Showing 27001 words to 30000 words out of 138998 words

Chapter 10 - Rai Biyu Book 1 Complete Hausa Novel

05 Feb 2025

731

babu wanda zai ji

“Ki yi haƙuri da abunda ya faru ranar nan, Wallahi ba da ke nake ba da mai Napep ɗin daya ɗauko ki na ke”

Ji na yi kamar ace akwai wuƙa kusa da ni na daɓa masa a ƙirji, wani ɗogon tsaki naja wanda ya jawo hankalin duk wanda ke shagon zuwa garemu, na ɗauki canjina na fice zuciyata na bugawa kamar zata fito saboda ɓacin rai.


NOT EDITED ⚠️

SHARE, COMMENT, VOTE.
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


1⃣7⃣

‘Ba a banza ya baki haƙuri ba, taya zai baki haƙuri mutumen da ba ya ganin kowa da mutuncin, ba dake yake ba kika mareshi sai kuma yanzu ya zo ya baki haƙuri, lallai akwai abunda yake nufi da ke’

Shine abunda na ke ta saƙawa a zuciyata, a zahiri kuma sai nan nemin tsarin Allah akansa.

“Allah ka min tsari da sherinsa”

Har na iso gida ina ta saƙe-saƙen abubuwa biyu a raina, maganar zubar da cikin Habiba da kuma haƙurin da Mustapha ya ba ni. Na samu kaina da faɗuwar gaba sakamakon hango Bilal da na yi a tsaye ƙofar gidanmu, cikin rashin kuzari na ƙarasa daman can babu kuzarin a tare da ni. Lokacin da na ƙarasa kusa da ƙofar gidanmu sai na tsaya dai-dai inda yake tsaye ina masa sallama.

“Assalamu alaikum”

A maimakon ya amsa min sai kawai ya ɗaga idonsa dake ƙasa ya kalleni.

“Miya hana ki zuwa aiki yau?”

Ajiyar zuciya na fara saukewa sannan na haɗe yawun da ke bakina na fara magana a daƙishe.

“Bana jindaɗi ne”

“Miyasa baki kira kin sanar min ba?”

Yanzu kan bansan mi zan ƙara ce masa ba, shirun da na yi ne ya bashi damar fassara ni da abunda yake hasashe.

“Saboda kin yi zaton na ganki ko? Wallahi Nawancy ban ganki babu Hijab ba, lokacin sa kike aikinki ina can ina nawa aikin, ba zan miki alƙawari ba amman zan yi ƙoƙari na kawar da idona daga kallonki idan kina aiki”

“Wallahi ba saboda haka ba ne Bilal, kawai akwai abunda ya ke damuna”

“Ko zan iya sanin minene?”

“Sanin ba shi da amfani, barin wannan sirrin a cikina zai fi min amfani”

Magana nake kamar zan fara kuka saboda damuwar da ke raina. Shi kansa ya fahimci haka saboda be saba ganina cikin irin wannan yanayin ba.

“Allah ya yaye miki damuwarki Nawancy, Allah ya zama gatanki, ƴa shiga dukan lamarinki ya tsareki daga dukan sheri, ya jiɓɓanci lamarinki, kada Allah ya barki da kanki”

“Amin”

Na amsa hawaye na bin fuskata. Ya lumshe ido ya buɗe.

“Ki shiga ciki, ni zan wuce, daman na rubuta wasiƙa a gurin aiki amadadakin cewar baki da lafiya”

“Zan shigo gobe”

Na faɗa ina share hawayen idona.

“Karki dakurawa kan ki, and if you need someone to talk to i'm here”

“Thank you Bilal you have encouraged me every time, Without you I don't think I could ever be fine”

Na faɗa kuka na cin ƙarfina sosai. Har ga Allah ina jindaɗin zama da Bilal yana ƙarfafan min guiwa, yana damuwa da damuwata ko kaɗan baya son ganin ɓacin raina.

“Get some rest”

Na gyaɗa masa kai sannan na shiga cikin gida ina jin kamar na rafke na faɗi. Ɗakinmu na nufa jiki babu ƙwari, sai na samu Habiba a zaune tare da Inna kwanon ruwa na gaban Habiba jiƙe da magani. Na zauna nima ina buɗe ledar maganin.

“Gashi ya ce wannan uku zaki sha, wannan kuma biyu biyu sai wannan shi ma uku”

Na faɗa mata yadda ya rubuta a jikin kwalin maganin, sauran kuma duka na ɗiba ne, wasu biyu wasu huɗu.

“Tau ki bari har a jima ki sha, yanzu na jiƙa mata tagargade da gishiri ta sha”

Cewar Inna ni kuma na kalleta cike da mamaki.

“Tagargade da gishiri kuma Inna?”

“Ee yana yanke mara, wai ko za a samu cikin ya zube”

Wani dogon numfashi naja na sauke, na san ko na yi magana ba lallai ne Inna ta fahimta ba, idan har kuma nasa ta bar cikin a can gaba wani abun ƴa faru zata ɗora laifin a kaina.

“Bani maganin na sha ko zan samu sauƙin zazzaɓin nan”

Habiba ta faɗa tana miƙo min hannu. Tashi na yi na ɗebo mata ruwa na miƙa mata maganin ta sha, sannan na je na yi alwala har na yi sallah tunani ne a raina.
  A tare da ita muka kwana a ɗakin, duk bayan minti biyu zuwa uku Inna sai ya miƙa mata tagargaden ta sha, haka ta kwana wulle-wulle sai abun ya zame mata biyu ga zazzaɓi ga ciwon ciki. Ita ke ciwon amman ni na kwana kuka ina jin zafin ciwon kamar a jikina ya ke, can kusan asuba Allah ya bata sauƙi har ta samu bachi.

Ni kuma na tashi da ciwon kai na yi alwala na yi sallah, ina zaune saman carpet ɗin ina karatun ƙur'ane har rana ta soma huduwa.  Tashi na yi cikin ƙanƙanen lokaci na shirya na aika Sakina ta siyo kunu suka sha domin ni ko ruwa bana iya kaiwa a bakina.
Haka na kama hanya zuwa gurin aiki ba tare da na saka komai a cikina ba, duk kuwa da kasancewar ana cewa fita ba a karya ba bashi da kyau. Har na isa gurin aikin jina nake kamar ba ni ba, sai nake jin kamar ba ni nake motsa jikina ba, wata ƙila saboda nauyin da na tashi yana min yau ne. As usual sai da nayi duk abunda ya dace tun daga kan rubuta suna da time na yi komai sannan na shiga cikin kamfanin na soma aikina.

Ina daf da ƙarewa a ɗaki na ƙarshe, Amina ta shigo tana min magana kaɗan-kaɗan.

“Ƙawata ana kiranki, wai kin yi mopping da ruwa da yawa, matar nan sai masifa take”

“Wacece?”

“Wata mai'aiki a nan ce amman ita babba ce dan har office tana da shi”

Ba musu na bita muka tafi inda ta ce ana kirana ɗin wato a ɗakin dana fara mopping, abun mamaki sai na samu Zinatu tsaye a ɗakin tana sanye da suit da baƙin gilashi hannunta riƙe da wani ƙaramin akwati.

“Nawwara ke kika yi mopping ɗin gurin nan?”

Na ɗaga mata kai alamar Ee.

“Amman fisabilillahi haka ake mopping? Wai miyasa idan zaku yi abu baku yinsa tsakani da Allah, yanzu idan gidanku ne haka zaki yi, aikin nan fa biyanku za'ayi amman kuka abu da kissa kamar kyauta kuke yinsa haka sam be dace ba, yau da safen nan meeting zamu yi da manyan mutane yanzu idan suka shigo suka duba yadda kamfanin nan yake ai sai kuja mana ɓacin suna”

Yadda ta runtse ido take min masifa kamar bata san wacece ni ba, tabbas na bar ruwa saboda ga gurin nan har yanzu be bushe ba, sai dai ba da gangan na yi haka ba, na yi mopping ɗin ne a lokacin da hankalina baya gurin, sai dai ban jidaɗin yadda take ɗaga min murya ba kamar wata uwata.

“Ki yi haƙuri zan kiyaye a gaba”

Na faɗa abunda yake har a zuciyata shine, ƙawata sai dai a nan kuma ita ce babba a gurin aikina, kuma dole ne na bita idan har ina son cigaba da aikin.

“Better”

Ta furta tana ƙoƙorin juyawa sai ga wani mutun ya shigo shima cikin shigar suit sai dai na shi blue ne tsaɓanin nata da suke baƙaƙe. Har ya buɗe baki ya yi magana sai kuma ya fasa sakamakon idonsa da suka sauka a kaina. Bakinsa a sake yake kallona fuskaraa na nuna alamun mamaki, hakan yasa kunya ta rufe ni domin tun da na shigo kamfanin a yau ban samu kaina da jin kunyar tufafin da ke jikina saboda damuwata ta mantar da ni komai.
Sai dai kallon da yake min ya ya karantar da ni da akwai wani abu, wata ƙila ya daba ganina da Hijabi yau kuma ya gan ni babu Hijabi ko kuma dai yana mamakin yadda na ke aikin ne, tau tsaya ma wai ni ina na san shi balle na yi tunanin haka ni dai fuskarsa bata min kama da wanda na sani ba, wata ƙila dai shi ya sanni ne kai sai ka ce wata ƴar film ko mawaƙiya.

Ni kaɗai na ke ta tsaƙe-tsaƙe na domin kuwa Zinatu ta daɗe da ficewa ɗakin, yanzu daga ni sai shi ne sai kuma Amina.

“Newcomer?”

Ya tambaya ni kuma sai na gyaɗa masa kai.

“Your Name?”

Ya sake tambaya.

“Nawwara”

Ya rausayar da kansa sannan ya sake kallon na from head to toe sai ya juya ya fice.

“Shine mai kamfanin?”

Ma tambayi Amina bayan ya fice, sai ta zaro ido.

“Tab mai kamfanin zai tsaya tambayar sunanki, ai yana zuwa gurin nan zai ɗaukeki mari sai kin manta hanyar garinku”

“Saboda me?”

“Saboda wannan kuskuren da kika yi”

Na taɓe baki.

“Ni kan ba zan yarda ya wulaƙanta ni ba, saboda kawai ina aiki ƙarƙashinsa”

“Aiko idan baki ɗauki wulaƙanci ba, baki shirya aiki a kamfanin nan ba, amman na ga mutumen kamar ya san ki”

“Ni ban ma taɓa ganinsa sai yau, da alama shima a nan yake aiki ko?”

“Shi ma babba ne a kamfanin nan, kuma ance suna shiri da mai kamfanin sosai wai amininsa ne, ko meeting ne idan be samu damar zuwa ba shi yake turawa”

Haka muka fito tana ta labarta abubuwa da dama akan kamfanin da kuma ma'aikatan gurin cikin har da Zinatu da take ita sabuwar zuwa, sai dai ita ta rigani zuwa da wata huɗu, yadda take ta yabon kirki da kuma halin Zinatu har sai da abun ya ban tsoro wata ƙila duk wannan mugun halin nata mu take yi ma shi mu da muke tsofin ƙawayenta.
Komawa na yi ɗakin na gyara sannan na dawo na cigaba da aikina, bayan na gama na fito na nufi gurin da ake rubuta suna na rubuta duk abunda ya kamata ina kamawa sai ɗaya daga cikin mutanen da suke reception ɗin ya miƙa min wata farar takarda, ya bani wani file wai na saka hannu, bayan na yi karɓa na nufo gurin da na aje Hijabi na ɗauka na saka sannan na kama hanyar fita daga kamfanin ina warware takardar.

Naira ɗari biyar ce a ciki sai kuma sunan Bilal a jikin wata ƙaramar takarda, na san ya yi haka ne saboda na nuna masa bana son na ganni babu Hijabi. Ƙasaitaccen murmushi ne ya bayyana a fuskata murmushin da na manta rabon da na yi irinsa. Ƙamarar takardar mai sunansa na ɗauka na jeta a bakina na taune zuciyata cike da shauƙi Bilal.

Wannan shauƙin shi ya kawar min da komai na damuwata har na isa gida. Da sallama na shiga Jamila da Noor suka amsa min domin sune a tsakar gida, Inna tana ɗaki tare da Habiba.

“Miya hana ku zuwa makaranta?”

“Noor ne ya ce ba zai je ba”

Cewar Jamila kamin Noor ya karɓe mata.

“A'a Wallahi ita ta fara cewa ba zata je ba, Anti Sakina ce kawai ta tafi”

“Daman haka kuke so, idan bana a cikin gidan nan babu mai matsa muku kuje makaranta”

Da faɗan na shiga ɗakinmu, sai na samu Habiba ita kaɗai kwance ƙasa ƙafafunta lulluɓe da ƙaton kuma tsohon Bedsheet ɗin Inna.

“Habiba”

Na kira sunanta a hankali, sai ta ɗago ta kalleni amman da dukan alamu kamar bata cikin hayyacinta, domin alamu sun nuna hakan. Hannu na kai na buɗe bedsheet ɗin dake rufe da ƙafafunta sai ga jini a gurin kamar an juye jalkar manja, ba shiri na saki bedsheet ɗin na yi baya-baya dafe da baki ido a waje, zuciya mugun bugawa kamar an ce min ga mutuwata nan kusa da ni.!



NOT EDITED
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


1⃣8⃣

Na yi saurin rufe bakina idona cike da hawaye na nufi waje da gudu, ɗakin Inna na shiga ban sameta a ciki ba, ina fitowa waje Inna na fitowa daga banɗaki tana riƙe da buta. Kallo ɗaya ta yi min ta ɗauke kai ta nufi ɗakinmu, ni kuma na rufa mata baya hankalina a tashe.

“Inna kin ga halin da take ciki kuwa?”

Ya gyaɗa min kai.

“Ko minti talati ba ki yi da fita ba, ta fara zubar jini ina jin cikin ne yake zubewa”

Tsugunawa na yi a gurin na dafe kai ina hawaye.

“Inna bata cikin hayyacinta”

“Dole ne zata yi haka saboda wannan ne na farko kuma kinga yarinya ce, amman zata warke zata dawo lafiya ƙalau”

“Inna dan Allah mu kaita asibiti”

Na faɗa ina fashewa da kuka, sai ta ce

“Babu inda zamu je Nawwara, zata warke”

Ta janye bargon ta soma gyara mata jiki ni ko ina duƙe a gurin ina aikin kuka. Haka muka wuni muka kwana babu wani canji sai ma ƙari, tun ina ganin tausayinsa har zuciyata ta fara raya min wasu abubuwa marasa kyau. Ita kanta Inna ta soma tsorata ganin mun kwana da ita a haka babu wani canji, ni ko na kasa zuwa aiki saboda ina ganin kamar idan na je na barta zan dawo na tarar ta mutu, ina jin kamar idan ina kusa da ita babu abunda zai sameta.
Can da yamma abun ya fara zuwa da sauƙi da har ina maganar ko Inna bata so sai na ɗauke ta na kaita asibiti saboda gudun kunya ba zan bar ƴar'uwata ta mutu ba.

Jikin nata babu ƙarfi amman hankalinta ya dawo, har ma ta ɗan jiro hannunta kaɗan ta ɗora saman nawa, kasancewar ina zaune ne kusa da ita saman tabarma. Numfashi take wahalce gaba ɗaya idanuwanta sun canja kamar wata tsohuwa.

“Sannu Habiba”

Na faɗa cikin muryar kuka ina mai tausayin ƴar'uwata, sai ta yi min murmushi hawaye ya fito daga gefen idonta.

“Ina Inna?”

Ta tambaya daker cikin muryarta na marar lafiya.

“Taje maƙota zata samo miki lafiya dubu”

Ta yi shiru tana lumshe ido, hakan yasa na tashi na ɗebo mata ruwa, na ɗan ɗaga kanta na kai mata kofin a baki, ba laifi ta sha da yawa kamar zata haɗe kofin har mamaki na yi na ce.

“Na ƙaro miki?”

Sai ta girgiza kai alamar a'a, sai ta rufe idonta tana numfashi a hankali. Ganin haka yasa na miƙe tsaye domin naje na kira Inna sai na ji ta kira sunana.

“Nawwara...”

Sai na koma na zauna ina kallonta.

“Na'am”

Na amsa ina kallon idonta dake rufe.

“Ance mace data mutu gurin haihuwa ana kyautata mata zaton samun aljanna saboda ta yi shahada, tau idan kuma mace ta muru gurin zubar da cikin banza fa?”

Ji nayi kamar jiri ya ɗibeni, hawaye uku-uku ya soma sauko min, ta farkon ido da kuma tsakiya, sai kuma ta gefen ido. Me Habiba take nufi ne? Wannan wace irin tambaya ce take min haka? Bakina a sake nake kallon yadda take numfashi. Ina haka Inna ta shigo, da fari gabanta ya faɗi ganin hadda hawaye suke min zuba sai dai ganin Habiba ta buɗe ido yasa ta ɗanji sanyi har ma da yin murmushi ta zauna kusa da ita tana nuna mata kulawa irin ta ƴa da uwa. Ta tsorata lokacin da takai hannu ta gwale idon Habiba, ya yi ɗorawa kamar marar jini, sai ta kalleni.

“Kamar bata da jini”

Kai kawai na iya gyaɗawa mata, sai ta miƙe tsaye da sauri tana kiran Sakina.

“Sakina zo ki siyo mata maltina da madara ta sha kamin muje asibiti”

Da gudu ta shiga ɗaki ta ɗauko kuɗi ta bada a siyo mata maltina uku da madara ta bata, sai kuma ta dawo ta zauna kusa da ita tana kuka.

“Na yi wauta Habiba yanzu zan kai ki asibiti, ban ɗauka abun har ya kai haka ba, kin zubar da jini da yawa”

A wahalce Habiba ta soma magana.

“Karki kai ni asibiti Inna, ko kin kaini mutuwa zan yi, kuma mutane zasu ji, na barku da damuwa, ƙara baki je ɗin ba domin Wallahi mutiwa zan yi-”

Na yi saurin kai hannu na rufe mata baki, sai ta lumshe ido, Inna ta tashi a firgice ta fita daga gidan tana kuka, kamar jira take na janye hannuna daga bakinta sai ta ce.

“Nawwara zan tafi na barki ke kaɗai...”

Na sake rufe mata baki ina kuka. Sai ga Inna ta shigo.

“Riƙata ga Napep can na na tsayar zamu kaita asibiti”

Kamar waɗanda suka ɗauki takarda haka muka ɗaga Habiba, jikinta ya yi sanyi sosai ƙwayar idonta baƙar ta ɓata ɓat sai farin kawai kake gani. Cikin hanzari muka saka mata wasu tufafin muka saka mata Hijabi muka ɗauketa sai gurin mai Napep.
Muna shirin shiga Napep ɗin Sakina ta dawo daga siyen madara da maltuna, tsabar hankalin Inna ya ɗauku bata ko iya karɓa ba muka kama hanyar asibitin uduth dake gawon nama, duk da da kasancewar mun san asibitin ta kuɗi ce.
Gudu sosai mai napep ɗin ke yi amman kasancewar tsakanin unguwarmu da asibitin uduth akwai ƴar tazara sai da tafiyar ta yi mana nisa. Muna isa bakin gate ɗin asibitin, Habiba ta sauke wani irin ajiyar zuciya ta kwanto da kanta dake jikina zuwa jikin Inna, rai ya yi halinsa ƴar'uwata ta amsa kiran mahaliccinta...!



I will updated 19 tomorrow morning.

RIJF Habiba😭
*RAI BIYU...♥️🖤*

Wattpad @Khadeeja_Candy


1⃣9⃣

Inna ta kai hannu ta kwanto da fuskarta zuwa saman hannayenta tana murmushi. Haske sosai fuskar Habiba take goshinta ya soma taruwa da gumi.

“Allah ga yata nan, ta aikata kurkure kuma na yafe mata, ina roƙon ka Allah ka yafe mata, ka karɓi baƙuncinta, Allah ka zama gatanta bata da gata sai naka, yau ƴata ta koma gareka Allah kuma nasan ba ka yi dan ƴata ba, kuma ba kayi ƴata dan ni ba, Allah ga ƴata nan ta dawo gareka, ƴata mutuminyar kirki ce dukan abunda ta aikata ta aikata ne saboda mu, Allah ka yafe mata, haƙiƙa kai mai yawan gafara ne”

Inna ce take maganar tana shafa fuskar Habiba, hawayen idonta na zuba a fuskar Habiba. Sai kuma ta ɗago ta kalleni.

“Kin ga abunda na aikata ko Nawwara? Saboda gudun kunya na kashe ƴata, ba a tambayar Allah miyasa ya aikata abu, abunda ya ga dama shi yake aikata a sanda ya so ga kuma wanda ya so, amman da ace ni ce na mutu a wannan lokacin zai fi, ko ba komai ni naga duniya Habiba ko yanzu take tasowa, Habiba ƴarinyar kirki kin samu rana, mutane da yawa suna fatar mutuwa a cikin wannan ranar ta jumma'ah-”

Tsakanin Habiba da Inna sai na rasa wanda zan tausayawa, Habiba da ta bar duniya da ƙirciyarta ko kuwa Inna da zata shiga wani tashin hankalin a dalilin rashinta?

“Na rasa *RAI BIYU* Ran mahaufinku da kuma na ƴar'uwarku, na mahaifinku saboda zalinci na ƴar'uwarku kuma saboda talauci, Allah na gode maka”

Mai napep ɗin ya juyo ya kalletaa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login