Showing 120001 words to 123000 words out of 134888 words

Chapter 41 - Tantiriya Agidan Yari Book 2 Complete Hausa Novel

03 Feb 2025

912

suke zaune ya zame ya kwanta Yana cewa a kira min Maryam ko zanji dadi.

Maman Annoor ce tace wannan abin fa ba na wasa bane Aunty Habiba,Iman ta fashe da kuka ta mike ta shiga bedroom tare da fadawa Saman bed tana kuka,Maman Annoor tace lallai ya kamata a Nemo Maryam don wannan wallahi itace ta yi Masa asiri,Annoor ta kalla tace kana da number dinta? Yana rawar Sanyi yace ehh...ya mika musu wayar,Iman ce ta fito da katon bargo ta lulluba Masa ta zauna a gefen kansa" kansa ya Maida Saman cinyarta ya kwanta Yana Nishi a hankali,Jikinsa ya dauki zafi sosai,Kawu yace Iman ku tafi daki ya kwanta,ta mike tare da rike shi ya tashi da kyar da bargon a jikinsa suka shige bedroom dinta na da" Saman bed ya kwanta itama ta kwanta suka shige bargon tare,Rungumeta yayi sosai a jikinsa Yana mata rada a kunne I'm sorry" Nima ban San dalili ba,Iman tana lallaba mijinta tace ko na cire kayan kafin Jin dumin?da sauri yace ae,tashi tayi ta sawa kofar key sannan ta cire kayan jikinta ta shige bargon tare da cire Masa nasa kayan ta rungume shi Kam" sosai shima ya makalkale ta.

Maman Annoor ce ta kira Maryam ta zaci Annoor ne tunda da wayarsa ta kira,da sauri ta daga tare da furta my love,Maman Annoor tace ba shi bane Mamansa ce,da sauri Maryam tace Ina yini Mama? wai a dole ita ta gari ce,Maman Annoor ta furta Annoor yace Yana sonki shi aurenki zaiyi,gashi bamu sanki ba ko zaki iya zuwa mu ganki sai muyi miki wasu Yan tambayoyi, Maryam taji zancen aure tace to yaushe kuke son ganina? Yau ma in da hali ai akwai lokaci" okay to bari nazo,tace yawwa gidan Kawunsu ai kin San gidan tunda a karkashinsa kike aiki,Maryam da sauri tace to,Bayan sun gama wayar,Abba ya Kalli Jauro ya tabe baki yace baka iya soyayya ba Jauro Amarya guda tayi abin Azo a Gani maimakon kace ban mu kashe sai ka tsaya sekeke da Kai kamar bishiyar dabino,Habiba dariya ta dinga yi tace ku dai wlh baza ku girma ba,Hashimu Allah ya shirye ka,Abba yace Allah ya shiryeni wlh tunda ba Yar Wanda na lalata,Kuma gani da iyalina muna zaune lafiya har fada nake nema muyi ma ai kuwa ba karamin shiryayye bane ni,Maman Annoor tayi dariya tana dauke fuskarta sabo da Jauro ya kafe ta da Ido kamar wani maye.

Jauro ya dawo tsakiyar matansa ya zauna Habiba a gefe Amarya a gefe,ya Kalli Habiba yace black beauty, ya Kalli Amarya Sadaka yalla wace ne zata kwace ni,Habiba tace na bar mata wlh har sati daya kwana,Abba yace ai baki birge ba Nan har kyauta kika yi Habiba,ke da zaki ce Jauro na barka kayi wata uku a dakin Amarya sai kice sati daya kacal sabo da dama ku gidanku Habiba gadon rowa kuka yi wlh,madarar shanu bakwa iya kyautarta,sanda kike tallan fura wacce irin tsada ce baki ba,ana ganinki da kwaryar nono har nunaki ake da baki ga uwar tsada can.

Jauro yace karka takurawa matata Kai Yar Innar taka mene bata yi ba,Abba ya gyara zamansa yace Yar Inna ta hau dokin zuciya fushi take dani kwana da kwanaki taki sakkowa,abin ya dameni Kuma Ina Jin Mohsin zan fadawa yazo ya tare min fadan nan,muna zaman mu lafiya na takalowa kaina yanzu gashi Yar Inna ta juya min baya,Jauro ya dinga dariya yace Allah ya Kara,idan ance Maka Dolo kaji haushi,Abba yace ka taba ji nace naji haushi in an ce min Dolo? Ni bana Jin haushi Wanda ya fada shine a wahale bakinsa ke aiki.

Maman Annoor kunyar Habiba take ji duk ta kasa magana,Abba yace to Habiba uwargida Kinga hukuncin Allah,haka Allah ya tsara kiyi hakuri da abinda aka miki,ba wai mun Kara aure bane Dan aci mutuncinki ba,Jauro yace ban gane mun Kara aure ba? Na Kara aure dai Kai Ina ruwanka a ciki ,wai Hashimu ko da Kai zamu shiga dakin Amarya ne? Abba mikewa yayi yace a'a Allah baka hakuri tunda baka gane hausar ba,ni na shiga dakin matar wani Allah ya tsare min,Jauro yace to zauna mana a karasa Abba yace a'a,Habiba tace Dan Allah ka zauna a kashe wutar Annoor tukun,da kyar Abba ya zauna,Abba baya fushi ba a fada da shi,yace ai ni Yar Inna yau Alala take mana,idan banci akan lokaci ba akwai kura,dama kadan take jira fushi take yi.

Ba a dade ba sai ga Maryam tayi Sallama cikin katon Hijab dinta har kasa,tayi shigar Kamala,ta shugo ta zube a kasa tana ladabi ta durkusa ta gaida su da ladabi,suka amsa,Habiba tace kece Maryam din? Maryam tana kasa da Kai ta dago fuskarta tace nice,Maman Annoor ce ta Mike da sauri tana nuna Maryam da yatsa tare da kiran sunanta tace Maryam kece? Maryam tace kin sanni ne? tace kece dai baki gane ni ba,Ina mahaifinki? tace Yana US Bai dawo ba,Maman Annoor tace to ai ke shirme kike yi Annoor din Yayanki ne Ubanku daya da shi,babu aure a tsakaninku idan baki yarda ba kira mahaifinki yanzu kice waye Annoor.

Maryam gigicewa tayi ta rude ta dakko wayarta a jaka tare da kiran Mahaifinta a waya,bayan sun gaisa tace Daddy wai dama kana da Da Annoor? Daddy yace Ina Annoor din? Dan Allah hadani da shi ya girma sosai Ina da pictures dinsa mahaifiyarsa ta tura min ta Whatsapp,Allah sarki ai ubanku Daya Maryam Yayanki ne shine Dana na farko,na zalunci mahaifiyarsa na zalunce shi,Allah yasa mahaifiyarsa ta yafe min,na nemi yafiyarta,yanzu shi kawai ya rage min, inshaallah next week zan zo Nigeria ki kaini Inda yake.

Maryam tuni ta fara kuka tana hawaye ta durkushe a wajen tace Dan Allah ku kira Annoor zan tonawa kaina asiri,wlh ban san Dan uwana bane na jini,ban sani ba na cutar da shi,shi yasa aka ce in Allah bai baka Abu ba karka sake kace Kai ta dole sai ka same shi.
Habiba tashi tayi taje ta dinga knocking tuni sunyi bacci har Iman din,da kyar Iman ta farka tace Ina zuwa,kayanta ta Maida jikinta tare da bude kofarta tace Umma,Habiba tace taso Annoor ku fito" tana fadar haka ta juya,Iman tashinsa tayi da kyar ya tashi ya zauna kayan ma sai da ta tayashi ya saka sabo sangarta,tace muje Umma suna kira,yace Allah yasa sun Nemo Maryam din na ganta,hannun sa Iman ta kama ta gartsa Masa cizo,ya saki Kara suka fito Yana yarfe hannu.

Yana fitowa yaga Maryam a zaune tana sharbar kuka,Abba yace Iman ku zauna,zama suka yi,baka Jin komai sai sautun kukan Maryam,tace dan Allah Annoor ku yafe min,na cutar da ku nasa kunyi Zina Bada saninku ba,tana kuka tana basu labarin yanda akayi duk ta kaisu hotel har Annoor yayi amfani da Iman basa cikin hayyacinsu,sannan ta Fadi duk irin asirin data dinga musu,tace wannan na karshe shine na sa Masa a kasan kujera ya zauna,Iman ta jawo Jakarta ta zaro Dan kwallon abin kamar carbi ta nunawa Maryam tace shine wannan? Maryam tace shi...shi....shine,Annoor yaji komai amma kala bazai iya cewa ba,tsafi Yana jikinsa,Iman tashi tayi ta rufe Maryam da duka da cizo da yakushi,Maryam tana kuka,Abba yace kyaleta Iman ko me zaki yi baza ki iya ramawa ba,cuta ce ta cutar da ku,amma wannan yarinya ke dai lokacin Jima'in cikinki tare babanki yayi da shedan lokaci guda suka aiwatar da shedan,Jauro yace tambadaddiya ba duk yanda aka yi a nono ta tsotso.
Cabdi cewar Habiba sai ki je ki karya tsafin naki ko,Maryam ta mike ta fice da gudu tana kuka,motarta ta shiga a lokacin ta wuce kauye wajen Malamin da yayiwa Annoor tsafin hanashi mu'amular aure,tana zuwa taci sa'a Yana Nan,tace Malam ka taimakeni Wanda na baka aiki a kansa kayi min Dan uwana nane na jini ubanmu daya,Malam yace na baki shawara ai tun farko kika dage.

Maryam tace da me yasa baka fada min Dan uwana bane tunda Kuna duba ai sai ka sani,Malam yace Allah ne yasan gaibu,Maryam tana harararsa tace ku dai makaryata,Yace ke ki shiga hankalinki badan Ina Tausayin yaron ba wlh bazan karya ba,sai na kassara rayuwarki,shuru Maryam tayi tace nawa zan biya yace dubu Hamsim,haka ta bashi akan ya karya aikin,wani garin magani ya bata yace kije ki zuba garin Nan na magani a hannunki ki kira sunansa sau uku sannan ki bushe garin yabi iska shike nan,Maryam tace zan iya yi a Nan garin? Yace ko a Ina ma,ta karba ta fito ta shiga motarta sai da tayi Nisa da garin sannan ta aiwatar da abinda Malamin ya sata sannan ta shiga mota ta dauki hanya,a ranar ta dawo kusan dare ma ta nemi jirgi ta tafi kudu,can ma haka ta kashe kudi mutumin yace idan ya karya sai ta kwanta doguwar jinya,tace ba komai aka karya asirin.

Kawu ne ya kira sunan Iman ku tafi gida to kawai Inshaallah zai karye,Annoor ya mike kawai ya fita Yana takunsa na zaratan matasa,Iman ta bishi kamar kurame ba Wanda ke kula wani,haka driver ya Maida su gida,suna shiga Palo ya rike hannun Iman ya fisgota idanuwansa cikin nata" haka kawai kamar zai dake ta" ya furta da izinin wa kika fita kika je Office dina? Iman tace da Izinin kaina da kaina,naje din fitar tawa ai tayi amfani tunda gashi nan da naje ai tattabeka akeyi dama kullum,haba shi yasa Dan hutun amarci ma kaki yi,Ina da operation yau,jibi Ina da wani marar lafiya critical condition,critical condition ashe Maryam ce take baka critical condition a jikinka, maimakon nayi aure nayi kiba kullum sai ramewa nake yi Ina Dan wuya sabo da halinka,auren zumunci ko tsiya a dake ka a hanaka kuka,Annoor Yana ta kallonta sai masifa take shi da ta yiwa laifi ta bishi Office ba izinin sa.

Sai da ta gama tace Kuma wlh baka isa ka min kishiya ba,babu kishiya sai dai ka sake ni,haka kawai da me zanji,ko tarihina ya isa ka tausaya min,ai dai ko da asiri to shima Yana iske hali,dama wa yasan me kake yi in ka fita,wasu likitoci wani tsoron Allah ne da ku dama,in ka fita dama haka kake yi da ma'aikatanka idan bakwa yi ta ya zaka bari ta dinga tabaka direct.
Annoor sai da ya bari ta gama sannan yace Iman ni kike fadawa haka? ae din Kai matsa can ko Dan ka rainani nima fa shegiyar kaina ce,dariya yayi kawai yace to Mama Iman zo ki dake ni mana kawai.

Iman sama ta haura da sauri,zama yayi a rantsatsen palon nasu Wanda ya gaji da haduwa ba abinda yake sai kamshi,kwanciya yayi Yana dafe kansa da yake Masa ciwo,Iman bata sake fitowa ba sai da ta Dade Sannan ta fito sanye da guntuwar gown wacce da kadan ta wuce mazaunanta,Yana kwance ya lumshe Ido yaji taku ya Dan bude idonsa kadan,Iman ce ta wuce tana tafiyarta tana latsa waya,idonsa ya lumshe da sauri yace Annoor ba kayan aiki namijin hotiho ga Abu amma ba dama,yanzu ko tabawa nayi shike nan kadarina ya karye Kuma,Bai san an karya asirin ba yaki yarda ya taba Iman,Inda yake tazo zata zauna tace matsa ko na zauna a kanka,tashi yayi ta zauna ya kwanta tare da dora kansa a cinyarta,gashinsa ta shafa tace ya jikin? yace Ina ruwanki ba tafiyarki kika yi ba,dariya tayi tace to kayi hakuri haushi naji, kawai kin rainani sabo da ba abinda nake iya tsinana miki,wanne irin ba abinda kake tsinana min?

Ba fa haka bane kawai kishi nake yi Kuma kasan ya zama dole tunda Ina sonka,haka dai kika ce amma ni nasan kawai Dan ba abinda nake baki ne,ba haka bane haba Beb ta shafo gemunsa tana murmushi,kanta ta duko a hankali tare da Dora lips dinta Saman nasa ta shiga tsotsa tace yau fyade zanwa mutum ko Banana tayi aiki ko kar tayi dole ma tayi,dariya yayi ba shiri yace Allah sarki Sweetener tana rashin lafiya, amma fa kina kiss din nan ta mike so take ta kawo nasan baza ta Kara 1mnt ba sai ta kawo,Iman ta mike tace bari na kawo Maka fruits" ta mike ta shige kitchen ta fito dauke da bowl ta kawo Masa gabansa da fork spoon a ciki suka fara aikin Shan fruits din,tace me zan dafa ne yau? Yace komai da nake ci ai kin sani in ma baza ki dafa bama a fadawa Rahma ta kawo mana daga gida,ko nayi mana order, Iman tace zan iya mana,Kitchen ta shiga ta dora girkin,miyar jajjage tayi da kifi sannan ta dafa musu farar shinkafa ta hada couslow tayi lafiyayyen zobo ta tafasa da bawon Abarba da kayan kamshi,bayan ya huce tayi blending Banana ta juye a ciki ta zuba sugar yayi mugun dadi ga amfani a Jikin Dan Adam ta shirya a dining sannan ta ganshi ya fito da alama wanka yayi cikin t-shirt fara me gajeren hannu da 3qutr yayi kyau matuka sai kamshi yake,gabansa ta karaso tana murmushi ta furta kayi kyau,Hugging dinta yayi gaba daya a jikinsa tare da furta I love you" da shagwaba tace Maryam din fa? shuru ya mata,sharewa tayi tace abinci Yana jiranka ta ja Masa kujera ya zauna tare da serving dinsa,ta zubawa kanta ta zauna itama,yau baza ki bani a bakin ba? Maryam ta baka,taci gaba da cin abincinta kamar ba itace tayi maganar ba,Murmushi yayi ya fara cin abinsa Yana kallonta,dakogowa tayi suka hada Ido, baki ta murguda Masa ta janye idonta daga cikin nasa.

Bayan su Annoor sun tafi Abba shi dai tafiya yayi,Yana zuwa gida ya samu Yar Inna ta cakare cikin Leshi fari yaji doguwar riga ta tsege dauri sai kace matar wani Gomna ta zauna a Palo tana gogewa Hashimu kayan sawa,sau tari kayansa marasa nauyi ita take wankewa ta goge masa,Kubra ta daure fuska da gaske take fushi da Hashimu,Abba ya kalleta yace kinyi a banza fushi da Hashimu aikin banza kenan,kamar baki sanni ba haba Yar Inna,na tuba nace bazan sake ba,yau wurin sati guda ko daki bama hadawa har sai yara sun gane,na gaji zan fadawa Mohsin.
Da sauri Kubra tace ka fadawa Mohsin Kuma? ae mana shi ya miki fada ai Kinga kinji kunya danki ya miki fada,Yar karamar yarsa ya dauka wacce take zama yanzu Yana mata wasa yace yarinya Yaya kike jiye min kamshin Yar Inna Yana nan ko kuwa ta daina sawa,ni nasan ta daina saka turaren yanzu tunda bama kwana tare dama Dan na yaba ake sawa to bani Ina zata saka,Yar Inna saura kadan tayi dariya ta daure tace Allah ya kiyaye na fasa shafa turare ni dama badan kai nake sawa ba.

Abba yaci gaba da yiwa yarsa rawa tana dariya yarinya yace ke kadai yanzu kike kula nononki ko Yar nan? Dariya Kubra tayi tace ajiye min 'Yata karka lalata min ita,wayar Yar Inna ce tayi Kara" Hashimu ya duba yaga Naila,daga kiran yayi,Naila tace Abba" yace Na'am"gaisawa suka yi tace Ina Umma fa? Yace gata tana fushi,ai fushi take dani mun Kai sati a haka taki hakura,Kubra tana ji bata kulasu ba,Naila tace Abba zata hakura ne,yace Abu yaki ci yaki cinyewa,ka Murda kambunka kawai Abba cewar Naila'' wanne kambu nake da shi Naila ni ba champion ba,ita ce take da Kambun ai,Bata wayar to,Abba ya mikawa Kubra ta karba,Naila tace Umma Ina yini'' ta amsa da lfy ya gida ya mijin naki? Lafiya Alhmdllh,lafiya dai ko? Naila tace dama shawara zaki bani Gani nayi kamar Spark ya juya min baya,Dariya Umma tayi,tace me yayi Kuma,Naila tace to tsakani da Allah Umma yau 3days bai kwalbe ba,dariya Naila ta bawa Kubra sosai,tace me yake yi to,tace daga Office sai bacci,in ya dawo da wuri da wuri ma laptop yake sawa a gaba da takardu ya dinga fama sai ya Kai dare sosai har sai nayi bacci,Kuma a rana sai yaje state biyu uku kullum aiki,gaskiya na gaji ni zamuyi fada da shi,Kubra tace ke yanzu Baki gane aiki ne ya Masa yawa ba,aiki ne ya taso Masa baki san Maza ba kenan,kika San me ya taso Masa ya sashi hakan

Koma ba aiki bane ai ba kullum ake kwana a gado ba,dole watarana a samu canji,ki daina damun kanki,abinda kike dai karki fasa Kuma ki koyi juriya a ko wanne hali kika tsinci kanki kiyi hakuri,bare ma aiki ne yasa shi,duk bake kike cinye kudin nasa ba,Naila tace har watana nawa da zan cinye kudinsa kin Kai dai wata biyar ko shida tunda cikin Beauty gashi ya fito ma,Naila tace uhm to shike nan Umma zan jure,Ina Hidaya? ta tafi lalle gobe za a kaita gidan miji,Kiwa mijinki godiya dubu dari biyar ya bamu,duk da Nabeel din ya zuba komai na kayan daki sai da ya Bada kudi,abinda muke so aka Kara siya mata,Baki ga gidan Hidaya ba Mashaallah yayi gida na gaske,Kinga kayan ciki du na kasar waje,kitchen ne ba a zuba abubuwa da yawa ba amma duk mun siya an zuba mata komai,zan tura miki ta Whatsapp ki Gani,Naila tace Alhmdllh ai ta turo min Lefenta gaskiya sunyi,Umma tace ai mu sai godiya ga Allah ta ko Ina rufa mana asiri Allah yake Naila tace ai kuwa Alhmdllh.

Gobe karfe nawa za a kaita? 5pm suka ce zasu zo daukan Amarya gidanta kusa da gidan Iman Inda Annoor yake,Naila tace shike nan tayi Kawa sai su zauna lafiya kar a dinga kishin faccalanci kishin banza mijin kowa daban amma mata suna kishi, Inshaallah baza suyi ba,Allah yasa cewar Naila tana cewa Umma Dan Allah ki daina fushi da Abba kiyi hakuri,ke Ina ruwanki bana son rashin kunya fa ai dama kunfi sonshi,Naila tace mudai Dan Allah a yafe masa Yar Innar Abba....tana fadar haka ta kashe wayar tasan Umma yanzu sai ta zageta.

Wayar ta kalla tace Naila wlh bata da kunya,Abba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login