Showing 3001 words to 6000 words out of 199108 words

Chapter 2 - Kanwar maza 3&4 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

783

musu gida, anya kan ki ɗaya kuwa?" Ganin duk sun tarar mata ya sanya ta ƙara sautin kukanta.

"Zaki rufe mini baki, ko sai na jibgeki tukuna" mama ta yi maganar a matuƙar fusace.

***
Ko da su iman suka dawo daga makaranta yau, gaba ɗaya sun lura da yadda ammi ba ta walwala, kamar akwai wani abu na damunta, nusaiba ma ta lura da hakan, sai dai iman ta kasa jurewa sai da ta magantu "Ammi, wata matsalar ce ta kuma tasowa ne?"

Ammi ta ce "Me ki ka gani?"

Gani na yi kamar wani abu na damunki, kamar jikinki duk a sanyaye yake.

"To, damuwa dai ba a rasata Iman, tausayin yarinyar nan nake ji"

Nusaiba ta ce "Wace yarinyar?"

"Rumaisa, yarinyar da ta dawo da sabir?"

Iman ta ce 'Ni dai ban taɓa ganinta ba, amma wani abun ne ya sameta?"

"A'a, sai dai ina tsoron kar wani abun ya sametan a dalilinmu, son da take yi wa yaron nan har tsoro yake bani, yau tun daga gidansu har nan ta zo a ƙafa wai dan ta ga yaron nan, ina tsoron kar mu ɗau hakkinta"

Nusaiba ta ce "Too ikon Allah, tana da ƙarfin hali gaskiya".

Ammi ta nisa ta ce "Ashe Mahmud kuma ya dawo"

Gaban iman ya faɗi, Nusaiba ta ce "Yaushe? Ganinsa ki ka yi?"

"Ban ganshi ba, amma sun haɗu da rumaisa"

Nusaiba ta ce "Mai ya ce mata?"

"A'a ban sani ba, sun haɗu dai ta zata takawa ne, shikenan dai ina son in ɗan fita an jima, zan je gidan turaki"

Iman ta ce "Ammi me zaki je ki ce masa? Ko akwai wata matsalar? Kin san mama tana ganinki za ta fara tunanin wani abu"

"A'a ina buƙatar ganinsa ne kawai, kuma ai ni ba wurinta zan je ba".

"To shikenan, a dawo lafiya".

Kafafen sada zumunta suka cigaba da ɗaukar hazo, a kan lamarin mutuwar aisha, adam yayi iyakar ƙoƙarin sa, wurin kawar da kansa a kan abun da yake faruwa.
Yana zaune a cikin motarsa, ya nutsu yana duba social media da yadda ake ta surutai a kan lamarin, kwatsam! Ya ci karo da posting ɗin Senator Usman wakili yayi posting a shafinsa yana yi wa adam ta'aziyyar mutuwar matar sa.

*A madadina da iyalaina, ina miƙa saƙon ta'aziyyata ga ɗaya daga cikin jami'an tsaronmu, Adam Sharif Galadima bisa ga rashin matarsa, ina fatan Allah ya yi mata rahama ya sanya ta huta, sai dai abun mamaki ne ace matar jami'in tsaro kamar wannan, da ya tsayawa ƙasa ace matarsa ta mutu a hannun'yan bindiga, wannan babban abun kunya ne ga ƙasa baki ɗaya*

Nan da nan mutane suka shiga tofa albarkacin bakinsu, in da suka dinga jinjinawa senator wakili na yi wa adam ta'aziyya duk da yadda ya sako shi a gaba, da ƙoƙarin binciko laifukansa.

Wata irin nannauyar ajiyar zuciya adam ya sauke, ya sake shafa fuskar wayarsa yayi sama, ya sake cin karo da gidan jaridar da suka fara wallafa cewar ya kashe matarsa, sun sake wallafa labari kamar haka.

*Lauje cikin naɗi, Abun da Kamar wuya gurguwa da auren nesa, ace babban jami'in tsaro guda, ayi garkuwa da matarsa ba tare da sanin hukuma ba, a ƙaddara an ɓoyewa duniya, domin gudun abun kunya ace jami'in tsaro ya gaza bayar da kariya a gidansa balle ƙasa, me zai sa ace an ɓoyewa hukuma, idan har rayuwar matar jami'in tsaro ba ta da amfani an gaza ceto ta su kuma sauran al'ummar ƙasa su ce me?.

Ayshercool.*
MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*

*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*

*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*

👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*

*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*

*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*

*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*

*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*

*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*

*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*

*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*

*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*

*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*

*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*

*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*

*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*

*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*

*15. Supplement for Acne, dark spots remover*

*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*

*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*






A hankali ya rufe datarsa, ya yi shiruu yana tunanin mai ya yi wa mutane haka, da har wasu suka sanya rayuwarsa a gaba suka mayar da ita hanyar su ta neman abinci.

A hankali ya ajiye wayar ya kunna motarsa ya tafi.


Baba uwani ce durƙushe a gaban Mummy, jikinta sai rawa yake yi, Mummy ta dubi baba uwani ta ce "Uwani me ki ke nufi ne? Ƴan kwanakin nan duk wasu ayyuka da na sakaki ba kya iya yi mini, sannan babu wani rahoto da ki ke kawo mini"

"Tuba nake ranki ya daɗe, ayi mini afuwa, ayi mini aikin gafara".

Ta ɗan ja numfashi ta ce "Yarinyar da aka ce ta zo da ɗan wurin Adam an ce ta na zuwa gidan nan haka ne?"

Baba uwani ta ɗan yi jimm sannan ta ce "Wallahi ba na ce ba uwar ɗakina, kin san yaron ko fito da shi daga sashin giwa ba ayi, babu wata hadima da aka amincewa zuwa in da yaron yake, ciki har da ni, dan haka ba na ce ba, amma akwai wata yarinya da take yawan zuwa, ban san alaƙarsu ba, amma zan iya cewa ita ce dan kuwa kwanaki na ji an ce za a kaita wurin mai girma turaki, amma abun da ya sa ban gazgata ita ce ba, yarinya ce fa sosai bana tunanin ita ce".

"Ba tunaninki nake son ji ba, abu ɗaya zan saka ki, daga yau idan ki ka sake ganin ta zo, ki yi gaggawar zuwa ki sanar da ni, bana son ta zo ta bar gidan nan ba tare da na sani ba".

"An gama ranki ya daɗe, in sha Allah zan sanar da ke"

"Saura wannan karon ma ki tsaya shashanci, tashi ki bani wuri " jiki na rawa baba uwani ta tashi ta bar ɗakin.

***
Jamil ne zaune a turakar turaki, bayan sun gaisa, ya ɗan gyara zama ya ce "Allah ya taimake ka, wata magana nake son mu tattauna idan babu damuwa"
Turaki ya jinjina masa kai ya ce "Ina sauraronka".

"Dama na ce game da riƙon ɗan wurin aisha, a hannun giwa yaron zai zauna kenan su cigaba da riƙonsa?".

Turaki ya ce "Eh, wannan hukunci in da zai zauna mahaifinsa ne yakamata ya yanke, ya rasa matarsa bai kamata ɗan kuma a saka masa ido a kan sa ba"

"Amma, ba kwa tunanin yana da kyau a sanya ido, idan maganar aure ta taso ya auri wadda za ta riƙe yaron da amana ta kula da shi?"

"Adam ba ƙaramin yaro bane ba, na san zai samo mace mai mutunci da kirki, ba zai auri wadda za ta cutar da yaron ba".

Jamil ya sake gyara zamansa ya ce "Amma ina ganin ku yakamata ku zaɓo wadda za ta maye gurbin aisha, kuma a ganina Samha ita yakamata ta maye gurbin aisha, a wannan karon yakamata a ba ta wannan damar"

Turaki ya ɗan yi shiru yana nazarin maganarsa, ya ɗago ya ce "Ka zo da magana kai ma, amma ka bari zan yi tunani a kai, kuma zan yi magana da shi in sha Allah, Allah Ya sanya hakan ya zama alkhairi"

"Amin ya rabb, Allah ya saka da alkhairi, Allah ya ƙara maka lafiya da nisan kwana"

Turaki ya jinjina masa kai tare da ɗan yin murmushi.

Duk wani ƙoƙari da dagewa, rumaisa tana yi wurin ganin ta kawar da tunanin sabir daga zuciyarta, amma abu ya ci tura, kullum sake jin ƙaunarsa take da tunanin sa a cikin zuciyarta.
Idan ta tuno da maganganun adam sai ta ji ina ma za ta iya zuciya, ace ko kallon sabir ba zata sake yi ba, balle ta ɗauke shi, amma ina sai ta ji ba zata iya ba, yanzu ma kawai daurewa take yi.
Gashi yanzu an ƙara mata tsaro, wataran mai sunan baba da kansa yake makaranta, islamiyya kuma tare da su huzaifa suke tafiya dan haka ba damar satar hanya. Haka za ta ɓoye ta yi kuka wasu lokutan dan tana kewar sabir sosai da sosai.

Yau asabar tana ta shirin tahafiz, mama ta ƙwala mata kira tana daga ɗaki.
Rumaisa ta shiga ɗakin, mama ta miƙa mata waya ta ce "Gashi Gwaggo ce za ta yi magana da ke".

Rumaisa ta karɓi wayar ta kara a kunnenta ta yi shiru.

"Hello rumaisa"

"Na'am".

"Ja'ira ki na ji na ba zaki yi magana ba"

Rumaisa ta ce "Ina kwana"

"Lafiya ƙalau, ya ki ke ya ƙarfin jiki?"

"Na ji sauƙi ai, har na koma makaranta ma"

"Ahh to Alhamdilillah, ya firgitar da ki ke yi fa cikin dare kin daina?"

"A'a ina yi wataran"

Gwaggo ta ce "Subhanallah, ki din ga addu'a sosai da sosai, dama zama a cikin wannan dajin ai dole ki yi gamo, wataƙila ma kin kwaso makarai. Zan saka a haɗo miki magunguna, a haɗo miki da kayanki a kawo miki".

Da sauri rumaisa ta tari numfashin Gwaggo ta ce "A'a gwaggo, kar a kawo mini kayan nan yanzu, ki ɗaure mini su, ki ɓoye su sosai, kar ki bari wani abu ya same su, zan gaya miki lokacin da za'a kawo mini"

"To shikenan babu damuwa in sha Allah, zuwa sati mai zuwa zan aiko miki da magunguna"

"Ni fa lafiyata ƙalau, ba wasu aljanu da na kwaso"

"Idan ma kin kwaso ai ke ba zaki sani ba, kuma idan aka kawo magani ki ka ƙi yi, da kaina zan zo har kanon na zane miki jikinki"

Rumaisa ta yi shiru, gwaggo ta gama maganganunta, ta miƙawa mama wayarta ta ɗau jakarta ta fice zuwa makaranta.

***
Ringing ɗin da wayarsa take yi ne ya sanya shi farkawa daga baccin da yake yi, a hankali ya yi miƙa ya buɗe idonsa, ɗan guntun tsaki ya ja, dan ya ji haushin katse masa barcin da aka yi.
Ya miƙa hannu ya ɗau wayar, ya ɗaga ya saka a kunnensa.
"Assalamu alaikum warahmatullah, barka da safiya"

"Yauwa barka" ya amsa murya can ƙasa.

"Ya gida ya ƙoƙari"

Cikin ƙosawa ya amsa da "Alhamdilillah, waye?".

"Khalifa Usman wakili ne, na kiraka ne domin yi maka ta'aziyya tare da jajanta maka abun da ya faru da kai".

"To ka saɓa lamba, ba wanda yakamata ka kira ɗin ka kira ba"

Khalifa ya ce "Na sani, ba Mahmud Sharif Galadima ba ne?"

"Eh, Adam sharif galadima yakamata ka kira"

"Ba laifi bane idan kai ma an yi maka ta'aziyya ai, abun da ya shafi adam ya shafeka"

"Kai ka ga, abun da ya shafe shi shi ya shafa, ku je can ku yi abun ku, don't ever involves me, ba na son fuska biyu, wataƙila da har zuciyarka da gaske ka ke ka kirani ka yi mini ta'aziyya sai in amsa maka, amma kowa ya san abun da yake tsakaninsa da mahaifinkaa da kai kanka, jiya mahaifinka yayi masa ta'aziyya a kafafen watsa labarai, kai kuma yau ka kirani wai kana yi mini ta'aziyya bana son munafuncinku na ƴan siyasa, kar ka sake kirana" ya yi tsaki ya kashe wayar ya ajiye.
Ya tashi zaune yana mamakin tsabar rashin kunya na wasu ƴan siyasar, ya san da biyu ya kira shi, ba dan Allah ba.

Ya miƙe ya shiga banɗaki domin ya yi wanka.

Ya gama abun da yake yi, ya fito ya shirya, ya fita falo domin karya, a falon ya tarar da Samha da Fauziyya ga ruky da Mummy sai hira suke yi, kuma da alama hirar ta su na da alaƙa da takawa.

"Wai ku ba ku da wata magana sai ta mutum ɗaya? Look for something else mana, kowa adam adam ku bar shi ya ji da abubuwan da suka dame shi".

Gaban Mummy ne ya faɗi, yaushe Mahmud ya fara damuwa da lamarin adam?.

Fauziyya ta ce "Kawai muna ɗan yin hira ne a kan yadda abubuwa ke ta faruwa da shi, social media ma sai zancen ake yi".

"Ni ma yanzu wannan yaron ya kirani, ɗan gidan wakili wai yana yi mini ta'aziyya, na ce kar ya sake kirana bana son munafunci da fuska biyu".

Waro ido Samha ta yi ta ce "Khalifa wakili kuma?".

"Shi fa, kar ma ya kuskura ya sakani a shirmensu ni buɗe masa aiki zan yi, rukky kawon breakfast zan karya"

'Mai wakili yake nufi da kiran Mahmud a waya wai zai yi masa ta'aziyya?' Samha ta tambayi kanta.

Tashi ta yi da sauri ta ce ta na zuwa, ta fice ta bar sashin zuwa harabar gidan, ta kira Khalifa a waya.

Sai da ta kira shi sau biyu sannan ya ɗaga.

"Wai me kake aikatawa ne da ka ke ɓoyewa?"

"Kamar me fa?" Ya tambaye ta cikin ko in kula.

"Kai ka ke sponsoring ake ɓatawa adam suna a gidajen jaridu ko?"

"Meye shaidarki na ni nake hakan?"

Cikin fushi Samha ta ce "Waye idan ba kai ba?"

"A tunaninki ni kaɗai ne maƙiyin adam? Ai ba mahaifina kaɗai yake da burin tozartawa ba, dan haka bani da lokacin sponsoring ɗin wasu gidajen jaridu su ɓata masa suna".

"To me kake nufi da kiran ƙaninsa wai kana yi masa ta'aziyya, shi ma janyo shi zaka yi cikin tsiyar ta ka?"

"Wow, kuna tare kenan few hours da kiransa har kin samu labari"

"Ka ga, kashedi zan yi maka, kar ka kuskura ka sanya Mahmud cikin shirmenka, na san ba zai wuce an ce maka baya shiri da shi da adam ba, amma ka sani har abada jini ya fi ruwa kauri, adam jininsa ne kuma ko ba jininsa bane ba, Mahmud ba irin wanda zaka yi wasa da su ba ne ka cimma burinka".

Khalifa ya yi dariya ya ce "Jini ya fi ruwa kauri, wane irin jini ne tsakanin ki adam da har ke ake wasan da ke? Ko daa yake wata kusan ta fi wata ai, and ba ke zaki gaya mini abun da yakamata na yi ba da wands ba zan yi ba, ina da abun yi yanzu, see you later" ya kashe wayar sa.

Ajiyar zuciya Samha ta yi ajiyar zuciya cike da takaicin biye wa Khalifa tun a farko.

***
Rumaisa ce zaune da wandon uniform ɗin islamiyya a jikinta, sai vest tana suyar wainar fulawa ita da Abdallah.
Ta ce "Yaya Abdallah ka san me nake sha'awa?".

"A'a sai kin faɗa" yayi maganar yana zuba ƙullin wainar a kasko.

"Ina so in ji na ce basir ne da ni, ya tayar mini"

Tsaki ya ja ya ce "Mahaukaciya ba zaki yi hankali ba, kin san meye basir ciwo ne fa".

"Eh, kawai dai burgeni yake yi, idan na ji an ce ina da basir"

"Sai ki yi ta yi ai, ba ki san masifar da ke cikin sa ba, ki je ki ji da yawon gudawarki da ki ka saba ba yau ba gobe, ya fiye miki alkhairi a kan ace basir ne da ke"

Tura baki ta yi, ta saka hannu ta gutsuri gefen wainar fulawa ta saka a baki, Abdallah ya ce "Kin ci a taki"

"Ƴar wannan ɗin?"

"Eh, uban wa ya ce ki ci ba a raba ba?"

Ta miƙa hannu ta ce"To bari na cinye guda ɗayan na ci a tawa" ya buge mata hannu ya ce "Baki isa ba uwar son zuciya"

Sallama suka ji, suka amsa gaba ɗaya, maman habiba ce, rumaisa ta gaisheta ta amsa mata cikin sakin fuska, tare da tambayarta ina mama.

Rumaisa ta ce "Mama tana cikin ɗaki ki shiga"

Bayan ta shige, Abdallah ya kalli rumaisa ya ce "Ina fatan ba wani laifin ki ka aikata ba?"

"Ni ba abun da na yi".

"Wallahi idan ƙararki ta kawo sai kin daku?"
Shiru ta yi masa ta hau lasar yaji.

Maman su habiba ta ɗan daɗe, sannan ta fito, mama ta rakota sai dai fuskar mama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login