Showing 27001 words to 30000 words out of 199108 words

Chapter 10 - Kanwar maza 3&4 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

789

da rumaisa a takure a falon mama, sai rarraba ido take yi, suka gaisa da mama ya sanar mata da Usman ya gaya masa abun da ya faru"

Mama ta ce "To, yakamata ka sake tunani a kan auren nan naku, ku gidan sarauta ba kwa son shirme, rumaisa kuma Allahn da yayi ta ba ta ji ko kaɗan, faɗa da maƙwabta faɗa wai har da ɗan daba, yaron da har kisan kai yake yi"

Adam ya kalli in da rumaisa take, ta haɗe rai saboda yadda mama ke kwance mata zani a kasuwa, ya ce "Me ya haɗaki da ƴan daba, har aka kama Aliyu?"

Shiru ta yi tana wulƙita ido, mama ta ce "Zaki yi bayani ko sai na mareki?"

Ƙasa-ƙasa da murya ta faɗi abun da ya faru, ta wani fannin tana da gaskiya, a kan me zai aiketa sayen sigari.

Adam ya ce "Ba damuwa mama, bari mu je a fito da shi, ba wani state CID, wani station ɗin ne?"

Usman ya ce "Dama yanzu zamu koma da mai sunan baba sai mu tafi gaba ɗaya " wani mugun kallo da mai sunan baba ya yi wa Usman ya sanya yayi shiru, Sarai Adam ya ganshi, dan haka ya ce "Bari mu je da wuri, kuma dole ita ma a tafi da ita".

Mama ta ce "Idan ma sun ƙi yarda, ku basu ita ku dawo mini da Aliyu" sanin ba ta da gaskiya ya sanya ta sunkuyar da kai ta yi shiru.

Mama ta so bin su, amma kasancewar yanzu magana ake ta siriki, mama ba zata iya shiga motar Adam ba.

Bayan tafiyarsu mai sunan baba ya ce "Amma ba kya ganin yawan shigarsu cikin al'amuranmu da yi mana alfarama, ba zai saka nan gaba su cigaba da kawo buƙatunsu ba, kuma ba yadda muka iya sai mun bi ba?"
Mama ta ce "Babana ka san na fi kowa taka tsantsan da gudun duniya, bana jin hakan, shi ya sanya na amince"

Ya ɗan rausayar da kai ya ce "Shikenan, bari na bi su a napep"

Suna tafe Adam yana kallon rumaisa ta mudubi, sai wani gyatsine baki take yi, tana harare-harare kamar mai shirin iskokai.

Cikin station ɗin suka shiga, aka yi musu iso wurin DPO, cikin sa'a suka tarar da malam shamsu a station ɗin yana ta cigaba da zigar kai su Aliyu CID.

Adam ya ce "Case ɗin ƙanina na zo mu yi magana a kai, na san shi ba mai laifi ba ne"

Malam shamsu ya ce "Ta ina, yana mana iƙirarin kisan kai a cikin unguwa"

Usman ya ce "Wai kai malam shamsu meye yake damunka, meye ribarka idan an rufe Aliyu ne?"

Mai sunan baba ne yayi sallama ya shiga, suka amsa masa ya nemi wuri ya zauna.

Adam bai ko kalleshi ba ya cigaba da magana ya ce "Da ku ka caje Aliyu kun same shi da makami?" DPO ya ce "A'a"

"Good, ɗayan fa, abokin rigimar ta sa"

"Eh, mun kama shi da wuƙaƙe da tabar wiwi"

Suna cikin maganar aka shigo da su Aliyu.

DPO ya kalli rumaisa ya ce"Ni mamakina ma da wai duk a kan wannan Yarinyar ce ta haɗa faɗan, ke meye ya haɗaku?"

Ta cunkusa baki ta ce "Cewa yayi na sayo masa sigari, kuma ni ba ƴar iska ba ce ba da zan taɓa sigari ina ƴa ma ce mai mutunci "

Adam a ransa ya ce "Ko wa ya tambayi jinsinta kuma oho'

Malam shamsu ya kada baki ya ce "Ƴar iska kum ta nawa, zance da ya cika unguwa"

Zabura rumaisa ta yi ta ce "Yaya usy ka ji ko? Yanzu idan na yi magana ace ba na jin magana, da kunnenka ka ji yana ce mini ƴar iska, ni fa bar ƴar iska ba ce ba, bana wasan banza da maza, meyasa ake ce mini ƴar iska?" Ta yi maganar hawaye ya wanke mata fuska.

Malam shamsu ya ce "Ke da aka ce an yi garkuwa da ke, ki ka dawo da ɗa, ai ba abun mamaki bane ba, tun da kowa ya san a unguwar nan ba ji ki ke yi b.... Mai sunan baba ya daki tebur da ƙarfi ya ce "Ya isheka malam"

DPO ya ce "A gaban nawa, da rashin mutunci da rashin sanin darajar doka".

Malam shamsu ya ce "Tuba muke Yallaɓai".

Usman yayi ƙasa da muryarsa ya ce "Uban waye ya saka ki yi kuka a gabnsa, salon ya rainaki, idan ya kuma gaya miki ki ce kin yi ɗin"

Adam ya numfasa ya ciro ID card ɗin sa ya bawa DPO ya ce "Ina son a bi tsarin doka, a bani Aliyu sannan a tura mai laifi gaba"

Ware ido DPO yayi ya ce "Ranka ya daɗe dama kai ne? Ai da ko waya ka yi ya wadatar ba wani abu in sha Allah, case ya mutu daga nan"

"And, shi wannan da yayi iƙirarin kashe Aliyu da wannan yarinyar, a kai mini shi state CID, sannan a kamo mini yaransa ma, zan bincika wanda ya saka aka sake shi ana tuhumarsa da kisan kai"

Dpo ya ce "In sha Allah ranka ya daɗe" baki buɗe malam shamsu ya din ga bin Adam da kallo, da mamakin ina suka samo Adam.

Adam ya dubi malam shamsu ya ce "Kai kuma, daga yanzu idan zaka yi gulmar, ka din ga nunawa mutanen unguwar ni, ka ce nine wanda yayi mata cikin shegen ta haifa, ta dawo ya karɓi abun sa, idan da wanda zai ɗau mataki a kan hakan ƙofa a buɗe take. A saya mini shi a ceil, sai na waiwaye shi"

Cikin tashin hankali ya ce "Dan Muhammad Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallama ka yi haƙuri, ka yafe mini, wallahi kuskure ne"

Adam ya ce "Kai Yanzu wannan da ko magana ma ba ta iya yi ba, ba ta san ma'anar abunda ake faɗa ba, ta yi maka kama da mai cikin shege? Ƙaddara ƴar ka ce zaka je kana faɗar wannan maganar?"

Ya sunkuyar da kai yana girgiza wa.

"Ko da wasa, ka kuma gaya mata wannan mummunar maganar, sunana Adam Sharif Galadima, zaka ga abun da zai biyo baya"

Ware ido malam shamsu ya yi, a radio yake jin sunan Adam, sai kuma ya san shi ne mamallakin katafaren gidan gonar da yake cikin unguwar, cikin tsuma ya ce "In sha Allah hakan ba zata sake faruwa ba, tsautsayi ne"

Duk da wannan abun da Adam ya yi wa rumaisa bai burgeta ba, aka bawa Aliyu kayan sa, suka fito daga station ɗin, Adam ya rungumo Aliyu suka fito, Usman ya riƙo rumaisa, mai sunan baba ya fito shikaɗai ya kama gabansa.

Cikin motar Adam suka shiga, ya kunna suka fita, suna tafe ya ce "Aliyu, dan Allah daga yau komai za ta tsoka no, ku ƙyaleta ita kaɗai ko zaneta ne ayi, ka ga yanzu haka kurum ta janyo maka kwanan ceil"

Aliyu ya ce "Ba ayi haka ba babban yaya, tuba muke yi"

"Ai ni ko ba a tare mini faɗa ba, ina da ƙarfi"

"Rufen baki ko na cillaki ta tagar nan" Usman yayi maganar yana nuna mata taga.

Ta yi shiru ba ta sake cewa komai ba, Adam da Aliyu kuma suna taɓa hira, rumaisa har mamaki take yadda yau Adam ya buɗe baki yana magana haka da Aliyu.

A ƙofar gidan su rumaisa Adam yayi parking, Aliyu ya yi ta masa godiya, Adam ya ce "Ka daina wannan godiyar mana, kar ka saka na ji kunya, ai kai nawa ne Aliyu a gaida mama" suka yi musabaha ya fita, Usman ya buɗe motar ya fita, rumaisa har ta fita Adam ya ce "Ke tsaya, Ammi ta bani saƙo na baki"

Rumaisa ta ɗan yi jimm sannan ta ce "Sunana rumaisa, ba ke ba" yai kamar bai ji ta ba, ya ɗauko ledar wurin ammi ya miƙa mata, ta ƙare masa kallo ta ce "Ni ammi ba ta ce za a kawo mini wani saƙo ba, ni ba zan karɓa ba, duk wani abu da ya fito daga wurinka bana so, balle nan gaba ka ce mini kwaɗayayyiya, gidanku da nake zuwa saboda sabir ma, a dole na haƙura, saboda gorin da ka yi mini, ina ji ina gani ina ƙaunar ɗana, amma ka saka na yi zuciya na daina ganinsa, ni ba zan karɓi abunka ba" ta tsallaka ta shige gida ta bar shi da kayan a hannu.

Ayshercool.ml
Chat me on what's app, to subscribe
yours.
08081012143
PAID BOOK NE, ₦500 VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK, SAI SHAIDAR BIYA TA 08081012143.




Sororo ya bi rumaisa da kallo, dan ba ƙaramin mamaki ta bashi ba, ba ya son mama ta fito ta ce za ta yi masa godiya, dan haka ya shige motarsa ya ja ya bar ƙofar gidan.

Mama kuwa murna ta din ga yi da ta ga Aliyu, nan da nan ta ce Yasir ya ɗora masa ruwan wanka, ta kalli Usman ta ce "Ina yake, na yi masa godiya?"

Rumaisa ta ce "Ai ya tafi" mama ta harareta ta yi mata shiru, dan haryanzu ba ta huce ba, da abun da rumaisan ta aikata.

Usman ya ce "Ina saƙon da na ji ya ce ki tsaya ki karɓa?"

Ta kwaɓe fuska ta ce "Ni ban karɓa ba, cewa na yi ya koma da abun sa ba na so"

Cikin takaici ya ce "Dalla matsa ƴar baƙin ciki, ke da ba roƙarsa ki ka yi ba, kawai sai ki ƙi karɓowa"

"Taɓ, haka kurum yayi mini gori wataran"

"Uban waye ya ce miki wanda aka haifa a cikin arziki yana gori? Ai idan kin ga mai kuɗi yayi gori, to dama matsiyaci ne, daga baya yayi arzikin kuma wataƙila a tsiyarsa zai mutu" ba wani fahimtar abun da yake faɗa ta yi ba, ta shiga harkokin ta. Sai dai ta kasa sakin jikinta, duba da yadda mama ta haɗe rai, taƙi kulata.

Aliyu ya yi ta basu labarin irin abubuwan da malam shamsu ya din ga faɗa a kansu da rumaisa, na ɓatanci da yadda ya ziga a ka kulleshi, duk ba a same shi da makami ko wani laifi ba.

Usman ya ce "Gajiyayyen wahalalle, irinsu ne masu ƙarewa a tsiya, kuma idan bai yi wasa ba, sai na ɗaga shi na buga da ƙasa. Ai ni abun da gayen nan yayi masa ya burgeni wallahi, da ya ce shi ne uban ɗan kuma ya karɓi abun sa".

Rumaisa ta yi farat ta ce "Yauwwa, na ji ya ce wai shi ne yayi mini cikin, to dama shi cikin yin sa ake yi, yi wa mutum ciki ake yi"

Aliyu ya ce "Bismillahi, ashe haryanzu hankalin da saura".

Ganin kowa ya yi mata shiru ya sanya ta ce "Yaya usy baka bani amsa ba".

"To me zan ce miki, wai ke haryanzu kanki a tukunya yake, baki san meye rayuwa ba, baki san me yakamata ki din ga tambaya ba, Allah ya sa mai sunan baba ya ji ki, shi sai ya baki amsa"

"To me na yi daga tambaya?"

"Idan kun yi auren sai ya baki amsar"

Aliyu ya kalli usman ya ce "Kai fa wasu lokutan sai a hankali, kai ba ka ji kunya ba kake gaya mata hakan?".

"To yaya zan yi mata bayani, ita kai kamar computer abun da ka zuba mata kawai shi ta sani, idan suka yi auren ai aikace za ta gani"

Aliyu ya ce "Kaii usman lafiyarka kuwa? Kar ka gurɓata mata tunani malam"

Mama da ke ɗakin ta ce "Ke, ki taso ki zo ki kunno mini maganin sauro" mama ta kirata, dan katse waccan hirar da suke yi, dan idan aka zurafafa rumaisan ba ganewa zata yi ba, kuma wani zancen za ta ɓallo.

***
Yanayin fuskar Ammi kawai ya kalla, ya san akwai matsala.

A nutse ya ce "Ammi na dawo"

Ta kalleshi, ta kalli ledar hannunsa ta ce "Wannan ledar fa?"

Ya kalli ledar ya ce "Saƙon da ki ka bani ne, ta ƙi karɓa"

"Saboda me?" Ammi ta tambayeshi cike da tuhuma.

"Ta ce baku yi waya ba, baki ce mata zaki aika mata da saƙo ba, dan haka ba zata karɓi abun hannuna ba na zo daga na yi mata gori wataran"

Ɗan jimm ta yi, ta wani fannin rumaisa tana da gaskiya, kuma ammi ta sake jinjina lallai rumaisa tana da tarbiyya.

"Dole fa ka sauke wannan shan ƙamshin, da sarautar ka dawo dai-dai level ɗin ta, domin ku fuskanci juna kai da ita, dan ba zan lamunci ku yi aure, ku din ga zaman doya da manja ba, kamar wasu maƙiya"

Adam ya ce "To in sha Allah" dan ya rasa mai zai cewa ammin.

Ta sake nisawa ta ce "Sannan na ji abun da ka aikata, Jamila ta zo har falon nan ta nuna ni da yatsa, ka saka mota zaka kashe mata ɗa, adam ƙiyayyar da ka ke yi wa ɗan uwanka har ta kai haka dama? Ka yi yinƙurin kashe shi?"

Adam ya yi shiru, ba tare da ƙoƙarin kare kansa ba.

"Kai a rayuwarka duk yadda nake tausaya maka, da yin iya ƙoƙarina a kan ka, baka gani ko? Kullum burinka ka tsokano abun da za ayi ta yi mana surutu, saboda wannan zafin zuciyar ta ka ko? Gobe in Allah ya kaimu ka je ka yi masa sannu, sannan ka bata haƙuri, magana kuma har ta kai kunnen wambai yana nemanka"

Dam ƙirjin Adam ya buga, ya je ya duba Mahmud, ya bawa Mummy haƙuri, sannan wambai yana nemansa.

Cikin dakiya ya ce "To, in sha Allah duk za a yi" ya juya ya fice daga ɗakin.

Ko abinci kasa ci yayi, abubuwa sun yi masa zafi sosai kwanan nan, ya tara ayyuka sosai a office, gashi duk iya binciken da yake ya gano, ko garkuwa da aisha shiri ne ya kasa samun komai, amma wasu daga cikin bayanan rumaisa, na nuni kamar da akwai wani abu a ƙasa,gata gardamammiya ya san idan jajjagenta zai yi ba zata yi magana ba, sai ta ga dama. Ga wannan batun auren nasa da ammi ta sako shi a gaba a ƴan kwanakin nan, babu damar ya motsa, sai ta yi zancen rumaisa, shi gaba ɗaya baya farin ciki da wannan auren.
Ga surutan da ake ta yi a kansa a media, kullum ƙazafi kala-kala, ayyukansa da ya ɗauko kan sace Aisha hankalinsa ya rabu biyu duk yayi sanyi, bai samu sun kammalu ba, tun sa shi ne jagoran aikin.

Ji yayi kansa ya fara ciwo, ga wani irin jiri da ya fara ɗibarsa daga zaune, a hankali ya ja jikinsa ya kwanta, gaba ɗaya bai san ta ina zai fara ba da matsalolin nasa.

***
Yau mama ko sallar asuba ba ta tashi ruma ba, sai da Usman ya tsula mata wayar caji a ƙafa ta tashi, ta yo alwala ta yi salla, ta gaida mama, amma maman taƙi amsawa.

"Mama wai dan Allah ba zaki kulani ba?" Ta yi maganar cikin damuwa.

"In kulaki in ce miki me? Ai ki je ki yi rayuwarki ruma nima zan yi tawa, ƴaƴana suna buƙatar rayuwata, ɓacin ranki ba zai ƙarasani ba, na yi magana a samo langa-langa ayi miki ɗakinki, dan ba zan cigaba da zama ɗaki ɗaya da ke, kina zucguna mini ba"

Ba ƙaramin mamaki mama ta bawa rumaisa ba, dan a ganinta mama ta daina sonta, ta tashi jiki a sanyaye, ta je yi shirin makaranta, ta tafi ba tare da ta sake kula mama ba, sai dai abun yayi ta damunta, ga wani irin son ganin sabir da take yi, ga kuma alwashin da ta ci a kan sa.

Ita kanta wasu fitintinun da take yi, tana son ta daina amma Allah ya gani, ba za a taɓa ta ta ƙyale ba.

Adam kuwa, Yau kamar wanda aka gayawa wani mummunan saƙo haka yake jin sa, komai ba ya yi masa daɗi, tasbihi kawai yake yi ko ya samu sassauci, ammi kuma ta sake nanata masa cewar ya je ya aiwatar da abun da ta ce na bawa Mummy haƙuri da duba Mahmud domin komai ya wuce.

Ba a son ransa ba sai domin cika umarnin ammi, ya nufi sashin Mummy.

Sai dai da ya tambayi Fauziyya, ta ce masa suna ɗakin Mahmud.

Kai tsaye bai jira wani iso ba, ya shiga sashin da Mahmud yake, yana zaune a kan gado, an ɗaure ƙafarsa da bandeji, da alama ƙashin ƙafar ya taɓu, amma ba irin so serious ɗin nan ba.
Mummy na gefen Mahmud tana takura shi ya ci abinci.

Mummy ta wani haɗe rai, Mahmud ya yi wa Adam kallo ɗaya, ya mayar kan abincinsa, aka rasa wanda zai amsa masa sallamar da yayi.

Hakan ba ƙatamkn ƙulara da shi ya yi ba , ya ji kamar yayi ficewarsa, amma ya san makircin Mummy.

Ya dubi Mummy ya ce "Na ji baki ji daɗin abun da ya faru ba, am sorry for it, shi kuma Allah ya bashi lafiya" ya juya zai fita Mummy ta ce "Dan Allah Adam wace irin ƙiyayyace kake nuna mana haka? Har ka taka ɗan uwanka da mota, meyake damunka ne?"

"Ba mayar da magana, ko bibiyar tarihi na zo mu yi ba, na baki haƙuri kar a sake saka mahaifiyata a duk wani abu da zan yi, ni na yi laifi ba ita ba"

"Amma Adam ni kake gayawa haka? Da na isa da kai, ko giwa ta nuna maka ina da muhimmanci a wurinka ai da ban tunkareta ba, kai zan yi wa sanin yi maka maganar ba shi da amfani, ba zaka saurara ba ya sanya na sameta".

"Kuma shine har da gayawa wambai? Idan haka ne maiyasa maganar ba ta tsaya iya nan ba?"

"Magana ake yi ta rai fa adam, yinƙurin taka shi da mota ka yi".

Mahmud ya ce "Mummy ki ƙyale shi dan Allah, kin san abnormal yake, kuma ko da ya takani da mota, za a iya ɓugewa da cewa ba shi da lafiyar ƙwaƙwalwa, sai dai zan sake ɗaukar nauyi, gidan jaridar fallasa su wallafa cewa ka yi yinƙirin takani da mota ka kashe ni" Mahmud yayi maganar cikin zunzurutun izgilanci.

A zafafe Adam ya juyo, ya ɓarar da kayan abincin, ya shaƙe Mahmud zuciyarsa na tafasa.

Mahmud ya kalli cikin idon Adam ya ce "Ka daina jin haushi idan an ce baka da lafiyar ƙwaƙwalwa, duk mutumin da bai iya sarrafa fushinsa ba, ƙwaƙwalwarsa babu lafiya ".

"Kai adam, ka cika shi kar ka kashe shi mana, jama'a ba kowa a kusa ne?" Mummy ta fara kwarmato.

Sanin cewa mutuncinsa zai sake zubewa, muddin aka sake zuwa aka gansu a yanayi mara daɗi shi da Mahmud, kuma ran ammi zai sake ɓaci, ya sanya shi sakin Mahmud, ya fice da sauri.

***
Maƙwabta suka

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login