Showing 72001 words to 75000 words out of 105783 words
sannan Mom ta fita ko da ta fita sadiq ta aika ma harara tare da ayana ma ranta idan sun dawo zatayima tufkar hanci.
Katafarin parlour su da aka ware danyi meeting suke zaune, tunda sadiq ya shigo gabansa ke yankewa yana fad'uwa yarasa dalilin hakan addu'a da ke bakinsa ya furta dan samun nutsuwa, duk kuma ya damu da yanayin daya bar fatu yafi tunanin harda hakan ya hanasa nutsuwa, majeed ne ya shigo tare da zama gefen sadiq ya miqa masa hannu suka gaisa dakyar sadiq ke danne zuciyarsa kan majeed da bata hakuri.
Alhaji Babba ne ya shigo sanye da babba riga tasha aiki sai sheqi kayan suke, da sallama ya shigo tare da zama a kujerarsa ta musanman wato kakan su sadiq, Ammi na gefansa na dama sauran jikoki da iyaye na gefe da yan uwa.
Taro ya fara budewa da addu'a sannan ya fara jawabin cikin nutsuwa ya ce, " ina maku barka da zuwa Allah yasa yarda ku ka zo taron nan lafiya mu koma gida lafiya, kuma na ji dadin yarda kuke zuwa wannan taro na qara dankon zuminci kamar yarda kuka sani ko wani lokaci muna samun alherai da yawa bangaran kasuwancin mu ina ma albishir da abubuwa da yawa na farin cikin a wannan shekara mun samu kimanin billioths of naire cikin ribar kasuwancin mu, mun talafawa gidan marayu da asibitoci mun biyawa mutun 30 kujerun maka..! kabara wajan ya dauka tare da hamdallah.
Gyaran murya Alhaji yayi ya ce, "Kuma ga muhimiyar sanawar Majeed ya samu matar da zai aura..! sadiq dake zaune saman kujera gabansa ya qara yankewa ya fadi ras-ras muryar Alhaji babba ce ta dawo masa dodan kunne, "Alhamdulillah mun nema an bamu saboda karamci, ba kowa bace sai yar gidan ibrahim wanda yake ruqo fatuha..! har gidan iyayan ta muje munyi bincike ashe ma akwai sanaya a tsakanin mu kuma sun aminci sun bada haka ya mana dadi matuqa..! wani irin gumi ne ya karyo ma sadiq maitsananin zafi take nan ya fara ji wutarsa na d'aukewa jikinsa rawa ya d'auka jin kalaman Alhaji yake tamkar saukar aradu, wani irin amo kalaman suke masa cikin brain, ba sadiq ba hata Mom sai da ta girgiza da wannan furucin, ita dake qoqarin furta abinda ke ranta sai gashi an masu shigar sauri da karfi kirjinta ke bugawa tana tunanin halin da d'an autanta dilo zai shiga, wata kalmar ya qara jefowa a karo na biyu "sadiq kuma mun yanke shawarar bashi kanwarsa Basma amma da sharadi idan har ya kawo wadda yake so nan da sati daya kamin asa biki to za'a basa dama ya auri wadda yake so, Basma ma kuma ta hakura wannan shine hukuncin dana yanke.! sannan ya kalli baban Basma ya ce, "Alhaji khabiru cika mana taro da addu'a..!
Gabaki d'aya parlour juyawa sadiq yake dakyar ya samu ya miqe, jiri na neman kadasa majeed ban da murna ba abin da yake finally yanzu zai samu fatu shawo kanta kawai ya rage masa, ko ta kan sadiq bai bi ba haka Basma baki har kunne tana ganin shawo kan sadiq ya so ta abu ne mai sauki kamar yarda Umma ta sheda mata.
sadiq ne kadai da Mom basu farin ciki, sai Hanan da tashin hankali ya hanata motsi sanin matsayin da fatu ta aje sadiq.
yana fitowa daga parlour parking space ya nufa cikin sauri ya bale murfin mota ya shiga, da gudu ya fisgi motar ya harba kan titi gudu yake tsulawa kamar zai tashi sama, ko ganin gabansa ba yayi saboda tsanin tashin hankali mara musaltuwa, fatu da majeed abun kamar a mafarki, yana isowa gida ya danna horn da karfi dan sam bai san mai yake ba, bala mai gadi na bude masa geta ya ce "Subhanilillah..! Saboda yadda sadiq ya shigo da motar da mugun gudu kamar zai tashi da bala mai gadi.
ko daidaita parking ya kasa ya bale murfin motar ya fito, cikin sauri ya wuce part dinsa yana shiga ya zame bakin kofa tare da dafe kansa, jijiyar kansa duk ta taso saboda tsabar tashin hankali maganar Alhaji babba na dawo masa, cikin dodan kunne miqewa yayi ya shige bedroom saboda har yanzu bai dai na ganin jiri ba, gani yake kamar kunnasa bai ji dai-dai ba wani irin kuka sadiq ya saki mai tsuma zuciyar mai saurare kneeldown yayi a wurin bakinsa na rawa yana furta, no..! No..! I cant believe abinda kunne na ya ji noo..! fatali da kayan d'akin sadiq yake kamar sabon kamu, duk abinda ya dauka ya wurga sai ya watse ya dawo kasa sai da yayima d'akin fata-fata ya shiga toilet da kayan jikinsa sakar ma kansa shower yayi, maganganun Alhaji babba har yanzu ke masa yawo a brain wata zuciyar ta ce "Wato jiya fatuha tabama majeed izinin turawa gidan su? Dama fatu ba so na take ba? Jikin sadiq na rawa ya furta Kalaman bakinsa hadeye kukan da yake yayi ba shiri ya fito sharkaf ya zauna kasan carpet bai damu da kayan dake jikinsa ba ya takure waje daya.
Bangaran fatuhu ko tunda su Mom suka fita gabanta ke faduwa, ta rasa dalilin haka ta rasa sukunin ta jin an bude kofar d'akin ya sata waigowa Mom ce tsaye bakin kofa murmushi fatuha ta saki wanda iya karshi la66anta ta ce, "Mom har kun dawo da wuri haka? eh tace tana qoqarin danne damuwarta, ta qarasa shigowa zama tayi kusa da fatuha cikin sanyi murya ta ce "Fatuha gobe da safe ki shirya zaki je wudil Baffa nasan ganin ki?" sannan ta tashi ta fita kallo fatuha tabi Mom da shi take nan jikinta ya haubari da tsoro-tsoro ko dai uncle ya kai qarata kauda zancan tayi tasan ma ba zanyi haka ba, amma zuciyarta na cike da tanbayoyi, ganin bata da amsa ta hakura.
Ola sadiq ya kira a waya bugu d'aya zuwa biyu ya dauka, "ina san ganin ka" sadiq ya fada a taqaice.
ko da ola ya zo ganin watsin da akayima dakin sadiq ya tsorata kallon sadiq yayi da magana a bakinsa, ganin fuskar sadiq ba annuri yaja baki ya tsuke, nuni ya masa daya gyara d'akin shi kuma ya shingida saman sofa, yana jin wani quna da suya da zuciyarsa ke masa hawaye daya na bin daya saman fuskarsa kamar ba soja ba,
Gabaki d'aya gidan Alhaji Ibrahim ba wanda ya rintsa, daga angel sai Abba ne kawai suka samu bacci,
bangaran sadiq ban da kukan zuci ba abinda yake, fatuha kuwa tunanin me yasa Baffa ke neman take? ko dai inna ce ta rasu? ba'a son fada mata girgiza kai kawai tayi.
Tunda safe fatuha ta tashi ta shirya cikin riga da sket dinta na atamfa yellow mai ratsin white a jiki masha Allah kayan sun hauta sai dai fuskarta tayi fayau, bayan ta kamala ta fito parlour cikin nutsuwa ta gaida Mom da Abba dake ta break angel na gefe itama ganin bata ga sadiq ba yasa gaban ta ya qara faduwa a karo na biyar jiki ba qwari ta zo ta hada tea kurba biyu zuwa uku ta aje Mom ce ta ce, "Fatuha har kin koshi?
"eh Mom dama idan zan yi tafiya bana wani cin abinci" to Mom tace, sannan ta qara da cewa, "ga driver nan zan had'a ku da shi idan ya kai ki yau zai maido ki, ki gaida mutun gida sannan idan kin isa ki kira ni ki fada min" lagwabe kai fatuha tayi ta ce, "Mom ai jiya wayar ta lallace"
"garin yaya?
"fadowa tayi daga saman dressing mirror ta dauke"
"eyya to bari na baki baby Nokia idan kin dawo a sake wata" to fatuha tace tare da shi ga daki ta dauko sim dinta, miqa mata wayar Mom tayi ta zura sim dinta ciki har ta kai bakin kofa ta dawo ta haurawa sama part din sadiq ta nufa a hankali ta murda handle din kofar taji kule gam tsoro ne ya kamata amma ba yadda ta iya haka ta dawo, tare da yima mom sallama angel ko sai rigama take sai tabi fatuha Mom ta hana.
Shigewa mota tayi driver ya harba da su kan titi cikin dan qanqanin lokaci suka isa wudil, cikin kwatancan fatuha har driver ya kawo ta gida fitowa tayi a hankali tana qare ma gidan su kallo gabaki daya gidan ya canza a yadda ta san sa, mamaki ne ya bayana a fuskarta qarasa shiga tayi ciki da sallamah Inna dake parlour ce ta fito da murna tana yima fatuha maraba da zuwa duk da fatuha ba'a cikin jin dadi take ba bata yadda inna ta gane ba, parlour ta jata suka shiga har yanzu mamaki ne shinfide a fuskarta tana qarewa gidan na su kallo yarda yayi kyau ko abirni sai haka ta ce cikin sanyin murya "inna waya gyara gidan nan? murmushi inna ta saki ta ce, "yaron arziki sadiq wallahi shi ya mana abin arzikin nan, ya canza mana gida ya koma kamar aljanna duniya" murmushi fatuha ta saki mai cike da jin dadi Baffa ne ya yaye labilan dakin ya shigo har qasa fatuha ta tsugunna ta gaisheshi amsa mata yayi a taqaice sannan ya samu wuri ya zauna, itama fatuha qasa tayima kanta mazauni tana jiran jawabin Baffa gyaran murya Baffa yayi da cewa, "Fatuha.!
Na'am Baffa.!
"Fatu nasan cewa na maki laifi amma kiyi hakuri ina fatan bazaki watsamin qasa a ido ba? ina fata bazaki bani kunya ba? duk wannan jawabin da Baffa keyi kan fatuha na qasa d'ago kai tayi ta ce, "insha Allah Baffa bazan baka kunya ba"
"yauwa diyar albarka, dama nasan baza ki watsamin kasa a ido ba, dama d'an uwan sadiq ne ya zo neman auran ki tare da iyayansa jiya daddare, mukanmu munyi mamaki da wannan zuwa fatuha ganin halacin da zura'a suka mana gashi nasan baban yaron hakan yasa na amince dan na lura yaron mai nutsuwa ne, Kuma dama neman auran budurwan anso iyayanta su za6a mata miji na gari da wannan nayi la'akari na za6a maki majeed a matsayin miji..! dagowa fatuha tayi a razane dan sai yanzu ta fahimci inda aka dosa idanuwan ta taf da kwalla suka ciko nan take hawaye suka fara anbaliya a fuskarta me yasa mai kyau zai mata irin wannan horan me yasa zai mata haka dama hukuncin daya dauka kenan dama majeed ne dalilin fushin da mai kyau yake da ita mai yasa bai ji ta bakinta ba, fita tayi daga parlour da gudu ta fada dakin inna ta saki wani irin kuka mai tsananin ban tausayi, inna ce ta dafa bayanta tana lallashinta cikin tattausar murya, "haba fatuha bai kamata ki watsawa muta nan qasa a ido ba duk halacin da suka maki banyi tunanin haka daga gare ki ba, kuma yaron nan kin san sa, kuma kowani mutun da qadarar dake zuwa masa fatuha idan dai majeed alkhairi ne a gare ki Allah ya tabatar ke dai na ki addu'a ne" haka inna ta dinga bitana tausar fatuha har ta samu tayi shuru tana sakin ajiyar zuciya, ko ruwa kasa sha fatuha tayi sai bayan sallah la'asar suka dau hanyar kano wayar tace dake cikin jaka taji qara message ya shigo sai a lokacin ta tuna da Mom tace ta kira ta curo wayar tayi ta karanta message din kamar haka,
Sister ina matukar farin cikin sanar dake yau buri na ya cika, mafarki na ya kusa zama gaske, tun jiya nake qoqarin kiran ki wayar taki shiga ba wani albishir bane ila yaya sadiq ya kusa zama miji a gare ni, sannan ina taya ki murnar zama in-law a gidan mu cikin family din mu daga Basma your sister..
Wani irin kuka fatuha ta saki mai cinrai ko qarasa karanta sakon ba tayi ba wayar ta fadi jikinta ban da bari ba abin da yake, ashuru driver ya juyo ya ce, "haba fatuha komai yayi zafi maganin shi Allah bai kamata kina kuka irin haka ba , addu'a ce makamin mumini..! duk wannan magana da ashuru yake fatuha ba jin shi take ba kalmar sadiq yazama miji na kawai ke yawo cikin qwaqwalwarta har suka iso garin kano fatuha na sheka kuka kamar ranta zaifi ta, ko da ashuru yayi horn aka bude geta kafin ya tsaida motar ta bale murfin motar ta fita da gudu sadiq da yanzu ya ji qarar shigowar mota daga labila yayi tare da koma ya cigaba da zarya a bedroom.
Da gudu fatuha ta haura sama ko kallon mutanan parlour batayi ba part din sadiq ta wuce Allah ya bata sa'a tana bude kofar ya bude, ganin bata gashin a parlour ba yasa ta shigewa bedroom da gudu.
fadawa tayi jikin sadiq dake tsaye tare da sakin kuka mai cinrai, rintse ido sadiq yayi yana jin yadda fatuha ke sheqa kuka, sai yanzu ya gane ba sa hannu fatu cikin abinda ya faru cikin sarkewar harshe ta ce, "Uncle dan Allah karkamin haka wannan horan yamin nauyi wallahi bazan iya dauka ba, kaji mai kyau..! my uncle..! my happiness..! dama ace mafarki nake abin da nake ji ba gaske bane..! ta ida zancan tare da sakin sabon kuka ta zame kasa.......
Written by
Salma mas'ud nadabo
Edit by
Raheenat
📘REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★We are the best★
http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opera_speed_dial_&yn= H-R
*Email* [email protected]
*Facebook* www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERS FORUM.COM
77_78
Kuka fatuha ke rairawa kamar ranta zai fita, gabaki d'aya jikinta rawa yake qafafuwan sadiq ta riqe cikin shashekar kuka ta ce, "Please uncle I beg you in the name of God a janye maganar auran nan, wallahi ban shirya yin aure ba yanzu ba, babu abinda ke tsakanina da majeed i swear.! taqara rushewa da wani sabon kuka har yanzu jikin fatuha 6ari yake bakinta na rawa ta ce, "uncle ya zanyi da karatu na? bayan duk duniya ba abinda nake so sama da shi, wallahi uncle ba abinda ke tsakanina da majeed kaji..! ta qara sakin kuka mai cin rai ( ko ni salma sai da na matse kwalla😥) da kyar sadiq ya sai ta kansa ya hade hawayan dake maqale a kwayar idanuwansa, juyawa yayi, ya d'ago fatuha tsaye dake durqushe tana kuka ya zaunar da ita zaman bed amma duk da haka ba daina kukan tayi ba jikinta sai rawa yake tana faman sauke ajiyar zuciya, fridge ya bude ya curo robar ruwa ya tsiyaya a cup ya miqa mata, kuka kawai take baji ba gani, aje cup din sadiq yayi saman bedside drawer ciki cool voice sadiq ya ce "Fatuha..! tsagaita kukanta mai sauti tayi tana kallon sadiq hawaye na sulalo mata, lallashin ta sadiq ya shigayi cikin sanyi murya ya ce, "Fatuha ina so ki sani ko kadan bani na maki haka ba dan me zan maki haka ba tare dana ji ta bakin ki ba" daura hannusa yayi a fuskarta, haka itama fatuha ta daura nata saman hannusa tana sauke ajiyar zuciya, ya cigaba da cewa "Bayan na dau alqawarin samamaki farin ciki har qarshan rayuwar ki fatuha? dan meyasa zan rusa maki mafarkin ki da alkwarin dana dauka? ina so ki kasance mai daukar qadara mai kyau da mara kyau, da anyi shawara dani fatuha ba abinda zai sa na amince a katse maki karatun ki, ko a baki abinda baki so, ko yanzu nasan majeed zai barki kiyi karatu kinji, ki kasance me yima iyayan ki biyaya zaki ga ribar haka, kuma insha Allah zaki so majeed saboda majeed nada kyawawan hali kuma yana son ki zai baki duk wata kulawa, ba zai bari ki taba zubar da hawayan ki a kansa ba, na tabbata yana sonki so haqiqa ki daure ko so d'aya ne ki sama ranki son majeed ko dan yana dan uwa na..! wasu zafafan hawaye ne suka gangarowa fatuha tana bin sadiq da kallo, dan ko bakin magana ta rasa, dama mai kyau bai ta6a jin sonta ba dama ita ke haukarta, tunda gashi shawara yake bata ta so wanin sa.
sadiq ko ban da daurewa ba abinda yake dan numfashinsa neman yankewa yake, sai ya numfasa yake cigaba da maganar saboda zafi da quna da qirjinsa ke masa ganin fatu zatayi nisa da shi, glass cup sadiq ya miqa ma fatuha da ruwa ciki amsa tayi jiki mace ta kafa kai ta shanye ruwan a hankali taji sanyin ruwan na ratsata, shiru suka dauka na mintina ba wanda ya tanka, can sadiq ya ce, "Fatuha kimin promise baza ki tada hankalin ki ba" dakyar fatuha ta iya furta to wasu hawayan suka sulalo, jiki ba qwari ta tashi tana qoqarin fita sadiq ya bita da kallo dan bai jin zai iya tsaida ta saboda ganin tama qara famamasa ciwo ne a ransa.
Tana fita sadiq ya kafa rubar ruwan ya shanye yana maida numfashi tare da ganin wasu taurari namasa yawo.
Tsayawa tayi bakin steps ta share hawayan ta dan bata san Mom ta gane cikin nutsuwa ta sako, tana wasa da yatsun hannuta Mom da fitowar daga kitchen kenan ita da baba jummai murmushi ta saki ta ce, "ah fatuha har kin dawo? eh tace tana qoqarin hadiye hawayan idanuwan ta Mom ta ce, "Ahamdulillah ya su inna?
"lafiya lau" ta ce, sannan Mom ta ce, "ina fata Baffa bai maki dole ba" d'aga kai fatu tayi alamar a'a idanu ta taf da hawaye tana wasa da yatsun hannuta baba jummai ce ta shafa fuskarta ta ce, "Alhamdulillah hajiya ni dai bani da abin cewa kun gama min komai a rayuwata" ta ida zancan tana matsar kwalla ta cigaba da cewa, "daga kawo