Showing 111001 words to 114000 words out of 134888 words

Chapter 38 - Tantiriya Agidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

931

zama lafiya Dan cacar bakin ma'auta sai dai naji a makwafta gashi Nan ko wanne gida ana wayyo wayyo da lamarin aure,amma ni kullum na shugo sai dai a tarbeni ayi min abinda nake so,Nima kullum Ina yiwa Kubra dai dai, Dan canja hali bana yi wlh yau bazan koma gidan ba sai tsakar dare.
Wata unguwar ya tafi kawai ya samu majalisa Dattijai ba Wanda ya sanshi shima bai San kowa ba ya zauna,Suna ta hirarsu,wani dattijo yace ai yau Balki ta fara fada ban Bada kudin manja ba na fice,ai duk masifar mace kawai ka fice ka bata waje,kullum kawo kawo mata ba tausayi ba Imani,Abba yace me yasa ka aureta kasan baza ka iya ba,magana ta Gaskiya ka hanata kudin manja sabo da tsiya ka fito Kuma ka bar gidan wannan zalunci ne ,to jira kake ta Nemo kudi ta siya tayi Maka girki kaje ka ci,Kai wannan bai kamata Balki tayi maka biyayya ba wlh,Kaci ka koshi sannan ka koma Balki ta sauke ma sha'awa indai haka ne ka fadawa Balki tayi asara a rayuwarta.

In banda asara ma me ta gani ta aureka,Baku da aiki sai ku zauna Kuna gulmar matayenku da munafuncin mutanen unguwa,Dattijai suna jinsa mamaki ya kamasu Bako yazo yana shigar musu zance.
Wani a cikin dattijan Yace Malam Rabiu kaji matar Liman Yusha'u ciki ne da ita? Jiya baka majalisa ta wuce muka Gani da idonmu,ai ta Nan ta wuce tana ta ja har ya fara tsufa ma,Abba yace Allah ya sakawa Liman da matarsa kallon matarsa da kuka yi da Kuma gulmarsa da kuke yi Allah ya saka Masa,ana zaune sai ga liman yayi Sallama a gabansa Kuma sai fara'a ana girmama shi Malam Liman ka karaso ya iyalin? Abba baki bude ya kalle su,yace Kaine Yusha'u Liman? Liman yace nine lafiya? Yace yanzu suka yi gulmarka data matarka sunce ta wuce jiya ta nan sun ganta cikinta ya fara tsufa suka kwashe da dariya.
Liman yace ai majalisar Nan munafukai ne kamar ba dattijai ba,Abba tashi yayi yace wlh gwara na koma gidana bazan iya zama a nan ba,ya tashi yayi tafiyarsa Kuma ba gida ya tafi ba har sai da dare yayi a masallaci yake samu yayi sallarsa.

Unguwarsu ya dawo ya shiga gidan abokinsa sun Dade har kusan Sha biyu na dare nai dawo ba,Yar Inna taga shuru shuru har Sha biyu,ga wayarsa bata shiga ta kira Mohsin ta sanar Masa.

Hankalinsu duk ya tashi Mohsin wurin 12:30am sai ga Abba ya shugo gidan ga yara suna gidan Naila ba kowa sai Yar Inna sai karamar da take goyo tana ganin Hashimu ya dawo sai murna harda rungume shi tace wlh ka sani kuka Ina ka tafi haka? wayar Mohsin ta kira tace ya dawo lafiya Lau sai lokacin hankalinsa ya kwanta shi da Beauty,Abba yace kinyi kuka da gaske Yar Inna? Kubra ta Harare shi tace ban sani ba,Abba yaji dadi shi dama haka yake so suyi fada kawai,tace wanne kuka ne banyi ba sabo da Allah tun safe har dare 12:30 ba dole na zaci ko kidnapping Dinka aka yi ba,gaskiya karka sake min irin wannan wlh wannan ai ba yi bane,Abba shi dadin masifar Yar Inna yake ji,yace ko banza dai munyi fada yau amma kullum sai????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? tarairayata a dinga tarairayata Ina ta yin soyayya, Dan Allah ki kwana a dakinki yau ke kadai Nima na kwana a nawa muyi fada kawai,nidai Allah ya gani hakurin nan ya isheni da zaman lafiya yayi yawa Ina za a Kai shi haka rayuwa ba jarabawa ba dadi ni bazan iya ba.

Dariya ce ta kama Yar Inna tace ohh dama duk Dan muyi fada ka tafi? yace ae gaskiya zan fada a gari na dinga yawo har dare yayi na tafi gidan abokina na Kai har kusan Sha biyu na dare sauran lokacin na karasa a masallaci,tsakani da Allah fa Ina zan iya kullum sannu da zuwa ana kaffa kaffa dani dadin yayi min yawa,babu matsalar da zata zo tasa na dinga tuna mutuwa, shi wannan Mohsin da Ina fargaba bashi da kudi yazo ya samu kudi,matarsa ba ta gari ba yazo ya samu ta gari Beauty,Naila tana prison Ina damuwa Allah ya yaye min ta fito ta auri me kudi tana zamanta lafiya Kuma babu rikici ba komai kullum shuru,ke nan kin gyara halayen ki abin naki ya wuce misali naga alama so kike ki tsallake siradi da gudu a lahira,gaskiya mu dinga fada Nima ko Hallare ta huta,Kubra tace Allah ya shiryeka,Allah yasa ka nutsu tunda aka haifeka a haka ai baza ka shiryu ba.

Kuma mutumin da rufa Maka asiri nayi na aureka aka tura min Kai dole,wacce wahala ce ban Sha ba ni na dauki nauyin yarana da Kai har suka girma Ashe Kai kudin Makka ka Tarawa Danka Kuma duk Shekara sai kudin aikin hajji ya tashi dole ka Dade kana tari,Abba yace yawwa Maza ki zobe ladanki,tace baza ka godewa Allah ba ya fitar mu daga wahala yanzu yayi mana ni'ima,tunda muka taso muke a wahala da talauci da jarabawar rayuwa, yanzu Allah ya yaye mana" ka nuna Kai baka so" kafi so mu kare a tashin hankali,Kai kanka in aka kalleka ai anga jarabawa da kanta,wannan ni aka jarabta da miji irinka wlh,ai irinku suna da yawa ana jarabtar mata dasu taka ma me sauki ce akan na wasu,kawai Dan kana so muyi fada sai ka bar gida ka barmu a tashin hankali wannan daga yau duk Inda zaka je bazan damu da Kai ba bazan sake nemanka ba ko a waya ta juya ta shige daki,Abba shi dadinsa yake ji yace nayi nasara haka nake so Allah yasa muyi sati a haka,ya wuce kitchen ya ebo abincinsa da kansa ya wuce bedroom dinsa.

Yar Inna tayi zuciya ta fita shirgin Hashimu,ko kulashi bata yi,Hashimu ya fito daga dakinsa misali 12 na rana,Yana mika ya Kalli Yar Inna a tsakar gida tana aiki,yace jiya na dade rabon da nayi bacci me dadi haka na samu freedom,babu kwakuma ba runguma,Ni wannan abu yayi min fada da masoyi dadi sai ka huta watarana in ana yinsa,Yar Inna ta Masa banza,ya fita yace bari naje na kasa kayan Miya me rabo ya siya mugunta na yiwa mata nasan yanzu wasu girki ya kure musu sai dai a tafi wajen wani,in aka daka ta Hashimu kowa ya kwana da yunwa,ya fice Yana fita ya kasa kayan Miya sai ga mutane ana ta zuwa siya yace dole sai wajena wai" dan masifa naki fitowa ma da wuri sai an jirani,Allah ya kyauta.

Annoor washe gari da asuba Kwanan Amarya Daya Yana farkawa ya farka da masifar sha'awa, Yana so ya dan murje Iman yaji dadi Iman tana baccinta bata sani ba ta sa hannu a kirjin Annoor tana shashafe shi tayi kasa wurin boxers dinsa ta jawo wandon kafin kace ya fara Nishi da gurnani kamar Wanda yake Kwalbewa yayi Yar Kara ya kankame Iman kamar zai rushe mata kasusuwa ba shiri ta farka,shi kuwa tuni ya kawo abinsa,gefe ya ja ya kwanta yayi flat a Saman bed kansa na kallon sama ya bubbuda hannaye yace na gama yawo tawa ta kare wlh bazan iya ba ni Kawu zan fadawa, na rantse da Allah ba ruwana da wani asirin aure zai tonu yayi ta tonuwa ke ni akan wannan ko sama zan iya Hawa da Speaker na sanar da duniya bazan iya ba,lalura idan ana boyeta ba a samun magani,wani daga labari zaka samu silar maganinka bazan iya ba, wlh,Iman mikewa tayi ta zauna tace wai releasing ka sake yi? Yace ae mana,tace Kai karfa ko ba sperm bane Yaya ko Aljana ce da Kai ne taga kyakyawan Bil'adama ta aurar min Kai Ashe akwai tsiya wallahi in kasan wata ce take bude Maka haja kana ci ka fada min gaskiya, mene haka ni baka taba min komai ba kawai ka dinga kawowa haka siddan,dariya yayi yace kika ce ba ruwanki ke,tace a'a yanzu da ruwana a wannan batu,sai dai baka mood fa zaka iya tabani ni naji dadi amma in kana sha'awa sai ka kawo ko hannu na ka rike" Ina lafiya ai bamu ga ta zama ba,bazan iya ba ni ba budurwa bace gaskiya,amma ana farko ka min raga raga yanzu Kuma ga auren sunna baza ayi ba wlh shedan mugu ne,acan dake na Haram ne harda min dinki yanzu Wanda za a samu Lada an hana Ina dalili wannan hali na shedan,a fara gwada na asibiti,Annoor yace nifa wannan abin bana jinsa a na asibiti ne Iman doctor ne ni,a gwada dai tukun idan baiyi ba sai a nemi maganin gargajiya sannan mu dage da karatun Qur'ani da Nafeela muyi ta addua.

Tashi tayi tace haba mace bata tsoron namiji daren farko Ina mutum a Nan,Ina namiji ai yau na tashi Ina Jin tsoronka shine gaskiya,Annoor Yana dariya yace au bakya tsorona yanzu? Iman tace akan me Ina dalilin Jin tsoronka,wlh sai na rama gorin da ka dinga yi min ni ba budurwa bace ai gashi Nan kaima ka hadu da jarabawa,Annoor yace Sanyi na dauka a jikinki ranar first night kece kika shafa min lalura,dariya tayi tace ko kaikayi ban taba ji ba a down Dina,yace ai ana yi yayi shuru bazai nuna ba, Infection kika shafa min,nidai in ba a jikinki na dauka ba a Ina zan dauka, kyau har kyau ciki duk Infection kin cuceni da yanzu Ina shagali kin cinye kaza a banza,wlh girki zaki fara yanzu zan fito nace kar a kawo abinci ba uwar da kika min mene na kawo miki abinci,Iman tana dariya tace Kaine ya kamata kayi aikin yanzu ko bude Maka nayi sadaka baza ka iya ba,hannu na ma ya isheka ka kawo gaskiya na hadu da yawa ni hannuna ma Oga ya taba kawowa yake gaskiya Allah ya min baiwa,Annoor yace zan gwada akan wata zan rike hannun wata naji zan kawo,Iman tace zaka fara ko Dan Allah karka yi nidai,Annoor a ransa yace ya zama wajibi na nemi wata na rike hannunta naji,tunawa yayi da Maryam mayyarsa a wajen aiki yace yawwa ga ballagaza tana kawo kanta yau zanje Office zan rike naji,sannan naje na rike Debora itama,wata Likita ce Debora tana mugun son Annoor,Yana tunaninsa Iman ta shiga tayi wanka da brush ta fito ya shiga,kafin ya fito ta shirya tayi Sallah sannan ta tsara kwalliyarta cikin dakakkiyar shadda pink,dinki na zamani ta hadu tayi kyau ba karamin kyau ta zuba ba,ta fito Palo tana taku dai dai tana kallon gidanta sai ga Rahma da Nabeela sun kawo breakfast lafiyayye,dinginshin karya ta fara tana yatsina tace kamar nasan zaku zo na fito.

Rahma har da dariya tace gogan ko an sake farke Inda aka dinke ne,Nabeela tace ai nasan za a rina an saci zanin mahaukaciya,Iman tace bana son wulakanci wato da uwata kuke an saci zanin Uwata sai ta fara kuka,Nabeela tace yau na shiga uku wallahi ba Dake nake ba Karin magana ce Kuma na manta ma Mamanki bata da lafiya,kiyi hakuri Iman,Rahma tace rabu da Yar iska dake ake mu muka miki laifi daga anyi Karin magana bisa kuskure,in zaki shagwabarki kiyiwa Ango shi ya miki laifi ba mu ba,sanda ake tabaki ba dadi kike ji ba,Iman tace banji dadi ba ni,Rahma tace ni nasan dadin fa yarinya Dan Romance din nan ana min shi ba abinda zaki gaya min sai dai sex ke an miki tuntuni.
Nabeela tace ni kuwa Ina nan Ina fama da nawa a jike,Iman ta bude Abincin ta gani,tace Kai bayin Allah ya akaji da taya Umma Habiba kishi?

Rahma tace Kawu wai harda shi aka daura aure Kai namiji sai a barshi wlh tausayi Umma take bani,Iman tace har ga Allah banji dadi ba,Nabeela tace nima haka wlh ban so ba,wannan abokin nasa ne ya zuga shi Abba,Iman tace shi Kuma fa mata Daya ce da shi jal ya kasa karawa tun auren fari, ke in kika ga matar nan yanda take ji da shi kamar yarinya Bata Jin kunya,dole ya kasa Kara aure sai abinda tace,Nabeela tace sai kace ta Masa asiri duk Inda ya Zauna Yar Inna,Yar Inna" suna dariya,Rahma tace wai Nan Sunan love ne Yana birgeni wlh Abba nan tab madaurin auren Iman, ya yanke sadaki da yawa yace Kuma sai idan baza a aura a haka ba a bar Iman ta Shekare a gida bazai daura ba,Suna ta dariya Iman tace yasa nayi tsada fa,Rahma tace muma a bashi ya daura namu ko zamu yi tsada.

Annoor ne ya fito ya Sha uban wanka ya zuba Gezna dark Arsh yana sheki da kamshi kamar yau za a daura auren,Rahma tace Ango an Sha Mai,yace me ya kawo ku gidan Amarya da safe haka,zuwa muka yi in ta kasa tashi muyi gashi,murmushi yayi yace gulmace ta kawo ku dama,Iman tace kyale su Sweet,Rahma tace Inye lallai ya tashi daga Yaya? Iman tace ae Ina Ango Nabeel? Yana can a wajen Kawu yace shi bai yarda ba wlh a kawo Masa Amaryarsa,Kuma tana Abuja gidan yayarta ance sai nan da sati wai Abuja zai tafi shi,Kawu yace Kai Nabeel dama haka kake? Yace ae shi jiya bai iya bacci ba,Kuma ance sai nan da sati biyu za a kai Masa Amarya sai kace zai zauce wlh ya hana kowa sukuni da zancen Amarya Hidaya,ga yarinya a waya Yar wannan yarinyar sai hure Masa kunne take da kalamai,Annoor yayi dariya yace ku daina ganin laifinsa,Iman abincin ta zubawa Annoor ta hada Masa tea da dai su chips da kwai,suka karya su Rahma suka ce su sun karya amma da suka rage sai suka cinye ragowar suka ce kar ayi asara suka tattara kwanikan suka musu sallama suka tafi,Iman tace ku kawo na rana fa,suka ce to.
Kwanciya tayi a Jikin Annoor tana tumurmusa shi,masifar son jiki ne da Ita,Yana so ya fita yaje Office yayi gwaji amma ta hanashi wai tsoro take ji,yace da me gadi fa da komai Yar aiki ma za a kawo miki soon,tace nidai baza ka fita ba.
Bacci tayi a haka bata sani ba ya lallaba ya kaita bedroom Saman bed ya kwantar da ita ya fice nufinsa kafin ta tashi ya dawo ma.

Asibitinsa ya wuce direct,Maryam tana ganinsa ta taho da sauri tace Sir Allah ya sanya Alkhairi amma yau kazo Office kamar ba Ango ba,fuska ya bata Yana amsa gaisuwar mutane yace Ina ruwanki,ki daina shiga safga ta yaja Kwafa,amma duk da haka ta bishi Office tana goge masa kujera,hannunta ya ruko sosai,ta tsaya tana kallonsa da mamaki,ta zaci ya fara sonta harda sakin Murmushi ta jefar da duster din Dake hannunta ta rungume shi sosai,da Iman ce tayi haka da tuni ya kawo,ko baya Jin Feeling ta yi Masa haka to sai ya kawo amma shuru kake ji,har tsayawa yayi ta sake rungume shi amma shuru bai kawo ba,Maryam tunaninta tayi nasara Yana janye jikinsa ya karkashe ta da Mari har biyu, ya hankada ta waje yace mayya wacce Bata San darajar kanta ba, jaka mahaukaciya fasika ya kulle kofarsa,Maryam tace wato dai baya so na idonta ya ciko da kwalla tana shafa kumatunta ta koma wajen Marasa lafiya tace dole sai ya Soni wlh.

Annoor zama yayi Yana ta tunanin kansa sai ya fito ya shiga Office din Debora tana ganinsa tace yau Oga da kansa a Office dina wow tana murna tazo ta fada jikinsa ta rungume shi harda shafa Masa kirji itama ya kwashe minti yafi biyar a haka ba abinda yayi baiji komai ba bare ma ya kawo,amma Iman dama yasan Yana da feeling a jikinta ko ya ta rabe shi tun Yana da lafiya ma sai yaji shock amma wannan shuru ba komai,jikinsa ya fisge ya dinga balbalin masifa wa Debora ya fice Yana zage zage ya koma gida,ya samu kuwa bata tashi ba,Umma Habiba ya kira ya gaida ta,ya gaida Jauro ma sannan ya kira Mamansa suka gaisa yace gaskiya shi baiji dadin ba Dan me zata auri Kawu ai an ciwa Umma Habiba fuska,Maman Annoor tace to bani da zabi ne wlh ya dade Yana bina,halacci da yayi min Bai cancanci nace bana sonsa ba,ita Kuma matar data rike miki yaro ta rainar miki shi har ya girma fa? ta zauna Dake kamar kawarta Kun zama kawaye ma sannan kizo ki aurar mata miji,Mama tace ni kaina ban so haka ba amma Allah yayi bani da zabi zanje na bata hakuri,ba ki kyauta ba dai gaskiya koma mene bai dace ba babu tsari Kuma.
Mama tace to kuyi hakuri na auri mijin uwarku nima bada so na ba,Annoor ya kashe wayarsa kawai.

A gefen Iman ya kwanta wani sha'awarta ta taso Masa dama tun da can Yana Jin hakan game da Iman,amma ko ya taba ta bai kawowa yanzu kuwa yasan Yana rungumeta shike nan,Iman ce ta bude idonta a hankali ta ganshi kwance a gabanta Yana ta faman kallonta,jikinsa ta koma ta makalkale shi,Ido ya lumshe kafin kace me ya fara shidewa sai kawowa ,Iman tana jinsa ta gane tayi kamar bata gane ba,tashi yayi ya zuba tagumi,tace ko Ruqiyya za a Maka ne wannan wanne masifa ce ne haka,yace Dan Allah ku kaini ayi min Ruqiyyar nan nima naga abin nan bana lafiya bane.
Nasan yanda zamuyi kana ji yau zan bude ma kana Jin feeling karka tabani Nima bazan taba ka ba,zan bude ma wajen shagali kawai ka shiga a haka mu gani,yace tab ai Ina taba wajen da Sweetener ta shike nan na kawo Kuma,Iman ta zaro ido tace kar na Kuma ji wlh kace Sweetener Ina ta isa a kirata da Sweetener banji dadinta ba ka dinga asarar kiranta da Sweetener sai ka bari ka warke tukun,Annoor Yana dariya yace harda gori Iman tace ai Ina Maka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login