Showing 177001 words to 180000 words out of 199108 words

Chapter 60 - Kanwar maza 3&4 Hausa Novel Complete

12 Dec 2024

824

tun da ba zaki daina ba, sai kin bar gidan nan yanzu"

Ammi ta ce "Mahmud ban gane me kake nufi ba? Me ta yi ne? Tsawon shekaru ina tare da ita rana tsaka ka ce ta tafi?"

"Ke kin ɗauketa mutum, kin kula da ita da iyalinta, ita kuma tsawon shekaru tana cin dunduniyarki, duk abubuwan da suke faruwa a sashin ki, Mummy na da masaniya a kai"

Gaban Ammi ya faɗi ta kalli baba uwani ta ce "Uwani, da gaske yake yi?"

"Wuce ki kwaso kayanki ki bar gidan nan, ki je dan kanki, ko ba a ɗauki wani mataki a kanki ba, hakkin mutanen da ki ka ɗauka ba zai barki ba"

Mahmud ya ƙi yi wa ammi cikakken bayani, ya kori baba uwani a gaban sauran hadimai, wanda ya san tilas maganar za ta watsu, ace ya yi mata korar kare ba tare da cikakken dalili ba".

Baba uwani na kuka, ta kwashi tsummokaranta, ta fita.

Gaba ɗaya ammi ta zama confused, Barira ta ce "Ai ni na san baba uwani ba zata sauya hali ba, nayi mamakin rashin tona mata asiri, da maman sabir ba ta yi ba".

Jin abun da ta faɗa, ya sanya ammi ritsa Barira, barira kuwa ta kwashe komai ta gaya mata.

Ammi sai da ƙafafuwanta suka nemi gaza ɗaukarta, saboda tashin hankali da zullumi, hadimar da ta amincewa tsayin shekaru, ita ce ta ci amanar ta.

Kasa jurewa tayi, a daren ta je gidan takawa, hankali a tashe, dan kuka take suka je gidan. Wanda hakan ba ƙaramin ɗagawa ruma da takawa hankali yayi ba.

Rumaisa ta tabbatar mata da ta san baba uwani muguwa ce, tun a lokacin da ta din ga gaya mata takawa mahaukaci ne, da lokacin da ta ce Mummy tana yi wa takawa asiri maganar ta koma kunnen Mummy.

Rumaisa ta tabbatar mata da cewa, Mahmud ya gaya mata ya sha ganinta cikin dare a sashin Mummy, amma ya ce kar su tona mata asiri a lokacin, saboda basu da cikakkiyar hujja, yanzun ma tun da ya ce ta tafi, yana da dalilin yin hakan, kuma ko daga baya an tayar da magana, suna da cikakkiyar hujja a kan ta yanzu.

Sai a lokacin ammi ta din ga tuna wasu daga cikin abubuwan da suka gabata, tabbas idan da babu munafuki a sashin ta, babu yadda za ayi wasu maganganun su din ga fita.

Sai dai a hakan ma, ruma ta ɓoyewa ammi binne-binnen da baba uwanin ke yi mata a cikin gidan.

Takawa ya din ga rarrashin ammi yana bata haƙuri, tare da yin faɗa dalilin da ya sanya Mahmud ya kori baba uwani kai tsaye, ba tare da girbar abun da ta shuka ba.

Ammi ta daɗe abun nan yana ci mata zuciya, ta daɗe tana jinjina tsawon lokacin da baba Uwani ta yi, tana zaluntar ta, ta hanyar kwasar sirrinta tana kaiwa wajen Mummy.

Baba uwani bayan ta fita cikin kuka, ta kira Mummy ta sanar da ita halin da ake ciki, wanda hakan ya faru a dalilin ritsa Mummy da yayi suna waya da baba uwani, dan sai da suka samu saɓani ma.
Babu kunya Mummy ta ce "Ba abun da za ta iya yi mata, sakacinta ne ya janyo mata"

Baba uwani ta sha mamaki, ba ta taɓa tunanin abun da Mummy zata gaya mata kenan ba.

Sannu a hankali rumaisa ciki ke tasawa, tayi ta ɓoye-ɓoye, gashi yau da lafiya gobe babu, haka nan take zuwa makaranta.
Ga koke-koken ba gaira ba dalili, wai ita rasa abun da yake yi mata daɗi.
Sai dai takawa yayi ta rarrashin ta, ya san ƙuruciya ce da rashin sabo.

Iman kuwa kusan awanni kaɗan sai sun yi waya da mai sunan baba, idan ta maƙale a kan waya, har mantawa Ammi take yi da ita.

Ammi ta ce "Iman dan Allah ki ƙyale yaron nan yayi aikinsa mana, maƙal-maƙal a kan waya ko gajiya ba kwa yi ne?"

Rufe fuska tayi tana murmushi, dan kuwa ba ta yi zaton ammi ta ɗagota da yawan wayar nan ba.

Ɓangaren mai sunan baba, yanayin aikinsa yayi masa daɗi, sai dai kewar gida da yake yi sosai, sannan ya fuskanci akwai tarin kitimurmura da rashawa a aikin.
Sai dai yadda yake umar ɗin sa bai canza ba, ba ruwansa da kowa aikinsa ne kawai ya dame shi.

Sallama aka yi a office ɗin sa, ya amsa tare da kallon ƙofar.

Wani babban mutum ne ya shigo, fari sol da shi, cikin manyan kayansa.

Mai sunan baba ya yi masa ƙuri da ido, ya ƙaraso ya zauna suka yi musabuha da mai sunan baba.

Ya ce "Namu ne ka na jin hausa ko da turanci zan yi" yayi maganar cikin guɓatacciyar hausarsa ta cikakken bafulatani"

Mai sunan baba yayi murmushi ya ce "Ina kama da bayerabe ne?"

"To ai abun naku ne, wasu lokutan ba a banbance ku hausawa".

"Eh amma irin naku da kun ga junanku ku ke ganewa"

Mutumin yayi dariya, duk da yau ya fara ganin mai sunan baba, kamalarsa ta burge shi.

Ya ce "Masha Allah ya aiki?"

"Aiki Alhamdilillah"

"To da dai ba kai nake tararwa a office ɗin nan ba".

"Eh, sabon ma'aikaci ne ni"

Ya ce "Yauwwa ni fa in ce. Kayana ne nake ta sintiri ayi mini clearance, amma bayan gama biyan duk wani haraji sai wani hanya-hanya ake yi mini, ana dai nuna mini sai na bayar da cin hanci, sai dai ba dan babu kuɗin ba, bayarwa ne ba zan yi ba. Tun da na san kayana ba na laifi bane"

Ikon Allah mai sunan baba yake gani, hatta yadda mutumin yake kallonsa, tamkar iman ce a zaune a gabansa.

Ya ce "Wasu irin kaya ne? Fanta ne, buredi da ƙosai ne ko kuma shanu"

Mutumin ya sake yin dariya ya ce "Ka fa dame ni fa, ko dai babarbare ne?"

Cikin murmushin sa na ƙasaita ya ce "Ba ɗaya, mai ɗakina ce bafulatana, ai ni akwai amana a tsakaninmu"

"Ahhh ashe ma sirikinmu ne, ina fatan ka bayar da nagge 100, kafin a baka" yayi maganar yana ciro wayarsa daga aljihu da take ringing.

Ya cewa mai sunan baba "Afuwan dan Allah"

Ya kara wayar a kunnensa, yana magana da fulatanci, mai sunan baba yana fahimtar wani abun, sai dai ya ji yana cewa Ade a cikin maganarsa.

Ya gama wayar ya girgiza kai ya ce "Ade na da damuwa. Wai mahaifiyata na ɗaukko daga garinmu, na dawo da ita nan Lagos gabana, na din ga ganinta. Ni da matata fa ƴan uwa ne, kuma akwai wasu ƴan uwana da na ɗaukko duk muke zaune tare. Amma ta saka an kirani a waya, wai na rabota da danginta na zo na ajiyeta a nan, ita tunanin shanunta da awakinta ma take yi. Ace Allah ya yi mini rufin asiri, amma uwata na ƙauye ai lamari ya ɓaci"

Mai sunan baba ba wai dan halayyarsa ce sakin jiki hira da mutane ba, sai dan son cigaba da kallon ƘUDURAR ALLAH (Kar ku manta da sabon littafin NAZEEFA SABO NASHE, da tuni ya fara zuwar muku, kar ku yi ƙasa a gwiwa wurin bin wannan ƙayattacen littafin)
Mutum mai matukar kama da matarsa, ya fara tambayar kansa anya mutumin ba shi da alaƙa da Iman ɗin sa.

Hira suka ɗan yi da mutumin, yana bashi labarin rigimar Ade, kuma ya ke gaya masa akwai mataimakin shugaban ƙungiyar fulani ta ƙasa a familynsu, Ade Allah ya yi wa iyalanta rufin asiri, amma ita ta dage sai zaman ƙauye.
Mai sunan baba ya bashi labarin, shi nasu gidan, da ƴan uwansa, tare da tattaunawa a kan jajircewar iyaye mata idan aka mutu aka bar su da yara.

Haka suka din ga hira, daga baya suka yi exchange ɗin numbern waya, mai sunan baba ya ce zai sake duba maganar kayan na sa.

***
Ƴan kwanakin nan, Mummy tana ta fama da ciwon kai, ta je asibiti an yi mata teses amma bai daina ba, ko san haske ba ta yi sosai.

A hankali kuma Allah ya taimaketa ya fara sauka, shiryawa tayi zata fita, tana son yin waya, amma tata ba network, dan haka ta karɓi wayar ruƙayya ta saka lambar wayar da zata kira, ta yi wayarta.

Sai dai bayan kammala wayar, ta ga saƙo ya shigo wayar ruƙayya daga Jabir.

"Wallahi ruƙayya idan ba ki zo kin same ni ba, mun cigaba daga in da muka tsaya ba, zan watsa videos ɗinki, duniya kowa ya gani, and i mean it"

Bakin Mummy ne ya fara rawa, ƙafafuwan ta suka nemi gaza ɗaukar gangar jikinta, cikin tsananin tashin hankali da mamki, ta dawo falo in da ruƙayya ke kallo. Fauziyya na chatting.

Tana zuwa ta jefa nata mata wayar, ta ce "Me wannan saƙon yake nufi?"

Gaban ruƙayya ya faɗi, ta ɗauki wayar, ta karanta, a take ta fara kuka tana girgiza wa Mummy kai.

"Ki gaya mini me saƙon nan yake nufi?"

"Mummy zan yi miki bayani dan Allah"

Danneta mummy ta yi tana hargagi ta ce "Ni zaki tonawa asiri ruƙayya, wace irin alaƙa ce a tsakanin ki da Jabir? Wallahi gara na kashe ki, na kashe banza, akuya ce ke? Da ke za a haɗa kai a janyo mini abun faɗa? Ni Lubabatu da Jabir za su haɗa kai su cuta? Ni?" Da ƙyar Fauziyya ta janye Mummy daga kan ruƙayya da tuni numfashinta ya fara sama-sama.

Ruma ce zaune daga ita sai mini skirt da brezia, domin kuwa kayan ma ita yanzu damunta suke yi.

Ta ƙurawa Adam ido, "Ya dai babyna, jikin ne?"

"To jiki ai sai Alhamdilillah, papa baka gano smoke ɗin ba haryanzu?"

"Mimi da na gano, ai da na gaya miki, bashir suna nan suna bincike a kan al'amarin, kuma an gano wurin da ki ka ce ana ɗibar ma'adanai, mun yi magana da hukumar mu ta katsina ana targeting wurin, kama su ake son yi red handed kamar yadda na gaya miki"

"Papa, na san na yi maka laifi, tun haɗuwarmu yakamata ka san komai, amma na din ga yi maka wasa da hankali. Ka san dalili?"

Ya ce "A'a"

"A wannan lokacin da ka san komai, zaka yi aiki da zuciya ne, zaka iya ɓata aikin, saboda kana kan jin raɗaɗin abun da ya faru.
Anty Aisha ta bani labarin komai, wanene kai, abubuwan da suka faru a rayuwarta da taka, rashin jituwaku tsakaninka da Mahmud, sannan a ƙarshe ta roƙi da na auri mijinta, saboda tana ji a jikinta zan iya taimakonka, idan har zan rayu a tsakanin ƴan bindigar daji marasa imani da tausayi, in zauna a cikinsu da baƙin taurin kai, har na din ga abun da nake so wasu lokutan, su ƙyaleni, to lallai zan iya tanƙwara zuciyarka da koya maka haƙuri da sassauta fushinka.
Na tubure na ce ni fa ba zan aureka ba, dan ba ka yi mini ba, mussaman da ba ma jituwa, amma ta cigaba da yi miki magiya, tare da roƙon in taimaki rayuwar mijinta, ita tayi iya nata ƙoƙarin ta kasa".

Rumaisa ta ɗan yi shiru sannan ta ce masa "Lokacin da anty aisha za ta mutu, ta cigaba da nanata mini, ta bar mini jaririn ta, kuma ta bar mini mijinta, dan Allah kar in bari ƴar uwatta ta aureka, kuma in tabattar an samu daidaito tsakanin ka da ɗan uwanka, domin samun farincikin ammi.

Papa, wakili na da saka hannu a yin garkuwa da anty aisha, dan ƴan bindiga sun ambaci sunansa, cikin dare suna zaton duk mun yi bacci".

Ƙirjinsa ya buga da saurin gaske ya kalleta.

"Amanarka na karɓo papa, shiyasa nake iya ƙoƙarina da zuciyata da jikina domin baka kariya, da tabattar da cika alƙawarin da na yi wa anty aisha. Ina neman afuwarka bisa wahalar da kai da na din ga yi, but Alhamdilillah atleast na cika wasu daga cikin alwashin da na yi"

Shiru yayi ya sunkuyar da kai, ya kasa cewa komai.

Rumaisa ta ɗago kansa ta ce "Papa fushi ka yi?"

Cikin tsananin ƙarfin hali, da hawayen idonsa ya kasa ɓoye damuwar, ya ce "Mimi ba ki yi mini komai ba, ni ya cancanci na yi miki godiya mimi, ban san da wasu kalaman zan yi amfani ba ma" yayi maganar yana kwanciya a jikin ta.

Ta kalli hannunta da hawayen sa yake ɗiga a kan hannunta, ta saka hannu tana share masa hawayen, tare da shafa sumar kansa.

"Mimi ba kya so na? Saboda alƙawarin aisha kawai ki ke tare da ni?"

"To ai ban san me zan ji idan ina son ka ba"

Yayi murmushi ya ce "Shikenan, but i already fall for you, ni ina son ki sosai rumaisa i love you, and i will surely keep loving you, to my last breath. Ina son ki rumaisa".
Ji ta yi tsigar jikinta na tashi, kalamansa na ratsa ko ina na jikinta, har wani lumshe ido take yi saboda daɗin kalamansa.

Ta yi ajiyar zuciya ta sake cewa "Papa, jaridar da suke wallafa ci maka mutunci, lokacin da anty aisha ta rasu, Yasir ya bi diddigin gidan jaridar, daddyna ya gano wakili ne suke ɗaukar nauyinsa, dan ya ce mini sun taɓa kiransa har aka nemi ya bayar da haɗin kan cutar da kai, ya ce ba ruwansa. Kaga dole a cikin family ba za a rasa wanda suka haɗa kai da shi ba, ake cutar da kai"

Ya lumshe idanunsa ya ce "Mimi kaina ya daina ɗaukar wannan abubuwan ma, bari na samu nutsuwa"

"Idan ka samu nutsuwar, ka yi bincike sosai a cikin gida. Sannan ka sani tun a yanzu ka sanya wa ranka cewar, zaka iya gano su waye, amma samun hukunci da adalci sai a wurin Allah, amma ba a wannan ƙasar ba"

Ya numfasa ya ce "Ina sauraren Bashir ne, na ji me za su ce mini, nayi magana da su barrister ma, waɗan da ki ka ce mini kin yarda da su, muna kan faɗaɗa bincike"

"Nima ni da ƴan team ɗina muna ta ƙoƙari, Allah ya yi mana jagora" ya jinjina kai ba tare da iya yin magana ba.

Abu kamar wasa mai sunan baba yake ta ƙoƙari akan kayan Alhaji Aminu ɗan fulani, kuma kasancewar an samu sauye-sauye a wurin, cikin ikon Allah komai ya zo masa da sauƙi, dan ana daf da releasing ɗin kayan.

Alhaji Aminu yana yawan kiran sa, su gaisa, shi kuma mai sunan baba, sai ya tambaye shi ina Ade, ya ce masa tana nan tana rigima.

Alhaji Aminu ya matsawa mai sunan baba, a kan lallai ya zo gidansa su gaisa, dan yana bawa Ade labarin sa, ita kuma ta ce tana son ganin sa.

Mai sunan baba ya ji a ransa yana son sanin ahalin Alhaji Aminu, ko zai samu abun da yake son tabattarwa, ko Alhaji Aminu yana da alaƙa da Iman.

***
Tamkar za su kacame da dambe, haka suke musayar yawu, tamkar ba aminan da suka kwashi shekaru suna cin mushe ba, tamkar ba tare suke ƙullawa da kitsa duk wani hatsabibanci ba.

Mummy tamkar za ta ari baki, saboda haƙilo da bala'i.

Hajiya Lubabatu a fusace ta kira Jabir a waya, a kan lallai ya zo tana son ganinsa, ta ajiye wayar ta kalli hajiya jamila ta ce "Kar ki sake kiran ɗa na da mazinaci ɗan iska, idan ma hakan ne, sai ki ce mazinata ƴan iska".

"Na faɗa ɗin, koda yake barewa ba ta gudu ɗan ta yayi rarrafe ba, tun da sai da ki ka yi yawon tazubar ki ka gama ki ka tuba aka yi auren. Kin yi wa mijinki asiri, kin ya da shi a Germany, kin cigaba da watsewa a gefe, ke ki yi ɗan ki yayi".

"Jamila kina nufin ni ce nake biye² ni zaki yi wa sharri? Ko kin manta kema irin abubuwan da ki ka shuka, yayan giwa da ki ka din ga sadaukarwa, da ƴaƴan Adam, ai ni ban kai ga aikata kisan kai kamar ke ba"

Jabir ne yayi sallama, suka yi shiru suka waiwaya.

"Sannu munafukin Allah ta'ala"

Jabir ya ce "Mummy lafiya kuwa?"

Mummy ta ce "Saboda kai watsatstse ne, mara mutunci, na amince maka na amincewa uwarka, amma ku ka zalince ni, wace irin alaƙa ce tsakanin da ruƙayya har ka ke iƙirarin yaɗa hotunanta?"

Yayi shiru yana kallon Mummy.

"Wallahi lubabatu sai kun yi dana sanin abun da ku ka aikata mini, kai ba da ni ka ke zancen, dabba ɗan akuya".

"Kar ki sake kiransa ɗan akuya, ruƙayya ce babbar akuyar da ba ta san ciwon kanta ba"

Mummy kawai ta fice, zuciyarta na wani irin zafi, kuka take son yi amma ba ta son bayyana karayarta a fili.

***
Mai sunan baba ya amsawa Alhaji Aminu cewar zai kai masa ziyara ya gaida Ade, sai dai yana fargabar kar ya ga abun da bai yi tsammanni ba, zai fi kowa farin ciki, idan aka ce a sanadinsa Iman ta samu ko wani ne a danginta, duk da rashin hakan ba ya nufin zai juya mata baya ne.

Kiran Iman yake yi yana zancen zuci, ta ɗaga video call ɗin ta ce "Hi dear"

"My yellow, how are you?"

"Fine Alhamdilillah, ya aiki?"

"Ai akwai shi, yanzu salary ya shigo, na ce let me call the person close to my heart"

Tayi murmushi ta ce "Alhamdilillah ala kulli halin, mun godewa Allah" kallonta yake sake yi, hatta yanayin gashin girar iman, irin na Alhaji Aminu ne.

"Ya naga kana kallona ne, na canza ne?"

"Bakomai, yanzu ya za ayi da salaryn nan ne?"

Iman ta ce "Ai zaka shigo kano ko? Ka ce fa ƙarshen wata zaka zo".

Ya ce "Eh, ranar Alhamis zan shigo"

Ta ce "To Allah ya kaimu, idan ka zo sai ayi shawara, ka turawa mama dubu ɗari a sai mata abun da take so kan ka zo na neman albarka".

Ya ce "To ƴar mama, za ayi in sha Allah, zan cigaba da waya, zamu yi magana anjima"

Ya ajiye wayar yayi shiru, yana cigaba da fatan Allah ya sa Alhaji Aminu yana da alaƙa da Iman.

Har gida Alhaji Aminu ya aika da direba, aka ɗaukko mai sunan baba, yana da matuƙar karamci da son mutane, kamar ya goya mai sunan baba da ya ganshi a gidansa.
Aljannar duniya, an kashe dukiya an zuba kayan alatu a gidan nan, kamar ba za a mutu ba, karen da yake gadin gidan kuwa bayan mai gadi, shi kansa ba na Nigeria bane ba.
Ga iyayen motoci a parking space.

Ya ce wa mai sunan baba "Mu je ka fara ganin Ade, ka gaya mata ta haƙura da tafiya ƙauye ko Allah ya sa ta yarda".

Tsohuwa ce, a ƙalla zata shekara tamanin da biyar, tana zaune a ƙasan carfet, tana shan fura, sai mita take da fulatanci ita da jikokinta.

Ta ɗaga kai ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login