Showing 69001 words to 72000 words out of 138998 words
kofin ya nufi wani ɗakin, da shigarsa ya ɗauko wani akwati ya buɗe ya ɗauki ƙwanƙwaƙo ƙarami ya buɗe sai ga cocaine cikin wata farar leda da sauri ya ɓasge ledar ya zuba garin a hannu yana shaƙa kamar ba gobe.
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @KhadeejaCandy
*Dedicated to My Asmee*
3⃣7⃣
Ina fitowa daga banɗaki na zauna saman tabarma da na tashi sai Noor ya miƙon wayata da ke hannunsa.
“Momy gashi an kira na ɗauka amman ba ayi magana ba”
Ina karɓar wayar na duba sai na ga number Jibril number nan ce da ya saba kirana da ita.
“Ka yi magana?”
“Ee amman ban ce ance komai ba, sai na ce idan kin zo zan faɗa miki sai na kashe”
“Na shiga uku Noor miyasa ka yi magana?”
Hankalina ya tashi sosai zuciyata na ta raya min Jibril zai gane cewar Noor ɗansa ne.
“Momy ban ce komai ba”
Ya faɗa ganin yadda duk na bi na rikice, kai na gyaɗa masa naja shi zuwa saman ƙafafuna na zaunar da shi na rumgumeshi, muna haka wayar ta ƙara ringing ina dubawa na ga Number Jibril sai na kashe wayar gaba ɗaya, gabana sai faɗuwa yake, zuciyata na nuna min Jibril zai uya zuwa gidan nan a yanzu ko anjima saboda ɗansa.
Unƙurawa na yi na tashi sai ga Jidda ta shigo bakinta ƙumshe da sallama, sai jikina ya ƙara yin sanyi har na ke ganin kamar ita ma tare take da Jibril.
“Noor tashi kaje ɗaki yi sauri”
Sai da ya gaisheta sannan ya tashi ya nufi ɗakin, ita kuma ta zauna kusa da ni tare da dafani.
“Ki kwantar da hankalinki ba zan cuceki ba, ba kuma za a haɗa baki da ni a cuceki ba”
“Idan har ni be cuceni ke zai cuce ki”
“Mustaphan da kika sani a baya ba shi ne a yanzu ba, Wallahi ya canja Nawwara kuma saboda ke ina ganin wannan kaɗai abun farincikine ace ta dalilinka wani ya shiryu”
Na gyara zamana ina kallonta da kyau.
“Bakin san waye Mustapha ba shiyasa kika wannan maganar, baki san iya ta'asar da ya yi ba shiyasa kike ganin kamar ya canja”
“Ya canja Nawwara ko ki yarda ko karki yarda Mustapha ya canja, ganin da kika mana tare yazo gurina ne saboda yana neman yafiyarki, yana son na taimaka masa na nema masa yafiyarki”
“Kin san abunda ya aikata min kuwa?”
“Shine mutumen da ya yi fyaɗe ya bata dubu ashirin ko? Ko ba wannan ba ne?”
Kallon mamaki na yi mata.
“Ya faɗa miki kenan?”
“Ya faɗa min komai saboda kawai yana neman yafiyarki, ki dubi girman Allah Nawwara ki yafe masa ko ya samu sassaucin rayuwa”
“Taya kika san tuban gaskiya ya yi? Maza suna yaudararmu Jidda saboda sun san mu mata muna raunin zuciya, sukan yi amfani da wannan damar su sake cutar da mu”
“Ba zai taɓa cutar da kr ba Nawwara, tun daga lokacin da kika taɓa marinsa ya ƙyaleki zuciyata ta raya min Mustapha son kin yake ko kuma son wani na ki, ya isa shaidar kirki cewar Mustapha tuban kirki ya yi tun da ya biyo ki har ƙofar gidanku ya nemi yafiyarki, idan har yana son cutar da ke ba zai taɓa neman yafiyarki ba, zai iya sakawa a ɗauko masa ke ya yi miki yadda ya ke so, zan iya dafa miki ƙur'ane cewar Mustapha tuban ƙwarai ya yi kuma ya yi nadama”
“Ba zan yafe masa ba da gangan mutun zai aikata abu sai kuma ya dawo neman yafiya, da ace be mata fyaɗe ba da bata samu ciki ba da duk be kaita ga halaka ba, da yanzu ƴar'uwata tana nan raye”
Na faɗa zuciyata na mugun ƙuna. Sai dai abunda ya fito daga bakin Jidda ya kusa ya ruɗar da ni ko kuma ma na ce haukatarda ni gaba ɗaya.
“Ashe jahila ce ke Nawwara, karatun addininki be amfaneki da komai ba, baki da imani ko kaɗan saboda baki yarda da ƙaddara ba, kuma bari na gyara miki kalamanki da ace yar'uwarki bata je ta kai kanta gunsa ba da be samu damar yi mata fyaɗen ba, kuma ko da Mustapha ko babu Mustapha dole Habiba zata mutu kuma dole sai wani ya yi mata fyaɗe kuma dole sai ta yi ciki saboda yana rubuce cikin kundin ƙaddararta, tirr da halinki Nawwara tirr zuciyar da bata yarda da ƙaddara marar kyau ba sai mai kyau, Allah ma muna masa laifi ya yafe mana balle ke da Allah zai cewa faɗi ki mutun kuma ki faɗin ki mutu dan dolenki, zuciyarki bata da kyau Nawwara saboda babu imani babu tausayi a cikinta, bawan Allah nan ko shi da hannunsa ya kashe Habiba ya kamata ki yafe masa tun da har yace miki ya tuba, balle fyaɗen da idan aka bincika daga shi har ita suna da laifi-!”
Tun da ya fara maganar na ke kallon yadda take dantsar baki tana faɗa min duk maganar da tazo daga bakinta idonta na hawaye kamar yadda nima nawa idanuwan suke hawaye, cikin muryar kuka na ce.
“Faɗa min nawa Mustapha ya biyaki Jidda? Dala dubu nawa ya biyaki da har tasa kika goya masa baya tsaɓanin aminiyarki? Da me ya siye zuciyarki har kika ƙoƙarin ɓata abotarmu?”
“Da imani da tausayi ya siye zuciyata, ni na yarda da ƙaddara a yayinda ke baki yarda da ita ba”
“Saboda baki dan yadda na ke ji ba Jidda, a gaban idona yar'uwata ra rasa ranta saboda wannan azzalumin”
“Na san yadda kike ji, amman na fi jin yadda Mustapha ya ke ji saboda ƙaddara ta faɗa kansa wacce bata wuce faɗawa kowa ba”
Tana kaiwa nan ta miƙe tsaye ta fice ta barni a gurin ina ta hawaye da mamakin kalamanta. Jin ana kiran sallah isha'i yasa na tashi na wanke fuskata na yi alwala a waje na yi sallah isha'i kamar yadda na yi ta magariba.
Bayan na gama addu'o'ina na tashi na nufi ɗakin Inna, ko da na shiga na tarar tana sha'u da wutiri Noor da Jamila kuma na saman gado suna mugun wasa, ƙasa na zauna kusa da ita ina jiran ta ƙare idona suna kan ɗana da ke ta sukuwa saman gadon.
“Noor bari mana gadon Inna zaka yi sukuwa”
Da sauri ya sauko sai ya nufo inda na ke yana faɗin.
“Momy zaki ara min wayarki na yi game ko?”
Sai a lokacin na tuna da na bar wayar a wajen da na zauna har na yi a zamar tashi na fita na ɗauko wayar cike da fargaba na kunnata ina shigowa ɗaki, zan miƙawa Noor naji ƙarar shigowar saƙo, hakan yasa na tsaya dubawa.
_Matiƙar baki dawo aiki gobe ba, wannan shegen saurayin na ki zamu sallameshi kuma try me_
Ba shiri na zaro ido gabana ya shiga faɗuwa na furta shiga uku da kirama kaina hallaka.
“Na shiga uku na lalace”
Da sauri duk suka kalleni har Inna dake jan carbi.
“Miya faru?”
Kallonta na yi sai kuma na rasa ta yadda zan mata bayanin ga Noor da Jamila har Sakina duka idonsu a kaina, saurin goge saƙon na yi na miƙa masa wayar.
“Ungo je kayi game ɗin”
“Momy miya faru?”
“Ba komai kuje waje da Mama Jamila sai ku yi”
Yana karɓa sai suka yi waje ni kuma na zauna kusa da Inna idona cike da ƙwalla na kama hannunta na riƙe sai na kasa yin magana hawaye suka fara yin aikinsu.
“Nawwara mi yake damunki?”
Hannuna ɗaya na kai na share hawayena yayinda wasu ke ƙara zubo min.
“Inna ko na faɗa miki ba zaki fahimce ni ba, kuma fushi zaki yi da ni”
Nan take hankalinta ya tashi ta damƙe hannayena biyu tana kallon cikin idona.
“Me kika aikata har haka ne Nawwara? Abunda ƴar'uwarki ta aikata shi kika aikata kema?”
“A'a Inna Jibril ne”
Na faɗa ina sosa kaina hawaye na sauka a fuskata.
“Wane Jibril?”
“Baban Noor”
Da sauri Sakina ta tashi zaune daga kwancen da take tana kallona, Inna kuma ta saki baki. Ni kuma na rasa ta inda zan fara mata bayani.
“Kamfanin da na samu aiki ashe na Jibril ne, ni ma ban sani ba sai daga baya....”
Haka na bi na zana mata komai tun daga farko har ƙarshe ban ɓoye mata komai ba, har maganar siye gidan da kuma wannan saƙon da ya aiko min yanzu.
Lunshe ido ta yi ta jingina da gado tana sauke ajiyar zuciya.
“Miyasa kika ɓoye min wannan tun farko? Da ace kin shawarce ni da duk abun be kai haka ba, har yanzu baki san ƙima da matarba uwa ba ko? Wani na waje ya ji sirrinki mahaifiyarki bata sani ba? Akwai wanda ya cancanci ki yi sirrin da shi fiye da ni?”
“Ba haka ba ne Inna, kawai ina tunanin irin halin da zaki shiga ne idan na faɗa miki, wata ƙila ma ba zaki fahimce ni ba, kuma abun zai tsaya miki a rai ki riƙa tunanin wanda ni kuma ba zan so haka, Wallahi ban ɓoye miki da wata manufa ba bayan wannan”
“Ƴaƴan mazani kenan masu yarda da ƙawaye fiye da uwaye, masu yin gaban kansu waɗanda suke ganin kamar tasu zata fisshesu”
“Dan Allah Inna ki yi haƙuri”
Na faɗa ina kuka.
“Amman da gaske Jibril ya baki haƙuri kuma kika mare shi ya ƙyale ki”
Sakina ta tambaya, ni kuma na ɗaga mata kai.
“Idan har yafiyarki yake nema ba zai tsaya jiran ki kawo kanki ya nemi yafiyarki ba, sai dai na nemi inda kike ya zo ya baki haƙuri kuma ya nuna miki ya yi nadama”
Cewar Inna, ni kuma na ce.
“Bana ma son ya zo dan ba zan yafe masa ba”
“Allah ma aka masa laifi aka roƙi ya yafe balle ɗan'adam? Idan baki yafe masa ba ai kya bashi ɗansa idan ya zo karɓar abunsa”
“Haba Inna duk wulaƙancin da ya yi min ya ce ɗan nan ba nasa ba ne sai kuma na bashu Noor gaskiya ba zan iya ba”
“Akwai hujjar da ta zata hana ni ganin ɗansa ne?, idan har ya dawo ya buƙaci ɗansa ki bashi kawai shine masliha a gareki da kuma mu, ku bar shi da Allah Nawwara idan har kika yi haƙuri sai ki ga kyakkyawan sakamako daga gurin Allah amman matuƙar kika ce zaki rama abunda ya yi miki Allah zai iya barinki da dabararki a ƙarshe sai ki cuci kanki, amman idan har kika barshi da Allah sai ya saka miki.
Ma a son mace da irin zuciya da halinki Nawwara, duk da zata iya ɗaga hannunta ta mari namiji ta kuma tsaya ta ci masa mutunci akan abunda zata iya kawar da ido ana mata kallon marar tarbiya kuma marar mutunci da kamun kai, raunin zuciya tausayi kawaici kunya haƙuri abubuwa da aka fi samu sun gurin ƴa mace,
Na san Jibril ya zalinceki Nawwara, amman ki barshi da Allah karki yarda ki ce zaki ɗauki fansa wannan ba halin musulmin kirki ba ne”
Daker na iya tsayar da kuka da na ke har na furta.
“Ni ba zan iya yafe masa ba Inna”
“Ban ce ki yafe masa ba, amman ki bishi a hankali kuma ki yi taka tsantsan”
“Kuma ba zan bashi Noor ba be cancanci zama ubansa ba, ni ba zan iya yafe masa ba”
“Har gobe ina faɗa miki rufin asirinki ne idan har ya dawo ya nemi ɗansa, ni kuma ban ce ki yafe masa ba”
Sakina ta dawo kusa da mu tana faɗin
“Amman gaskiya idan har aka bashi Noor ya ci riba biyu”
“Ba riba ya ci ba, Wallahi ina da tabbacin Allah ba zai barshi hakan nan ba, wata ƙila ya jarrabeshi ko zai jarrabeshi nan gaba, duk ɗa ai ƴaƴan maza ne ba na mata ba, itama wani auren zatayi ta haifi wasu ƴaƴan, ni dai abunda na ke so da ke ki yi min alkawari zaki riƙe mutuncinki kar kuɗi da ƙyaliƙyalin duniya ya yaudari zuciyarki ya kaiki ga faɗawa halaka”
“Na miki alƙawari Inna ba zan sake sakaki hawaye ba”
“Allah ya miki albarka, ki je gurin aikinki ki koma kamar yadda ya buƙata, amman karki taɓa nuna masa saboda Bilal kika dawo, kar ki nunawa Bilal saboda shi kike aikin, ko wannensu ki nuna masa saboda kanki kike yi kuma zaki iya dainawa a ko wane lokaci, idan har kika bar aikin yanzu zai kori Bilal kamar yadda ya faɗa, wanda hakan zai jefaku ciki wani halin, kuma baki san ta wace hanyar zai ƙara ɓullo miki ba”
“Amman Inna ina ganin kamar yana son ya yi amfani da damarsa ne ya sake cutar da ni”
“Ba zai sake cutar da ke ba, waya sani ko saboda ke ya dawo garin nan da aiki? Wanda ma yake likita miya kawo shi aikin kamfanin? Baki taɓa tambayar kanki ba?”
Na yi shiru ina nazari, sai Sakina ta yi karaf ta ce
“Wata ƙila yasan ta samu aiki a kamfanin shiyasa ya zo”
Inna ta amsa mata.
“Nima haka na ke tunani, ƴaƴan manyan masu kuɗi basa ganin irinmu talakawa da mutunci, yana ganin kamar ƙasƙanci ne a gareshi yazo neman yafiyarkin kai tsaye, bana tantama shi ne ya aiko mana da ɓarayin nan kuma ya siye gidan nan saboda ki matsu ki koma aikin a kamfanin kamar yadda yake buƙuta ta yadda zai iya kyautata miki har ya nemi yafiyarki cikin sauƙi, da ace cutar da ke yake son yi da wata hanyar zai ɗauko ba wannan ba, kuma kin ga idan har yana da wata niyar ta daban akanki babu yadda za'ayi ya ki mareshi a bayanar jama'a ya ƙyaleki har ma ya risina ƙasa yana baki haƙuri, wannan saboda yana ganin bashi wata mafita sai ita ne shiyasa ya ɓullo miki ta hanyar Bilal”
“Amman ina tunanin be san da Noor ba ko?”
Sakina ta tambaya. Sai Inna ta amsa ta
“Ya san ya barki da ciki, sai dai be sani ba ɗan yana raye ko baya raye, wata ƙila ma yasa an masa bincike akan haka, amman ki yi tunani Nawwara dukan mutumen da ya yi miki wannan wulaƙanci yana kunyar ya tunkareki kai tsaye ya nemi yafiyarki, kuma ta hanyar aikin nan da zaki yi a ƙarƙashinsa zaki iya fahimtar irin rayuwar da ɗan ki zai yi idan har ya zauna gunsa, ke da shi duka ƙurciya da wauta tana cinku”
Shiru na yi ina ta nazarin maganganun Inna akwai hiƙima da kuma ƙamshin gaskiya a duk abunda ya faɗa, ni kaina na san da Jibril be yi nadama ban iya na masa irin wannan cin kashin a gaban ma'aikatansa ba, kuma babu dalilin da zai ya riƙa bibiyata har yana neman na dawo aiki.
Ajiyar zuciya na sauke nasa hannu ina share hawayena, Inna kuma tana amsa sallamar da almajiri yake yi.
“Assalamu alaikum wai ance ana sallama da Nawwara a waje”
Da fari gabana ya faɗi na fara tunanin mai min sallamar.
“Waye ne?”
Na tambaya a cikin muryata mai amon kuka a cikinta.
“Haka ya ce wai bawon Allah ne”
Zan ƙara tambayarsa sai ga Noor ya shigo da gudu ya miƙa min wayar.
“Momy ga Uncle Bilal ya ce na baki”
Ina karɓa na kara a kunne already Noor ya yi picking.
“Nawancy gani nan akan hanya”
“Ka ce ma ka iso”
Sai kawai ya yi dariya ya kashe wayar, jin haka yasa na ce da almajirin ya ce ina zuwa, wayar na miƙawa Noor ni kuma na tashi na je waje na wanke fuskata na shigo na shafa mai sannan na saka Hijabi na fita.
Mustapha na tarar ƙofar gida sanye da jallabiya yana kallon ƙofar gidan, waigawa na yi gabas na duba yamma ban ga mai kirana ba hakan ya tabbatar min da cewar shi ne yaƙe kirana.
“Miya kawo ka nan kuma? Kamin nan dai bari na fara taya ka murna ka yi nasarar haɗa ni da ƙawata ta faɗa min har abunda ban zaci zata iya faɗa min ba, burinka ya cika”
“Ba burina kenan ba, burina ki yarda na tuba kuma ki yafe min”
“Akwai aiki a gabanka babba Mustapha, yafiyar Ubangiji ta fi cancanta ka nema ba tawa ba”
Sai ya kirana sunana a hankali.
“Nawwara idan na kai kaina kotu aka min hukunci zaki tafe min?”
“Allah ya rufa maka asiri karka tonawa kanka”
“Ina ma ace zan iya raba zuciyata biyu ki karanta ki ga abunda yake raina”
“Kasan zaka nemi yafiya ka aikata?”
“Ƙaddarata ce ta zo a haka, an rubutoni a cikin ƙaddarar Habiba kamar yadda aka rubutoki a cikin ƙaddararta, Wallahi da nasan Allah zai jarrabe ni da sonki da ban yarda ba kalli Habiba balle har wani abu ya shiga tsakanina da ita”
Ya faɗa yana ƙwalla, har na buɗe baki na sake masa wata maganar sai na hango Bilal tafe, sai na tattarahankalina na maida gurinsa gudun kar ya zargi wani abu, hakan yasa Mustapha waigaya ya kalleshi.
Tsayawa Bilal ya yi cak sai kawai ya ɗago min hannu daga can inda yake ya juya ya koma.
“Ka gani ko? Ka hana masoyi ya ƙaraso kusa da ni”
Na faɗa a tsawace.
“Yi haƙuri”
Sai ya yi saurin juyawa ya bar gurin cikin sauri, na daɗe tsaye bakin ƙofar wai ko zan hango Bilal ya dawo amman har na gaji ban dawo ba hakan yasa na juya na koma cikin gida raina a jagule.
Assalamu alaikum habibaties. Ina nan lfy kalau sai dai phone dina ce ta ci screen amman yanzu an gyara, Alhamdulillah.
A cigaba da gashi...
*RAI BIYU...♥️🖤*
Wattpad @Khadeeja_Candy
*Dedicated to My Asmee*
3⃣8⃣
MUSTAPHA POV.
Be taɓa tattabar da cewa yana son Nawwara ba sai yanzu, wani irin abun yake jin yana dibarsa masar misaltuwa, kalamar da ta furta ga waninsa na masoyin da ta kira Bilal yake jin kamar ace shi ne.
Kai tsaye ya wuce part ɗinsa sai ya kwanta rairai ƙasan carpet ya lumshe idonsa, babu abunda yake tunani sai halin rayuwar da ya jefa kansa, da ace be kasance mazina ci ba da babu abunda zai hana Nawwara ta so shi, tunani yake abunda zai faɗawa Allah idan har ya mutu a yau ba tare da ya tuba, son nawwara yasan jarabawace Allah ya ɗoro masa gashi tana da ɗawainiya da shi ta hanashi sukuniina ga ya mutu? Tabbas zai yi ƙoƙarin juye rashin Nawwara amman azabar Allah fa zai iya jureta? Wacan azabar da za'ayi ma mazinata ba da irin wannan jarabawar ba ce da wuta mai kamar kunu za a ƙona fatarsa bayan azabar da za a gada masa cikin ƙabari.
Buɗe ido ya yi sai ya ɗaga hannunsa sama yana kallon farar fatar hannunsa, sai ga hawaye sun gangaro daga idanuwa zuwa gefen kuncinsa, unƙurawa ya yi da zimmar tashi zuwa