Showing 126001 words to 129000 words out of 138998 words
kai na kalleta idanuwa cike da hawaye.
“Amman Inna kina ganin wannan dalilin kawai ya isa yasa Mahaifiyarsa ta hana shi aurena?”
“Ya isa mana, idan kika duba daman can ai ba sonki take ba, kuma tana ganin an wulakanta mata da, ni kaina babu irin maganar da bata fada a gabana ba lokacin da na ke zuwa duba shi, amman idan har Allah ya rubuto ke matarsa ce Wallahi bata isa ta hana ba, ki sawa kanki wannan”
Na gyada mata kai na share hawayena sannan na mike tsaye ina amsa sallamar da naji wani namiji na yi a waje, bakin kofar na nufa babu mayafi a jikina hakan yasa na leka da kai na yayinda jikina yake cikin gidan, wani saurayi saman babur hannunsa rike da ledoji sai ya miko min.
“Ga sako daga Candy Restaurant Jibril ya ce a kawo ma Noor”
Kamar ba zan karba ba, sai kuma na mika hannu na karba ba tare da na ce masa komai ba, dakin Inna na dawo na aje ledodin tare da fadin.
“Wai Jibril ya aiko a kawo ma Noor, ni ban gane masa ba ya raina abincin gidan nan ko mai?”
“Ba raini ba ne, yana ganin dacewar hakan ne kawai”
“Ina Noor din?”
“Yana bandaki tun dazu ya shiga”
Cewar Inna sai gashi ya shigo dakin yana tafiya a hankali.
“Momy gurin kaikayi yake min”
“Karka sosa dai ciwon zai iya tashi”
Na fada masa, sannan na juya na koma dakinmu jin wayata na ringing. Jibril ne yake kirana katse kiran sai ya sake bugowa cikin fushi na dauka
“Wai ba zaka daina kirana ba ne?”
“Amman kin san ba ke na kira ba Noor na kira dan me zaki dauka? Na ce ina son magana da ke ne? Da na na kira kuma kin sani na ce zan siya masa waya saboda na rika kira ta nan kin hana ya kike so na yi”
“Akan me zaka aiko masa da abinci bayan kuma kasan muna da shi”
“Ta nan kika bullo kuma? Na aiko masa ne saboda na san ya saba da abincin ba zai iya cin wani abinci bayan wannan ba a yanzu, kuma ina da hakki na ciyar da dana bana son wata dogowar magana da ke dan Allah ki bashi waya na tambayi lafiyarsa ko kuma na zo gida yanzu na duba shi”
Kashe wayar na yi na koma dakin Inna sai gashi ya kira na mikawa Noor suka gaisa, sun dade suna waya daga karshe Noor ya fita daga dakin ya koma can gurin bandaki yana magana kadan-kadan da alama wani abun yake fada masa, sannan ya dawo ya kawo min wayar.
“Momy wai ya ce yana gaida Inna da kowa da kowa amman ba da ke ba”
Ya fada yana dariya, tabe baki na yi na tashi naje ya dauko kofi na zuba koko nasa suga na dawo dakin na zauna ina sha, domin shi kadai na ke jin zan iya sha kasancewar bana cikin dadin rai. Guraren goma da kwata ina yi ma Noor wanka tsakar gida sai ga Baba Sulaiman ya shigo bakinsa kumshe da sallama. Ina kallonsa nasan ba lafiya ba
“Baba ina kwana?”
“Lafiya kalau ina mahaifiyarki?”
“Tana daki. Inna fito ga Baba”
Na kwara mata kira bayan na bashi amsa. Sai ga Inna ta fito sanye da Hijabinta ta zauna bakin baranda tana gaisawa da shi.
“Na ce masa ko akwai abunda ya shiga tsakanin Bilal da Nawwara ne?”
Na tsayar da wankan da nake ma Noor na kalleshi gabana na faduwa. Sai Inna ta ce
“Miya faru”
“Ya aiko yanzu nan wai a bashi kayan aurensa ya fasa kuma wai ya yi magana da ita ya fada mata yace ta fada mana zai aiko ya karba”
“Sulaiman ai gaka ga yarka waka a bakin mai ita ta fi dadi”
Inna ta fada tana nuna masa ni.
“Ke Nawwara ya aka yi?”
“Jiya ne da yazo ya ce wai mahaifiyarsa ta ce bata yafe masa ya aureni ba, shine ya ce ya fasa aurena...”
Na fada ina kokarin fashewa da kuka.
“Daman Wallahi sai da muka raya a haka dukan mu sai da muka yi maganar nan, daman nasan irin rigingimun da suka faru ba zata bari ya aureki ba, Yakunbo ma sai da ta ce haka, amman matar nan ba ta yi tunani ba sam”
“Ni kaina na zargi hakan ganin irin maganganun da suke ta fada gabana”
“Ni kaina ina jin wasu abubuwan sai dai ka toshe kunnenka tun da ba a taruwa a zama daya, kuma a unguwar nan ma har a abunda ya kai unguwarmu babu abunda mutane basu fada ba, kuma kin san mutane da zuga Allah yasa haka shi ya fi alheri”
“Amin, nima haka na ce kuma in mijinta ne babu wanda ya isa ya shiga tsakaninsu”
“Tau Allah ya kyauta daman dai na ce sai na ji ta bakinta ne kamin mu bada kayan, Allah ya baki wani”
Ya fada ganin irin hawayen da nake, sannan ya mike tsaye ya fice cike da damuwa, daman kayan ba a nan suke ba, tun da aka kawo lefen aka maida shi can gurin Yakunbo kasancewar nan gidan ba Namijj kuma ina tsoron kar a biyo dare a tararda mu. A gaskiya na ji babu dadi na ji ni a cikin wani kalar yanayi mai kamar an yi min mutuwa, ban tabbatar da cewar Ina son Bilal sai a wannan lokacin, yanzu shikenan an raba mu kenan? A wunin ranar kasa sukuni na yi a cikin gidan mu, ana kiran la'asar na dauki Hijabi na nufi gidansu Jidda. Ina shiga na fashe musu da kuka daga ita har Maman Nura wato mahaifiyarta sai da hakalinsu ya tashi, sun tausaya min kuma sun nuna min rashin jidadinsu a fili lokacin da na labarta musu abunda ya faru.
“Yanzu duk soyayyar nan da kuka yi da Bilal ace be aureki ba gaskiya abun be yi dadi ba”
Cewar Jidda, sai Mahaifiyarta ta ce.
“Ni daman Wallahi ban dai fada ba ne, amman na san ba duka iyayene zasu iya bari dansu ya auri bazarawa ba, ko mai aure daya balle mai biyu kuma har da da, yanxu kuma ga abunda ya faru”
“Amman ni Wallahi da zaki min wani abu da kin auri Jibril ko dan mahaifiyarsa ta ji haushi, kuma ga Noor sannan mutumen yana son ki sosai, kin ga sai ma ya maiye gurbin kwanakin da suka rage a daura miki aure da shi”
Jidda ta fada, sai mahaifiyarta ta karba nata.
“Ni dai haka na gani, wani lokacin abunda kake so ba lallai ne ya zama alheri a gareka ba, kuma so da yawa kana kin abu ya zama shine alheri a gareka, ki baiwa Allah zabi kawai”
Wani irin abu na ji ya daki zuciyata, sam bana jin zan iya kara zaman aure da Jibril, indai har ban aure Bilal ba to be cancan na auri Jibril ba, taya ma zan yi zaman aure da mutumen da ya wulakanta ni ya nuna min ba ni muhimmanci a rayuwarsa.
“Na baiwa Allah zabi kuma na san zai zaba min abunda duk yafi zama alheri a gareni, amman ina jin kamar ba zan iya zaman aure da Jibril ba”
Jidda ta dafani.
“Zaki iya Nawwara, tunda kina son Noor kuma kina son farincikin danki, karki damu da rashin son da kike masa, abu mai muhimmanci shi yana sonki kuma so mai tsanani, kuma kinsan hausawa na cewa mai son ka be ganin ramarka, kuma kara ka auri wanda sonshi ya fi na ka yawa zaka fi jindadin zaman aure fiye da wanda ke kika fi sonshi, zan cigaba da miki addu'a kamar yadda na ke yi ma kaina Insha-Allah”
Hawayena na share na gyara zamana, ita kuma ta tashi ta fita saboda kiranta da aka yi a waya. Sai kusan magariba na baron gidan na dawo gida.
Bayan na yi sallama magariba na zauna ina ta karanta lahaula wala'kuwwati da carbi adadin da zan iya, saboda tana yaye damuwa kuma matukar kana cikin damuwa ka lizinci karanta ta Allah zai maka mafita.
Can kusan sallah isha'i na kira wayar Bilal sai suka nuna userbusy haka na yi ta trying suna amman na kasa samu daga karshe na gane ya saka number ta a blacklist ne. Wasa wasa aka kwana uku a haka na kasa cin abincin kirki saboda tunani, ba damuwa ce ta dame ni ba damuwar Bilal ce ta dame ni domin na san yana so na, kuma mutane da yawa zasu masa dariya idan har be aureni ba, duk na bi na rame kamar marar lafiya, jikina babu wani kuzarin kirki kasancewar bana iya cin abinci mai nauyi sai fura ko koko ko tea.
Ranar da aka kwana hudu da faruwar hakan ina zaune, da misalin biyar da rabi na yamma sai ga Asiya yar wajen Baba Sulaiman ta zo kiran wai na zo Baba Sulaiman da Baba Dahiru suna kirana, gabana ya fadi da farko kuma naji tsoro sai dai ance karka ji tsoron kira ka ji tsoron laifi da ka yi, kuma ina tunanin addu'a ta ce Allah ya amsa wata kila iyayen Bilal ne suka dawo a gyara maganar.
Sai da na fadawa Inna sannan na dauki Hijabi na saka muka fita tare. Muna shiga zauren gidan gabana ya fadi ganin Baba Sulaman da Baba Dahiru da kuma Baba Audi wato kanen mahaifina da yayyensa a zaune saman tabarma tare da Mahaifin Jibril da abokinsa wanda suka zo tare lokacin da wadancan abubuwan suka faru da kuma Yayan Jibril da wasu mutane maza da ban wayancin fuskarsu ba a zazzaune.
Sallama na fara yi bayan sun amsa gaishesu sai Baba Sulaiman ya nuna inda zan zauna, ba musu na zauna kaina a kasa gabana sai faduwa yake ina jiran jin dalilin kiran.
“Jibril ne ya aiko da iyayensa su nema mishi aurenki kuma ya ce kun yi magana da shi akan cewar zai aiko kin amince, amman mu baki fada mana ba, hakan yasa na ce ba za a yanke hukunci ba sai an kiraki an ji ta bakinki”
Na yi shiru ban ce komai ba, still kaina a kasa zuciyarta cike da tsanar Jibril. Sai Baba Audi ya katsa min tsawa.
“Ki bude baki ki yi magana mana, dukan mu ba yara balle ki tsaya yi mana wasa, da baki muke son jin amsarki ba da shiru domin ke bazawara ce ba budurwa ba, cewar kin amince shi zai tabbatar mana da cewar kin amince haka Annabi ya ce”
Dago kaina na yi na kallesu dukansu ni suke kallo amsata kawai suke son jin...
[11/18, 10:07 PM] Farar Mace...: *RAI BIYU...♥🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
5⃣8⃣
Kaina ya yi nauyi sosai ta ya zan iya watsa kasa a gaban manyan mutane kamar wadannan? Mi zai biyo baya idan na ce ban amince ba? Wane irin fahinta Baba Sulaiman da Baba Dahiru zasu min?
“Ban zata zai aiko da wuri haka ba, shiyasa ban fada muku ba”
Na fada yayinda nake maida kaina kasa.
“Yanzu dai ba wannan ba, kin amince ko baki amince ba?”
Baba Dahiru ya tambaya. Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na amsa.
“Na amince”
“Al-hamdulillah, Allah ya miki albarka Nawwara kin ceci rai”
Abunda ya fito daga bakin Mahaifin Jibril kenan fuskarsa shinfide da farinciki.
“Tashi ki koma gida”
Cewar Baba Sulaiman, haka na taso kamar marar lakka a jiki na fito daga gidan na nufo gida, tun a hanya kuka ya fara kamani amman ban yarda na yi ba sai da na iso gida, ina shiga na fashe da kuka kamar an min mutuwa.
“Lafiya miya same ki?”
Inna ta tambaya tana rike da tsintsiya. Faduwa na yi zaune.
“Inna wai iyayen Jibril ne suka zo neman aurena?”
“Ban gane suka zo neman aurenki ba”
“Mahaifinsa ya turo da wasu mutane ya ce ni nace su zo, wai su nema masa aurena, shine Baba Sulaiman da Baba Dahiru da Baba Audi suka kirani suka tsareni suna tambayar wai na amince ko aa”
“To mi ya faru?”
“Na ce na amince”
“Shine kuma kika zo nan kina kuka”
“Ni bana son shi Inna ba zan aureshi ba”
Sai Inna ta nuna ni da tsintsiyar da ke hannunta.
“Wallahi kin yi kadan karyar karya take Wallahi, wato ni gani ice mai dadin zama shine zaki zo nan kina min kukan ba zaki aureshi ba ko? Ni da kika raina ai miyasa baki fada musu tun can ba”
“Baba Audi zai iya yanka ni”
Na fada cikin kuka.
“Oo to sai ni da nake rarrashin ki zaki xauna kina min kuka kamar yadda karamar yarinya ko?”
“Wallahi ko an daura auren nan ba zan tare ba”
“Tashi kije gasu can ki fada musu tun basu tafi ba, ko kuma ni na yafa mayafina na je na fada musu kina nan kina kukan ba zaki yi auren ba”
Jin haka yasa na yi saurin tashi na shige dakin Inna dan nasan duk Baban Audi ko Baba Dahiru suka ji wannan maganar na shiga uku yanxu bayan na ce na amince kuma na ce ban amince ba ai zasu ce ina musu wasa da hankali. Kuka na yi sosai dakin Inna rayuwar da zan yi gidan Jibril nake hangowa, taya zan rayu da mutumen da ya wulakanta ni? A yanzu ma zai iya kara wulakanta ni saboda yana ganin a bagas ya same ni kamar wacan lokacin, kuma zai yi ta tunanin ina son sa wanda hakan zai bashi damar sake wulakantani kuma na san har duniya ta nade Jibril ba zai taba sanin mutuncina ba.
Sai da yamma Baba Sulaiman da Baba Dahiru suka zo gidan tare da kwalaye minti da cingan da sauran abubuwan da ake kawo wa na baiko, suka labartawa Inna abunda ya faru, ta nan nake jin sun yanka sadakina dubu talatin abokin Abbah ya biya dubu dari kasa, kuma sun saka kwana shida da suka rage na aurena da Bilal sun maye gurbinsu da Jibril. Baba Sulamain har dadi yake ji wai yafi son haka ta yadda Bilal kawai da familynsa zasu ji an daura min aure.
A daren ranar kasa bachi na yi sai na kwana ina raya daren da sallah nafila da karatun qur'ane Allah na mikawa lamurrana har yanzu ban cire rai daga auren Bilal ba.
JIBRIL POV.
Tunda su Abbah suka kama hanyar gidansu Nawwara gabansa ke ta faduwa yana sauraren irin amsar da zasu dawo da ita, Abbah na kiranshi ya tsaya karanta addu'a sannan ya daga zuciyarsa cike da fargaba.
“Kana ina?”
“Ina gida Abbah”
“Ka zo gida ka same ni yanzu”
“Abbah bata amince ba ko?”
“Ta amince har mun biya sadaki kuma kwanakin da suka rage na wacan da bata aura ba aka maida da naka”
Rudewa ya yi yana tsaye ya zauna sai kuma ya sake tashi tsaye.
“Abbah are you serious?”
“Ah wasa na ke da kai? Ko wasa ake da lamarin aure?”
“No no i mean thank you gani nan zuwa”
Abbah ya kashe wayar yana murmushi. Sai Jibril ya fadi ya yi ma Allah sujudar godiyar, sannan ya mike tsaye yana wani irin dariya kamar mahaukaci har da jjjiga jiki, zuwa can kuma ya fara rawa takawa ya farayi a hankali a hankali kamin ya fara yi da karfi har da su kada kwankwaso, sai kuma ya yi tsalle ya fada saman kujera.
“Oh my God i just can't believe this Al-hamdulillah Allah”
A take ya fara hango irin rayuwar da zasu yi da Nawwara idan aka daura musu aure, ya dade yana ta ayyana irin jindadi da gatan da zai nuna mata sannan ya tuna cewar Abbah yana can yana jiranshi kuma yau zai bar garin. Cikin hanzari ya fita gida, zuciyarsa fari kal saboda farinciki, har ya yi kamar ya kira Nawwara sai ya tuna da riske yayi mata sai ya fasa dan yasan tana nan tana fushi da shi. Ko da ya isa ya samu su Abbah na cin abinci shi kan ko ruwa kasa sha ya yi saboda farinciki, rabon da ya yi farinciki irin wannan har ya manta, kallo daya zaka masa ka gane yana cikin farinciki.
Wasu batutuwan Abbah ya tattauna da shi akan auren bayan ya fada masa yadda komai ya gudana. Sannan suka tsaya tsara yadda za ayi.
“Zan ba Hajiya ta hada mata kayan sawa na tufafi da komai da komai da ake, kai kuma sai ka bata kudin da zata yi hidima da wuri saboda kar lokaci ya kure, na fadawa iyayemta bama son komai, saboda haka idan an daura aure sai ka fara gyaran gidan kamin nan da wata daya ka gama sai ta tare”
“No Abbah a cikin week din nan ma za a iya komai a kudi ne matsalar kuma da an bada kudi za ayi komai a cikin lokaci, kuma ba dole sai furniture ba dole sai anyi order a abroad ba a nan ma Kano Kaduna ma za a iya samu na wajen, Abbah na fi son ana daura auren ta tare ranar gudun kar wani abu ya shiga”
Abbah ya dan tsaya kallonsa ya so ya fahimce cewar cilastawa Nawwara yayi sai kuma ya tuna da irin son da yake mata ko da ita din bata son shi ba matsala ba ne. Su yi maganganu sosai akan auren da kuma yadda za a tsara komai, ciki har da zancen da Jibril ya bijiro da shi cewar baya son a yi masa taso sosai gurin daurin auren domin ba kowa yake son a sanarwa ba.
Bayan sun gama Jibril ya raka Abbah da babban yayansu da kuma abokin Babansu da Kannen mahaifinsa airport suka hau Jirgin Abuja, shi kuma ya dawo gida.
Tun daga ranar Jibril ya fara shirye shirye, a bokansa na baya da baya ja a jikin saboda abotarsa da Siraj yanzu kan ya zubar da wannan halin yaja kowa a jikinsa, sai dai be yarda ya yi amini a cikinsu ba domin a yanzu ya wayance da duniya.
NAWWARA POV.
Tun da aka saka lokacin Inna ta cigaba da shirye shiryenta kamar yadda ta fara, babu yadda Jidda ba tayi ba akan na je gurin gyaran jiki amman na ki, duk wani shirye shiryen da amarya take idan an kusa aurenta ni ban yi ba, ban da rama da baki ma babu abunda na yi, ranar da step mother dinsa da yayanta da wasu familyn Jibril suka kawo lefe ma na sha kuka sosai, basu karbi komai ba, ni ban ma san za a kawo lefen ba dan tun lokacin da aka saka