Showing 24001 words to 27000 words out of 199108 words
kada ya ce "Ni ki ke gayawa haka?".
Fitowa ta yi zata wuce shi, ta tafi, amma ya sanya ƙafarsa ya kwashe na rumaisa, a take kuwa ta faɗi ƙasa, manjan hannunta ya fashe, ta datse goshi.
Idan da abun da rumaisa ta tsana, bai wuce ganin jini a jikinta ba, jiki na rawa ta tashi ta kalleshi, ya kalleta ya ce "Sai na tsarge hanjinki da wuƙa, na kashe banza ni zaki nemi ki zaga wata jagwal da ke"
Cikin hanzari malam lawan da sauran mutane suka fara lallaɓa ɗan kada suna bashi haƙuri, rumaisa ta shiga cikin shagon, ta dumbuzo ƙwan da ke kan teburi, ta fito ta shiga jifan ɗan kada da shi.
Rikicewa malam lawan yayi, dan yanzu aka sauke ƙwan ko lissafawa ba ayi ba, ji ta yi zuciyarta na tafasa, ta juya da gudu ta tafi gida.
Aliyu na ganinta ya ƙare mata kallo ya ce "Meye haka?" Cikin kuka ta kwashe komai ta gaya masa, nan da nan ransa ya ɓaci ya ce "Mu je" mama na banɗaki tana gyaran murya, amma Aliyu ya ja rumaisa suka yi waje.
A ƙofar shagon suka tarar da ɗan kada, har ya karɓi sigarinsa ya fara sha, malam lawan kuma yana ta masifa, yana sai ya je gidansu rumaisa an biya shi, shi kansa ɗan kada yayi alwashin sai ya kashe rumaisa, saboda wulaƙancin da ta yi masa,ta din ga jifansa da ƙwai.
Idan da abun da samarin gidan maman suka tsana, bai wuce taɓa Wannan tilon yarinyar ba, dan haka a zafafe Aliyu ya ƙarasa, yana zuwa ba tambayar ba'asi ya ci kwalar ɗan kada, ya shiga kifa masa mari.
Kokawa ta kacame, ga ɗan kada a buge, dan haka ya kasa wani abun arziki, Aliyu ya din ga haɗa masa naushi.
Da ƙyar mutane suka shiga tsakani, ana rirriƙe ɗan kada yana rantsuwa sai ya kashe Aliyu.
Mama kuwa a gigice ta fito daga banɗaki, jin wanda rumaisa ta tsokano, dan babu wanda bai san yadda ya addabi unguwarsu ba.
Mama ta kira mai sunan baba a waya, ta ce masa duk abun da yake ya bari ya tafi shagon malam lawan, Aliyu ya fita ba ta san mai zai aikata ba.
Aliyu kuwa ya kalli ɗan kada ya ce "Jinina da na zuriyar gidanmu ya fi ƙarfin mutum irinka, duk wani hauka da iskanci da kake ji da shi a unguwar nan ƙyaleka aka yi, ƙanwata ta fi ƙarfin wawan mutum irinka su cutar da ita"
Malam lawan ya ce "Wai Meye haka ne Aliyu, ina nan aka sace ƙanwar ta ku me ku ka yi, sai yanzu zaku haddasa mana masifa a cikin unguwa"
"Wallahi malam lawan, duk shekarun da muka yi tare a unguwar nan, idan ka taɓa rumaisa sai na tuɓe na yi maka bugun sakwara, saceta kuma da aka yi wannan ƙaddararta ce, ba yadda muka iya"
Rumaisa ta riƙe hannun Aliyu ta ce "Yaya mu tafi gida"
Da ƙyar rumaisa ta riƙe hannunsa, suka juya suka fara tafiya, sai dai ana sakin mai kada, ya zare wuƙa ya nufi Aliyu da ita gadan-gadan yana ihu.
Ihu rumaisa ta saka ganin wuƙa tsirarata, wuƙa ba ta wasa ba an nufo yaya Aliyunta da ita, wanda ba da tabbacin ita aka nufo ko shi. Aliyu ya hankaɗeta, ya kuma riƙe mai kada suka hau kokawa ga wuƙa tsirarta.
Aliyu ya danne mai kada a ƙasa, ya ɗau wuƙar ya ce sai ya yankashi da ita a wurin.
Nan aka din ga kokowa da Aliyu, aka kasa ƙwace wuƙa.
Rumaisa ta ce "Yaya Aliyu kar ka yi kisan kai, amma dai ka yi masa dukan tsiya".
Cikin takunsa na isa da taƙama, ya din ga ture dandazon mutane, ya ƙarasa in da Aliyu yake kan mai kada ana fama da shi, ya riƙe hannun Aliyu mai wuƙar ya murɗa, ya jefar da wuƙar, sannan ya ɗago shi daga kan mai kada ya tsayar da shi a kan ƙafafuwan sa ya Kalleshi ya ce "Meya haka? Shaye-shayen kai ma ka fara ne?" Ya kalli rumaisa ya ce "Duk saboda ke ko? Sai ku wuce mu tafi ai".
Daga kwance mai kada ya ce "Na rantse da girman Allah, idan har ina yawo kana yawo a unguwar nan, sai na kasheka na kashe matsiyaciyar yarinyar nan, na ga uban waye gatanku"
Aliyu ya sake tunzura, jijiyoyin kansa suka kumbura, mai sunan baba ya kalli mai kada ya ce "Idan kana zubar da jini a unguwar nan kai da yaranka, ana tsoronku, kar ka ratso ta gidanmu, wallahi duk wanda ka zubarwa da jini in dai ɗan gidanmu ne, kaima sai na zubar da naka, ka kiyaye"
Ya riƙe rigar Aliyu, hannu ɗaya ya tankaɗa ƙeyar rumaisa zuwa gida.
Mutane wasu har da shewa, abun ya burgesu, kaf unguwar nan babu gidan da suke da haɗin kai da nunawa juna soyayya kamar gidansu rumaisa.
A gigice mama ta tashi da suka shigo, ta ga jikin Aliyu duk ƙasa, rumaisa kuma da fasashshen goshi, duk da ba ta zubar da jini da yawa ba.
"Mai sunan baba, maiyafaru?"
"Kar ki damu, ba abun da ya faru"
Mama ta riƙe Aliyu da yake huci ta ce "Ina fatan dai ba abun da ya sameka ko?" Ya girgiza mata kai alamar a'a.
Mama ta ce "Duk saboda wannan jairar yarinyar ne, da ba zata bari a zauna lafiya ba? Ina ke ina faɗa da gagararren ɗan daba saboda ɗorawa kai bala'i" Mama ta yi maganar tana ƙoƙarin kai mata duka, amma mai sunan baba ya tare ya ce "Ki ƙyaleta please, baki ga ta ji rauni a goshi ba, ki yi haƙuri"
Mai sunan baba ya sakata a gaba, ya kai ta chemist, aka duba goshin, Allah ya taimaketa babu ɗinki, suka dawo gida.
Mama ta kai ƙarshen ƙulewa da rumaisa yau, ta din ga yi wa ƴan mazan faɗa a kan biye mata wurin tare mata faɗa.
Kasancewar maƙwabcin su rumaisa malam shamsu, yana cikin ƴan kwamitin unguwa, shi ne mataimakin ƴan ƙato da gora, yana dawowa aka sanar masa da abun da ya faru a unguwar, nan da ya ji ya samu damar rama wulaƙancin da rumaisa da yayyenta suka yi masa, kai tsaye ya je ya sanar da ƴan sanda abun da ya faru.
Mama har ta bar sallahun a rufe gida, ƴan sanda suka yi sallama, suka ce sun zo tafiya da Aliyu.
Duk yadda aka so sasanta lamarin, abu ya gagara, ga Abubakar ya koma makaranta, Mai sunan baba da Usman suka bi bayansu, amma har wurin sha ɗayan dare, ƴan sanda suka ƙi bayar da Aliyu, ƙarshe ma suka sanar da su cewa sashin kula da manyan laifuka na bamfai zasu turasu, tun da Aliyu ya yi iƙrarin kisan kai.
Haka mai sunan baba suka koma gida, jiki a sanyaye, mama ta rasa in da zata saka kanta saboda tsananin damuwa da tashin hankali, tare da ɗora zargin komai a kan rumaisa.
Adam kuwa bayan ya kammala cin abinci, ya tashi ya yi wa ammi sallama, ammi ta ce "Yauwwa, na ce ba" Adam ya ɗan tsaya yana kallon ammi.
"Dan Allah gobe in Allah ya kaimu, tun da da wuri zaka fita, kuma ka ce zaka je gidan gona, dama unguwar su matarka ne, zan baka saƙo ka kai wa rumaisa"
Adam ya kalli Ammi ya ce "Matata kuma? Kuma ni zan kai ssƙon?"
"Ban isa ba kenan?"
Ya ce "A'a tare da sunkuyar da kai"
"A yanzu kana da wata matar da ta wuce rumaisa ne? Zaka kai mata saƙo, kallonka kawai nake yi, har na je wurin turaki na dawo ba ka tambayi yaya muka yi ba, kuma ya zama dole ka din ga zuwa wurinta, saboda ta saki jiki da kai, kuma ka daina yi mata wannan muzuran"
Adam ya jinjina kai yana wasa da yastun hannunsa.
"Je ka, da safe in Allah ya kaimu kan ka wuce, ka biyo"
Bai ce komai ba ya fice.
Ayshercool.
Chat me on what's app, to subscribes yours
08081012143
*PAID BOOK NE, ₦500 NE VIA 0009450228, AISHA ADAM JAIZ BANK SAI SHAIDAR BIYA TA, 08081012143*
Gaba ɗaya ji yake duk wani girma da mutuncinsa sun zube, kamar shi ace wai zai je wurin wata ƴar yayyiyar yarinya yayi zance da ita, wai zai aureta, ko aurensa na fari aisha ta kammala deegree ya aureta, wannan shi ba ya tunanin ko primary ma ta gama.
Mama kuwa kwana ta yi ba barci, sai addu'a kawai da take yi, ji take tamkar ta rufe rumaisan da duka, dan bayan gama ƴan koke-kokenta tuntsirewa ta yi ta hau bacci.
Mama ta kalleta ta girgiza kai ta ce "Allah ya shiryeki, ya ganar da ke"
Da asubar fari, bayan rumaisa ta idar salla, ta tafi ɗakin su mai sunan baba ta yi sallama, suka amsa mata.
Ta leƙa ta ce "Yaya usy jiya kun dawo da yaya aliyun?"
Abdallah ya ce "Wuce ki bawa mutane wuri, duk ba ke ki ka janyo ba, karfa kawai"
Mai sunan baba ya kalli Abdallah ya ce "Kar ka kuma gaya mata haka, bai dawo ba a can ya kwana, duk saboda ke, gaba idan ki ka sake, ke zan kai musu in karɓo shi, dan mun fi son sa a kan ki, mara kai kawai"
Sumi-sumi ta juyo za ta fito, ta fuskanci kowa haushinta yake ji yau.
Usman ya ce "Wallahi yau da na ga malam shamsun nan a masallacin asuba, ji na yi kamar na ɗaga shi na wurga shi cikin kwalbati, shi ne babban munafukin da ya je ya kai wa ƴan sanda"
Mai sunan baba ya ce "Ba ruwanka da shi, ku bari mu kashe wannan case ɗin tukuna".
Abdallah ya ce "Ni malam lawan mai shago na kusa kifawa mari, ya biyo ni wai rumaisa ta yi masa asarar ƙwai cret huɗu, wai in zo in biya, na ce masa sai dai mu yi kokowa ya ɗiba, gaba ɗaya mutane fuska biyu ce da su".
Rumaisa da take tsaye tana jin su da sauri ta ce "Wallahi ko kret ɗaya bai yi ba, bai fi guda shida ba fa"
"Au laɓe ki ke yi mana ko?" Abdallah ya faɗa yana nemo abun duka.
Da gudu ta shige ɗakin mama, sai dai irin kallon da maman ta yi mata, ya sanya ta rasa in da zata saka ranta.
Haka ta tsuguna ta takure, da duku-dukun mama ta shiga kitchen, ta girka abinci, gari na yin haske, ta ce lallai mai sunan baba ya taso su tafi station ɗin.
Mai sunan baba ya ce "Mama, idan kin je wurin nan babu abun da zaki iya a kai, ki bari zan je ni da Usman"
Mama ta ce "Ni dai ka ƙyaleni na je na ga a yaya ya kwana?"
"Lafiya ƙalau ya kwana, kuma in sha Allah zamu dawo miki da shi, ki yi haƙuri" da ƙyar mama ta yadda, ta basu abincin suka tafi.
Rumaisa ta ce ita ba zata tafi makaranta ba, sai yaya Aliyu ya dawo.
Mama ta ce "Aikuwa ba ki isa ba, sai kin shirya kin tafi, wataƙila kan ki dawo na huce, dan da na kalleki haushi nake ji, haka kurum saboda ke kin saka an kulle mini ɗa, mara jin magana" shiru rumaisa ta yi tana kallon mama, kenan yanzu mama ta daina son ta?.
Jiki a sanyaye ta shirya, mama ta hanata kuɗin makaranta, ba babban abun da ya sake ƙular da mama, irin yadda rumaisan ta zauna ta naɗi abincinta, kamar abun bai dameta ba sosai.
Haka ta tafi makaranta, tana tunani kala-kala, amma har ga Allah abun ya dameta.
Kamar yadda ammi ta buƙata, da safe Adam ya je gidan, a lokacin su iman duk sun tafi makaranta.
Ya ɗau sabir yana yi masa wasa, sai dai ƙememe yaron nan yaƙi dariya, sai bin sa da yake da kallo.
Ammi ta fito suka gaisa, ta ce "Yanzu wurin aikin zaka tafi?"
"Eh, na biyo na karɓi saƙon ne".
Ammi ta ce "To, tun da baka tambayeni ba, ni bari na gaya maka yadda muka yi da turaki".
Ya sunkuyar da kai yana wasa da hannun sabir.
"Mun tattauna da shi, ya ce mini in bari ya dawo daga umara, zai yi magana da su wambai, dan na san akwai ƙalubale, tun da rumaisa ba jinin sarauta ba ce, ko ƴar wani sananne ba, dan haka zai yi muku Addu'a a can, da ya dawo aka daidaita kuɗin aure za'a kai, bayan salla idan Allah ya kaimu za ayi"
"To, Allah ya wuce mana gaba".
"Amin, wai da ce mini yayi, Jamil ya ce ko za'a maye gurbin Fulani da samha, ni dai ban ce komai ba na shigar da maganar rumaisa, dan ita ta fi kwanta mini"
Adam har mamakin ƙaunar da Ammi take yi wa rumaisa yake yi, tabbas da so samu ne, Samha ta maye gurbin aisha, dan ita ta isa mace da hankalinta da iliminta, kuma Samha ta daɗe tana son shi, ya san hakan, amma ammi ta dage a kan wannan ƴar yayyiyar Yarinyar.
Ya numfasa ya ce "Allah ya kyauta"
Ammi ta miƙa masa leda ta ce "Gashi nan, sabuwar jakar makaranta ce, da litattafai da turare, ka kai mata ka ce ina gaisheta"
Adam ba yadda ya iya, ya karɓa ya amsa da to.
Ya fita riƙe da ledar kayan a hannunsa, ya san zuwansa wurin Yarinyar nan, ba abun da zai ƙara masa sai raini.
A harabar gidan ya tarar da Mahmud, tun da ya dawo yana ganin shige da ficen motocinsa, amma basu ta ɓa haɗuwa ba sai yau, yana tsaye a wurin parking space ɗin Adam, kusa da in da zai ɗau motarsa.
Adam bai kula shi ba, shi ma bai kula shi ba, ya je ya buɗe motarsa ya kunna, ya ɗan jima a ciki, amma ya ga Mahmud ba shi da niyyar matsawa, ya din ga danna horn, amma Mahmud ya yi burus, ba tare da wani ɓata lokaci ba Adam ya bawa motar wuta, yayi reverse, ai kuwa ya buge Mahmud, ko kaɗan Mahmud bai kawo Adam zai yi masa haka ba, kan ya ankara ya ga Adam yana ƙoƙarin bi ta kansa, ba shiri ya mirgina, Adam ya ja motar da gudu ya bar gidan.
Ma'aikatan gidan suka yo kan Mahmud suna yi masa sannu, suna ƙoƙarin ɗaga shi, sai dai ciki gwasalewa ya nuna musu shi zai iya tashi, sai dai abu kamar wasa, da ya miƙe ɗin ƙafa taƙi takuwa.
***
Rumaisa tana hanya tana addu'a, Allah ya sanya yaya Aliyu ya dawo, Allah ya sa komai ya wuce, sai dai ko da ta iso gida, ta tarar da Usman da mai sunan baba amma babu Aliyu. Cikin damuwa ta ce "Yaya usy ina yaya Aliyun yake?"
"Ke, case ɗin nan fa maƙabcinmu malam shamsu, ya yi uwa yayi makarɓiya yana ta kambama abun, gaba ɗaya ma sun ƙi saurarmu a station ɗin, wai sai DPO ya zo, DPO na zaci wanda ku ka yi case ɗin nan ne kwanaki, ashe an canza wani, sun kafi wai sai an je state cid tun da aka yi iƙrarin kisan kai".
Rumaisa ta ce "Na shiga uku, ba fa yaya Aliyu ne ya ce zai kashe shi ba, shi ne ya ce zai kashe shi".
"Koma menene ba ke ki ka janyo ba rumaisa, duk abun da mutum zai gaya miki sai dai ya shiga ta kunnen dama ya fita ta hagu, saboda wautarki kin jefa ɗan uwanki a wahala"
Usman ya ce "Dan Allah mama ki daina faɗar haka, ƙaddara ce"
A fisace mama ta ce "Rufe mini baki, ko na make ka, ai duk gidan nan babu mai koya mata rashin ji irin ka"
"Allah ya baki haƙuri, ba ri mu yi salla mu koma".
Adam kuwa ko kaɗan bai ji babu daɗi ba abun da ya yi wa Mahmud, dan a lokacin nan yadda ya hasala, da ya samu dama sai ya taka shi da mota uban kowa ya huta, ya sauke masa wannan girman kan da rashin mutuncin da yake ji da shi.
A haka yake wurin aiki, ya gama abun da yake yi ya fito, yana da niyyar zuwa gidan gona, sai dai dole ya je ya kai wannan saƙon kan mama ta ɓata ranta.
Mahmud kuwa ƙarshe, sai ka shi sashin Mummy aka yi, a rikice take tambayarsu maiya same shi, suka gaya mata Adam ne ya buge shi da mota.
Nan da nan ta hau ta fara bala'i "Wannan wane irin wulaƙanci ne, anya Adam bai fara shaye-shaye ba? Ko dai haryanzu haukar ce a kansa, tayaya zai taka ka da mota? Wallahi ba zan lamunta ba sai na ɗau mataki"
Mahmud ya ɗan cije lips ɗin sa ya ce "Ki rabu da shi zan rama ne, yanzu ni dai ƙafata zafi take yi ki yi wani abu a kai"
"Wallahi ba zan ƙyale ba, Fauziyya ɗauko key mu tafi asibiti kawai, Allah ya sa ba wani abun ne ya samu ƙafar ba"
"Mummy, dan Allah ki rabu da shi, am just testing his anger, ashe yana nan a yadda yake bai canza ba" yayi maganar cikin zolayar Mummy.
Cikin fushi ta ce "Ka rufe mini baki, this is an serious issue, ba zan bari ba" ganin yadda ta ɗau zafi ya sanya shi yin shiru yana kallon ƙafarsa.
A ƙofar gidan su rumaisa, Adam ne a tsaye, yake kiran wayar Aliyu, amma shiru bai ɗauka ba, wayarma a rufe take, ya kira har ya gaji, ya aika yaro ya ce ace ana sallama.
Usman ne ya fito, domin duba waye, ya tarar da Adam a tsaye, ya ƙarasa yana wani basarwa, suka gaisa sama-sama.
Adam ya ce "Aliyu nake nema, na kira wayarsa ba ta shiga"
Usman ya kalleshi, ya lura ta su ta zo ɗaya da Aliyu sosai.
Ya ce "Ya ɗan haɗu da tsautsayi ne" ya bashi amsa a taƙaice.
"Wane irin tsautsayi kuma?"
"Eh waccan yarinyar ce ta tsokano ɗan daba, ya je tare mata, kuma dama ta yi rigima da maƙwabta, shi ne mai gidan ya saka aka kama su, tun jiya muke zuwa police station, an ƙi sakinsa, yanzu ma komawa zamu yi"
Mamaki ne ya sha kan Adam, duk rumaisan ita kaɗai ta janyo wannan tarzomar.
Cikin mamaki ya ce "Wai duk ita wannan Yarinyar ce ta yi faɗa da ɗan daban?"
Usman yayi wani irin murmushi ya ce "Wannan ta wuce tunaninka, ka san ƙanwar maza ce, bamu raineta da tsoro ba"
Adam har cikin ransa ya ji babu daɗi kama Aliyu da aka yi, ya ji da rumaisan aka kama ita da ta janyo abun.
Ya ce "Ko zan iya magana da maman?"
Usman ya ce "Ok, bari na yi mata magana".
Bayan an yi wa Adam iso ya shiga gidan, ya tarar