Showing 48001 words to 51000 words out of 138998 words
shower ya lumshe ido yana sauraren yadda tsanyin ruwa ke ratsa jikinsa.
‘Nawwara will never ever ever forgive Jibril for what he did to her’
Shine abunda ke ta masa yawo a cikin kai, zuciyarsa na wani irin zafin, sai goma har da kwata sannan na bar bathroom ɗin cikin yanayi marar daɗi.
Vest ya saka da ɗan guntun wando, be shafa mai ba amman ya shafa turare, sannan ya fito parlour ya haɗa ma kansa tea ya zauna saman cushion yana kallon hoton nawwara Tea ma sai ya gagara sha. Yana zaune gurin har shaɗayan dare ta buga be ko motsa daga inda yake ba. Siraj ne ya turo ƙofar falon ya shigo hannunsa riƙe da takardu masu yawa, ɗakin karatun Jibril ya nufa ya aje takardun sannan ya dawo ya zauna kusa da shi yana faɗin.
“Gaskiya yau Jibril ka bani mamaki, wai su waye iyayen yarinyar nan ne da har zata wulaƙanta a gaban jama'a ka ƙyaleta?”
Sai a yanxu ya gincira saman kujerar yana cigaba da kallon hoton Nawwara.
“Maruƙar haka zai sa ta yafe min, zan jure har sai ta yarda da na yi nadama kuma na tuba”
“Wannan ba revenge ba ne, it's an embarrassment, ko ma mi kayi mata baka cancanci ta yi maka wannan tuzarcin ba, su fa mata ba a ƙyalesu hakan ya bata damar cigaba ne, gaba ɗaya yau ak kamfanin nan kai aka wuni ana magana wannan ai tozarci ne”
Murmushi Jibril ya yi ya kalli Siraj ya ce.
“Data mareni a gaban mutane na ji yadda ta ji a lokacin da na mareta airport, na ji yadda ta ji a lokacin da na mareta a gaban iyayena, na ji yadda ta ji a lokacin da na mareta a bakin titi na jefar da ita na yi tafiyata, at least now na san yadda mutun yake ji idan aka disgashi gaban jama'a”
Siraj ya juyo yana fuskarta shi da kyau ya ce.
“Kana da banbanci da kowa Jibril be kamata ka auna kanka da sauran jama'a ba, weather you like or not abunda yarinyar nan ta yi maka bata kyauta ba”
Miƙewa Jibril ya yi tsaye ya nufi window falon yana faɗin.
“You're my new tight friend Siraj, bana son kana faɗar wata kalma marar daɗi a kan nawwara, saboda hakan zai sa na tsane ka ita kuma na ƙara ƙaunarta, zan iya jure ko wani kalar wulaƙanci daga Nawwara matuƙar hakan zai sa ta yafe min, soyayyata da ta rasa a can baya ita nake son nuna mata a yanzu, kulawar da na gagara bata a da, ita na ke son bata a yanzu.
Na wulaƙanta yarinyar sosai Siraj irin wulaƙanci da ban taɓa tsamanin Allah zai jarrabeni da son kamar haka ba, a gaban idonta na ke shigowa da budurwa a gidanta kuma ta dafa mana abinci ta haɗa mana ruwan wanka, ta san fasadi muke aikatawa amman haka be taɓa damunta ba, ko da yana damunta bata taɓa nuna min ba. Idan ta dafa abinci sai ta kawo min tana jiran na yaba mata amman sai na kushe wani ko ci ba zan ba, idan ta yi kwalliya tana jiran na yaba mata ba zan kalleta ba, ban taɓa riƙa hannunta da nunan sha'awaba sai idan zan hukunta ko kuma na doketa, idan mahaifina ya tambayeta ko akwai wata matsalar sai ta ce masa babu komai muna zaune lafiya...”
Hawaye ya zubo masa sai yasa gefen hannunsa ya shafe yana cigaba da kallon titi kasancewar window yana fuskantar titi ne.
“Lokacin da na gano tana da ciki, sai na saka mata maganin bachi a lemu ta sha, da tayi bachi sai na cire mata tufafi na ɗauki hotonta na kai ayi editing aka haɗa da na wani, da gangan na sa aka ɗauko min mahaifinta aka zo da shi garin abuja na tarasu da mahaifina na ce cikin da ke jikinta ba nawa ba ne ga wanda ya yi mata shi nan, i'm very fool Siraj can you imagine na ɗauki hoton mamata na haɗa da hoton wani saboda kawai bana son ta kuma ban shirya haihu da ita ba a wannan lokacin...”
Ya zuba hannayensa aljihu hawaye na ta masa zuba, sannan ya sauke ajiyar zuciya.
“A gaban mahaifinta da mahaifina na nuna waɗancan hotunan kuma na ce na saketa saki uku, sai mahaifina ya ce min saki uku idan aka yi su a take a matsayin saki ɗaya suke dan haka na yi haƙuri na maida matana, jin wannan yasa nace na sake tsaki ɗaya tsaki biyu tsaki uku, a ranar Nawwara ta riƙe min hannaye tana roƙon na rufa nata asiri na karɓi cikin nan, wannan roƙon da ta yi min sai yasa mahaifina ya yarda cewar ba cikina ba ne.
A ranar mahaifina ya tabbatar min da sai na yi nadamar abunda na yi mata, saboda yana ganin ta bi maza ne domin kawai na kasa bata kulawa, ashe da gaske zan yi nadama. Bayan na rabu da ita mace huɗu na aura suka kasa zama aure da ni, wasu basa mutunta ni kamar yadda take, wasu kuma su nuna min suma ƴaƴan manya ne ba zasu iya abu kaza da kaza ba, daga lokacin na fara kewar Nawwara, kuma duk wannan auren da nayi babu wacce ta taɓa samun ciki da ni, kuma ba dan bana haihuwaba ba dan ina da wata matsala ba sai dai isgilancin da na yi Allah ya jarrabe ni, sai bayan na yi aure na biyar ashe ita ba ɗana ba ne ban ganr haka ba sai da na auna jininsa, gudun afkawa cikin wata matsalar sai step mom ɗita ta aura min ƙanwarta, sai da tafiya ta tafi sai na gano kasheni take son yi ta ci gado tun da bana haihu ita kuma tana son haihu amman bata son fita ta bar ɗaular gidana, sai ta saka min guba a abinci shine ciwon da har yanzu yaƙi warkewa a jikina, bayan na rabu da ita na dawo na cewa mahaifina ina son naje gidansu Nawwara, sai ya ce min shi ba babu ruwansa kuma ba da yawun bakinsa ba, saboda na kunyatashi na tozarta shi kuma na ci amanarta bayan shi ne silar aurena da ita, daga ƙarshe ya ce be yafe min na taka ƙafata ƙofar gidansu Nawwara ba, tun daga lokacin sai tunaninta da halin damuwar da na saka ta ya riƙa damuna, wani lokacin na kan rufe kaina ni kaɗai a ɗaki ina kukana amman babu mai bani haƙuri saboda mahaifita bata raye.
Komai nawa sai ya tsaya cak, idan naje asibiti bana iya komai sai tunani da damuwa, wannan ne ƴasa Abbah ya dawo da ni kamfaninsa na nan sokoto saboda na rage damuwa, na jidaɗi da Abbah ya yi min haka ko ba komai ni ma zan yi rayuwa garin da Nawwara ta taɓa rayuwa, lokacin da na zo na haɗu da kai, na saka nemanta sai ka ce min ta mutu kuma iyayenta ma sun mutu, daga lokacin na yafe farinciki da walwala a tare da ni.”
Ya juyo ya kalli Siraj sannan ya ce
“Nawwara ce kawai macce da ta samu ciki da ni ta hanyar halak, Nawwara ce kawai take kula da ni kamar mahaifiyar da ta haifeni, Nawwara ce kawai zuciyata ke ƙauna, ko a can baya ba ƙaunarta ne bana yi ba kawai dai ina ganin ta shigo rayuwata ne a lokacin da be kamata ta shigo ba. Dan haka karka sake faɗin wata mummunar kalma akan Nawwara, na zan iya tukararta kai tsaye ta yafe min ba, amman idan muna zama a guri ɗaya ita da kanta zata fahimci halin da nake ciki ta yafe min, i need to work with her, i need to be close to her”
Yana kaiwa nan ya share hawayensa ya nufi Bedroom ɗinsa, ya bar Siraj a tsaye yana jinjina lamarin.
*** *** ***
Kukana ya yanke tun kan na iso gida, sai dai hakan be hana mahaifiyata fahimtar ina cikin damuwa ba, ga shi na dawo da wuri ban daɗe ba.
“Lafiya kika dawo yanzu?”
“Lafiya ƙalau kawai faɗa muka yi da wani na mareshi sai suka ce na dawo gida”
“Faɗa kuma? Da namiji miya haɗa ku”
“Na goge gurin ne sai yazo yana min masifa har da riƙa hannuna na ni kuma na mareshi”
“Tau kin kyauta kin yi abun a yaba miki kowa ya yi miki ba dai dai ki riƙa hannu kina marensa kinji Allah ya miki albarka”
Na san baƙar magana ta yi min wacce ke nuna bata jidaɗin abunda na yi ba.
“Amman Inna ni ce nai gaskiyafa”
“Idan kina da gaskiya sai ki ɗaga hannu ki mareshi wata ƙila ma ya girmeki, duk wani hali da ba naki ba Nawwara yanzu kin ɗauka kin ratawa kanki, wannan zabin zuciyar na Habiba ke aka saukewa shi? Ita tafi sai masifar ta dawo kanki, wannan ba halinki ba ne Nawwara, kuma ba tarbiyar gidan nan ba ce”
“Yi haƙuri Inna na miki alƙwari ba zan sake ba”
Na faɗa idona cike da ƙwalla, domin ni kaɗai na san halin da nake ciki, ita kanta da tasan wanda na mara da bata min wannan masifar ba. Ɗakinmu na wuce na ci kuka sai da na gode Allah sannan na fito.
Bayan sallah magariba, Bilal ya kirani a waya ya sanar min yana waje, na ɓata lokaci kamin na fita saboda na san maganar da zai min ba zata wuce ta abunda ya faru yau ba, sallama na yi masa amman be amsa min ba sai ya jefo min tambaya.
“Ance min kin kirashi da azzalumi, shi kuma ya baki haƙuri har ya yi iƙirarin kiranki da matarsa, shine Baban Noor ko Nawancy”
Na gyaɗa masa kai
“Shine”
“Daman kin san nan kamfaninsa ne kike aiki?”
“Ban sani ba sai yau”
Wani dogon numfashi yaja ya sauke.
“Na yi farinciki da ya gane kirkurensa, ko ba komai Noor zai san mahaifinsa na gaskiya”
Na yi saurin girgiza masa kai idanuwa cike da ƙwalla.
“Ba zai sani ba Bilal ba zan iya bashi Noor ba, be san zafin ɗana ba, be san yadda na yi na haifi ɗana ba, be san wahalar da na sha kamin da bayan na haifi ɗana ba, ko sau ɗaya ƴan'uwansa ba su taɓa biyo sawunna su duba lafiyar ɗana ba, Noor be cancanci Uba irin Jibril ba, Dan Allah dan girman Allah karka faɗa masa ina da ɗa zai iya raba ni da ɗana Bilal”
“Ba zan faɗa masa ba, amman dole wata rana zai gano, lokaci yana zuwa Nawancy zaki koma ke da shi kamar ba ayi ba”
Ya faɗa muryarsa na nuna tsantsar damuwar dake cikin ransa.
“Ba zamu koma ba Bilal, babu wanda zuciyata take so take ganin ƙimarsa kamar kai, kai kaɗai ne mutun da zan tuna na yi murmushi, Wallahi kai kaɗai zuciyata take ƙaunara Bilal”
“Ina jin tsoron faruwar wani abu Nawancy”
“Babu wani abun da zai faru, sai idan ba son aurena kake ba, ba son ƙwarai kake min ba, daman can zaka biye abunda mutane suke cewa ka gujeni”
“Ba zan taɓa gudunki ba Nawancy, ina ƙaunarki sosai”
Ya faɗa yana ƙoƙarin kai hannu ya share min hawayena sai na yi saurin saka nawa hannun na share, sai kawai ya saka min dariya.
“Na jidaɗin wannan abun ko ba komai kin nuna min yadda kika so na”
Ni kuma sai na cire talakmena na gwaɗa masa a hannu har sai da ya yi ƙara.
“Ka daina taɓa ni da wannan hannun”
“Nima ba son raina yake taɓa ki ba, kawai dai shi ɗin ne ya damu sai ya taɓa ki, amman ranar da zai taɓa halalinsa zan ga bakin da ya isa ya hana shi”
Na zaro ido ina mamakin kalaminsa, sai ya kannemin ido ɗaya yana murmushi. Mum yi firar da ta ɗebe min kewa fira irin ta masoya firar da ta gusar min da duk wani tunani da damuwa har sai da na dawo cikin gida. Bayan na yi sallah isha'i na ci abincin dare kaɗan saboda kar Inna ta gano abunda yake damuna.
Dakimmu na dawo da zimmar bachi amman sai na kasa rayuwar da na yi a abaya ta dawo min...
FLASH BACK.......
_______________________________________
I can't wait na ji tarihin Nawwara zamanta da Jibril.. 💃
#RB
#TEAM MUSTAPHA
#TEAM JIBRIL
#TEAM BILAL
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
2⃣8⃣
Khadija shine sunan da mahaifina ya saka min, sai ya yi min alkunya da Nawwara, duk da kasancewar ba ni ce ta farko ba, ƴaƴƴuna hudu maza duk basu tsayaba sai ni da nazo a ta biyar kuma mace.
Bayan ni sai da mahaifiyata ta shekara biyar sannan ta haifi Habiba, a lokacin Mahaifina yana ta faɗi tashin rayuwa na nema mana abunda zamu ci.
Ba zan kira kaina da kyakkaywa ba, sai nasan ni ba mummuna ba ce, abunda kawai zan iya shaidar kaina da shi shine na ɗauko fari da kuma dogon hancin mahaifiyata kasancewarta fulani, gashin kan ba a magana na girata ma askewa nake balle kuma na gadon bayana dake ƙayatarda mai kallo.
Siye da siyarwar na fatoci, Sana'ar iyaye da kakkanina ce sana'ar wacce mahaifina ya buɗe ido ya samu kansa a cikinta har muma muka zo muka tarar anayi, kowa ya tashi a gidan ana buɗa masa shago ko kuma a haɗashi da wanda zai riƙa masa ja gaba kan sana'ar har ya kafa tashi.
Kusan zan iya cewa sana'ar bata karɓi mahaifinmu ba, tun lokacin da ya fara ba riba ba kuɗi, wani lokacin har kuɗin wani sai sun shiga ciki su ƙi fita, duk lokacin da mahaifinmu ya siyo fata da zimmar saidawa sai karaya ta sameshi wacce zata zama silar da ba zai iya maida kuɗin ba, yayyunsa da Yakumbo da kuma Hajiya Lamtana Allah ya jiƙanta sai suka ɗauki karan tsana suka ɗora ma Ramatu wato mahaifita, a ganinsu ita ce bata da ƙashin arziki, sukan ce wai can kamin ya aureta a lokacin da yake saurayinsa yana sa'arsa lafiya sai da ya aureta sannan komai yaso ya lalace.
A lokacin ina ƙarama amman abun yana min zafi sosai saboda yana damun mahaifiya sosai, har na riƙa kallonsu a matsayin maƙiyanmu wanda har yau shine a zuciyata, domin a lokacin a gaban idonmu suna faɗa wai uwarmu mai farar ƙafa ce wanda hakan suke tunanin ba komai bane ko kuma mu bamu kula ba alhalin yana mana zafi sai dai bamu isa mu nuna ba kasancewar gidan taro ne, ko tari kayi sai anji, Babban gida irin gidan nan ne da kakanni suke siye sai iyaye da jikoki su taru a gidan kowa ya keɓe wani ɓangare nasa ya kafa nasa iyalin.
Lokatuta da dama takan keɓe ita kaɗai ko kuma da mu tayi ta kuka tana roƙon Allah ya bawa mahaifina wani aikin duk da bashi da wani karantun zamani a wacan lokacin, muna haka wani maƙocinmu Malam Buba kuma abokin Baba da yake yawan zuwa Abuja ya faɗa ma Mahaifimu cewar wani attajirin mai kuɗi a garin Abuja yana neman mai masa gadi kuma ya ce baya buƙatar kowa sai bahaushe ɗan'uwansa, Malam Buba ya kasance yana masa gadin wani babban kamfanin siyer da kayan alatu ne dake can garin Abuja.
Muna zaune gida ranar wata talata, bayan mun gama cin kwaɗon ƙanzo, sai Baba ya shigo da far'arsa yana labarta mana abunda Malam Buba ya faɗa masa, Inna ta yi murna sosai kuma ta nuna jindaɗinta, a nan suka yanke shawarar ba zasu sanar da Yakumbo da Hajiya ba saboda sunsan ba zasu bari yaje ba, sai suka haɗa kai da Malam Buba ya faɗa musu Babanmu zaije Abuja ya kai fatune saboda ana bukatarsu a can, sun yi na'am suka masa addu'ah da fatan nasara, sai Baba ya karɓi fatun bashi da sunan idan yaje can zai aiko da kuɗin.
Ranar da zai tafi munyi kuka sosai ni da Inna har ma da wasu mutanen gidan saboda muna ganin kamar ba zai dawo ba, tafiya nisa kuma har garin Abuja garin da a wacan lokacin muke ɗaukarsa kamar wata ƙasar dabam.
Bayan wata ɗaya da tafiyar mahaifinmu sai gashi ya dawo cikin shigar mutunci da kamala, sai dai ya ɗanyi rama kaɗan ya kuma yi haske, ya labarta mana komai yake muna nan cikin ranshi wannan tunanin ne ya hanashi ƙiba, har ma yake faɗa mana cewar mai gidansa ya ware masa wani ɓangare na gidansa ya bashi ya ce ya ɗauko iyalansa su dawo nan kuma ya zo mana da kuɗi mai yawa.
Ba ƙaramin yaƙi akayi ba kamin Hajiya ta yarda ta barmu aka tafi da mu, a nan ma sai da ya yi mata wata ƙaryar cewa ya canja sana'a yanzu yana siye da saida takalma ne na fatu har ma ya ce mata hayan gida ya kama a ƙauyen Abuja acan zai zauna da mu ya cigaba da sana'arsa.
Amaina huɗu a mota kamin mu sauka zaria, aka siya min abinci da ruwa na cika cikina ni da Habiba sannan muka cigaba da tafiyar, ko da muka shiga garin Abuja ina bachi, sai da motar ta tsaya sannan Inna ta tasheni muka koma can wani ɓangare na tashar, Baban mu ya ari wayar wani ya kira Alhaji ya sanar masa mun iso domin ba a shiga da wani abun haya a unguwar.
Dare ya yi sosai har Baba ya yanke shawarar zuwa gurin abokinsa Malam Buba mu kwana a can sai ga ƴan komisho sun zo suna neman Malam Musa Kafinta, a nan suka haɗa mu da mutumen yanayin yadda Baba ya gaisa da shi sai ya tabbatar da cewar ya sanshi, ashe direban Alhajin ne.
Ni da Inna duk da tsoro muka shiga motar saboda ganin Babbar motar kamar wannan wacce ni dai zan iya rantsuwa hannuna ma be taɓa kaiwa akanta, amman yau zan shigeta. Ina ta rabon ido har muka iso wata kyakkyawar unguwa. Idona be ƙara buɗewa har sai da muka iso cikin ƙaton gidan dake cike da ababen more rayuwa.
Iyalan mutumen ne da Alhajin shi kansa suka fito suna tarbonmu, har yake bawa Baba haƙuri akan rashin ɗaukoshi da wuri wai yaje meeting ne kuma sai ya manta sai da ya dawo gida sannan ya tuna.
Cikin Falonsu muka shigo sai suka saka mai aikinsu ta kwashi kayanmu