Showing 45001 words to 48000 words out of 199108 words
wayar, ya saka a kunne yana lumshe ido.
"Anty rumaisa, barka da safiya jiya ki ka yi bacci na kira kin yi barci".
"Ke! Ba wayarta bace kar ki sake kirana wayata ce ba tata ba" a wannan karon ma ba ƙaramar razana ta yi ba, cikin rawar murya ta ce "Yi haƙuri, na zata wayar mama ce".
"To ta umar ce, ki ka sake kirana ni da ke ne, an hana mutane barci tun jiya, ki yi ta wani yenyen, ba zaki buɗe baki ki yi magana ba" ya ƙarasa mitar yana kashe wayar.
Nusaiba da take gefenta ta ce "Wannan wane bala'e'en ne haka?" Iman ta girgiza kai ta ce "Ba kowa, ga Sabir nan bari na je na kwanta"
Nusaiba ta karɓi Sabir, ita kuma ta tashi ta tafi ɗakinta tana tunanin yadda mai sunan baba ya faɗa haka take magana.
Sunansa da ya faɗa umar ta sake maimaitawa, dole yayi masifa, ta faɗa a ranta.
Tana shiga ɗakinta ta ji tamkar an shaƙeta, kuma ta kasa gaba ta kasa baya, hannu ta saka tana riƙe wuyan nata, amma ta ji numfashinta yana neman ɗaukewa. Cikin fita hayyaci ta sulale Jikinta ta faɗi ƙasa.
Can katsina kuwa, Gwaggo har da taka rawa saboda murna, tana faɗin Allah ya dubi ƴar marainiyarta, za ta yi a gidan daraja, gidan sarauta gidan masu abun hannu.
Nan da nan ta ce ba zama, azo a kama wasu daga cikin dabbobinta a sayar, ta fara saye-sayen kayan da za a kai wa rumaisa.
Iman kuwa ba a tashi sanin halin da take ciki ba, sai bayan wasu awanni, da nusaiba ta ji ta shiru, ta shiga ɗakin ta tarar da ita a ƙasa a sume.
A kiɗime ta je ta sanar da ammi halin da ake ciki, ranga-ranga aka ɗauki Iman zuwa asibiti, ba tare da ta san waye a kanta ba ma.
***
Gidansu ruma kuwa, mama ma ta fara shirin tafiya kasuwa, domin fara saye-sayen da za a buƙata, dan ba ta taɓa kawo wa rumaisa aure yanzu ba, amma cikin ikon Allah, sai gashi ba tare da wani shiri ba, dan ko ƴan kwanuka ba ta fara saya ba.
Rumaisa na uwar ɗakan mama, tana ta zane-zanenta, mama sai mita take ba ta son zane-zanen nan, wataƙila ma zanen ne yake sanyata firgita cikin dare.
Rumaisa ta yi dariya ta ce "Haba mama, zanen ne zai tsortani, kin ganni nan kin san bana tsoron kowa sai Allah, balle wani zane".
"Kya ji da shi dai" ta yi maganar tana fita falo.
Yaya Abubakar ya yi sallama a falon mama, mama ta amsa masa ta ce "Garbatina ya aka yi ne?"
"Fita zaki yi ne?"
Mama ta ce "Eh, kasuwa zan shiga na fara saye-saye".
"To da magana nake son mu yi, amma idan kin dawo ma yi"
"A'a, zauna ka gaya mini sai na fita"
Suka zauna, Abubakar ya kalli mama ya ce "Mama, kamar yadda muka yi da ke, na je na ɗan zazzaga unguwar ina tambayar ya yanayin gidansu yake, da kuma shi kansa mu'amalarsa da mutane, to sai dai sakamakon baki ya rabu biyu. Wasu suk ce mutumin kirki ne, mai yawan kyauta, da girmama mutane kuma miskili ne, wasu kuma sun ce ba shi da kirki, yana da faɗa da zafin rai wai kwanan nan ya taka ƙaninsa da mota, ba wannan ne ya fi ɗaga mini hankali ba, wai ana kyautata zaton maye ne, kuma yana da taɓin hankali!!!
Ayshercool
08081012143
*MAMAN MEENAT COLLECTION, MAMAN MEENAT SUPPLEMENT/SKIN CARE*
*SHIN YAR UWA KINADA LABARIN* *SHAHARARRIYAR MAI SAYAR DA SUPPLEMENT DIN NAN KUWA?*
*TO IDAN BA KI SANI BA KIYI MAZA KI GARZAYA DOMIN KEMA KI SAMU RABONKI DOMIN ZATA GYARAKI TSAF KI FITO KAMAR SABUWAR AMARYA, KEMA KI SHAGA CIKIN MATAN DA SUKE HASKAKAWA KAMAR TAURARO. SHIN ƘURAJE NE SUKE DAMUNKI, KO KUMA MATSALOLIN JIKINE KAMARSU RAMA BUSHEWAR FATA KARANCIN NI'IMA NE KO BUDEWA NE, KO KUMA INFECTION? KO KUMA SO KI KEYI FATARKI TAYI LAUSHI KIDIN GA SHEƘI KINA HASKAWA? TO MAZA KI GARZAYO WURIN MAMAN MEENAT DOMIN KI SAMUN MAFITA CIKIN SAUKI, ACIKIN FARASHI ME SAUKI*
*SANNAN YAN UWA KUSANI DUK* *SUPPLEMENT DIN DAZAMU KAWO MUKU SAI MUNYI BUNCIKE AKANSHI DAN TABBATAR DA INGANCINSHI MUN TABBATAR DA CEWA BASHI DA WATA* *MATSALA GA LFY, AKWAI MASU CEWA SUNSHA SUPPLEMENT AMMA HAR YANZU SU BASUGA WANI CANJI BA, TO YAR UWA KODAI AN BAKI FAKE KO KUMA BA'A BAKI WANDA YA DACE DAKE BA, KO KUMA BAKISHA YADDA YA KAMATA BA, DOMIN KISANI YAR UWA KAFIN KI FARA SHAN* *SUPPLEMENT AKWAI WASU KA'IDOJI DAYA KAMATA ACE KIN KULA DASU KUMA KIN KIYAYE, MATUKAR KINASO SUYI MIKI AIKIN DA KIKESO CIKIN SAURI, WANNAN KA'IDODIN SAI KIN NEMENI ZAN SANAR MIKI, DOMIN BAZAN IYA KAWOSU ANAN BA SBD SUNA DA YAWA*
*Yar uwa muna da duk wani supplement da kuke bukata masu kyau da inganci tested and trusted, sayen na gari mai da kudi gida, gaskiya da Amana shine takenmu 08039437158.*
👉 *Supplements suna da yawa amma ga kadan daga cikin su.*
*1. Supplements na gyaran jiki ciki da waje*
*2. Supplements na gyaran gashi da farce, dasa haske mekyau ba irin na bleaching ba*
*3. Supplements mai da tsohuwa yarinya anti aging wanda zaisa ki kullum ki koma kamar yarinya matashiya*
*4. Supplements na karawa fata kyau da sheki glowing skin*
*5. Supplements na masu fama da ciwon jiki da stress da rashin samun isashshen bacci*
*6. Supplements na masu ciki, da masu shayarwa wanda zai kara miki lfy keda babynki*
*7. Supplements na gyaran jiki da gashi, kara hasken ido da sauransu*
*8. Supplements me kara lfy da karawa garkuwar jiki karfi.*
*9. Supplements na karin ni'ima da dandano da tightening ciki da waje*
*10. Supplements na magance cututtuka, kamar matsalar ido ulcer, infection, karawa garkuwar jiki karfi, etc*
*11. Supplements na gyaran nono da mazaunai breast/hips Enlargement*
*12. Supplements na gyaran HQ ciki da waje*
*13. Supplements na rage tumbi slimming capsule/flat tummy Lipton*
*14. Supplement na whitening/glowing skin*
*15. Supplement for Acne, dark spots remover*
*Sannan ga wadanda sokeso jikinsu yayi kyau sosai amma basa son susha supplement to albishirinku muna da kowanne irin mai na gyaran jiki da kuke bukata irinsu lotion, cream, soap, scrubs, face Cream,sun screen, serums concentrate, hair oil, hair cream face mask etc, sannan ga masu fama da matsalar ciwon jiki wadanda kullum sai sunsha magani suke jin dadi ko iyaye ko kakanni, to albishirinku kuma mun kawo muku cream, soap na ciwon jiki masu kyau da inganci wadanda indai kana amfani dasu ka huta shan maganin ciwon jiki da yardar Allah*
*Muna saida duk wasu nau'in supplement Lotion da kuke bukata, sannan Maman Meenat collection ba anan kadai ta tsaya ba muna saida turaruka kowanne irin na wuta dana jiki, da Airfreshners, sayen daya ko sari ke dai kawai neme ni a wannan number call or chat 08039437158*
Dafe ƙirji mama ta yi tana salati, ta ce "Ɗan nan, da gaske kake wannan maganar?"
Abubakar ya ce "Wallahi da gaske nake, kuma ba a bakin mutum ɗaya ba, ni da wani abokina Abdurrahman muka je, abun da na jiyo kenan".
Mama ta ce "Ya salam! Yanzu menene abun yi?"
"Ba wata maita a musulunci, haka malaminmu ya gaya mana, to so suke a fasa shikenan a fasa bani Sabir ɗin, ko kuma kuɗin da aka kawo ɗin suke so a mayar, ƴan baƙin ciki ne kawai".
Mama ta kalleta ta ce "Ke! Waye ya saka da ke? Da ke ake ke zaki yanke wa kanki hukunci?"
"Mama ba haka bane ba, to kuɗin za a mayar, idan aka mayar kuma an fasa ba za a bani Sabir ba fa kenan"
Aliyu ya shigo yana tambayar meyafaru?.
Mama ta gaya masa abun da ya faru, Aliyu ya kalli ruma da ta kumbura baki ya ce "Ke ki na son sa a haka?"
"Ba fa maye bane ba, ƙarya suke yi. Ni fa bana son shi, amma idan aka fasa ba fa zasu bani Sabir ɗin ba, kuma mama ba kwanan nan aka ce shi ya kashe Anty Aisha ba, kuma ƙarya ake yi masa ba? To wannan ma ina ga ƙarya ake yi masa, ni dai ko za a fasa, kar a mayar da kuɗin nan, kuma a bani Sabir".
"Ke ki ka nema musu kuɗin, ido a kwabo" Yaya Abubakar yayi maganar yana dungure mata kai.
Aliyu ya ce "Mama, bana tunanin wannan abun ya kai a fasa aure saboda shi, dama rumaisa na buƙatar tsayayyen namiji jajirtacce, saboda halinta, sannan shi mutum ne fitacce, irin wannan sharrin ba abun mamaki bane ba, ban ƙaryata b kai tsaye, amma ke ki ka gaya mini addu'a da ki ka din ga yi, kina jin son abun a ranki, lamarin ya kwanta miki a ranki, da bai kwanta miki ba sai mu ce babu alkhairi, dan babu hijjabi tsakanin addu'arki gareta da Allah, a ganina mu cigaba da addu'a babu ma'ana a kawo wannan zancen ma, tun da ai ita ma rumaisan tana son sa ko?"
"A'a nifa ba son shi nake yi ba, kawai saboda a bani Sabir ne".
"To amma ai ke ki ka ce mai kuɗi ki ke so, kuma mai kyau wanne ne bashi da shi a ciki?"
"Wannan har wani kyakykyawa ne? Kullum yana wani zazzare ido"
Mama ta ce "Tashi ki bar wurin nan, mara kunya, ana maganar aurenki kina tsoma baki"
Aliyu ya ce "To sanin ma'anar auren ma ta yi? Amma mama ya kike gani? A kan wannan dalilin zaki saka a ɗauki kuɗin da aka kawo shekaranjiya a mayar musu ne?"
Abubakar ya ce "A'a ba ayi haka ba, na gamsu da maganganunka nima, mu cigaba da addu'a dai, Allah ya zaɓa abun da ya fi alkhairi"
Mama ta amsa da Amin, sannan ta tashi ta saka Yasir a gaba suka tafi kasuwa.
Likitoci suka karɓi iman, kasancewar asibitin sun san matsalar Iman, nan da nan suka karɓeta.
A duk lokacin da ciwon ya tashi, Asibitin ake kawota, tun tana yarinya abu kaɗan sai ta yanke jiki ta faɗi ta suma. Aka din ga binciken abun da yake damunta har ƙasar waje, ƙarshe dai aka ce zuciyarta ce ke kumbura wasu lokutan.
Ammi ta alaƙanta hakan, da yawan damuwa da take yi, mussaman a lokacin yadda ake tsangwamarta, hakan ya sanya hankalin ammi ya tashi sosai.
Ta din ga faɗi tashi, domin ganin iman ta samu lafiya, tayi iya ƙoƙari iman ta samu sauƙi, sai dai lokaci zuwa lokaci jikin ya kan motsa.
Yanzu haka ammi hankalinta ya tashi, ba ta ƙaunar ganin wani abu ya sami iman, shiyasa kullum cikin addu'a take yi mata, Allah ya sanya iman ta samu miji nagari, wanda zai iya haƙuri da ita ya jurewa larurarta.
Sai dai a wannan karon, su kansu likitocin lalube suke yi a cikin duhu, ake ta bankawa Iman ruwa da allurai, aka yi hoton zuciya, amma zuciyarta lafiya ƙalau.
Hajiya Sauda ce zaune a turakar turaki, ta dube shi ta ce "Ranka ya daɗe, ni baka gaya mini ina ku ka je ba ranar juma'a, ka zo mana da abubuwa na ciye-ciye, haryanzu baka ce mini komai ba"
Turaki da yake cin ayaba, ya ce "Dama dole ne duk in mu ka je sai an gaya miki?"
"A'a tambaya dai kawai na yi, na zaci wani abun alkhairin ne ya samu ai"
Ya ce "Eh, kusan haka, abun farincikin ne"
"Kamar me fa?"
"Aure muka je nemawa takawa, na gidan galadima"
"A'a, neman aure kuma, yaushe Aishan ta rasu, da har za a nema masa wani auren?"
Turaki ya ce "Addini ya bashi dama, Aisha ta kai watanni huɗu da rasuwa babu laifi a ciki dan yayi wani auren".
Danne fushinta ta yi, ta ce "Amma wa zai aura haka da na ji ka ce, kun je nema masa aure".
"Eh, wata yarinya ce, ƴar mutunci iyayenta masu dattaku sosai, su suka bamu wannan kayan duk da na zo da su".
Cikin son bugun ciki ta ce "Kuma ƴar waye? Ai na zata iman zaku aura masa, ta maye gurbin aisha"
"To, idan lokaci yayi zaku ga koma wacece, koma itan ce, ko ba ita bace ba"
"Amma dai Allah ya baka yawan rai, ni na rasa dalilin da ya sanya, ka fi fifita ƴaƴan wasu a kan naka, na rasa me muka yi maka da ni da yarana. Tsakani da Allah duk yadda Samha take ƙaunar yaron nan a wannan karon ba zaku yi mata adalci ta maye gurbin aisha ba, taƙi auren kowa ta dage sai shi, amma ka yi burus, ku ke je waje nema masa auren wata?"
Turaki ya ce "Ban fifita kowa a kan ƴaƴana ba, sai dai son da nake yi wa ƴaƴana, ba zai sanya na zaɓi son zuciya ba. Ba zai yiwu sun kawo wadda suke so ya aura na wuce masa gaba a matsayina na ubansa, na yi amfani da ƙarfin ikona, na ce sai ya auri ƴa ta ba, ki sani zan iya tursasa shi ya auri ƴa ta, amma ba zan iya tursasa shi ya so ta ya kyautata mata ba, na yi mata nasiha tun ba yau ba, a kan ta haƙura da shi, ta yi addu'a ta nemi wani ta aura, har haɗata da na yi da ɗan gidan madaki, Muhammad Sani, ya ce ya na sonta ta watsa mini ƙasa a ido, sai yanzu kuma ku ce ga abun da ku ke so sai na yi, ba zai yiwu ba, kuma ku yi haƙuri, da Samha da takawa duk ƴaƴana ne, ba wanda zan yi wa dole a kan wani abu da yake son zuciya"
Ba ƙaramin ƙuluwa ta yi ba, da jin maganganun turaki, ba ta sake cewa komai ba, ta tashi ta bar ɗakin.
Zainab ce ta shiga falon mama, in da Samha ke zaune tana kallon tv, hannunta riƙe da wayarta, ta zauna tana faɗin "Ohh God, ita wannan yarinyar ita kenan kullum cikin ciwo?"
Samha ta kalleta ta ce "Wacece?"
"A status ɗin Nusaiba na gani, wai iman babu lafiya, ba ta san waye a kanta ba ma, shikenan ita giwa kullum tana hanyar asibiti saboda ƴar tsintuwa, dama ta mutu ko sa huta gaba ɗaya"
Samha ta yi ajiyar zuciya, tare da ji a Jikinta, aikin ta ya fara aiki kenan.
Fuuu mama ta shigo falon,. Kamar mai tafiya a kan iska.
Duk suka bita da kallo, suna tambayar ko lafiya?.
"Hmm, ni da turaki mana, ya gaggaya mini magana a kan kawai na ce, meyasa bai saka adam ya auri Samha ba, wai nema masa aure suka je yi ranar juma'a.
Ƙuuuu Cikin Samha ya bayar, wani irin fargaba da faɗuwar gaba ya kamata, neman aure aka je yi wa Adam?.
"To kin ji, a wannan karon dai kya haƙura ko?" Zee ta yi maganar tana kallon Samha.
"Mama, neman aure kuma? Ba iman za su bashi ba?".
"Bana tunanin ita ce, wata ce daban gaskiya, tun da ya ce sun je nema masa ne, da ita ce ai ba sai sun yi haka ba"
Wani irin gumi ne ya shiga ratsowa daga cinyar Samha, gaba ɗaya kanta ya toshe, saboda jin abun a bazata an shammaceta da yawa.
"Amma mama wacece haka?"
"Oho ina na sani, bai gaya mini ba, ni takaici ma bai barni na san wacece ɗin ba".
Cikin hanzari, ta tashi tafi ɗakinta zuciyarta na yi mata zafi, tsabar wulaƙanci a waje ma ake je aka nema masa wata bayan ita gata a zaune an san tana san shi
Zama ta yi daɓas a gefen gado, zuciyarta na ƙuna, wannan shine baba na ɗaka gemu na waje, amma mayar da ita wata sako tumaki ɓallo jakai.
"Tun da naga aikin malamin nan yana aiki, Adam da ni ka ke zancen, wallahi kana ji kana gani sai an mayar da kai mace, ba zaka amfani kowacce mace a rayuwar aure ba, sai dai ta kalleka ka kalleta, amma kai da sake kwamciya da wata matar, har abada sai dai idan ni ka aura, zaka gane baka da wayo".
***
Mai sunan baba yana tsaye a kitchen, yana kwashe abinci, kasancewar mama bata nan, babu kowa a gidan, mama tana kasuwa, sai shi da ya dawo gidan yanzu, yayi saurin ɗora girki, dan ya san tsaf rumaisa zata dawo a kowane lokaci idan ba a gama abinci ba, idan ta din ga kwanciya tana kuka, sai ta saka ya daketa. Ga lokaci ya riga ya ja.
Mama ce ta kira shi a waya, ya ɗaga yayi sallama.
Ta amsa sannan ta ce "Babana kana ina ne?".
"Na dawo gida, na ɗora girki ne".
"Yauwwa, dan Allah idan rumaisa ta dawo, ka saka ta yi wanka ta yi salla, ka tafi da ita asibitin da ta kwanta, an kwantar da iman ku wakilceni ku dubata, yanzu muka yi waya da hajiyar, wai an kaita asibiti ba ta san waye a kanta ba, ni kuma bana tunanin zan dawo da wuri".
"Tom" ya faɗa a taƙaice ya ajiye wayar, ya cigaba da aikinsa.
"Assalamu alaikum" rumaisa ta yi sallama, sai dai kan ya amsa ta fara cewa "Wani gardin ne yake yi mana abinci yau, Allah ya sa yayi daɗi, na ji ƙamshin miyar har tsakiyar kaina, Allah yasa ko shinkafa an gama, in fara rage hanya, dan yunwar da nake ji ba a cewa komai" ta ji shiru ba a amsa ba, ta nufi kitchen ɗin tana cewa "Baƙon aljani muka yi ko kurma, da nake magana aka shareni".
Tozali da tayi da shi ne, ya sa ta ci wani wawan burki, rabon da yayi girki har ta manta, dan haka ba ta kawo shi ne ba.
"Yi haƙuri, ban san kai ne ba, dan Allah ka yi haƙuri"
Kifi yake sakawa a miyar, ba tare da ya kalleta ba, sum-sum ta bar wurin ta koma ɗaki ta kwanta.
Mai sunan baba bai tashi gaya mata saƙon mama ba, sai da ta fara shirin islamiyya, ya ce "Na gaya wa shugaban makarantarku ba zaki shiga ba yau, zamu je dubiya"
"Ina?" Ta tambayeshi tana kallonsa, sai dai ta manta shi mai sunan baba, idan ya ce ayi kawai ayi, ba tare da tambayoyi ba.
Har suka tafi dubiyar, mamaki take yi, waye babu lafiya, ta lissafa wannan ta hango wancan, amma ta kasa gano waye babu lafiya.
Sai dai ba ta ƙara sarewa da al'amarin ba, sai da ta gansu a asibitin da aka kwnatar da ita.
Lambar mama ya kira, ya tambayeta wani ɗakin ne, ta sanar