon kuka ne ya taso min, yayi sauri ya hade bakinsa da nawa, sai da yaji na tsayar da kukan sannan ya sake ni, na ture shi da sauri na fara kokarin mike wa, ina jin kaina yana juyawa, wayyo Allah baffana, wai baffa ya tafi ya barmu shikenan ba zamu sake ganin sa ba? Na runtse idona ina hango kyakykyawar fuskarsa ta fulani mai cike da kwarjini da fara'a, innalillahi wa inna ilaihir rajiun, sultan naji ya sake rike ni yana kokarin zaunar dani "Moon zaki fadi fa, menene hakan wai? Shi yasa tunda aka kaishi asibiti aka ce kar a gaya miki saboda an san halinki" na juyo da sauri ina kallonsa bibbiyu, nace "asibiti? Au dama bashi da lafiya amma baka gaya min ba? Daya mutum ma har sai da aka binne shi sannan za'a gaya min" ya sake kokarin rike ni na ture shi, yace "to inda an gaya mikin ma menene zaki yi masa? Za ki cire masa ciwon ne ko kuma zaki hana shi mutuwa?" Da karfi nace "I could have been there for him, I could have hold his hands and say goodbye to him" yace "and what difference will that make?" Nace cikin fada "It would have make me feel better". Na rufe fuskata da hannayena na fara kuka a hankali mai shiga zuciya. Duniya kenan, ina nan ina enjoying rayuwata ashe Baffa yana can yana sallama da duniyar gabaki daya. Sultan ya zo ya durkusa a gaba na, har yanzu swimsuit din jikinsa a jike take yace " ya salam, moon da kinsan yadda nake jin kukanki a raina da kin daina, da ina da dama da ba zaki taba kuka a rayuwar ki ba, amma ba zan iya dawo miki da baffa ba, dan Allah ki tausaya min ki daina kukan nan haka" ni haushi ma naji yana bani, daga shi har sauran 'yan gidan mu duk haushi suke bani, tunda duk muna waya dasu kuma duk sun san baffa yana asibiti amma babu wanda ya gaya min. Ya dora hannunsa akan cinya ta na ture hannun na juya baya na na cigaba da kuka na. Ina jin shi ya mike ya shiga toilet, naji alamar shower sai kuma ya fito ya shirya, har lokacin ina zaune ina kuka na, yazo ya zauna kusa dani, na matsa. Yace "am sorry Love, nasan bashi da lafiya amma kinka yanayin da kike ciki, ga problem din bp dinki, wannan yasa aka ce kar wanda ya gaya miki, babu wanda yasan mutuwa zaiyi saboda babu wanda yasan gawar fari sai Allah. Am sorry" yayi kokarin juyo dani in kalle shi amma naki yarda, ya rabu dani yace "zan je airport yanzu in gani ko da akwai plight zuwa Nigeria yau ko gobe. Please dan Allah promise me you will stop crying" ya zagayo ta side din da fuska ta take, ya saka hannu ya bude fuskata dana rufe da hannuna, fuskarsa tayi abin tausayi, ya goge min hawayen fuskata, yace "kinji abinda na gaya miki? Ina so inje in samo mana plight tickets amma bana son in barki kina kuka kuma, please ki daina sai in tafi. In baki daina ba kinga ba zanje in sama mana plight ba ballantana mu tafi Nigeria" na goge fuskata ina kallonsa nace "na daina to" yace "promise" nace "I promise" sai da yaga na tsaida hawayena sannan ya fita, yana fita na hau kan gado na kwanta na cigaba da kuka na.
Wajan karfe daya ya dawo, inajin shigowarsa na rufe idona kamar bacci nake yi. Ya dan jima a tsaye yana kallona sannan ya hawo gadon ya dan taba jikina, yace "my God, kukan ki ka cigaba kenan ko? Bayan kinyi min alkawarin ba zakiyi ba" bance masa komai ba, naji ya sauka daga kan gadon, na bude idona ina kallonsa naga ya dauko first aid box din mu ya dauko min magunguna na, ya dauko bottle water ya bude ya hawo gadon ya mikar dani tsaye ya bani nasha. Na koma na kwanta ina kallonsa nace "so.., when are we going?" Ya dan shafa kansa yace "babu plight zuwa Nigeria yau da gobe, sai jibi idan Allah ya kaimu." ya miko min tickets guda biyu na karba ina kalla, that means sai Baffa ya kwana uku da mutuwa sannan zanje gida. Na lunshe idona ina jin jikina yana relaxing saboda maganin da nasha. Ina nan a kwance ina kallon sultan yana kokarin fara hada mana kayan mu, yayi waya restaurant ya fada musu abinda zasu kawo mana for lunch, da kyar na tashi nayi sallah na koma na kwanta. Bana kukan yanzu amma kuma raina gaba daya babu dadi, duk maganganun da muke yi da baffa ne suke dawo min rai na. Irin nasihohin da yake yawan yi mana akan gudun duniya, akan zumunci, akan biyayya ga iyaye da kuma miji. Da kyar sultan ya matsa min na danci abinci na koma na kwanta. Karfe biyar na yamma sultan ya gaji da zama shi kadai ya fita waje, sai kuma gashi ya dawo da sauri yazo ya daga ni tsaye ya fara kokarin cire min riga, na rike hannu sa, "sultan menene haka?" Bai ce min komai ba ya dauko wata rigar mai kauri da dogon hannu da collar ya saka min, ya saka min hula da safa ni dai duk ina kallonsa, nace "ina zamu je kuma" yace "kifi zaki je ki kamo mana ki gasa mana muci da daddare" na dan bata fuska nace "kifi kuma? Ni ban iya kama kifi ba" yayi murmushi yace "yau zaki koya, common, let's go" ya kama hannuna muka fita. A hankali naji na dan fara sakin raina, bawai na daina jin zafin mutuwar bane ba, na dai daina jin haushin sultan. Wani boat muka dauki haya muka shiga, daga ni sai shi, shi ya tuka ya kaimu tsakiyar ruwa sannan ya dauko wani dan kwando ya bude ya dauko wata kugiya ya daura zare a jikinta, sannan ya zagayo ya zauna a baya na, ya saka kafafuwansa a both sides dina, ya kama hannayena da nasa, ya saka fuskarsa a wuyana yace min a cikin kunnena "I am going to teach you how to catch a fish" cikin raunanniyar murya nace "sultan Baffa ne fa ya mutu, how can I just be busy catching fish bayan Baffa ya bar duniya?" Yace "mutuwar Baffa tana nuna mana abubuwa da yawa, daya daga cikinsu shine; there is an ending to life. Duk shekara, duk wata, duk sati, duk yini, duk awa, duk minutes, duk second din daya wuce ba zai dawo ba. What we need to do is to make the best of our time kafin namu lokacin muma yazo. We should live our life because it is a gift from God. Baffa yaji dadi, yayi rayuwa mai tsaho kuma mai kyau, ya tafi ya bar zuri'ah mai albarka. Wani tun kafin yayi aure ma yake mutuwa, wani tun yana yaro ma kafin yasan menene rayuwa yake mutuwa, wani ana haihuwarsa yake mutuwa, wani kuma tun a cikin mahaifiyar sa yake mutuwa, shi ko duniyar ma bai gani ba ballantana yaji dadinta. Wani kuma zai yi rayuwar mai tsahon har yakai kamar shekarun Baffa amma kuma sam babu abinda ya tsinana a cikin ta, babu abinda in ya tafi za'ace ga abinda ya bari na alkhairi sai dai na sharri. Amma baffa kuma fa? Ko mu daya bari ba mun isa mu taya shi gode wa Allah ba? Mu taya shi neman rahamar ubangiji ba?. Mutuwa is a circle of life, wani ya mutu sannan a haifi wani. Jiya da baffa ya mutu hundreds of babies were born all over the world,