Showing 75001 words to 78000 words out of 138998 words
kujerar mai juyawa, komai daki daki na bishi ina kallon da dubawa sannan na kula da ƴar danjar da ke ƙara a gefen teburina, sai kuma computer ta soma nuna min mutumen da ke waje, wato Bilal yana riƙe da wasu takardu.
Gabana ya faɗi sosai sai na soma tunani da wace fuskar zan kalli Bilal shi kuma wane irin tunani zai min.?
JIBRIL POV.
He's just can't believe Nawwara tana ƙarƙashinsa a yanzu, wani irin daɗi yake ji yana ta yi ma Allah hamdalla, cike da so da ƙauna yake kurɓa tea da ta haɗa masa yana wani lumshe ido.
Jin ya yi ba zai iya jure jin wannan farincikin shi kaɗai ba, ya ɗauki wayarsa ya danna number Siraj dan labarta masa.
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
*Dedicated to My Asmee*
3⃣9⃣
Ba ni da wani zaɓi face na bashi damar shiga, domin nasan komai dare daɗewa dole zai sani. Kamar yadda Rabi ta nuna a wacan karo haka na danna sai ƙofar ta buɗe masa, a ta biyu mai gilashi muka riƙa kallon kallo ni da shi. Ƴar ƙaramar danjar sai tsuwa take tana nuna min agogon hannunsa da pose ɗin kuɗinsa sai kuma takardun da ke hannunsa.
Ban damu da ce masa ya aje ba na sake dannawa ta buɗe ya shigo yana ta kallona kamar wanda be sanni ba. Hanzarin miƙewa na yi tsaye Cikin yanayin damuwa na zan masa magana sai ya rigani
“Takardun nan zaki kai wa oga ya saka hannu”
“Na yi ta kiran wayarka ban samu ba, miyasa ka kashe wayar”
“Zamu yi maganar anjima let's do this now”
Yawun bakina na haɗe kana na ɗaga masa kai sannan na karɓi takardun kai tsaye na nufi office ɗin Jibril duk kuwa da kasancewar ya yi min gargaɗi ɗazu akan na daina shigowa ba noticing, waya na tarar yana yi fuskarsa shimfiɗe da farinciki tea da na haɗa masa yana hannunsa sai kurɓa yake, yana ganina sai ya yayi hanzarin yanke wayar ya kalleni, sai dai be ce min komai ba jira yake ni na fara masa magana.
“Hannu zaka saka a waɗannan takardun Bilal ne ya kawo”
Na faɗa kamar mai shirin yin kuka, domin har ga Allah ban jidaɗin yadda na ga fuskar Bilal kamar baya cikin farinciki. Saman tebur na aje masa takardu sai ya duba ya saka hannu sannan ya miƙa min. Ni kuma na karɓa na juyo jiki ba gwari na miƙawa Bilal takardun sai ya karɓa yana faɗin
“Congratulations”
Ni dai ban ce masa komai ba har ya juya ya isa gurin ƙofar sai ta buɗe masa da kanta ya fice. Faɗuwa na yi saman kujera da ke kusa da ƙofar ta zaman baƙi ina sauke ajiyar zuciya, har ga Allah na san dole ne sai Bilal ya zargeni amman ta yarda zan fahimtar da shi ne aiki tasowa na yi na dawo saman saman kujera ko kuma na ce kujerar office ɗin na zauna zuciyata a jagule, ina ta tunani mafita sai bachi ɓarawo ya yi gaba da ni.
Babu komai a mafarkina sai Jidda da Mustapha, wai ya mata fyaɗe kuma ya kasheta ga ƴan sanda da mutane cike a gidansu, ni kuma sai aikin kuka na ke ina kiran Mustapha, abunda ban sani ba ashe har a fili na ke kiran sunansa.
“Mustapha...”
Abunda na furta kenan daga farkowatawa, sai na ga Jibril tsaye a kaina yana kallona, hakan yasa ni saurin zabura na tashi.
“Me zaka min?”
“Me kike tunanin zan miki? Mayaudariya kina spn Mustapha kina yaudarar Bilal ko?”
“Ina ruwanka babu ruwanka da rayuwata”
Sai ya mire baki tare da ɗaga kafaɗunsa sama alamar abun be dame shi ba.
“Tashi muje meeting, baki da aiki sai bachi abunda ya kamata ace ke zaki faɗa min lokacin meeting ɗin ya yi amman wani ne daga can waje yake sanar da ni”
Na tashi tsaye idona kan agogon office ɗin da ke nuna ƙarfe goma sha ɗaya na safe, shi ya fara fita ni kuma ina binsa a baya har muka shiga Lifter, a nan ya miƙa min ƙaramar jakar da ke hannunsa.
“Kin duba akan me zamu yi meeting ɗin?”
Na girgiza kai alamar ban sani ba, sai kawai ta cigaba da kallona ko kunya baya ji, ni kuma na yi kamar ban ganshi ina ta kallon numbobin lifter, sai dai haka be sa ya ɗauke idonsa daga kallon da yake min ba har lifter ta tsaya a hawa na uku ta buɗe da kanta, sai na yi saurin fita duk da ban san inda zamu shiga ba, sannan shi ma ya fito sai ga Rabi ta tare mu ta karɓi layin wayata wai zaa saka min numbobin ƴan ƙamfanin ta yadda zan gane duk wanda ya kirani.
Ko da muka shiga ɗakin taron mun tarar da mutum biyar wannna abokin nasa Siraj sai kuma Zinatu da wasu ɓakin fuska uku, yana shigowa duk suka miƙe tsaye ya miƙa ma baƙin fuskar hannunsa suka gaisa sannan ya gabatar musu da ni.
Ɗaya daga cikinsu ne wanda na ke zaton ba musulmi ba ne ya miƙo min hannu dan mu gaisa yana faɗin sunansa.
“Divid Sam”
Sai Jibril ya yi saurin miƙa masa na sa hannun a ƙaro na biyu, ya kuma amsa masa kamar ni ɗin.
“Nawwara”
Ni kuma na zauna a kujerar da ya nuna min, ban maida hankalina kan abunda suke tattaunawa ba, sai dai hakan be hanani fahimtar cewa wani kamfanine yake son siye, har aka yi meeting ɗin aka gama Siraj da Zinatu idonsu na kaina duk wani motsi da nake suna kallona har na soma jin babu daɗi.
Tare muka fito daga ɗakin taron sai ya koma daga bayana yana kallon tafiyata, hakan yasa ni ƙara sauri na shiga tifter, sai da tana daf da rufewa sannan ya ƙaraso ya shigo, still yanzu ma idonsa na kai, da alama dai kallona daɗi yake masa, ko kuma yana min ne dan kawai na tsargu, sau ɗaya na ɗago na kalleshi sai yayi min kwarjini sosai na yi saurin sadda kaina ƙasa ban sake kallonsa ba har Lifter ta sauke mu a hawa na biyar, har na miƙa jiki na fita sai ya riga fita.
“Baki iya competition da ni”
Ya furta daidai lokacin da zai fice, a nan na kalli bayan kansa sannan na fito muka doshi office ɗin, da fari na tsaya tunanin wa zai buɗe mana tun da ba mu bar kowa a ciki ba, muna isa sai kawai naga wata ƙaramar na'ura tana ɗaukar fuskarsa, sai ƙofar ta buɗe masa ya shiga, ina zuwa na shiga sai wani jan layi ya shata yana ta ƙara.
“Ki tsaya a nan karki raunata kanki, ba zaki iya shiga yanzu ba saboda bata tantance fuskarki ba”
Bayan ya shiga ciki da kamar minti biyu sai ƙofar ta buɗe min. Ina shiga ya jawo ni gaban computer ta ɗauki hotona ya saka sunana sannan ya juya ya shige Office ɗinsa.
Ina zaunawa idanuwa suka kai kan agogon Office ɗin na ga ɗaya da kwata, lokacin Sallah azahar ya yi, wata ƙofar da ke cikin Office ɗin na nufa ina taɓawa sai ta soma ƙara tana nuna min na saka password, ta biyu kuma ina turawa na ga toilet, daman shi na ke nema, alwala na yi na fito na d8ba ko'ina na gurin babu carpet ɗin Sallah sai na shimfiɗa ɗankwalina na yi dashi bayan na gama, na nufi Office ɗinsa dan tunatar da shi lokacin Sallah ya yi.
Zaune na sameshi yana ta aiki a system ɗinsa, kamar jira yake na shigo mayun idanuwansa suka dawo kaina har na ƙaraso kusa da teburinsa.
“Lokacin Sallah ya yi”
Iskarka bakinsa ya busar sannan ya kalli tsadadden agogon hannunsa.
“Idan na gama aikin nan zan yi”
“Har sai ka gama aikin? Jibril mi ka ɗauki sallah ne? Sallah ita ce rukuni na biyu daga cikin rukunan addinin musulunci, kuma ita ce gimshiken addinin musulunci. Barinta kafirci ne da yake fitar da mutun daga cikin addini, babu addini babu musulunci ga wanda ya bar sallah namiji ko mace!”
“Ba fa kafiri ba ne ni, ina sallah”
“Na san ai kana sallah, amman ba akan lokacinta ba, ina mamakin avunda zai ɗaukewa mutun hankali har ya watsar da bautar Ubangijinsa, kasan irin azabar da Allah ya tanadarwa masu wulaƙanta sallah kuwa? Jinkira sallah lokacin ya fita ba tare da wani uzuri na shari'a ba, wannan tozarta sallah ne kamar yadda Allah ya faɗa a suratul Maryam aya ta hansi da tara zuwa sitti : Sai mutanen banza suka maye bayansu, suka tozarta sallah, suka bi sha'awace-sha'awace na saɓo; to ba da daɗewa ba zasu haɗu da gayyu wato wani gwalolon azaba a cikin wutar jahannama, sai fa wanda ya tuba.
Farkon abunda za a maka hisabi da shi a cikin ƙabarinka sallah ce, kuma ita ce zata tayaka zaman ƙabari (Allah ka bamu ikon tsaida Allah akan lokaci 🙏😭)”
Tun da na soma maganar yake kallona fuska a sake, da alama na burgeshi ne ko kuma mamakina yake oho, but to my surprise sai na ji ya ce
“Thank you, da kika tunatar da ni, babu wanda ya taɓa faɗa min wannan, inshallah zan gyara ko dan na samu damar rayuwa da ke a aljanna”
“Aljanna kowa gidansa daban, na Jibril daban haka ma na Nawwara daban”
Dariya ya yi kamar ba shiba ya miƙe tsaye ya nufi wata ƙofar da nake zaton banɗakine a ciki. Ni kuma na juyo na fito, sai na samu computer tana nuna min Rabi da ke waje, sai da na zauna sannan na buɗe mata sai ta shigo fuskarta a sake kamar ko yaushe.
“Ga sim ɗinki anyi miki dukan abunda ya dace”
“Thank you, amman yanzu idan ina son na kira general meeting a madadin Jibril ya zanyi?”
“Sir Jibril zaki ce ko kuma mai gida”
Ta faɗa sannan ya buɗe wani ɗan ƙaramin littafi dake gefen teburin ta soma nuna min
“Wannan number zaki kira, idan an ɗaga ba sai kin tsaya gaisuwa ba, kawai ki ce Sir Jibril ya ce haɗa masa general meeting, idan emergency ne sai ki faɗa, idan kuma meeting ɗin yana da date da time sai ki faɗa, zasu haɗu a hawa na biyu room 24 domin shi ne kawai ɗakin da yake iya ɗaukar yawan ma'aikatan da ke kamfanin nan, idan har ya yarda ki yi magana a madadinsa zaki iya zuwa kiyi idan kuma shi zaiyi da kansa sai ki raka shi”
“Thank you so much”
“Your welcome”
Sannan ta juya ta fita, ni kuma na saka number da ta nuna min a telephone zuciyata na ta raya min kar na yi, idan har na yi haka na yi karanbani, wata zuciyar kuma na nuna min idan har na yi haka na taimaiki Jibril da rayuwarsa har da da sauran ma'aikatan.
Sai kawai na dannan kiran na ce ina buƙatar a haɗa min meeting ɗin gagawa, ni kuma na tashi na fita riƙe da wayata na nufi lifter, ina sauka hawa na biyu na soma ƙirga ɗaki, har na hango ɗakin da mutane suke shiga. Tsayawa na yi sai na kasa ƙarasawa ina ta tunanin ma yadda zan ce musu abunka da wanda be saba ba, sai kawai na juya na koma lifter, na yi mamakin yadda ina isowa bakin ƙofar office ɗin sai kawai ta buɗe min.
Ina shigowa na samu Jibril tsaye yana jiran shigowata.
“Akan mi kika kira general meeting kuma emergency?”
“Am sorry”
“Ba hakuri na ce ki ba ni ba, dalili zaki faɗa min”
“Da na yi ƙoƙarin na faɗa musu idan lokacin sallah ya yi kowa yaje ya yi sallah, sai kuma na ga kamar na maka karanbani”
“Karabanni ne mana, ba yau yau kika kama aikin ba?”
“Am sorry”
Na faɗa cike da nadama sai ya matso kusa da ni.
“Is okay, zan faɗa musu da kaina indai har haka kike so, follow me”
Yana faɗar hakan ya nufi ƙofar fita na bishi, tare muka isa da kansa ya faɗa musu cewar a yanzu da lokacin sallah ya yi kowa ya aje aikin da yake yaje ya yi sallah, daman akwai masallaci a cikin kamfanin. A yanayin yadda fuskokin musulmin ma'aikatan suka nuna sun yi farinciki sosai kuma sun nuna jindaɗinsu har ma da yin godiya.
Ina tsaye gefen Jibril Bilal na kallona kamar zai cinye ni, irin kallon nan da mutum zai kasa gane manufarsa sai hakan yasa duk na bi na tsargu, mu muka fara fita sannan sauran suka fito. A bayan na tsaya ina amsa waya shi kan gogan na ku tuni ya yi nisa tare da Siraj.
Dpo ne ya kirani wai an bashi number ta daga gida, saboda ya zo be sameni ba kuma yana son magana da ni, a ina nake ya zo ya tafi da ni.
“Na kusa dawowa aiki, idan na dawo zan kira ka”
“Okay”
Daga haka na kashe wayar, na cigaba da tafiyata. Ko da na shiga office ɗin ƙpfar Office ɗin Jibril tana buɗe ina hango abokinsa sai dai ban san mi suke tattaunawa a akai ba har sai da na zauna sannan na soma jiyo muryar abokin nasa.
“Be kamata ka sake mata har haka ba, so ai ba hauka ba ne....”
Sai kawai na ji an ba ƙofar gam an rufe, bayan wani ɗan lokaci sai abokin nasa wato Siraj ya fito kamar cikin ɓacin rai ya fice ba tare da ya kalli inda na ke ba.
Takardar da ke gabana na ɗauka na duba sai na ga lokacin meeting ɗinsa da wani Hon Usman Dahiru ya yi, a maimakon na kira sai kawai na tura ƙofar na shiga.
Saurin saka bayan hannunsa ya yi ya kare hancinsa, sai dai abunda be sani ba abunda ke gabansa a farar takarda mai kamar hoda ya taɓa masa hannu, juyawa na yi zan fita sai ya kira ni.
“Naj”
Ina juyowa ya ce
“Madarace na ke sha ina fama da ulcer”
Ni dai ban ce masa komai ba na juya na fita, ina shirin zama sai gashi na fito daga office ɗinsa ya biyoni.
“Madara ce Naj”
Nan ma kallonsa kawai na tsaya yi, sai ya ɗaga hannayenasa sama domin shi ma yasan ban yarda da shi ba.
“Fine cocaine ce shikenan?”
“Allah ya wadaranka Jibril, kullum abunka gaba yake ba baya ba, har yanzu akwai tattoo a jikinka, yanzu kuma cocaine kake sha bayan neman matan da kake? A haka iyeyenka za su nuna ka a matsayin ɗansu ɗan ka kuma ya nuna ka a matsayin uba? Iya yau kawai na zauna da kai, amman na ga halaye masu marar kyau a tare da kai, wasu baka canja ba wasu kuma sabbi ne, na yi nadamar da na taɓa saninka a rayuwata Jibril...”
Na faɗa cikin hawaye da kuka na ɓakinciki da jin zafi, yanzu irin wannan mutunen ne na haihu da shi? Ina baƙincikin da ya kasance uban Noor sam, ɗa na be yi dacen uba ba, dan haka ban zan nuna masa ko kuma faɗa masa cewar Jibril ne ubansa na gaskiya ba.
“Bana neman mata Naj, Aisha ce kawai na ke taraiya da ita ma kuma na daina na tuba, cocaine ɗin ma akwai dalili shanta da na ke, amman na ji kamar kin yi wata magana, na ji kin ce ɗa me kike nufi akwai abunda ya kamata na sani ne?”
Ganin yadda yake matsowa yasa na yi hanzarin miƙewa tsaye har ina ɗauke numfashi, shi kuma yana ta kallona kamar mai karantar abu a fuskata, sai takowa yake har sai da ya kowa daf da ni...!
“Ina da ɗa ko Nawwara...?”
____________________________________
Zaku ga wasu kalmomin kamar ba a ƙarasa ba wasu kuma ana mistakes da yawa ana dai akwai errors or omissions a ciki, hakan yana faruwa ne saboda rashin editing, idan har na ce zan tsaya editing zai ɗauke ni tsawon lokaci ban yi updated ba domin editing ya fi bani wahala fiye da typing.
Fatar zaku fahimta kuma zaku min uzuri 🙏
FOLLOW ME
VOTE
COMMENT
SHARE
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
*Dedicated to My Asmee*
4⃣0⃣
JIBRIL POV.
“Ee kana da ɗa”
Shine kawai abunda Jibril yake son jin ya fito daga bakin Nawwara, wani irin bugawa zuciyarsa take da sauri, ido cikin ido yake kallon Nawwara tsantsar gaskiyarta yake son ganewa, yadda ta saki baki tana kallonsa shi kansa yasan subul da baka ta yi, yadda take numfashi yake karantar da shi irin faɗuwar gaban da ke ranta.
“Kana da ɗa mana ƴaƴama zan ce, ba ka auri Aisha ba ta haifa maka ƴaƴa, na tuna ai tun kamin ka aureta ma ta samu ciki, wanda kake labarwa abokinka farinciki fal a ranka, kuma bayan ita maybe ka ƙara auren wasu matan sun mahaifa maka ƴaƴa ko kuma ka musu cikin shege”
Lumshe ido ya yi ya haɗe yawun dake bakinsa ya dunƙula hannunsa ya matse sosai kamar zai dake, har ga Allah baya jindaɗin kalamanta, duk lokacin da ya tuna rayuwarsa ta baya yana jin babu daɗi ballr kuma ace ita ce da kanta take tuna masa da wannan, hakan na karantar da shi cewar ba zata taɓa yafe masa ba kuma ba zata manta ba.
“Ina cikin da na barki da shi?”
Ya faɗa yayinda da buɗe idonsa da suka rine suka yi ja sosai.
“Cikin da ka kace ba naka ba ne? Ai na zubar domin ba zan iya ɗaukar shege a cikina ba”
“Ba zaki iya zubarwa ba, ba zaki iya kashe rai ba ko da kuwa ɗan shegen ne da gaske”
Kallonsa ta yi sai ta yi murmushi.
“Ashe kai da kanka ka san ba ɗan shege na ɗauka a cikina ba, amman ka ce ba naka ba ne ka haɗa hotona da hoton wani namiji wanda ban taɓa sanin inda ya fito ba, saboda kawai kana neman rabuwa da ni? Da na dawo da ciki sai suka kira da karuwa wannan dalili yasa na zubar da cikin”
Ta faɗa hawaye na fitowa daga idonta fuskarta kuma ɗauke da murmushi.
Wani irin ƙuna yake ji a cikin ransa, zuciyarsa zafi take kamar an kunna masa wuta, yana jin rashin kyautawa a duk lokacin da ya tuna abunda ya aikata mata, tabbas yanzu ya yarda akwai wawanci, shashanci a tare da shi, duƙursawa ya yi ƙasan guiwoyinsa ya kama Hijabinta sa gashi yana hawaye.
“Dan Allah Nawwara ki yi haƙuri dan Allah ki yafe min”
“Daman na faɗa, saboda ka riƙa neman yafiyata yasa ka cilasta min aiki a tare