Showing 75001 words to 78000 words out of 105783 words

Chapter 26 - Captain Sadiq Book 1 Hausa Novel Complete

18 Jan 2025

726

fatuha aiki sai gashi ta zama yar gida har zaku aura da ita hajiya na gode na gode, Allah ya bar zuminci" baba jummai ta fada tana share kwalla idanuwanta Mom  ta  ce, "haba baba ai duk mun zama d'aya ai fatuha ta cancanci abinda yafi haka, kamar  'ya take  waje  na" Mom  ta  fada  cikin  sanyin  murya  tana  mai  taya  sadiq  bakin  cikin  rashin  fatu duk  halin  da  yake  ciki  tana  sane  sarai, haka baba jummai ta dinga zuba Godiya sannan tasa kai ta fita, fatuha kuma ta shige bedroom  ko da shiga d'aki sana'ar ta fara wato kuka dan ya zamar mata jiki daga shekaran jiya zuwa yau,  bedside drawer ta bude ta ciro sarqar da sadiq ya bata tana kuka tana  zancan zuci, dama  duk  abin da sadiq  yake  mata  ba  so  bane  mai  yasa  captain  zai  mata  haka, bayan  ta  jima  tana  fama  da  sonsa  tun   kan tasan  me so tunda  tasa  kafarta gidan ta  kamu  da  son sa  amma sai gashi wani  sabon kuka ne  ya  kwacewa  fatu kuka  ta  ci sosai har ta gaji sannan bacci ya dauke ta.

      Bangaran Basma ban da murna ba abinda take daga  ta  kama  wannan  pillow  sai  ta  saki ta  Kama  wannan, tana  jujuyawa  cikin  dakinta  cike  da annushuwa, duk wasu qawayanta ta fesa masu zata auri handsome, har wani jin ta take a sama yanzu, zata  auri  captain.
                     majeed ko ya kira layin fatuha har ya gaji yanke shawarar zuwa gidan gobe yayi yaga sanyin idaniyansa, duk  da  cewa  yasan  ya  mata  katsalandan a ganin  sa  komai  zai  wuce, sannan ya juya ya gyara kwanciyarsa cike  da  kewarta.

      Washe gari
             Kiran sallah ne ya tashi fatuha jiki ba qwari ta shiga toilet ta sheqa waka ta dauro alwala wani irin jiri ke dibar ta, saboda kukan da tasha jiya dakyar ta iya gabatar da sallah ta zura uniform dinta ta dauki school bag din ta ta fito,

        Ko da ta qaraso dining area Mom ce da Abba sai angel dake gefe cikin nutsuwa ta gaishe su kamar kullun taja kujera ta zauna, ruwan tea kawai ta iya hadawa tana sha kamar tana shan magani kamshin turaran daya  doki  hancinta ne  yasata dagowa sadiq ne cikin uniform dinsa yana riqe da briefcase dinsa, yasha kyau har ya gaji sai dai fuskarsa ba walwala angel ce ta gaishesa ya amsa  tare da yi mata peck, kallon shi fatuha take har ta kasa kauda idanuwanta haka shima sadiq ita yake kallo tuni idanuwan ta suka ciko da kwalla girgiza mata kai sadiq yayi alamar kar tayi kuka, yana murmushin  dayafi  kuka  ciwo lumshe ido tayi tare da qoqarin hadiye kukan da ke niyar kuboce mata, sallamar majeed ce ta doki dodon kunanta, ware ido tayi tana kallon kofar sanye yake da uniform dinsa shima sai sheqi yake yayi  kyau  har  ya  gaji, qarasowa yayi tare da gaishe da su Mom amsawa tayi cikin fara'a, tare da cewa, "ya su Umma?
     "su Umma lafiya lau Mom" sadiq dake tsaye take fara'asa ta dauke daurewa yayi ya tataro nutsuwarsa ya saki murmushin karfin hali ya  ce, "my man yau kai ne da sasafe nan? Sosa keya majeed yayi tare da kallon fatuha kauda kai tayi ta cigaba da juya tea din dake  gabanta dan ba sha take ba.

        Haka sadiq ya dinga danne zuciyarsa, fatuha kuma haka ta gama juya tea din ta tashi tare da daukar school bag dinta, ta ja hannu jidda suka fice tare da yima Mom sai sun dawo, tana fita majeed yabi bayan ta haka shima sadiq kasancewar office zasu.

   Zata shiga mota majeed ya ce, "baki ji ba..! daure fuska fatuha tayi dan wata tsanar majeed take ji juyowa tayi a fusace dan ta gayamasa mara dadi hango sadiq tayi bakin mota da alama su yake kallo, kauda kai sadiq yayi yana wani jin suya a zuciyarsa da rad'ad'i bale murfin mota yayi ya shige, murmushi fatuha ta saki wanda iyakar shi la66an ta ta ce, "uncle majeed ina kwana" cikin zaquwa ya ce, "lafiya lau my love," cikin sanyi murya ya ce "Fatuha!"
       "na'am.! tace a taqaice dan dakyar take masa magana saboda tsanarsa da ke bin zuciyarta ya  ce, "nasan na maki laifi my love naje nayi abu bada sanin ki ba amma please kiyi hakuri" wasu sabin hawaye fatuha ta hade ta ce "Ba komai.! tana qoqarin bale murfin mota ta  tsinkayo  muryar  majeed "idan dai kin hakura please ki bini nayi dropping na ki? daure fuska fatuha tayi dan bata jin zata iya bin majeed a yanzu, lagwabe kai majeed yayi ya ce, "please ki bani dama duk da nasan bani da mazauni a zuciyar ki, musanman  dana  maki  karantsaye, amma dan Allah kiyi hakuri ki so ni koda kad'ane, tunda nataso ban ta6a samun yarinyar da ta kwanta min a rai ba kamarki ba, fatuha please ki bani dama na gwada maki soyayyar da nake maki" haka majeed ya dinga magiya dakyar ya samu fatuha ta shiga motar shima sai da jidda suka shige ya ja motar.

        Sadiq dake zaune cikin mota yana kallo su duk yadda suke, dakyar ya iya saita nutsuwarsa tabbas yasan duk ranar da fatuha ta zama malakin majeed ba abin da zai hana shi zama gawa, dakyar ya iya bude baki ya ce ma driver "ja mu  tafi.! ba musu yabi umarnin ogansa suka bar haraban gidan.
         suna zuwa wajen aikin Sadiq ya 6ale murfin mota ya fito tare da daukar jakarsa, ahankali yake tafiya kamar kazar da kwai ya fashema aciki, duk inda ya wuce ma'aikata nata gaisheshi hannu kawai yake d'aga masu, domin jiyake bakinsa yayi masa nauyi, yana zuwa office dinsa yabude yashiga, yayi jifa da Briefcase dinsa ya zauna bisa kujera wani kuka ne ya ku6uce masa mai radadi da ciwo, jiyake duniyar nayi masa zafi, bai ta6a sanin yana kaunar fautuha ba sai yanzu da yake shirin rasata, na  har  abada Why majeed ! me yasa zakamin haka? me yasa kake neman rushemin farin ciki na? me yasa zakace kana son Fatuha alhalin nafika bukatarta a yanzu, na  fika  son ta why  majeed..!  da karfin tsiya ya daki teburin dake gabansa ya ce, "nooooo Fatuha tawace insha Allah, danni aka  halice ta" wani murmushin karfin hali sadiq yayi (da ni Salma nakasa gane ma'anar hakan)

        Majeed nayin parking a harabar makarantarsu Fatuha ta kama murfin motar zata bude, da sauri ya dana wani remote ya rufe koffofin motar, cike da tsiwa ta dubeshi suna hada ido dashi ta sunkuyar da  kai kasa, batasan meyasa majeed yake mata kwarjini  ba duk yanda taso yimasa rashin kunya suna hada ido zata nemi nutsuwarta ta rasa, murmushi majeed yayi ya ce, "Haba My love, ya za'ayi kifita kibar mijinki da tsananin tunanin ki? ya kamata ki fada min wata kalma da zai sani tunanin ki koda ina office ne please matata kada kice min a'a" takaicine ya lullu6e Fatuha, ban da iskanci gidan uban wa aka d'aura mana aure dashi da har zai kirani matarsa taja tsaki a ranta mtsss, a fili kuma ta ce "Please uncle kabarni natafi dan Allah" ta karasa maganar kamar zata masa kuka "Sorry my lovely zaki tafi amma dan Allah kiyi min murmushi ko zan samu nutsuwar zuciyata?" Fatuha ta ce a ranta "Dan iska shege mugu kawai Allah yasa zuciyar ka ya dawama da bakin ciki kamar yarda kake qoqarin sani, A fili kuma tayi murmushi da iyakarshi le6enta, majeed ya bud'e masu kofar da sauri ta fita tayi gaba, jidda na qoqarin binta majeed yaciro kudi masu yawa yaba jidda shi kansa baisan ko nawane ba tayi masa godiya tare da masa peck a kumatu ta tafi da gudu domin har Fatuha tayi mata nisa, shima majeed cike da farinciki ya bar harabar makarantar.


Written by
      Salma mas'ud nadabo

Edit by
     Raheenat

📘REAL HAUSA FULANI WRITER'S FORUM🐄
★We are the best★

http/mobile.Facebook.com/Real-Hausa-fulani-writers-forum RHFWF-173984973194167/?refid=52&red=opera_speed_dial_&yn=H-R

*Email* [email protected]

*Facebook* www.Facebook.com/REALHAUSAFULANIWRITERSFORUM.COM

             
                     79_80

     Ko da fatuha  ta shiga class ba wani walwala, haka su Nana suka dinga tanbayar ta mai ke  damunta ta fada masu meke damun ta, amma firtaqi gaya masu damuwar ta, Nana ce ta ce, "fatuha kenan baki daukemu a matsayin qawayan ki ba ko wayanda  zamu  kashe  tare  mu  birne  tare ba? Shiyasa zaki boye mana abin da ke damun ki" Zara ce ta budi baki ta ce, "Kyale ta Nana ai dai mun san matsayin mu yanzu, bai  zama  dole  ta  fada  mana damuwarta  ba" Zara na qoqarin jan Nana subar seat, fatuha ta riqe Zara ta  ce, "please kuyi hakuri, zan fada maku damuwa ta.! ta ida zancan hawaye na sulalo mata, duk abin ya faru haka fatuha ta kwashe ta fada masu ta  karashe  zancan  da  cewa, "ina  son  captain  so  mai  tsanani  wanda  ke  tafiya  tare  da  bugun  numfashina  amma  sai  gashi  lokaci daya" kuka fatu  ta  saki mai  cin  rai ta  fada  jikin  Nana tana  gunjin  kuka, Zara taji haushi ba kadan ba haka  suka dinga bama fatuha hakuri tana raira kuka dakyar suka shawo kanta.

         Bangaran majeed ban da dad'i ba abinda yake ji, zuciyar shi fes take daya lumshe ido kyakyawar fuskar fatuha yake hagowa sai ya qara sakin smile, matsala sa  daya  da  fatu  ta  kasa  sakewa  da  shi.

      Jingine yake saman kujera office ya rasa sukuninsa, idanuwan shi na lumshe saboda nauyin da suka masa har wata masasara ke rufe shi ga wani  irin  zafi da qirjinsa ke masa, tamkar  an  daura  masa dutse  mai  nauyi a hankali ya ware sexy eye's ball's dinsa da suka rine sukayi jaa wayarsa dak'e ruri cikin aljinhunsa ya curo sabuwar number ce baro-baro a screen din, da kamar ba zai dauka ba sai ya daure ya dauka tare da karawa a kunne, daga  dayan  bangaran cikin zazakar muryata cikin yauki Basma ta masa sallama, amsawa yayi a taqaice tare da tanbayar, "wake magana? gyara kwanciyar tayi daga inda take tare da kankame wayar dan wani irin sanyi ke ratsata, dan gyaran murya tayi cike da shagwaba ta ce, "Yaya sadiq ni ce fa Basma..! ko number ta ashe baka da ita? ta ida zancan cikin shagwaba Sadiq dake kishingide saman kujera, ranshine ya qara suya dan shi duduniya ba macan dake birge shi ko bashi sha'awa kamar fatuha, ko wannan magana ma da take yi jiyake kamar tana watsa masa ruwan zafi,  tsuke fuska sadiq yayi kamar tana ganinsa ya ce, "Yanzu ina wani aiki ne letter mayi magana idan na dawo gida" bai jira cewarta ba ya katse wayar tare da yin wurgi da ita ta daki bango ta dawo watse ko ta kanta bai bi ba ya sa kai ya fice daga office din, domin idan ya cigaba da zama tabbas kwakwalwar shi da zuciyarsa suna iya bugawa.
            bin wayar tayi da kallo tare da dan bata fuska, ta aje wayar ta kwanta.

    Ko da aka tashi su fatuha majeed ne ya zo daukar su, ganin shine yasa ta had'a gira sama data kasa dan ba abinda ta tsana kamar ganinsa, ba yadda ta so haka ta bale murfin motar ta shiga tare da gaishe shi, kallon ta yake mai cike da so da kauna, sannan ya ce "My love daga gani yau kin sha wuya da yawa? ina fata dai kina kulla min da kanki?" dan guntun tsaki fatuha ta ja ciki-ciki sannan ta ce a cikin zuciyar ta "Har wani kira kake na kulla ma da kaina mtww dan iska kawai" muryar  majeed ce ta doki dodan kunnan ta a karo na biyu ya ce, "My love! ko duk gajiyar ce tasa ko magana ba'a san yimin?" dan smile fatuha tayi wanda iyakar shi la66an ta ta ce "A'a" murmushi majeed yayi tare da cigaba da driven, haka ya dinga janta da surutu tana amsa masa sama-sama sannan ya wuce da su shoprite yayi masu siyaya ice cream da cake, jidda ko sai dadi take ji dan har yanzu bata san inda aka dosaba.

 
        Suna kunna hancin motar su, suka ci karo da sadiq wanda shima dawowarsa kenan wani irin dogon numfashi sadiq yaja a duk lokacin da yaga majeed da fatuha, numfashinsa sai ya nemi ya dauke ko qirjinsa ya dinga masa zafi, dakyar ya iya d'aga kafarsa dan baya so ko fuskar su ya gani sun fito a tare, amma sai dai kash majeed ya riga ya kira sunan sa. lumshe ido yayi ya tsaya chak! sai da ya kwashe yan mintina sannan ya waigo tare da sakin smile din karfin hali, ta gabansa fatuha ta raba ta wuce jidda nata zuba masa surutu sannan itama ta shige, miqa mashi hannu majeed yayi suka gaisa ya  ce, "big man duk yau ban ganka a office ba"
       "oh ina cikin office ina wani aiki ne gobe ma nake so na wuce Lagos"
          "Lagos kuma? me zaka je yi lagos? cewar majeed
          "zan je nayi 2week ne cikin ruwa na dawo"
        "Eyya to Allah ya taimaka"
  "Amin..! yana qoqarin shigewa majeed ya ce, "Baby..!
      "yes..! ya ce a taqaice
"dama ina so muyi wata magana"
       "ok mu shiga ciki" ok majeed yace tare da bin bayan sadiq suka shiga part din sadiq briefcase dinsa sadiq ya aje tare da rage kayan jikinsa ya shiga toilet, ya dade a toilet din baiyi wankan ba yana kukan bakin ciki sannan ya tashi yayi wanka, sanye da bathrobe ya fito da qaramin towel a hannusa yana goge jikinsa, majeed na zaune saman sofa shima tashi yayi ya shige toilet ya sheqa wanka ya fito ko da ya fito lokacin sadiq ya shirya cikin black 3 quarter  da white shirt mai gajeran hannu, yana zaune saman sofa idanuwansa lumshe, shiryawa majeed yayi a tsanake sannan ya bude wardrobe din sadiq ya ciro riga da wando riga blue sai dark blue jeans sannan ya bude fridge ya curo fresh milk ya tsiyaya a cups ya miqama sadiq ya amsa.
           zama yayi kusa da sadiq ya ce, "Please ina so kamin taimako guda daya please?
      "ok inajin ka indai baifi karfina..! murmushi majeed ya saki ya ce "Bai fi karfin ka ba"  gyara zama sadiq yayi yana sauraran majeed riqe hannusa majeed yayi cikin lagwabe kai ya  ce, "please baby kamin hanya fatuha ta so ni..! tsura masa ido sadiq yayi da idanuwansa da suka ciciko da kwala hadiye su yayi yana saurara majeed ya  cigaba  da  cewa, "baby ina  son  fatu wallahi ina sonta i  love  her  more than how  you  think, ban ta6a jin son wata  d'iya  mace ba kamarta ba, baby karkayi tunanin irin son da nake ma sauran yan'mata nake mata a'a son ta nake da gaske ba  da  wasa ba, idan har  na rasata zan iya rasa rai na ina  jin  sonta mai  yawa  sadiq  na  kamu  da  sonta  mara  musaltuwa  ina  manta  kai a  gabanta  ita  ce  bugun  zuciyata sadiq...!  majeed ya fada, da  sauri-sauri  numfashin  sadiq ke  gudu  zaune  yake tamkar  an  dasa  akwai yana bin majeed da ido kamar sakarai gabaki daya  jikin shi ya mutu sai zuciyarsa dake tsinkewa kamar zata fito waje dan  tashin  hankali, dan matse hannusa da majeed yayi ya sasa dawowa daga duniyar tunanin, smile ya saki yana  kallon majeed  ya  ce, "my man karka damu kaji d'an jama aji take amma nasan zata so ka kaji, kasan yadda mata suke amma nasan zata so ka  har ku dai-daita  babu  macan  da zata  same  ka  ta fasa kai  kasan  da haka, kana  da  abinda  kowace  'ya  mace  zata  so ka" murmushi majeed ya saki tare da kaima sadiq hug ya ce, da  gaske  Bros..!
      "Eh mana.!
"Ka  tabbata  fatu  zata  so  ni?
    "Sosai  ma..! hawaye dake  maqale  idon  sadiq  ne suka cigaba da anbaliya dan ko yasan ya rasa fatuha, dan baya fatan abinda zai samu majeed dan uwan shi abokinsa mai  son  farin  cikinsa bashi da aboki dan uwa saman da majeed, mai  yasa  ma  tun  farko  yake  kishin  d'an  uwan  nasa, lokaci yayi da ya kamata ya ba zuciyarsa hakuri jin majeed zai zame jikinsa yasa sadiq saurin share hawayansa tare da sai ta kansa murmushi suka sakar ma junan su, fira suka fara sama-sama kiran sallah magrib ne ya tashe su.

  1week letter

      Shirye-shiryan aketayi a family house, kasancewa yau za'a sa rana biki duk wanda ka kalla cikin farin ciki yake musanman Basma da majeed.
       zaune suke cikin d'akin yan'mata sunata zuba hira muryar Basma kadai ke tashi fatuha na gefe tana matsar kwalla dan har yanzu gani take kamar wasa, kamar kuma  a mafarki tashi tayi ta fita daga d'akin ganin kayan da ake ta wucewa da sune yasa jikin fatuha qara sanyi.
       fitowa tayi daga parlour hango qanan Baffa tayi su baba Barau  kasancewa  komai Abban sadiq  ya  ce zaiyi  tunda  fatu  hannusa  take, wasu hawaye ne masu zafi suka sulalo mata yanzu ta tabbatar za'a samata rana da wanda bata so a matsayin miji kuka ne ya ci karfin ta, fita tayi daga gidan gabaki daya dan ko sanin inda zata ba tayi ba jefa  kafar  kawai  take  kan  titi, can baba jummai ta fado mata a rai keke napep ta tara ta shige  ta ce, a kaita gadan qaya" kasanwcewar gidan baba jummai kan titi yake bata wani sha wahala kwatantawa mai napep  gidan ba kukan da take yasa mai keke napap din bar mata kudin saboda ya tausaya mata.
          ko sallama bata cika ba ta shige gidan, baba jummai dake qoqari fita, fatuha ce ta fada jikinta tare da sakin kuka kamar ranta zai fita, rud'ewa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login